🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 Bismillahir rahmanir raheem.... 01 FREEDOM COLLEGE OF NURSING AND MIDWIFERY(FCNM) KANO... Dogon building ne mai matukar kyau da tsaruwa...sannan yanada girman da baka isa kace ga iya inda ya tsaya ba...daga ciki akwai makeken surrounding mai daukeda shukoki iri daban daban da sukayi matukar qawata wajen...ga wani tafkeken titi da ban samu ganin iya inda ya tsaya ba a shimfide hadda roundabout kamar dai normal hanya...kallo daya zakayima makarantan kasan bana 'ya'yan kananun masu kudi bane domin tun daga yanayin gini da yanda akayi tsarinta ko university albarka...a takaice dai kallo daya zakayima FCNM kasan makaranta ne daya amsa sunanshi makaranta...kuma makaranta ne da duk wanda ka gani a ciki zakasan iyayenshi manya manyan attajirai ne...ko ina yayi tsit sai few students dake kaiwa da kawowa kasancewan duk students suna classes dinsu sai securities da masu gadi da kowa ke various post dinshi...ana wangale gate wata Hadaddiyar Range Rover ta shigo ciki baqa wulik daidai da glasses dinta baqin tint ne a jiki hakan yasa baa iya ganin wanda yake ciki...ta karasa parking lot da aka rabashi biyu tareda indicating staff and students parking area...kai tsaye staff parking area motan ta nufa tayi parking cikin wani babban car park da yafi duk sauran na wurin girma...securities da some of staff da sukaga shigowan motan sukayo inda tayi parking da sauri kamar yanda suka saba duk proprietor yazo har rige rigen zuwa tarbanshi sukeyi snn su take bayanshi har zuwa office dinshi...driver na gama parking ya bude ya fito saidai kafin ya zagaya ya bude motan wadan nan mutanen sun rigashi nan take mutumin dake cikin motan ya bayyana...legs dinshi yafara saukowa waje kafin shima ya fito a hankali yana kallon mutanen...matashi ne da ak'alla bazai wuce 31 to 32 years ba...dogo ne sosae don cikin maza goma da kyar zaa samu guda daya wanda tsayinsu zaizo daidai dashi duk da cewa yanada dan jiki kai tsaye bazaa kirashi da siriri ko kuma mai qiba ba...komai tsawon namiji duk ya jera dashi sai yaga ya zama gajere kusa dashi...sannan yanada wani irin haske mai daukan ido wanda kallo daya zaka mishi ka gane ba full blood bahaushe bane...ko hannunshi ya daga zakaga tarr sbd tsabar farinshi...sanye yake cikin three piece suit dark blue dayayi matching da jikinshi sosae...tun daga gashin kanshi har zuwa sajenshi sun kwanta luf gashi sai shinning suke as a result of gyara da sukesha...yanada round face mai daukeda dogon hanci da matsakaicin baki...sai eyes dinshi da duk ya ware maka su a kanka saika tsorata sbd tsabar girmansu and su kansu eyeballs dinshi abun kallo ne..fararene tas sai wajen bakin kuma nashi ya kasance golden brown...sune irin idanun dake ladabtar da mutum komai rashin mutuncinshi...sune kuma irin idanun da suke sanya mata kware mishi domin kallo daya zakayi musu ka gane ba kowane irin ordinary eyes bane...they are kind of special kaman yanda mamallakinsu shima ya kasance special...hannu yaketa faman mikawa staff din nashi suna gaisawa domin bai son durkuson da suke mai sam...yafi gane suyi musabiha kmr yanda addinin musulunci ya tanadar...bayan sun gama gaisawa suka shiga binshi a baya har zuwa office dinshi as always driver na rikeda brief case dinshi...secretary na ganinsu ta mike da sauri ta bude office din suka shiga...bayan ya zauna ya dauko kudi ya basu suka fita suna zabga mishi godia as always...Obi driver ya ajiye mishi briefcase shima ya fita...Ngozi(his secretary) ta shigo itama ta gaisheshi snn ta mika mashi schedule dinshi tareda wasu files kmr yanda ta saba...bayan ya karba tasake mika mashi wani envelope tana fadin"Sir you have a message from Kinana Hospital"...baice komai ba ya sake karban envelope din ya ajiye...ganin har yanxu tana tsaye yace"is there anything else?.."da sauri tace"Ss..Sir its Doctor Bukar...he said.."bata karasa baya katseta da fadin"hold it... how many times do i have to tell i dont want to hear about him?.."kai a kasa tace"Sorry Sir"...yace"this should be your very last warning...if you dare repeat this mistake again you are fired"...jikinta har ya fara rawa tace"am very sorry sir... i will never do that again"...ba tareda ya sake kallonta ba yace"you can go"...yana rufe baki ta juya ta fita daga office din...shi kuma ya dauki files data shigo dasu ya fara dubawa...yayi signing inda ake bukatan signing dinshi snn ya shiga duba schedules din...ba wasu schedules bane masu yawa kawai staff meeting zasu fara 9 zuwa 10:30...by 11 zai shiga Area Hostel ya duba construction na new apartments da ake a both male and Female hostel sai kuma ya shiga College Clinic by 2...tsaki yaja yana ajiye file din shi bai cika son shiga college clinic ba shiyasa yayi employing Dr Bukar sbd ana samun cases din da sukafi karfin nurses...dukda iya students ake dubawa ciki shidai bai cika son shiga ba sam...yanxu gashi dole saiya shiga tunda Dr Bukar din was fired...ya jingina da kujera yana shafa lallausan gashin kanshi...ya zama dole ya sake employing wani Dr dan bazai iya hada duk aiyukanshi da shiga college clinic ba tunda ba ko yaushe yake shigowa college din ba sai Thursdays da Fridays...sauran ranakun yana hospital dinshi mai suna FREEDOM SPECIALIST HOSPITAL... duba agogon hannunshi yayi yaga yanada sauran time kafin 9 dan haka ya janyo computer dinshi ya fara aiki a ciki...sai yanxu na samu daman karema office din nashi kallo and i was like"Wow wow wow"...my people its one huge office you know...tunda nake ban taba ganin office mai kyau da tsaruwanshi ba...daidai da funitures dake cikin office din abun kallo ne hadda su dinning ko office din governor sai haka lol😂...a jikin wall din office din wani katon picture dinshi ne yana sanye da white suit daya matukar yi mishi kyau sosai...ya sunkuyar da kanshi yana rubutu aka dauki picture din da gani bai san an dauka ba amma fadan kyawun da yayi is a waste of saliva...a kasan pic din an rubuta Dr.BOBBY ATTAHIR WAZIRI...sai kuma in bracket aka rubuta CEO FREEDOM GROUP OF SCHOOLS AND HOSPITALS...Landline dake ajiye kan table dinshi ne ya fara ringing...yana dauka secretary dinshi tace"The Provost wants to see you sir"...a takaice yace da ita"ohk"snn ya ajiye wayar...ko two minutes baayi ba wani matashi ya turo kofa ya shigo...yana sanye cikin white shirt long sleeve da black trouser yayi tuck in shirt din...dogo ne shima mai haske saidai kallo daya zakayi mishi ka gane ba bahaushe bane...ya karasa ciki ya zauna yana kallonshi with a smile yace"the Proprietor Sir"...dan dagowa yayi ya watsa mashi wani kallo snn yacigaba da abinda yake...daya guy din ya bata rai yana cewa"nidai ka dena hararana da wnn big golden eyes din naka pls...haka nan kasa na fara having nightmares"...dena operating computer yayi yajuya yana facing dinshi sosae...cikin husky voice dinshi yace"Nuruddeen"...da sauri ya amsa da"yes Bobby"...yace"just go straight to the point nasan tunda kazo office dina akwai abunda ya kawoka...say what you want to say"...kmr jira yake kuwa ya gyara zamanshi before yace"its about Dr Bukar..dont you think he deserve a second chance?.."tsaki Bobby yaja tareda fadin"i don't want to talk about him"...da sauri Nuru yace"but you have to Bobby...give him a second chance...we are all bound to make mistakes so forgive him tunda har yayi nadama...please!"...girgiza kai Bobby yake voice dinshi na nuna tsantsan bacin ran da yake ciki yace"i will never forgive that bastard..never"..dafe goshi Nuru yayi ya rasa ta yanda zai bullo mishi...can yace"Bobby me kakeyi ne haka?...this is unlike you?.."yana rufe baki yace"bazan taba yafema wnn mutumin ba...i trusted him amma yaci amanata...this is the problem with Hausa Fulani people...kwata kwata basu san alkhairi ba snn basu da imani basuda rikon ama.."Nuru bai bari ya karasa ba yace"enough please!...zaka fara kou?...you are always looking for a way to insult Hausawa ko Fulani sai kace kai ba bahaushen bane"...da karfi Bobby ya buga table dake gabanshi cikin karaji yace"stop calling me bahaushe niba bahaushe bane...infact babu abinda ya hadani da hausawa so mind your tongue"...murmushi sosai Nuru ya saki yana kallon yanda yake ihu sai kace cewa yayi shiba musulmi bane...har kullum baya dena mamakin kalar kiyayyan da Bobby kema Hausa Fulani...ya tsanesu to the core shiyasa ko cikin staff da securities dinshi yawanci ba hausawa bane infact a duk Company dinshi da kyar zaa samu hausawa goma da suke aiki...ko a wurin aiki baison hada hanya da hausa fulani ya rasa gane kan wnn kiyayya...and the funny part of abun is shi kanshi Bobbyn jinin hausa fulani ne...his father was Fulani from Gombe state and his Mother Igbo from Enugu state shiyasa always yake considering kanshi as igbo sbd Mom dinshi is one...wnn dalilin yasa ko cikakken hausa bai iyaba sbd bayi yakeba idan yana mgn da hausa zakaji kaman he is learning cox yanda yake pronouncing words din kadai zaisa ka fahimci ya hada jini da qabilu and a gidansu ma kuma sunfi magana da english ko igbo din at times ko da hausa akayi mashi mgn sai ya amsawa mutum da English ko igbo...yasan idan yaci gaba da jan mgnr ransu ne zaizo yana 6aci dan haka ya mike hands dinshi a aljihu yace"See you at the meeting"snn ya fita daga office din...Bobby ya bishi da kallo cikeda takaici...wlh ba don alaqar dake tsakaninshi da Nuru ba yau saiya ci mutuncinshi for calling him bahaushe...he hates everything that has to do with hausa fulani...he hates them with passion...Nuruddeen abokinshi ne tun a University...tare sukayi karatu a America saidai shi Bobby yayi specializing ta bangarori da dama shi kuma Nuru baiyi ba...Dr.Nuruddeen Ugochuku Dominic shine cikakken sunanshi and he is also a muslim igbo from imo state zama ya kawoshi kano har ya hadu da Bobby a America...bayan sun kammala karatu sun dawo yayi mishi provost din FCNM sbd abotan dake tsakaninsu...shima kuma ya rike mishi amana dan tsahon shekaru basu taba samun matsala ba. 10:30 sharp suka fito daga meeting...direct Bobby office dinshi ya koma har yanxun ranshi bai dena baci kan abunda Nuru yayi mishi ba...yana shiga ya wuce ya hadama kanshi coffee snn ya zauna kan one of luxury sofas dake cikin office din yana sipping coffee din a hankali yana sauke numfashi...dama duk yake cikin bacin rai baida abun sha daya wuce coffee shiyasa ko a gida yanada coffee machine a flat dinshi duk yaji yana son sha hadawa kawai zaiyi...saida ya shanye coffeen yana kokarin komawa seat dinshi wayanshi dake aljihunshi ya fara ringing... yana daukowa yaga My Mummy rubuce kan screen with all sort of heart emojis...murmushi kyakykyawa ya saki kafin yayi picking call din wanda har hakan ya bani mamaki sbd yanda naga lokaci daya duk wann sadness dake kan face dinshi ya bace...hakan alama ne na tsanstan kaunar dake tsakaninshi da Mom dinshi...yana dauka cikin igbo yace mata"Mummy nah"...itama da igbo din tace"Bobby nah"...yana sake sakin smile yace"Mummy how are you?.."tace"ina lafia Bobby..yanxun wani employee dinka yazo ya sameni"...shiru yayi yana tunanin waye?..lokaci daya kuma zuciyarshi tace mishi Dr Bukar ne...jin baiyi mgn Mummy tace"are you there?.."yace"yes am listening Mummy"...tacigaba da fadin"he said his name is Dr Bukar...he told me all that happened between you two kuma ya fadamin yayi nadama dan haka ina ganin you should get him back to his job inshaAllah bazai sake faruwa ba"...Bobby yayi shiru yana sauraronta kmr ruwa ya cinyeshi...yasan wnn duk plan din Nur ne...shine nan zai tura Dr Bukar wurin Mummy sbd yasan bazai taba iya tsallake umarninta ba...wani bacin rai yaji yazo mishi amma bazai iya nunawa Mummy ba kmr yanda bazai iya tsallake umarninta ba...tunda yake Mummy bata taba sashi yin abu yakiyi ba and bazai so ya fara yanxun ba especially not because of that bastard dan haka yayi lowering voice dinshi sosai yanda bazata gane he's angry ba yace mata"it's ohk Mummy inshaAllah zan maidoshi...i will talk to Nur sai ya kirashi ya fada mishi"...yana iya jiyo farin cikin da Mummy ta shiga kafin tace"nagode sosai Bobby Allah ya maka albarka...Allah kuma ya baka kids da zasu maka biyayya kmr yanda kakemin"...murmushi kawai yayi without saying anything... itama bata damu da cewarshi ba don tasan dama bazaice din ba tunda duk tayi mishi zancen aure ko yara haka yake behaving...kwata kwata ta kasa gane kan Bobby akan wnn alamari...tace"you send Obi by 1 yazo ya daukan muka abinci"...saida ya wani marairaice muryanshi yace"Mummy yau ba sai an kawo ba pls...am not hungry"..tun kafin ya karasa Mummy tace"No i insist..yanxun zan barka kacigaba da aikinka and make sure you take care of yourself"...yana wani lumshe eyes dinshi yace"i will Mummy..bye"...itama tace mishi"bye"..snn sukayi sallama...mikewa yayi a fusace ya fice daga office din zuwa office din provost wato Nur...secretary dinshi na ganinshi ta mike sauri tana wani sandarewa kaman taga soldier tace"good day sir"...ko kulata baiyi ba ya banka cikin office din...Nur na zaune da wata lecturer a gabanshi tana mishi bayanin wasu abubuwa kawai sukaga mutumi a gabansu...baidai ce komai ba sai huci da yake like an angry lion...Nur na ganin haka yasan sunyi mgn da Mummy dan haka ya mikama malamar file dinta yace"am sorry miss Fatima kije zuwa gobe ki dawo mu karasa"...ba musu ta mike da sauri ta fita daga office din dan Allah ya gani tsoron Bobby takeji...bama ita kadai ba almost all of his staff tsoronshi sukeji sbd yanda face dinshi kullum a daure kuma mistake karami sai yaceya kori mutum...saida yaga ta fita snn ya juyo yana kallon Nuru da angry eyes dinshi yace"why did you do that?.."Nuru ya koma seat dinshi ya zauna yana daga shoulders dinshi yace"because i have no choice"...a fusace Bobby ya sake fadin"but how dare you...who gave you that right...haka nan sai ka ringa tura kowane jick and jerk yana mgn da mahaifiyata...are you sick or something?.."dagowa Nur yayi ganin yanda yake ihu kawai sai yasa daria...Bobby ya sake kulewa dashi yaji kaman ya watsa mashi mari..."so i have become a mad person right?.."da sauri yace"No..kawai wnn hakilon da kake yake bani daria...kan dan karamin abu kaman wnn kake bacin rai haka...haba mana...you need to stop this pls"..wani malolo Bobby ya sakeji yazo ya tokareshi...bai sake yunkurin cewa komai ba kawai ya juya ya fita daga office din...kai tsaye nashi office din ya koma yana cizon dan yatsa...agogon office din ne ya buga 11 dan haka ya sake ficewa zuwa inda motarshi yake...Mr.Obi na ganinshi yazo ya bude mishi motar ya shiga snn shima ya shiga suka nufi hanyar hostel...ta mirror ya hango motar Nur na binsu a baya don tare dashi zasu shiga hostel din...shi kanshi hostel din tafiya ce mai dan nisa tsakaninshi da inda classes dinsu suke...a fisrt gate suka fara tsayawa inda Male Hostel yake suka shiga suka duba aiyukan snn suka wuce next gate inda anan Female Hostel yake...basuyi wasting time ba nan ma suna gamawa kowa ya shiga office dinshi suka koma cikin school...har yanzun Bobby bai denajin haushin abunda Nur yayi mishi ba domin baiyi niyyar dawoda Dr Bukar ba sam dukda dama can sbd Nur din ya daukeshi aiki amma da bazai dauki bahaushe ya ajiye clinic dinshi ba...kowa office dinshi ya wuce.. Basu sake fitowa ba sai lokacin sallah...da yake staff masjid daban yake dan haka Nuru baiyi wahalar hango abokin nashi ba...yana kokarin zuwa ya sameshi kawai yaga ya mike ya fita shi kuma sai ya saki daria yana girgiza kai...yasan halin kayanshi tsaf duk wnn fushin babu inda zaije dole haka zaiyi hakuri ya barshi ko bayaso...shi kuwa Bobby ko office bai komaba ya nufi Clinic dake ta bayan office dinshi...Clinical instructor na ganisnhi ya mike tareda gaisheshi.. Bobby ya amsa a takaice snn ya bukaci sanin if there is any complicated case ko kuma emergency da yake bukatan doctor's attention... da sauri Mutumin da ya dauko wani file guda daya ya fara mishi bayanin patient din da yanayin ciwon nashi kawai sukaji wani hadadden kara daga cikin Clinic din...Bobby ya kalli mutumin yana kokarin yin mgn ya sakejin wani karan this time around hadda magana amma bai gane me ake cewa ba...ranshi ne yaji ya sake baci ya kalli mutumin tareda ware masa idanuwansa yace"what the hell is happening here?..where is this sound coming from?.."da sauri mutumin yace"pls sorry sir...i think its.."Bobby bai bari ya karasa ba ya juya ya kama hanyan ciki inda yake jiyo sound din da sauri mutumin ya bishi a baya...so yake ya mishi bayanin ba wani serious abu bane amma he won't dare sbd yanda yaga ranshi ke baci ba abunda bazai iya aikatawa ba...suna kara kusantowa karan da sukeji na kara karfi...saida sukazo daidai injection room snn ya tsaya...yana tura kofan daidai lokacin ta sake sakin wani karan tana fadin"aunty Meena dan Allah Nooo...wlh idan kika bani magani zansha amma banason injection pls pls plssss"...wani kullutun bakin ciki yaji ya sake tokare mai makoshi...yanxu dama duk wnn ihun akan common allura akeyinshi?..a fusace ya tura kofa ya shiga ciki aikuwa gaba daya mutanen dake ciki suka juyo suna kallonshi...shima kallonsu yakeyi daya bayan daya fuskanshi daure yanda kasan bai taba daria ba...Nurse Meena ce tsaye rikeda injection da swab a hannunta sai kuma wata student sanye da uniform dinta farare sol da ratsin pink a hannun riga alaman midwifery take karanta knn...dayar kuma tana tsaye ta kankame wadda ke sanyeda uniform din jikinta har shivering yakeyi sbd tsabar tsoro...dogon hijab ne a jikinta daya haura guiwarta da kadan sai skinny trouser dake jikinta red...almost rabin gashin kanta is out sbd batasa dankwali ba kuma hijab dinta ya dan zame kadan...gaba dayansu ba wanda hantar cikinshi bai duri ruwaba sbd wanda suka gani tsaye a wurin...da sauri Meena ta risina tana fadin"good afternoon sir"...ba tareda ya saki face dinshi ba yace"afternoon... what's going on here?.."da sauri Meena tayi pointing yarinyar dake sanye da hijab tace"Sir batada lafia ne shine doctor yace a bata wnn injection din to ita kuma batason injection shine take kuka"...wani haushi Bobby ya sakeji ya juya yana kallon yarinyar da idanunta ke runtse sai sauke ajiyar zuciya take...murya a kausashe ya kalli wadda take rikeda ita yace"let go of her right now"...da sauri ta matsa daka jikinta tana sunkuyar da kai gabanta nata aikin faduwa...itadai ko Allah yasan bakaramin tsoron Proprietor dinsu takeba...shi kuma ya tsayar da idonshi kan yarinyar da har yanxu bata bude idanu ba dukda cewa tasan shine a wurin kuma jikinta bai bar shaking ba sbd tsabar tsorata da tayi..duk iskancinta tana tsoronshi sbd tasan bashida mutunci ko kadan...saida ya sake daure face dinshi snn yace"C'mon open those eyes before i slap you"..da sauri ta bude idanun nata ta dora a kanshi..sai kuma tayi kasa dasu da sauri sakamakon kadawar da hantar cikinta yayi...ya mikama Nurse hannu ba musu ta mika mashi injection din snn ta sake dauko another swab da hand glove shima ta mika mashi...yana karba ya ware idanunshi masu ladabtar da fitinannu a kanta murya cunkushe yace"come over here"...tana dago kanta taga injection a hannunshi sai ta fara yarfa hannu tana fadin"dan girman Allah Sir..."bata samu courage din karasawa ba sbd idanunshi da suka ladabtar da ita...ta juya tana kallon friend dinta data rakota clinic din wai ko zata taimaka mata amma sai taga kanta a kasa...ta kalli nurse da clinical instructor suma duk taga alaman a tsorace suke sai ta shafama kanta salama ta shiga takawa a hankali sbd ciwo da kafanta ke mata har zuwa inda yake...hawayen dake zuba a idonta kuwa ko pump albarka...Bobby na tsaye da injection a hannu yasa glove a both hands dinshi har saida ta karaso snn ya sake murtukewa yace"turn your back"..batayi musu ba ta juya bayanta jikinta nata rawa...kallo daya yayiwa Meena ta gane me yake nufi dan haka ta karaso inda suke tareda kama hijab din jikinta ta daga bayan tayi covering dinsu da screen...ta sauke wandon jikinta a hankali nan take fair bombom dinta ya bayyana iya daidai inda zaayi injection din...Bobby ya dauke kanshi gefe tareda dan risinawa ya zura injection din a jikinta aikuwa ta saki wani irin ihu tana kokarin kwace kanta Meena tayi mata kyakyawan rikon da bazata iya kwacewa ba...saida ya gama injection din snn yayi disposing syringe a safety box ya cire glove dake hannunshi itama yayi disposing snn ya juya ya fita daga injection room din clinical instructor ya bi bayanshi...ita kuwa wadda akaiwa injection sai yanxun ta samu daman saki kukanta...tana kokarin dukushewa a wurin friend dinta tai saurin kamata suka zauna kan bed tanata kokarin mulmula mata wurin amma sai kaucewa take wai bataso a taba...zaunawa tayi kusada ita saida ta gama gursheken kukanta snn ta kamata suka fito daga dakin tana takawa da kyar sbd rikewan da kafan nata ya sakeyi...every month haka take fama duk zatayi period sai yasa mata ciwon kafa ko ciwon baya haka za'ayita tata6urza da ita kan allura sai kace small baby...har sukazo wucewa ta bayan office din Bobby bata dena kuka ba...saida suka fita ta samu daya daga cemet shairs dake wajen admin block ta zaunar da ita akai snn tayi dialing number da tayi saving da Lamido's Bestie a wayarta...tana fara ringing ya dauka yana fadin"are you done?.."a hankali tace"yes muna ta wajen admin and kayi sauri kazo dan ta isheni da kuka"bata jira ko zaice wani abu ba ta kashe wayarta...ba bata lokaci kuwa sai gashi yazo inda suke...saurayi ne da akalla zaikai 25 years..baqi ne dogo kuma kyakyawa dashi yana sanye cikin uniform dinshi complete white yayi tuck in shirt dinshi...da sauri ya zauna kusa dasu yana duban mai sanyeda uniform yace"Billy kin tabbata ta samu sauki kuwa?..duba fa yanda take kuka?.."harara me kyau Billy ta watsa mishi tace"kajika da wani magana sai kace bakasan halin bestyn naka ba...allura fa akayi mata shine take wnn abun kamar an yankata"...bata rufe baki ba wadda akama alluran ta dago tana dubanta fuska shabe shabe da hawaye tace"ni wlh gara a yankani akan dai ayimin allura...sbd tsabar mugunta inata ce miki kizo mu gudu amma kika ki har saida wnn azzalumin yazo"..rai a bace Billy ta mike tana kokarin barin wurin tace"ba laifinki bane Lamido laifina ne da nake damun kaina a kanki...next time dama kina fara rashin lafiyarki saidai bestyn naki yazo ya kawoki Clinic amma bani Bilkisu ba...kuma wlh saina kira Ammi na bata labarin duk iskancin da kikayi"...tana gama fadin haka tayi wucewarta ta barsu a wurin...Lamido ta sake fashewa da matsanancin kuka shi kuma bestyn nata ya danyi kasa da murya yace"besty dont mind Billy kinji..yanxu ki daure ki tashi in maidaki hostel sai ki samu ki huta sosai"...yana rufe baki ta hau girgiza tana hawaye tace"i dont think i can walk besty..gaba daya leges dina sun sake rikewa"..ya sake fadin"daurewa zakiyi besty just try it zaki iya"...ba musu ta dafa kujeran da take zaune tareda mikewa da kyar...shima mikewan yayi ya nufi inda motarshi yake ya bude snn ya dawo ya taimaka mata suka karasa wurin..tana shiga shima ya zaga ya shiga snn tayar da ita suka nufi gate din hostel. Alhamdulillah Allah ya sake dawo dani habibties with another unique and interesting love story💞💞saidai this time around tafiyan nada bambanci dana baya domin kuwa Dr.BOBBY na kudi ne...masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank sai a tura evidence of payment through 07063800556. Ina mika dumbin godia ga all of you out there Allah ya biyama kowa bukatunshi na alkhairi💞 Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 02 A bangaren Bobby yana komawa office yayi sanitizing hands dinshi with a hand sanitizer snn ya fada kan sofa ya zauna yana jin haushin abunda ya faru...gaba daya bacin ranshi sai ya karu fiyeda wanda yake ciki already...tunda yake bai ta6a ganin sangartacciyar yarinya kamn wnn yarinyar ba...allura kawai takema wnn abun...kawai yau ta sashi yin abunda ya manta yaushe rabonshi dayi koda a gidane kuwa..ya manta when last yayima wani injection ko yan gidansu akwai Nurse dake musu injection shi Mummy kadai yake yiwa amma yau wnn spoiled brat din saida ta tilastashi yayi mata...yana zaune lokacin da sukazo wucewa yaji wani gursheken kuka da takeyi kamar wadda akama operation...haka nan yaji kaman ya dauki bindiga ya harbeta har saita dena wnn kukan...For Gods sake injection kadai take yima wnn ta6aran?..wnn wace irin lalatacciyar yarinya ce?..wai meyasa wasu iyayen if sunga sunada kudi sai suyita spoiling yaransu haka?..meyasa yaran masu kudi yawancinsu sangartattu ne?...koda yake ba duka masu kudi suka taru suka zama daya ba dan shidai yasan a gidansu ko Miemie ce tayi wnn iskancin ba abunda zai hanashi lakada mata dan iskan duka...sai faman sakin tsaki yake feeling extraordinary hot inside...yana cikin shan coffee Mr.Obi ya shigo da abinci daga gida...ya karaso ya ajiye kan table snn ya mishi sallama ya fita...shi kuma Bobby ya maida kanshi ya lafe jikin kujera tareda lumshe ido...kaman daga sama yaji voice din Nur akanshi...bai bude idon ba sai cewa yayi"waya baka izinin shigowa office dina?.."Nur ya dauki basket din abinci ya nufi dinning dashi kafin yace"har saina wani jira an bani izini?..ko dazu ma kawai nace bari in dana ne?.."bai sake cewa komai ba saida ya mike ya isa dinning din ya zauna snn yace"why are you doing this?..meyasa zaka tura mutumin nan wajen Mummy?.."a nuste Nur yace"because you are not willing to listen to me...kai kanka kasan da kayi abunda nakeso tun farko bazai kaimu ga hakaba...kuma mutumin nan yanada kirki Bobby kaddarane kawai ya fada mishi snn yanada iyali kuma duk ta karkashinka suke samun abinci yanxu kanaso kayi musu cutting hanyar samun abincinsu sbd small mistake daya aikata?.."a hankali Bobby ya sauke ajiyar zuciya before yace"amma daga small mistakes ake zuwa har manyan mistakes ka sani...kan wane dalili zaka turashi wurin Mummy"Nur yace"nayi maka alkawari inshaAllah bazai sake ba...to be honest banajin dadin yanda kake kasa hakuri da workers dinka...sbd suna aiki a karkashinka ba yana nufin su slaves dinka bane...suma mutane ne kamar kowa and suna bukatan a ringa yi musu uzuri akan wasu abubuwan...banajin dadin wasu maganganun da suke fada a kanka shiyasa nakeso ka gyara"...tunda ya fara mgn Bobby yayi shiru yana sauraronshi yasan gaskia yake fada mishi yana kuma jin dadin yanda abokin nashi ke zaune dashi tsakani da Allah shiyasa komai dacin gaskia yake fada mishi ita...ganin yayi shiru yana tunani Nur dake kokarin kai loma baki yace"so yau azumi kakeyi knn?.."baice mishi komai ba yayi serving abincin shima ya shigaci a hankali...suna cikin cin abincin yace mishi"kasan me na gani a clinic yau?.."a hankali Nur ya girgiza kai alaman aah...saida ya sake sakin wani tsaki cikeda takaici yace"a spoiled brat..wata yarinya ce mai shegen shagwa6an tsiya...can u imagine yarinyan dake high institution ta tsaya tana kukan injection?.. wlh if u see how she was crying zakayi tunanin surgery akai mata..she was crying out loud kaman mara hankali..gaba daya ta karasa spoiling mood dina for the rest of the day..i feel like strangling her"...saida ya gama Nur ya shiga murmushi gamida girgiza kanshi yace"i think it was Lamido"..da sauri Bobby ya kalleshi yace"how do you know that?..besides mace kaji nace maka ba namiji ba.."Nur ya saki wani murmushi yana sake kai loma bakinshi yace"ai bama ni ba kaf FCNM bana tunanin akwai wanda baisan who is Lamido ba...jikar Lamidon Gombe ce...and duk college din nan Ita kadai na san tanama allura wnn kukan...she is allergic to injections"...Bobby na tabe bakinshi yace"ba wani allergy tsabar iskanci ne kawai da kuma sangarta"..Nur na girgiza kai yace"bazaka gane bane Bob...tunda nake ban taba ganin mace kaman yarinyar nan ba...she is so different from other girls...komai nata special komai nata unique...kaga na farko she is beautiful kai she is more than beauty itself... Snn she is intelligent...wlh ban taba ganin yarinya mai brain dinta ba..she is a genius tunda ta shigo makarantan nan take overalling kaf department dinsu...gata very young snn gata da goog heart...gata kum..."bai kai ga karaswa ba Bobby ya katseshi da fadin"malam hold it plss...this one you are saying as if you are taking about your girlfriend"..da sauri Nur yace"she really is an angel Bob you will never understand"..still bai bari ya karasa ba yace"naji enough talking about her now and ka sake cemin Bob you'll see the other side of me"...sake kai loma Nur yayi yana murmushi yace"wnn other side of you din ai koda yaushe cikin ganinshi nake..har devil side of you ma duk na gani so am not afraid"tsaki kawai Bobby ya saki baice mishi komai ba duk ya sake spoiling mood dinshi...suna gama cin abincin ya kira Mr.Obi yazo ya tafi da ragowar...sai a lokacin Bobby ya samu damar ce mishi ya kira Dr.Bukar yace mishi ya dawo bakin aikinshi..Nur yasaki kyakyawan smile kafin yace"i've already done that ai..tunda mgn yaje wurin Mummy nasan dole zai dawo ai"...harara Bobby ya maka mashi yace"wato u did it on purpose koh?.."Ugo ya daga shoulder dinshi tareda fadin"yes". Karfe 4 ya fara shirin barin College bayan ya dawo daga masjid...kafin ya fita office wayanshi ya fara ringing yana dubawa yaga Sister akan screen...baiyi wasting time ba ya dauka yana cewa"Aunty Sumy how far"...daga daya bangaren sis dinshi tace"Bobby kanajina?...wata qawata ce ta kirani wai yarinyanta ba lafia sun kaita hospital dinka shine tace i should please ask u kaje ka duba musu ita plss"...saida ya gama sauraran abunda ta fada snn yace"but Aunty Sumy akwai many doctors a hospital din fa?..kinsan ni yau ba ranan shiga hospital bane yanxu haka ina cikin college"...Aunty Sumy ta sake yin kasa da murya tace"haba dan qanina...kirana fa tayi sbd tasan na isa insaka kaje...yanxu kawai sai in kirata incemata kace bakaza samu daman zuwa ba...kana ganin ya dace hakan?..kanaso ka nuna mata ban isa da qanina ba knn?.."dan daure face yayi yana turo baki yace"Aunty Sumy are you emotionally blackmailing me now?..this is not fair"..da sauri Aunty Sumy tace"ba wani emotional blackmail am just telling you the fact..dan Allah ka taimaka kaje ka duba musu ita Please otherwise zasuyi tunanin ban isa da qanina ba"...yayi shiru kamar bazaice komai ba sai can yace"i will go"...Aunty Sumy ta washe hakora tana fadin"yauwa my Lil bro Allah ya maka albarka kaji...Allah baka mace ta gari"...yana tabe baki ya kashe wayarshi yana kunkuni...cikin ranshi yace"tunda kin gama dani ai dole kice haka"...bai sake wasting time ba ya fita daga office...kafin ya karaso Mr.Obi ya bude mishi mota dan haka yana zuwa ya shiga ciki shima driver ya shiga suka fita daga makarantan...kai tsaye yacema Mr.Obi"Hospital zaka kaini". FCNM Female Hostel,Apartment C Room 2a. Zaune take tsakiyar gado ta zuba tagumi da duk hannayenta...gaba daya hankalinta naga Macbook dinta dake ajiye gabanta suna video call da yan gidansu...kana ganin yanda ta daure fuska take faman turo baki zaka fahimci fada akeyi mata...fara ce sosai kamar ka tabata jini ya fito kuma kallo daya zakayi mata ka gane Fulani blood ke running a cikin veins dinta dan she is full blood Fulani of Gombe state...face dinta daukeda siririn pointed nose da cute red lips masu masifar kyau sai kuma sexy idanunta da suke nan farare tas dasu kaman na larabawa...gashin kanta nada tsawo sosai tayi parking dinshi a tsakiya ta saki jelan nata yawo a gadon bayanta...red jessy ne a jikinta mai daukeda tambarin Manchester United a kirji sai black trouser dinta three quarter...daidai da bedsheets da pillow case dake shimfide kan bed dinta Red ne mai daukeda tambarin Manchester United ko ta ina...wnn alama ne na she is a die heart fan of MUFC...babu dankwali ko hula a kanta hakan kuma ya bayyanar da silky black hair dinta da yake nan a barbaje...ganin yanda ta bada hankalinta kacokam ga vidoe call datake yasa nima na karasa dan inga da wanda take magana...wata mace ce da kallo daya zakayi mata ka gane mahaifiyarta ce sbd tsananin kama da sukeyi da ita...hatta dimples dinsu da yake lostawa duk sukayi motsi da cheeks dinsu iri daya ne...dukda ba a zahiri nake ganinta ba dimples din are so visible da kana dora idanu a kanta zaka gansu...cikin fushi takeyi mata fada snn ta karkare da fadin"kuma wlh duk na sake jin ance kinyi irin wnn rashin hankalin sai ranki yayi mummunan baci tunda ke har yanxu bazakiyi hankali ba...kece babba amma kullum rashin hankalinki karuwa yake...na tabbata ko Yusra da take karama bazatayi wnn iskancin da kikeyi ba kawai sbd zaayi maki allura sai kiyita zubama mutane ihu kina musu kuka sai kace karamar yarinya?..dont worry daddynku yana dawowa dama zan fada masa ga abunda kikeyi a makaranta"...tunda Mom dinta ta fara fada batace wani abu ba sai yanxu...hankali a tashe murya tamkar zata fashe da kuka tace"Ammi dan girman Allah karki fadama daddy kinji wlh bazan karaba...Ammi kinsan yanda allura yakemin shiyasa nayi kuka wlh amma i promise bazan kara ba pls pls plssss"..ta karasa mgnr hawaye na wanke mata fuska...tasan muddin mgnr nan yaje kunnen daddy ta gama yawo...ta sanshi sarai mutum ne shi mai zafi shiyasa baya daukan nonsense kuma ta tabbata idan yaji mgnr nan yana iya zuwa har Kano yayi maganinta tunda tun tasowarta ake wnn rikicin da ita akan allura...tun tana yarinya dama duk zaayi mata allura saidai ya tsaya a gabanta rikeda bulala snn zata yadda...har zuwa yanxun kuma ta kasa sabawa dashi...tana rufe baki Ammi tace"to wlh na sakejin mgn makamancin haka sai kinci ubanki kuma itama Bilkisun zan fada mata duk kika fara period sai su barki da abunki tunda ke har yanxu bakisan annabi ya faku ba"...da sauri ta sake cewa"am sorry ban karawa"..Ammi bata sake cewa komai ba sai tsaki data saki tareda mikama sisters dinta dake zaune tun dazu suna jira suyi mgn da ita Macbook din hannunta kafin ta fita daga parlorn...da sauri ta goge hawayenta dan bataso su gani...immediate sister dinta mai suna Husna ta shiga duban screen din fuskanta da wani murmushi tace"hajia Adda mai kukan allura"..da sauri ta dago idanunta tana watsa mata harara tace"so na zama abokiyar wasanki ko Husna?..raini ya fara shiga tsakanina dake ba?"...Husna ta shiga girgiza kai tace"kai Adda dan Allah nidai bance haka ba...kawai dan nace mai kukan allurr"..bata karasa ba ta daka mata wani hadadden tsawa tace"Husna kina hauka?..ni kike fadama mgn haka koh?.."Husna tayi shiru tana duban yar uwar tata baki a tsuke tace"Allah ya baki hakuri..laifina ne ma dana dage sai nayi mgn dake..sai anjima"..daga haka ta mike da sauri ta ajiye Macbook din ta tafi dakinsu abunta...Yusra ta matso da fara'arta sosai tace"Adda don't mind her kinji?..she is not a good girl"..lokaci daya murmushi ya maye gurbin face dinta tace"of course she is not habibty..how are you?.."Yusra tace"ina lafia Adda..ya karatu"...saida ta dan bata rai snn tace"karatu ba dadi habibty kuma ina missing dinku sosai"..tace"muma muna missing dinki Adda amma Hammanmu yace duk zai sake zuwa wurinki damu zaizo"...tace"to shikenan habibty i can't wait to see you...yanxu ki bama Hamma Macbook muyi mgn dashi"..ba musu ta mike zuwa inda Hamman nasu ke zaune yana sararonsu ta mika mashi MacBook din...yana amsa yaja cheeks dinta tareda mikewa ya fada dakinsa...saida ya zauna akan bed snn ya daidaita screen din yana dubanta da kyau yace"so you are done"...tana wani tale baki tace"Hamma Ammi kaman zata cinyeni sbd fada...hadda cewa saita fadama daddy nidai dan Allah kace mata kada ta hadani dashi kaji"...murmushi ya saki yana cigaba da kallonta yace"ai ke dince Maama bakya jin mgn...na rasa gane wane irin tsoro kikema injection da duk akazo yi miki sai kin tarama kanki jama'a sai kace ba health personnel ba"...tana sake turo bakinta tace"Hamma dan ina health personnel dole sai naso allura ne?.."yace"ya kamata kiso ta mana tunda kina yiwa mutane"..ta rungume hannunta a kirji tana girgiza kai tace"nidai aah wlh..dan inayi bashi yake nufin dole nima sai anyi min ba...yanxun yaushe zakazo ka ganni kaga fa yau almost 6 weeks knn baka zo ka ganni ba"..yana murmushi yace"i will come inshaAllah nima ba karamin missing dinki nakeba...aiyuka ne kawai sukamin yawa suka hanani zuwa ganin qanwata"...nan da nan ta saki smile daya bayyanar da dimples dinta tace"to yaushe zakazo Hamma?.."yace"zanzo Maama amma ba yanxu ba...kinga wnn week din daddy zai dawo amma inshaAllah yana tafiya zamuzo har su Husna"..tace"to shikenan Hammana thank you"..shima yace"thank you cutie pie amma yanxu qafan ya warke koh?.."tana gyada mishi kai tace"ya warke wlh...kuma ko injection din ma bayamin ciwo kaman yanda yakeyi da...kilan proprietor dinmu bashida zafin hannu"...murmushi kawai Hamman nata yayi kafin yace"ohk ki samu ki kara hutawa yanxu and kice ina gaishe da Billy da kyau"..da sauri tace"zataji inshaAllh...besty fa?.."saida ya danyi jim snn yace"shima ina gaisheshi"...ta sake amsawa da zaiji snn sukayi sallama...ta ajiye Macbook dinta a gefe tana sauke ajiyar zuciya tace"Finally"...tana kokarin kwanciya Billy ta fito daga kitchen hannunta rikeda bowl data dama custard a ciki...tana karasowa ta janyo table ta dora mata akai snn tace"ga custard din nan idan zakisha"...Aysha ta dan daga ido ta kalleta sai taga fuskanta daure tace"haba mana Billy...haba my besty..fushin bai kare bane har yanxu?.."harara Billy watsa mata tace"kije ki nemi inda bestynki yake dai amma ba a nan ba...kawai dazu kikasa mutumin nan yayita watsa mana wadan nan shegun idanun nashi masu kama da na aljanu...saura kadan na saki fitsari wlh sbd tsabar tsoro"...Aysha na kokarin fashewa da daria tace"haba Billy fitsari kuma sai kace wanda taga mala'ika"...Billy tace"ba gara mala'ika ba Lamido shi yanada imani snn aikin Allah yakeyi...amma Proprietor fa kullum fuskanshi a haka yake sai kace namijin saniya"...wnn karon daria Aysha ta saki sosai sai kace ba itane me kukan allura ba dazu...saida tayi me isarta tace"wlh ni kaina bansan sanda na shiga hankalina ba...gaskia idanun mutumin nan basuyi ba a rayuwa...kawai kuna hada ido da mutum kiji kmr yayi miki asiri"...Billy ta sauke ajiyar zuciya tace"shiyasa ni ko hanya bana son hadawa dashi ballantana mu hada ido hantar cikina tazo tana kadawa"...kafin Aysha tayi mgn wayanta ya dauki ringing...ta dan tsayar da dariyanta snn tayi picking tareda fadin"my bsty"..a daya bangaren yace"besty ya jikin naki?.."tace"na samu sauki sosai besty"...yace"to Alhamdulillah wajen injection dinfa?.."saida ta kalli Billy taga yanda take ta wani tabe baki snn tace"shima da sauki sosai...Billy tace wai ita bazaka tambayi yanda take ba"...da sauri Billy tace"Allah ya kiyaye yaushe na fada miki haka?..me ma akai akayi wani Sa'eed da har zan damu dan bai tambayeni ba...ya dade baiki tambayata ba wnn matsalarku ce ba nawa ba"...Aysha najin Billy ta fara mgn tayi putting nata on speaker tace"besty kanajin mutumiyar taka koh"...yace"inaji rabu da ita besty duk wnn maganganun da take fada basu kai zuci ba...i know she is boiling inside sbd mai girma Sa'eed bai tambayi ya Bilkisu take ba"...tun kafin ya rufe baki Billy ta sake fadin"nikam Allah yayi min tsari da ganin wnn rana...kudai kuje can kuyita abunku amma bada Bilkisu ba"..Aysha dai na zaune gefe tana sauraronsu tanata yi musu daria...ta kasa gane wnn 'yar tsama dake tsakanin Billy da Sa'eed tun tale tale...tun farkon haduwarsu basa jituwa sam suna haduwa zasu fara tsokanar juna sai kace mage da bera...Friendship dinsu kuma ba karamin sake karfi yakeyi ba...dukda kasancewar kowa state dinshi daban karatu ne kawai ya hadasu a kano ba karamin shakuwa sukayi da junansu ba...shi Sa'eed dan kaduna ne sunanshi Sa'eed Mukhtar Makarfi...shekarunshi 25 yana karantar basic Nursing a FCNM dukda cewa saida ya kammala Bsc dinshi kawai sbd sha'awan Nursing profession yayi joining FCNM kuma sai Allah ya hadashi dasu...yanxu haka yana final year...Billy kuma asalinta jihar Bauchi...Bilkisu Ibrahim Muqaddas shine cikakken sunanta...she is a 2nd year student of Basic Midiwifery...class dinsu daya da Lamido likewise hostel dinsu..ita kuma Aysha Ahmad Lamido shine complete sunanta...suna kiranta Lamido kasancewar almost kowa a school abunda yake kiranta dashi knn...mahaifinta bafulatani ne Alhaji Ahmad Adnan Lamido shine present deputy controller general na Nigerian Custom Service snn shine 'da na biyar cikin jerin 'ya'yan Lamidon Gombe Alhaji Muhammad Adnan Lamido...mahaifiyarta kuma Maimunatu itama asalin bafulatanar Gombe ce...yara uku garesu Aysha itace babba sai Asma'u da suke kira Husna sai kuma Yusra data kasance 'yar auta...shi Kuma Hamma Najeeb cousin brother dinsu ne da mahaifinsu ya rike tun kafin a haifi Aysha shiyasa suka saba dashi sosai dan idan ba fada akayi ba bazaka taba tunanin Cousin dinsu bane. Wnn knn... Bobby bai samu dawowa gida ba sai after magrib...haka kuwa ya shigo gidan rai a hade sbd tsabar gajia da yayi...driver na shigowa ya samu wuri yayi parking snn ya bude motan ya fito saidai tun kafin ya zagaya ya bude mishi kofa mai gadi yazo ya bude yanata faman mishi kirari sai kace wani sarki...Bobby bai iya ce mishi komai ba sai hannu daya daga mishi kafin ya nufi entrance...tun daga compound din gidan zaka gane mamallakinshi ba karamin mai kudi bane duba da girma da kuma tsagwaron kyau da kuma tsaruwar gidan...katoton Mansion ne daya amsa sunan Mansion saidai abu daya daya bani mamaki is yanda naga gidan shi kadai ne kaf girman layin nasu..ko makota basu dashi dan sai kayi tafiya mai nisa daga nan kafin ka fara hango gidajen mutane...cikin raina nace kilan mutanen gidan basu son zama cikin mutane...ga uban motoci zube cikin compound din bila adadin sai kace ba kudi ake sawa ake siya ba...hatta plate number dake jikin motocin nashi duk sunanshi ne a jiki tunda daga Dr.Bobby 1,2,3 har zuwa ba adadi dan ban samu damar irga adadin yawan motocin ba...ajiyar zuciya na sauke ina jinjina baiwar kudi da Allah yayi masa at such young age snn nabi bayanshi zuwa cikin gidan...bai samu kowa a central parlour ba sai tv dake aiki sai kuma sanyin ac da qamshin freshener da suka hadu suka bada wani sassanyan qamshi a dakin...shi kanshi palorn abun kallo ne...bai tsaya wasting time ba naga ya nufi wani corridor suit dinshi rataye a shoulder dinshi...another parlour naga ya shiga wnn karon dai da akwai mutane a ciki...ya karasa ya zauna kusada wadda kallo daya nayi mata na gane Mom dinshi ce...if you see yanda yayi da face dinshi zai baka daria sosai...ya lumshe eyes dinshi tareda dora kanshi shoulder dinta voice dinshi can kasa cikin igbo yace"Mummy am home"...Mummy na shafa kanshi fuskanta daukeda wide smile itama da igbo din tace"welcome back son..akwai gajiyan aiki koh"...ya danyi pouting lips dinshi before saying"gajia sosae Mummy...kawai Aunty Sumy tace lallai sai naje na duba yarinyan friend dinta a hospital"..Mummy na cigaba da shafa kanshi ta maida dubanta kan Aunty Sumy dake zaune gefe tana aiki cikin system dinta tace"gaskia Sumayya baki kyauta min ba..haka nan kin wahalar min da yaro"..aunty sumy daria tasa sosai kafin tace"Mummy dan yaga kina biye mishi nefa yake wnn abun...ko Sabeer da yake dan auta baya wnn shagwaban da yakeyi..you better grow up wlh wnn shagwa6an babu inda zai kaika"...ta karasa mgn referring to him. Littafin Dr.BOBBY na kudi ne...masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank... sai a tura evidence of payment through 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 03 Sake pouting lips dinshi yayi yace"Mummy blackmailing dina fa tayi wai idan banjeba friend dinta will think bata isa dani ba"...Mummy na kokarin bude baki tayi mgn wata yarinya da batafi 16 years ba ta shigo parlorn da wani mugun gudu kaman wadda kura ko zaki ya biyota...ta tsallaka ta boye bayan Mummy ba tareda ta lura da Bobby da har yanxun ke rungume jikinta ba cikin sauke numfashi tace"Mummy talk to uncle Sab plss...haka nan ya sameni a dakina wai na shiga mishi daki na taba Macbook kuma nidai Allah ban taba mishi komai ba..ko hanyan dakinshi ma banjeba"...tana rufe baki sai ga Sabeer din ya shigo parlorn shima a sukwane yanata kalle kallen inda zai hangota ya fara cewa"Mummy kinga Miemie kawai na ajiye abuna taje ta tabamin koh?..Mummy Allah kiyi mata mgn idan ba haka ba i will..."Bobby bai barshi ya karasa ba ya daka mashi wani tsawan da hatta Miemie dake boye bayan Mummy batasan time da ta fito tana rarraba idanu ba...ya shiga binsu da wani mugun kallo gaba dayansu aikuwa ba shiri duk sukayi kasa da idanunsu domin babu mai karfin zuciyar da zai iya jure wnn kallon da idanun Bobby ke binsu dashi...lokaci daya duk suka shiga taitayinsu dan ba karamin tsoronshi sukeji ba..haka zalika idanunshi ba karamin ladabtar dasu sukeyi ba musamman Miemie da duk ya zuba mata su sai taji kaman ta saki fitsari a wando sbd tsoro shiyasa duk gidan ba wanda suke tsoro kamanshi dan ko kadan baya saurara musu sbd yanda kullum cikin rikici suke yanda kasan tom and jerry...kullum cikin one rigima or the other suke duk kuwa da tazaran shekarun dake tsakaninsu aikinsu knn...saida ya gama binsu da matsiyacin kallo snn ya sauke idanun kan Miemie yana sake tamke fuska yace"meya kaiki dakinshi?..ban ma hanaki zuwa dakinshi ba?.."jiki na rawa Miemie tace"ka hana Uncle Bobby amma wlh nidai banje dakinshi ba...ina cikin zamana fa kawai yazo yace wai na shiga mishi dakinshi"...saida ya bari ta gama tsaf snn ya maida dubanshi ga Sab still fuska daure yace"kai ya akai kasan ta shiga maka daki?.."da sauri yace"Uncle Bobby na gama aiki cikin Macbook dina ko saving banyi ba na tafi masjid shine ina dawowa kawai naga tayi deleting"..yana rufe baki Miemie tace"Uncle Bobby i swear he's lying ni ban taba mishi komai b..."bata samu sararin karasawa ba sakamakon wani kallo da Bobby ya shiga binta dashi...yana pointing Sabeer yace"mate dinki ne shi da zakice yana karya?.."da sauri ta girgiza mishi kai alaman aah...Bobby yacigaba da fadin"menene sunanshi?.."hawaye na cikowa idonta tace"Uncle Sabeer"...ya sake fadin"who is he to you?.."hawayen da suka cika idanunta na zuba kan fuskanta tace"he's my Uncle"..wani kallon Bobby yacigaba da binta dashi ba shiri ta sake cewa"he's my mother's brother"..Bobby yace"good..ko don sbd wnn matsayin baiyi deserving respect dinki ba?.."wnn karon da kyar ta iya bude baki sbd kukan dake cin karfinta tace"he deserve"..yace"then why are you not respecting him?.."tayi shiru...ya sake cewa"am talking to you"..still kasa mgn tayi sbd kuka da yaci karfinta...shi kuma ya sake juyawa ga Sab ya sakar mashi wani kyakykyawan harara tareda nunashi da finger dinshi yace"and you...kaima baka kama girmanka..kawai sbd anyi maka deleting abu sai kace ita tayi?..kasan kanason abun mai yasa bakayi saving before going out ba...this is going to be the very last warning da zan baku wlh...duk na sakeji wani cikinku yace wani yayi mashi wani abu duk sai nayi maganinku...C'mon get lost"..tun kafin ma ya rufe baki duk suka juya sum sum suka koma inda suka fito...Aunty Sumy da har yanxun hankalinta ke kan abunda takeyi tace"na rasa wnn rigima dake tsakanin Miemie da Sab a gidan nan...ace yara kullum cikin fada kaman wanda aka haifesu a iraq?.."Mummy ma girgiza kai ta shigayi tana fadin"har yanxun akwai sauran yarinta a tattare dasu ne amma inshaAllah watarana zasu daina just continue praying for them...kai kuma Bobby go and freshen up sai ka fito kaci abinci"...baiyi mata musu ba ya mike tareda kama hanyan Flat dinshi walking majestically like a king...wani dogon corridor naga ya shiga snn yabi ta wani kofa kawai sai ganinshi nayi cikin wani parlon...fadin haduwa da tsaruwar wurin is a waste of time...bai tsaya nan parlorn ba ya wuce bedroom dinshi kai tsaye ya rage kayan jikinshi tareda fadawa toilet...ni kuma nayi amfani da wnn daman na shiga karema dakin nashi kallo...komai na cikin dakin white ne daidai da curtains,sofas da carpets duk farare ne...snn dakin yanada girman da zai iya daukan almost 2 sets of bed bayan wanda already suke zube a cikinshi...ko ina tsaf tsaf dashi ga wani kamshi dake tashi ko dakin amarya albarka...a jikin bangon dakin katon picture ne na wani mutumi dake sanyeda Uniform na Nigerian Custom da alama yana tafiya aka dauki hoton...a can kasa an rubuta COL ATTAHIR ADAMU WAZIRI sai in bracket aka rubuta CONTROLLER GENERAL NIGERIAN CUSTOM SERVICE 2014-2018...a kallon farko da nayiwa mutumin na tabbatar da shine mahaifin Bobby dan yana kama dashi sosai unlike Aunty Sumy da Sabeer da sukafi dauko kamannin Mummy...asalinshi bafulatanin Gombe ne mahaifinshi Alhaji Adamu Abdullahi Wazirin Gombe...shine first son din waziri snn yanada tarin siblings maza wanda suka hada uba daya domin bayan shi mahaifiyarshi saida ta dauki lokaci kafin ta sake haifan qanwarshi Munubiya wanda tun daga ita kuma Allah bai sake bata haihuwa ba...ya hadu da Mummy(Nadia)a kano lokacin tana karatu a Buk nan take kuma yaji yana kaunarta...saida aka kai ruwa rana sosai kafin aka bari ya aureta kasancewar ba bahaushiya bace...Sumayya itace first daughter dinsu an sa mata sunan only sis din Mummy data rasu gab da haihuwarta sai Bobby da yaci sunan Dad dinshi Attahir shi kuma auta Sabeer yaci sunan Waziri Adam knn...Miemie kuma daughter din Aunty Sumy ce da younger sis dinta mai suna Ilham(idan muka juya labari zakuji bayanin komai in detail..this is just an introduction). Washegari ya gama shirya kanshi cikin suit as always ya nufi parlon Mummy don yin breakfast saidai ga mamakinshi Miemie kadai ya samu zaune a dinning tana pressing phone dinta...sanye take cikin uniform dinta complete da alama ta gama shirin tafiya school...tun kafin ya karasa dinning din data hangoshi cikin igbo tace"Uncle Bobby Iboola chi"(Uncle Bobby good morning)...yace"kedu ka odi"(how are you)..tace"adimm ma"(i am fine)...yana gyada kai yace"where is everyone?.."tace"Aunty dai ta shiga kitchen yanxu...Mummy da Uncle Sab kuma basu fito ba"..baice komai ba ya juya ya kama hanyan dakin Mummy...zaune ya sameta gefen gado waya kare kunnenta..karasawa ciki yayi ya zauna tareda kama hannunta har ta kammala wayan snn yace"Iboola chi Mummy"...Mummy ta dan kirkiri murmushi tana shafa uban gashin kanshi da yasha gyara tace"iboola chi..how was your night"...yace"fine Mummy"...tace"yau ka kusa makara"...yace"wlh Mummy bacci ne ya daukeni..kuma baki tasheni ba"...murmushi ta kara saki before tace"ai ba aikina bane tashinka a bacci Bobby...aure ya kamata kayi kawai"...ya bata rai yana turo lips dinshi yace"Mummy stop it plss"..ture kanshi tayi daga jikinta tace"i will not stop...haka nan kake tunanin zakayita min zaune a gida without getting married?..you better wake up cox you are dreaming"...sake bata rai yayi yana squeezing face dinshi kaman zaisa kuka yace" Mummy please!"...daria ya ba Mummy sosai ganin yanda yake bubbuga legs dinshi...gaskian Sumayya da take cewa ko Sabeer bai kai Bobby shagwaba ba...saida ta gama dariyan snn ta dan daidaita face dinta tace"da gaske so nake kayi aure Bobby...i want to see your kids running all around this house before i die..i really want to see that"...shiru Bobby yayi yana sauraronta bai san me ya kamata yace ba...sam baison promising nata abunda yasan bazai iya ba...ba wai aure ne baiso ba aah dalili guda daya ne yake ganin zai mishi katanga da yin aure har abada...wnn dalilin kuma shine dangin mahaifinshi...yasan definitely duk ya dauko aure dole familyn uba sune suke taka rawan gani...shi kuma a yanxu bashida makiya da suka wuce familyn dad dinsu..he hates them to the extent that duk wani bafulatani a duniya yakejin ya tsaneshi especially those from Gombe sbd munanan abubuwa da suka aikata musu shi da Mum dinshi da kuma siblings dinshi...wnn dalilin yasa ya yanke ma kanshi hukuncin indai saida dangin mahaifinshi zaa bashi aure to ya gwammaci bazaiyi aure ba har ya koma ga mahaliccinshi...wnn shine dalilinda duk yanmatan dake rushing dinshi baya kulasu cox he will never get married...Aunty Sumayya ce ta shigo dakin tana sanye cikin dogon riga na wani blue lace tayi daurin dankwalinta das da alama ta gama shirin office itama..kyakyawa ce sosai gata da wani irin haske mai daukan ido dukda ba kama sukeyi da Bobby sosai ba kana ganinta zaka gane thesame blood ke running a veins dinsu...a fuska idan ka kalleta bazaka ce ta haifi Miemie ba sbd kyawun jikinta sak na Mummyn su ne...itama a ido ba kowa ke yadda ta haifesu ba kuma har yanxun jikinta nada kyau kaman bata fara tsufa ba...ta karaso ciki tana dan hararanshi tace"Mummy Allah ki dena bari yana kwanta miki a jiki haka...qatoto dashi instead of yaje yayi aure shine zaizo yanama mutane shagwaba like a small baby"...da sauri ya dago da kanshi yana kallon Mummy jin again Aunty Sumy na mgnr aure..smiling yaga tanayi sai ya juya ga aunty sumy itama yaga haka kawai sai yace"hada baki kukayi koh?.."Mummy ta dan dungure mishi kai tace"ba wani hadin baki gaskia ne kawai..kuma idan bakayi wasa ba da kaina zan samo matar da zan aura maka"..Bobby ya wani kwabe fuska kaman zaisa kuka aunty sumy na daria...Mummy kuma mikewa tayi zata fita daga dakin tace"oya ku fito ayi breakfast"..duk cikinsu ba wanda yace komai har ta fita daga dakin...shima Bobby ya mike hannayenshi zube cikin pockets dinshi ya saki wani smile da kana gani zaka san na tsokana ne kafin yace"Aunty Sumy don't worry dama da akwai wani doctor a Hospital dina da yaketa min nacin yana sonki..ina ganin i will just have to talk to him indai da gaske yakeyi kawai ya fito ni zan bashi aurenki"...tun kafin ya karasa mgnr Aunty Sumy ta kai masa rankwashi a kai tana daria...shima yana dariyan suka fita daga dakin. Jennifer cook dinsu na gama jere abinci kan dinning Miemie ta mike tareda fara serving...saida ta zubama kowa sai ga Sab ya shigo yana ta yatsine fuska...kai tsaye kujeran dake kusada Mummy ya zauna bayan ya matsar da kujeran kusada nata sosai kawai ya dora kanshi shoulder dinta yana dan yatsine fuska yace"Mummy am sick"...a hankali Mummy ke shafa kanshi tace"meke damun dan autana?.."fuska a kwabe kaman zaisa kuka yace"headache ne Mummy..jiya ko bacci ban samu nayi ba sosai"..dago kanshi Mummy tayi tareda kai hannu tana feeling temperature dinshi tace"eyya sorry love.. yanxu ka samu kaci wani abu sai Bobby ya dubamin kai kafin ya fita"..ba musu Sab ya gyada mata kai ita kuma ta janyo plate ta fara serving nashi...Bobby da tun dazun yake kallonshi yana hararanshi yace"yanxu headache din kakema wnn abun ko Sab?..only headache kakema wnn kwararaton"...langabar da kai Sabeer yayi without saying anything... Aunty Sumy na smiling tace"kai da kake fake auta ma kayi shagwa6a bare shi da yake authentic auta"...harara kawai Bobby ya watsa mata bai sake cewa komai ba...kowa ya maida hankali kan abincin da yakeci...suna dab da gamawa Aunty Sumy tace"umhum Bobby mgnr interview da na fada maka this coming monday zaayi inshaAllah..hope you'll come over?.."girgiza kai yayi yace"nima i have alot on my table so kuje kuyi interview dinku Allah ya bada sa'a"..tun kafin ya rufe baki ta sake cewa"hope bada gaske kake ba?..why zakace baka zuwa a matsayinka na proprietor?.."shima tana rufe baki yace"Aunty you are the MD zaa iyayin komai a gabanki ba sai dole naje ba..a kyaleni ma inji da aiyukan Hospital dana sauran colleges din"...Mummy dake sauraronsu tace"wich interview are you talking about?.."da sauri Aunty Sumy tace"Mummy interview da nace maki zamuyi na new teachers da zamu dauka...primary section muna buqatan Islamic and Basic Science teachers...secondary section kuma English and Geography..dan Allah Mummy talk to him kada yace bazaiyi attending ba please..zuwan nashi is very important besides ba dadewa zaayi anayi ba"...juyawa Mummy tayi tana dubanshi tace"ya kamata kaje Bobby..i see nothing wrong with that"...kasa cewa komai yayi sai kai kawai daya daga mata...tunda Mummy tasa baki kuma ai mgn ya kare..itama Aunty Sumy sanin hakan ne yasa tayi involving Mummyn a mgnr sbd tasan bazai taba tsallake umarninta ba...a iya saninta da Bobby abu daya ne yake jayayya da Mummy shine idan tayi mgnr familyn dad dinsu wnn kam ko mgnr baya bari yayi nisa yake stopping nashi sbd bayason yakai limit dinda zata umarceshi da yaje garesu shi kuma ya watsa mata kasa a ido...yau shekara biyar knn da rasuwar mahaifinsu kuma tun daga ranar babu wani cikinsu daya sake yin koda hanyan Gombe idan ka cire Sabeer dake Police Academy Wudil...alqawari ne ya daukan ma kanshi babushi babu zuwa Gombe har abada..haka ma Mummy da siblings dinshi duk babu mai zuwa...ko Wudil din ma da Sab keyi watarana sai yaji kaman ya cireshi sbd bai son yin hanyan Gombe at all...ba don bai son katse mishi karatunshi da yayi nisa ba da babu abinda zai hanashi cireshi daga makarantan. Suna gama breakfast kowa ya tashi Miemie da Aunty Sumy mota daya suka shigo zuwa school shi kuma Bobby saida ya fara duba Sab kmr yanda Mummy tace snn ya shiga nashi motan shima suka wuce College. Mummy da Sab kuma suna gida kasancewar shi Sab din yana hutun makaranta. FCNM Female Hostel. Da sauri take shiryawa tanayi tana duban time sbd bata son suyi latti..tasan idan Billy ta shigo taga bata gama shiryawa ba masifa ne zata sauke mata shi kwando kwando...daure take da dan towel dinta red daya tsaya daidai laps dinta...white skin dinta na nan sai glowing yake kaman wata amarya...gashin kanta sai digar da ruwa yake wich makes it look sexy...tana kokarin sa uniform dinta Billy ta shigo dakin cikin nata uniform riga da wando sai hula a kanta ba hijab...ta karasa ta zauna gefen gado tana duban Aysha daketa faman shiryawa tace"Lamido kinsan meke faruwa cikin Hostel din nan kuwa?.."Aysha dake kokarin jona hand dryer jikin socket tace"bani insha qawata"...Billy na tabe baki tace"ina yarinyar nan Binta Gumel?.."Aysha tace"what about her?.."sake tabe baki Billy kafin tacigaba"kinsan dama tun muna 100 level take son Sir Abdool shine in fada miki jiya taje har office dinshi ta fada mishi wai ita sonshi take shi kuma ya koreta a office dinshi bayan ya kora mata warning kar ta sake zuwa inda yake shi yanada wadda yakeso...shine sbd karamar 'yar iska ce ita tazo ta tara friends dinta a Hostel tana fada musu wai kece kika shiga tsakaninsu kika rabashi da ita..wai da ita yakeso amma kina fara kulashi ya fara mata wulakanci..kinji fa shegiya sai kace bamu san tun da can ita kadai take haukanta ba..na tabbata Sir Abdool bazai taba kula wnn qazamar ba mtsstsstww some people are annoying wlh"...ta karasa mgnr da jan dogon tsaki...Aysha batace komai ba saida ta gama drying gashinta tayi combing tareda yin packing snn ta zauna tana fuskantar Billy tace"Allah yasa dai ba zuwa kikayi kika kulata kukai rigima ba"...harara Billy ta wasta mata mai kyau kafin tace"kema ai kinsan bazan kyaleta ba...zuwa nayi na tona mata asiri na fadama kowa yanda take nace mishi bayan ko damuwa da ita baiyi ba"...tana gama fadan haka ta kamo hannun Aysha ta rike cikin nata tareda dubanta sosai tace"Lamido dan Allah ki duba mgnr Sir Abdool din nan plss...mutumin nan fa da gaske yake sonki kuma he wants to marry you...kina ganin yanda mata suke rushing akanshi zaki san ba abun yarwa bane...kinga he's handasome he's rich snn yanada kyawawan dabi'u kuma bashida son mata he's a husband material Lamido dan Allah ki reconsodering mgnr nan plss"...ta karasa mgnr in pleading tone...hannunta Lamido ta sake kamawa itama tana dan murmushi tace"wlh Billy na rasa abunda mutumin nan yayi miki kike mugun sonshi haka...nifa ba cewa nayi bana sonshi ba kawai dai yanxu ba time din soyayya bane a wuri na..kin manta deal da mukayi da daddyna?..yace indai na kammala makarantan nan successfully yayi min alqawari zai turani abroad karatu kaman yanda naso tun a baya kuma ina tsayar da miji kema kinsan Lamido cewa zaiyi ya fito ayi biki kawai ni kuma gaskia am not yet ready for marriage nafiso in gama cin zamani na yanda ya kamata..besides idan na shirya yin auren ma sugar daddy zan aura kin sani"..ta karasa mgnr tana wani blushing...Billy bata bari ta rufe baki ba tace" amma dai nasan a cikin deal din naku baiyi mentioning banda kula samari ba koh?..kuma karki fara cemin sbd karatu ne baki kulashi dan nasan you are lying...ko da soyayya ko babu soyayya babu abinda zai canxa brain dinki Lamido you are genius ko bakiyi karatu ba passing exams dinki kike dan Allah give him a chance kinji..dan Allah please!.."murmushi Aysha ta saki har yanxun suna rikeda hannun juna sai kuma ta dan turo lips dinta tace"But i told you sugar daddy nakeso fa.."dogon tsaki Billy ta saki zata mike ta bar wurin Aysha ta dawo da ita da sauri still tana smiling tace"shikenan shikenan naji zan bashi chance and it's only because of you..yanxun ki tashi mu karasa shiryawa mu fita nasan yanzu bus na can yana jiranmu"...rungumeta Billy tayi tana fadin"thank you so much qawalli tah...thank you bestyn Sa'eed"...Aysha ta mike daga gadon tana daria tace"kin tuna da mutuminki knn?.."itama Billy mikewan tayi still smiling tace"dan rainin hankali ba...tunda uwata ta haifeni ban taba ganin dan rainin hankalin mutumi kaman Sa'eed ba..he is so annoying"..Aysha ta fashe da daria tana tsokananta wai ko son juna suke..itadai Billy banza tayi da ita as batada abunda zatace mata...a gurguje suka karasa shiryawa kowa ta zura hijab dinta da ko boobs bai gama rufewa ba snn suka fita bayan sunyi locking dakinsu...haraban Hostel din suka fita inda students da dame ke wajen suna jiran bus da yake kaisu school yazo...baa jimaba kuwa yazo nan kowa ya fita suka shiga ciki suka tafi. Hostel din nasu nada girma da kuma tsari sosai dan gate har biyu ne dashi...gate na farko gidaje ne guda uku wanda matrons da suke kula dasu suke zaune da securities guda biyu hadda police officer...shima yana shimfide da katon compound kafin ka isa next gate inda kana shiga zaka tarar da another compound mai cikeda shukoki sai kuma apartments kusan guda 12...ko wanne apartment sama da kasa ne snn each apartment has 6 rooms uku upstairs uku downstairs...each and every room kuma na dauke da two sets of medium bed a gefen kowane bed akwai bedside drawer me daukeda bedside lamp akai...sai study table dake ajiye each side of the bed sai kuma babban drawer na jikin bango shima on each side.. a tsakiya kuma human sized mirror ne kafe jikin bango sai toilet dake can gefe sai kuma dan kitchen madaidaici...inshort tsayawa fadan tsaruwan da rooms dama gaba daya Hostel din nasu sukayi bata lokaci ne..kawai dai yana da kyau da kuma tsari kaman ba college Hostel ba. Remeber we are still on our free pages so keep on subscribing before free pages su kare🤩 Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 04 Tafiyan almost 10 mins ne ya kawosu area classes...direct driver ya karasa inda aka tanada domin parking school bus din yayi parking snn students suka fara fita...Lamido da Billy ne karshen fita daga cikin motan as always...suna fitowa sukaci karo da Sa'eed dake jingine jikin motanshi yayi crossing legs dinshi yana kallonsu...murmushi kyakykyawa Aysha ta saki tareda nufan inda yake tana fadin"Besty nah"...shima murmushin ya sakar mata yace"yes my besty how are you?.."tace"ina lafia bsty yau kazo da wuri"..murmushi ya kara saki zaiyi mgn ya hango Billy dake tsaye dan nesa dasu tana tattabe baki irin a dole batasan da zamansu a wurin ba...daria sosai ta bashi ganin yanda take basarwa Aysha ma ta juya inda yake kallo sai taga Billy tsaye a wurin nan take itama dariyan ya kwace mata...saida sukayi me isarsu Billy ta gama cika taf saura kiris ta fashe Aysha ta karasa tareda kamota da sauri still tana smiling tace"haba mana Billynmu...me yayi zafi haka why are you frowning your face like this?.."harara Billy ta watsa mata tareda janye jikinta tace"malama let go of my hand badai ni kukema daria ba?..gani mahaukaciya koh"..da sauri Aysha ta sake riko hannunta tana jinjina rigima irin na Billy tace"Billy please mana..besty come and help me i can't handle her alone"...ba musu Sa'eed da har yanzun bai dena dariya ba ya karaso inda suke yana rungume da hands dinshi yace"C'mon mana Billy..we are not laughing at you sorry"...kyakyawar harara shima ya samu daga gareta kafin ta dan tabe bakinta murya can kasa tace"it's ohk na hakura and not because of you"...tayi pointing Sa'eed da hannunta..da sauri ya shiga gyada kanshi yace"hakan ma nine da godia hajia Bilkisu mai gadon zinare"...if you see yanda Billy ke tabe baki kaman wanda taga poopoo...mutanen nata kam banda kunshe daria ba abunda sukeyi...wato Billy is verry funny and annoying sometimes and yet she is the most coolest and amazing girl they both have ever come across...suna kokarin barin wajen wani saurayi ya karaso inda suke da sauri yana sanye da uniform exactly irin na Sa'eed idanunshi kacokam akan Aysha yace"Lamido i need to talk to you plss"...kallo daya tayi mishi tareda gyara tsaiwanta tana rungume da hands dinta tace"go ahead ina sauraronka"...kallon Sa'eed saurayin yayi then back to Billy before ya sake dubanta yace"Lamido in private plss...i can't talk in front of everybody"...tun kafin ya rufe baki Billy da tazo wuya tace"hello who are you referring to everybody...see tun wuri ma ka kama hanya ka bar nan cox she is not interested in talking to you and she will not listen to you"...fuskanshi na nuna tsantsan bacin ran da yake ciki ya sake tsayar da idanunshi kyam akan Aysha baya ko kiftawa yanaso yaga me zatace...ganin irin kallon da yake mata ta juya ta kalli Sa'eed sai taga shima kallon nata yake...ta juya ga Billy still itama idonta a kanta sai ta tsayar da idon kan saurayin da har yanxun ko blinking baiyi ba a hankali tace"am..Tajuddeen am sorry plss..i can't talk to you right now"..tun kafin ta rufe bakinta yace"really?..sbd friends dinki basa sona right?.. Lamido dan Allah why are you doing this to me?..tell me is it a crime to love you?..do you think bansan ciwon kaina ba da nake chasing dinki after all wulakancin da ke da friends dinki kukeyi min?..Lamido bakisan irin son da nakeyi miki bane..i love you so much wlh"...ya karasa mgnr cikeda rauni sosai...nan take Aysha taji tausayinshi ya kamata..koba komai Tajuddeen sonta yakeyi and duk mai sonka bai cancanci wulakanci daga gareka ba...amma she have no choice bataso tayi deceiving dinshi tunda ba sonshi takeyi ba...ganin yana kokarin barin wurin tayi saurin cewa"Tajuddeen am so sorry plss...kaga yanxun it's almost time for lecture amma i promise during break time zan nemeka"..da sauri ya juyo yana kallonta with a little smile yace"Really?.."daga mishi kai tayi a hankali nan take sai ga fara'a sosai kan fuskanshi yace"thank you so much Lamido..thank you"...bai jira jin me zata fada ba ya juya ya bar wurin da sauri...Billy ma ta bar wurin kaman zata tashi sama...Aysha ta juya tana kallon Sa'eed tareda langabar da kanta tana squeezing face dinta kaman zata fashe mishi da kuka...daria kawai Bestyn nata yayi tareda girgiza kanshi yana dan hararanta yace"what?.."hannu ta kai ta kama both ears dinta tareda narke murya tace"am sorry"..sake girgiza kan nashi yayi yana daria...ko minti biyu basu kara wurin ba suka nufi classes dinsu...a first floor suka rabu Sa'eed ya wuce class dinsu itama ta wuce 2nd floor inda nasu class din yake...direct seat din Billy ta nufa saida ta gama aikin rarrashi snn ta mike tana kokarin zama a seat dinta ta hangoshi ta window dan haka da sauri ta bar seat din nata tareda komawa can baya ta zauna sbd seat dinta a gaba ne and batason yanda yana lecture kuma gaba daya hankalinshi a kanta...kilan yau idan yaga bai ganta a gaban ba zai hakura...tana can ta fada tunani sai ji tayi colleagues dinta na fadin"Good Morning Sir"..shi kuma gaba daya hankalinshi ba kan gaisuwar da suke mishi yakeba so kawai yake ya lalabo inda take da ya sanyata a eyes dinshi ko zai danji dama dama...extreme end of class din ya hangota dan haka ya shiga takawa zuwa wurin idanunshi gaba daya suna kanta...yana sanye cikin yadin kufta dark arsh dinkin kaftan..kanshi babu hula sai gashinshi da yasha gyara yanata kyalli abunshi...right hand dinshi na sanye cikin pocket dinshi ya karasa gareta...daidai seat din da take zaune ya tsaya tareda zuba mata eyes dinshi...a jikinta taji yana kallonta amma sam ta kasa dagowa..tasan yanxu kaf class din hankalin kowa na kansu har wani shiru class din yayi ko tari ba maiyi duk sun tsaya kallon love...saida suka dauki almost 5 mins a haka ganin babu sarki sai Allah Aysha ta dago kanta a hankali tareda langabewa tana dan turo lips dinta ta sauke idanun a kanshi...wani murmushi taga ya saki kyakykyawa hadda gyara tsaiwa still kuma yana kallonta...a hankali ta dan daga kan nata aikuwa taga gaba daya class din an juyo ana kallonsu sai ta sake narkewa kaman zata fashe da kuka tana mishi signal ya dena kallonta amma sam kmr ma hankalinshi ba jikinshi yakeba...saida ya gaji da kallon nata dan kanshi snn ya juya har yanxun hannunshi cikin pocket dinshi ya dawo gaban class din ya tsaya...nan da nan duk suka dawo da kallonsu gareshi masu kuskus nayi masu kunshe daria ma sunayi...sai yanxun ya zare hanunshi daga aljihu tareda rungumewa ga chest dinshi yana fuskantar yan class din yace"class do you really want this lecture to take place?.."nan take suka hada baki wajen cewa"yes sir"...saida ya sake rungume hannunshi snn yace"then ask your class rep to come back to her normal seat"...yana rufe baki kuwa suka juya gareta kowa na fadin albarkacin bakinshi"Lamido come back to your seat plss...Lamido dan Allah ki dawo...Class rep ki taimakemu ki dawo...Lamido this Lamido that"..kowa dai yana fadan abunda yaga zai iya shi kuma gogan yana tsaye rungume da hannu yana kallonta...ganin yanda duk suketa faman yi mata magiya ta mike daga wurin fuskan nan ba sarari ta dawo front seat dinta ta zauna tareda folding hands dinta...Billy dake zaune bayanta banda smiling ba abunda takeyi...ko Allah yasan tana matukar son union din Lamido da Sir Abdool sbd ba karamin matching juna sukayi ba...shi kuwa saida yaga ta zauna snn ya sake takawa zuwa gabanta ya ajiye mata marker dake hannunshi yana binta da wani sassanyan kallo yace"you are going to be the lecturer today"..dagowa tayi da sauri tana kallonshi sai kuma ta shiga girgiza kai tace"Sir Please!"..shima girgiza nashi kan yayi yace"Lamido please!"..nan take class din ya dauki tafi da sowa...da yawa daga yan class din sunsan dama Sir Abdool nason Lamido coz ba iya boyewa yake ba...masu farin ciki nayi hakama masu black belle irinsu Binta Gumel🤪nayi...Bilkisu kam yau ji take kaman ta taka rawa sbd nishadi..gaskia Sir Abdool ba karamin dan soyayya bane...ganin babu sarki sai Allah Aysha ta dauki markern tareda bude bag dinta ta ciro medicated glasses dinta ta saka snn ta mike a hankali zuwa gaban board sai ta tsaya tana kallonshi wai ko zaiji tausayinta yace ta koma amma sai taga yama koma gefe yayi zaune abunshi...da kyar bakina ya iya furta"MashaAllah"...sbd tsananin kyau da glasses din idonta yayi mata...tunda nake ban taba ganin wanda yayima kyau kaman ita ba..gaskia ita kam Allah ya bata..she have everthing..she's from rich family sai kuma ga kyau ga brain ga class snn kuma ga kyakykyawan zuciya...'yan class din ta kalla suma dai daga masu yi mata daria sai masu yi mata gwalo hakan ya nuna batada wani option dan haka ta juya tana fuskantar Board din taji yace"our today's topic is Endocrine System"...bata juya ta kalleshi ba ta rubuta sunan topic din snn ta sake juyawa tana facing class din...a nutse ta fara musu bayanin Endocrine system tun daga introduction... gaba daya class din sunyi tsit suna sauraronta kuma suna fuskanta sosai dan dama ba yanxu suka fara jin lectures dinta ba...mostly ko tutorials zasuyi itake musu explanation...shi kam Sir Abdool kallonta kawai yake ful of love and affection..he loves this girl to the core..he loves her more than he could say...yanxun da yake sauraron lectures dinta sai yaji koshi bai zama lallai ya iya musu bayani haka ba..she really is intelligent..she is a genius shiyasa kullum sonta yake karuwa cikin ranshi har yakejin kmr heart dinshi zai fashe...he feel like yaje yayi hugging nata right now amma he won't dare...ita kuma Aysha explanation dinta takeyi sosai...komai saida ta fito musu dashi snn ta kammala kafin ta juya gareshi tace"Sir mun gama"..baice komai ba sai hands dinshi daya daga ya shiga clapping mata idanunshi a kanta nan kowa ya shiga tafa mata dan da gaske tayi kokari sosai...saida suka gama clapping din yace taje ta zauna...ba musu ta tafi ta zauna shi kuma ya taso yana tambayan if akwai mai tambaya sukace babu nan yayi musu sallama bayan yace suyi submitting assignment daya basu wa class rep ita kuma ta kai mishi office...yana barin class din suka fara tsokanarta wasu na fadin salon love dinsu da sir Abdool na burgesu wasu kuma na cewa kawai tayi accepting love dinshi dan sun dace da juna...itadai bata cema kowa komai ba ta tattara assignments din nasu ta tafi office dinshi...tana kai mishi bata tsaya ya jata da long story ba tace mishi zataje office din provost kan issue din Reproductive Health Lecturer dinsu data tafi maternity leave..haka nan ya hakura ya barta ta tafi ba dan ya gaji da ganinta ba..yasan ko zasu kwana nan yana kallonta bazai taba gajiyawa ba. Direct daga office din Sir Abdool ta wuce Office din Provost...bata samu secretary dinshi a wurin ba dan haka kai tsaye ta tura office din ta shiga da sallama...suna zaune kan sofa shi da Bobby suna mgn and bisa ga dukkan alamu important issue suke discussing... a tare suka juyo suna kallonta...idanu Nur ya dan ware yana kallonta with a broad smile kan face dinshi yace"ohh Lamido it's you?.."dan murmushin itama ta saki tana gyada kai tace"nice sir..sorry i banged in without permission secretary din ce bata nan"...saida ya mike daga inda yake ya koma seat dinshi ya zauna still yana murmushi yace mata"with or without permission you are always welcomed here so you don't have to apologize"...gajeren smile ta kara saki kai a kasa tace"thank you sir"...baice mata komai ba sai ma relaxing da yayi kan seat dinshi yana kallonta...tun daga kan legs dinta dake sanye da black cover shoe daketa shinning as a result of polish da yasha...zuwa pencil trouser da well shaped riganta daya tsaya iya guiwanta...shape dinta sai ya fito yayi daidai a cikin rigan dama gashi sai daukan ido suke sbd iron...a hankali ya gangaro da idanun zuwa chest dinta dake nan rabi a waje rabi kuma rufe da mini hijab sai kuma beautiful face dinta da yafi komai daukan hankalin mutane game da ita...dan bakinta data shafama lip balm sai kuma glasses dinta da yayi daidai da dogon hancinta...sai gashin goshinta zuwa sajenta da suke nan a kwance kasancewar babu hula ko dankwali a kanta...tunda ya fara kallonta dama tayi kasa da kanta bata dago ba tanadai jin yanda idanun ke yawo a jikinta...saida ya gaji da kallon nata dan kanshi yace"Bismillah mana"..ba tayi musu ba ta kara taking two steps zuwa gaban table dinshi ta tsaya...sai kuma ta juya a hankali tana facing inda Bobby daya maidasu invisible yake zaune tace"Good Morning Sir"...ko kallon inda take baiyi ba ballantana tasa rai zai amsa mata...gaba daya hankalinshi na kan wayanshi dake hannunshi...wani irin kullutu taji yazo ya tokare mata a wuya...tunda take baa taba humiliating dinta kmr haka ba...lokaci guda wasu zafafan hawaye suka ciko idanunta amma bata bari sun zubo ba tayi kokari ta maidasu snn ta sake juyawa tana facing provost idonta a kasa tace"Sir it's about miss Ayuba"...shima jikinshi a sanyaye dan baiji dadin abun da Bobby yayi mata ba yace"Ita ke daukanku reproductive health koh?.."kai kawai ta iya daga mishi...ya sauke numfashi yace"have you tried talking to Umar about it?."still kanta kasa tace"i did sir and unfortunately yanada lots of classes da yake taking"...shiru sukayi na wani lokaci kafin Nur yayi breaking silence din da fadin"ohk yanxu abunda zaayi kiyi amfani da course outline ko tutorials ne ki fara musu before i see what to do..inshaAllah zuwa Monday zaa san yanda zaayi"..kai ta sake gyada mishi smn ta juya zata fita daga office din yayi kasa da voice dinshi sosai yana kallon bayanta yace"Lamido kiyi hakuri kinji?.."nan ma kan ta sake gyadawa snn ta fita a office din...tana fita Bobby ya dago big idanunshi yana dubanshi rai a bace yace"laifin me akayi da kake bata hakuri?.."shiru kawai Nur yayi yana kallonshi dan yasan idan sukaja mgnr da nisa ransu ne zaizo yana baci...yasan Bobby da bala'i dan haka bazai kulashi ba amma yasan exactly yanda zaiyi maganinshi...dan haka sai ya mike daga inda yake tareda komawa kusa dashi ya zauna yana dubanshi da wani murmushi yace"babu laifin da akayi mata Sir.. ina bata hakuri ne sbd complain da tazo min dashi..yanxun ya kake ganin zaayi?..for almost three weeks knn babu mai daukansu reproductive health shi Umar aiyuka sun mishi yawa ita kuma miss ayuba ta tafi hutun haihuwa"..saida ya dan tabe baki before yace"sai kasa a nemo wanda kake ganin zai iya muyi employing dinshi"...kamo hannunshi Nur yayi still looking at him yace"but that is a long process..dole muna bukatan someone to take over kafin mu dauki wani"...a fusace ya kwace hannunshi tareda fadin"ai kaine provost so it's your responsibility ka nemi wanda zai taimaka musu bani ba"...gyara zama Nur yayi yace"amma kasan course din is a very sensitive course koh..dole ba ko wane zai iya daukanshi ba"..banza Bobby yayi dashi as shi baiga abun wani tayar da hankali a nan ba amma Nur yana neman yayi complicating things...ganin yanda yayi wani watsi dashi sai ya dan kautar da kanshi ya saki wani murmushi kafin ya sake juyawa yana duban Bobby da wani kalan tausayi a fuskanshi yace"ko kai zaka taimaka ka daukesu please?.."kallon are you alright Bobby ya bishi dashi tareda fadin"are you kidding me?.."girgiza kai Nur ya shiga yi yana cewa"wlh am not kidding Bobby da gaske nake..taimakawa fa nace kayi dan Allah"...tun kafin ya rufe baki Bobby ya saki hadadden tsaki yana binshi da digusting look yace"like are you serious?.. are you even listening to yourself?.."kamo hannunshi Nut yayi yana sake sassauta muryanshi kaman wanda yake gaban surukai yace"Bobby take it easy plss...taimako ne fa kawai zakayi please!"...sake fizge hannunshi yayi looking furious yace"and who told you ina son yin irin wnn taimakon?..na taba fada maka ne?..look if you dare say another word kan wnn issue wallahil azeem you'll see the devil side of me..haka nan sai inje class dinsu ince zan koyar dasu ko na taba fada maka ina shaawan lecturing ne?..of course i don't sbd haka mu bar mgnr haka indai ba so kake duk ranmu ya baci ba"...shiru Nur yayi for some minutse kaman bazaiyi mgn ba sai can yace"nasan you can do it..just think about it please"..bai rufe baki ba Bobby yace"you are also a medical doctor so duk abunda kake ganin zan iya kaima you can do it so just go ahead and do it ka dena damuna please"..ya karasa mgnr yana hade hands dinshi waje daya alaman begging...Nur bai sake cew komai ba kawai ya tsaya yana kallonshi...he's thinking of a way to convince him amma ya rasa...shi kuwa Bobby mikewa yayi a fusace zai fita daga office din Nur yace"yanxun ni ka watsa ma qasa a ido koh?.."ba tareda ya dakata da tafiyarshi ba yace"are you Mummy da bazan watsa maka qasa a ido ba?.."daga haka ya fice abunshi...shi kuwa Nuru wara idanuwa yayi sosai yana kallon hanyar da Bobbyn yabi yana sakin wani dan iskan smile yace"why didn't i think of this before?.."sai kuma ya kwashe da daria hadda tafa hands dinshi yace"Dr.Bobby you shouldn't have mentioned Mummy's name..now i know exactly how to force you"ya karasa yana sake fashewa da daria sai kace mara hankali...shi sam tunanin ya hadashi da Mummy bai zo mishi ba sai daya ambaci sunanta...yanxun kam yasan dole idan yayi mgn da ita zata sashi yayi ko yanaso ko bayaso..jingina kanshi yayi da kujera yana wani shafa gashin kanshi yace"what a brilliant plan!..Dr.Nuru kanka yana ja sosai wlh..Allah ya kaimu anjima". Ga masu tambayan ko zasu iya turamin kati your answer is no plss...bana amsan kati amma ko wurin masu pos kukaje zasuyi maku transfer..thank you all.❤️ Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank sai a tura evidence of payment through 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 05 Kai tsaye office dinshi ya wuce yanata faman tsaki domin har cikin zuciyarshi wani tukuki yakeji..a zahirin gaskia ba iya mgnr da Nur ya fada ne ya bata ranshi kadai ba hadda wnn yarinyar Lamido take ko Gidado...last time daya ganta a clinic sam ba wani tsayawa yayi ya kalleta ba amma dazu despite baya so saida ya kare mata kallo tsaf..kuma a iya kallon da yayi mata ya tabbatar da ta hada jini da fulani...shi sai yanxu ma ya tuna Nur ya taba fada mishi cewar 'yar Gombe ce...lokaci daya yaji gaba daya tsanar yarinyar ya samu matsuguni a zuciyarshi...da yasan bafulatana ce kuma 'yar Gombe da babu dalilinda zaisa ya dauki hannunshi mai daraja yayi mata allura dashi sbd gaba daya Fulani basuyi deserving help ko kuma pity dinshi ba a rayuwa...they are all not worthy of his kindness especially wanda suka fito daga Gombe ya tsanesu..ya tsanesu fiyeda komai..baisan meyasa ganin yarinyar kadai ya dawo mishi da abubuwan da suka faru tsakaninsu da dangin mahaifinsu ba...baisan meyasa tun farkon ganinshi da ita baiyi realising cewa bafulatana bace kuma 'yar Gombe ba har saida yayi mata allura...ya dafe kanshi yasan har abada da ciwon wnn abun zai mutu...yanada riko a rayuwa shiyasa har yanxun ya kasa mance abubuwan da suka faru tsakaninsu da 'yan uwan daddy kimanin shekaru biyar da suka wuce...sam baiji dadin taimakon da yayi mata ba kuma da ace yasan 'yan Gombe zasuzo su cika mashi makaranta da baiyi attempting bude makarantan bama at the first place..haka kuma da yanada damar da zaiyi banning 'yan Gombe and all Fulani from studying at his college da yayi hakan saidai it can never be possible...wnn yarinyan kuwa ji yake kaman yaje ya korata this instant ta bar mashi college dinshi...duk zuciyarshi ta cunkushe ga kuma takaicin da Nuruddeen ya sake dirka mashi duk sun taru suna barazanar fasa mashi zuciya..a fili ya furta"the fool..har wani tunani yake ni inje in zama lecturer dinsu..what nonsense!.."ya karasa mgnr yana dukan table dake gabanshi...haka dai ya karasa yini ranan bai tsinana uwar komi ba a office din...one nayi ya shiga toilet dinshi yayo alwala snn ya fita dan zuwa sallahn jumu'a...driver ya bude mishi kofa ya shiga shima ya zagaya ya shiga saidai kafin ya tayar da motar Nur ya fado cikinta da wani irin sauri kaman wanda aka biyoshi...Bobby bai ce mishi komai sai dan tsaki daya saki tareda kawar da kanshi gefe..shi kuma Nur ya saki hadadden murmushi yana kallonshi yace"i don't mind having a drive with my friend"...da sauri Bobby ya juyo yana kallonshi shima fuska tamke yace"well am not going for a drive as you can see..am going for prayer.. jumu'at prayer sbd haka get out of my car immediately"..kara sakin wani smile Nur yayi yana wani shafa gemunshi yace"i still don't mind going for prayer with my friend and we better get going idan bakaso muyi latti"..tsaki Bobby ya saki yana sakan mishi wani harara murya can kasa yanda driver bazai jiba yace"Fool"..da sauri Nur yace"godia nake my friend..i love you too"..watsa mishi harara kawai Bobby yayi tareda dauke kanshi dan yaga alama idan yaci gabada biyema Nur zai maidashi mahaukaci ne a gaban driver dinshi...shi kuwa Nuru murmushin cin nasara ya kara saki cikin ranshi yace"zakaga rashin mutunchi ai..badai Lamido kayima wulakanci ba dazun?.."tayar da motar driver yayi suka fita daga makarantar...koda suka isa masallacin saida Nur ya sake dirka mashi wani abun haushin..kallon suit dake jikinshi yayi sai ya dan saki tsaki yana girgiza kai yace"yau Friday dinma mutum bazai sa manyan kaya ba..some people need to grow up wlh..basu ajiye komai ba sai shegen zafin rai"...ko kallon inda yake Bobby baiyi ba amma ya shaka iya shaka.😂 Karfe biyu daidai suka baro masallaci...Bobby ba tareda ya dubi Nur dake zaune gefenshi ba yace"a ina zamuyi dropping dinka kasan ba komawa college zanyi ba ni..am going home"..da fara'a Nuru yace"don't worry muje gidan..dama mun kwana biyu bamu gaisa da Mummy ba"..Bobby bai sake yi mishi mgn ba har suka karasa gida...driver na gama parking ko jira ya fito ya bude mishi motan baiyi ba ya bude ya fita abunshi..shi kuma ya dauko briefcase dinshi yabishi a baya...shima Nur fitowa yayi zuwa cikin gidan yana daria kasa kasa gamida girgiza kai dan masifar Bobby daria yake bashi wlh...babu kowa central palor as usual suka wuce parlon Mummy...tana zaune da wasu yammata guda biyu da kallo daya Bobby yayi musu ya wani sake tamke fuska...a hankali ya karasa kusada Mummy ya zauna yanata wani basarwa cikin igbo yace"mummy sannu da gida"...tana murmushi tace"sannu Bobby ya aiki?.."can kasa kasa yace"fine.."Mummy ta maida dubanta ga Nuruddeen daya karaso shima ya zauna kusada Bobby tace"yau an tuna damu knn Nuru"..murmushi yake ya shiga shafa kanshi yace"wlh aiki ne kemin yawa Mummy...duk Bobby ya gama sakar min komai ko taimaka min bayayi"..girgiza kai kawai Mummy tayi tace"to ya aikin?..yasu Mom dinka?.."yace"duk suna lafia Mummy..ina auta?.."tace"auta bai dade da fita ba wai zasuje dubiyan wani abokinsu"..gyada kai Nur yayi alaman gamsuwa...sai yanxu yammatan dake zaune suka samu daman gaishesu...Nur kadai ne ya amsa Bobby kam saima sake tamke fuska da yayi...kallonshi Mummy tayi tace"Bobby bakaga Rayhan bane?.."fuskan nan ba sarari yace"na ganta Mummy"..tace"kuma baka iya amsa gaisuwa ba koh?.."a karkace ya juya yana kallon inda suke murya a dakile yace"lafia lau"..daga haka ya mike ya kama hanyar flat dinshi Mummy ta bishi da kallo kawai tana girgiza kai..cikin ranta take cewa"Ya Allah ka shiryamin Bobby"...shima Nur mikewa yayi yana duban Mummy yace"Mummy bari in shiga ciki"..kai kawai ta iya daga mishi dan Bobby ba karamin sanyayar mata da jiki yayi ba..ya juya kenan zai tafi aunty sumy da Miemie suka shigo parlon suma...dakatawa yayi da tafiyar tareda wara idanu sosai akan Miemie yace"hey pretty!.."murmushi ta saki itama ta karasa kusa dashi tace"Uncle Nur good evening"yace"evening pretty how are you..how was school?.."tace"Alhamdulillah"...juyawa yayi ga aunty sumy da har ta karasa kusa dasu Mummy ya wani daga hannunshi alamar salute yace"Allah ya taimaki babbar yaya..barka da rana"..aunty sumy na daria tace"barka dai Nur kwana biyu..ya aiki"..yace"normal normal aunty ya naki aikin?.."dan tabe baki tayi kafin tace" babu dadi wlh..duk Bobby ya sakar min komai ni kadai"..daria ya saki yace"nima haka nake fama dashi aunty..saidai hakuri kawai"..yana rufe baki Mummy tace"to ka wuce ka tafi Miemie zata kawo maku abinci yanxun nan"..bai sake mgn ba kuwa ya kama hanyar flat din Bobby...itama aunty sumy mikewa tayi bayan sun gaisa da baqin Mummy ta kama hanyar nata flat din itama...Miemie kuma Mummy tace taje ta cire uniform sai ta kai musu abinci...ba musu ta juya itama zuwa flat din mamanta. Yana shiga ya fada bathroom ko kayan jikinshi ma sai a bathroom din ya ciresu...ruwan sanyi sosai ya sakar ma kanshi wai ko zai samu yaje inda yake son yaje wala'alla ya samu saukin abunda yakeji amma inaa...shi abubuwan ma sun mishi yawa baisan da wanne ya kamata yaji ba..na farko waccan bafulatanar yarinyar da yakejin ya tsaneta sama da komai a dunia...sai kuma Nur da kalan iskancin da yayi koma yake kan yi mishi..yanxu kuma ga wnn jarababbiyar yarinyar itama tazo zata kara mashi akan wanda yake ciki already...shi ya rasa wnn masifa da bazata hakura ta kyaleshi ba tunda tasan ba sonta yakeyi ba..wlh ko yanada niyyar yin soyayya baiga dalilinda zai sashi kula mace marar class irin wnn ba..ace mace kaman chewing gum sai nanikewa kike ana koranki amma bazaki hakura ba..wnn wace irin rayuwa ce?. Koda Nuru ya shigo yanajin alaman yana bathroom sai ya nemi kan sofa ya zauna yana pressing wayarshi...after like 7 minutes Bobby ya fito daure da towel a waist dinshi...dagowa Nur yayi yana kallon pure white skin dinshi da ruwa ke tsere akai as result of wankan da yayi snn ya saki wani murmushi...murya can kasa ya furta"what a hottie!.."sarai Bobby yaji abunda ya fada amma bai kulashi ba ya karasa gaban mirror ya fara shafa cream dinshi...shima Nur sake juyawa yayi yana facing inda yake hadda su yin tagumi yana cigaba da kallonshi...kawai ayyana baiwar kyau da Allah yayi mishi yake...gani yake kaman Bobby is the most cutest and hottest guy alive...baisan why ba amma shi kam kyawunshi na burgeshi sosai...cikin ranshi yake ayyana idan shi da yake namiji yana admiring kyawun Bobby yammata kuwa ai kilan sai sunyi hauka akanshi cox yanada wani irin kyau da a kallon farko zaka fahimci hakan...ko dan kasancewarshi ruwa biyu ne oho?..dama ai ance duk dunia babu wanda yakai halfcast kyau so maybe shiyasa duk yan gidansu Bobby keda kyau tunda Mom dinsu igbo ce Daddy kuma Fulani...ta cikin mirror Bobby yaga yanda Nur ya sake juyowa yana zuba mishi ido kaman wanda bai sanshi ba dan haka ya dan saki tsaki tareda juyawa yana dubanshi yace"malam what is the look for?..haka nan ka kafa min ido kana starring..are you sick?.."numfashi Nur ya saki tareda sauke hannunshi daga tagumin da yayi before saying"kawai ina kallon hottie ne...the only cute and sexy man around..guy ba dole yammata suyita hauka kanka ba..ga Rayhan can ma tunda na ganta nasan zuwa tayi kuyi zance"...wani kululun baqin ciki yaji ya sake tokareshi just by mentioning Rayhan's name...Goodness he hates that girl with passion...he hates her like hell and not only Rayhan he hates duk matan dake kawo mishi kansu...he hates classless women...sbd tsabar baqin ciki ma kasa cewa komai yayi kawai ya juya zuwa closet dinshi ya shiga ciki ya sako white crazy jean da wata black polo snn ya fito fuskan nan ba fus...gefen bed dinshi ya zauna ya dauki wayanshi knn Miemie ta shigo dakin rikeda tray da aka dora transparent glass jug mai daukeda pineapple juice a ciki...kan dan table dake tsakiyan sofas din ta ajiye snn ta mike...tun kafin ta juya Bobby ya daka mata wani tsawa"Miemie bakida hankali koh?..kina hauka zaki shigomin bedroom without my permission?.. "jikinta har ya dauki rawa tace" Uncle Bobby nayi sallama f.."bai bari ta karasa ba ya shiga nuna mata kofa yace"leave immediately"...ba musu ta juya tana turo baki ta fita daga dakin...Nur ya juya yana dubanshi yace"kaidai bakayi ba wlh...baka ajiye komai ba sai shegen masifa mara amfani"...ya bude baki zaiyi mgn aka sake turo kofan dakin wnn karon Rayhan ce ta shigo daukeda tray din abinci...wani azababben zafi yaji ya faraji all over his body kaman ba yanxun ya fito daga wanka ba...like how dare this girl enter his bedroom like this...how dare she...Nur na ganin yanda yanayinshi ya sauya ya saki murmushi cikin ranshi yace"Allah ya kara"..a fili kuma kallon Rayhan data ajiye trayn hannunta yayi yace"sannu da aiki fa"..tana murmushi ta daga mishi kai...shi kuma ya mike yayi pouring juice da Miemie ta shigo dashi a cup snn ya fita palor yana sipping juice din yace"bari in baku space"...Bobby ya bishi da wani uban harara kaman idanunshi zasu fado kasa...idanuwan Rayhan a kanshi kaman zata cinyeshi itama...bata taba ganin wanda harara yayi mishi kyau kaman shi ba...rai a bace ya juyo da idanunshi gareta voice dinshi har bai fita sosai sbd bacin ran da yake ciki yace"how dare you?..how dare you enter my bedroom without my permission?.."a hankali tace"am sorry..Mummy tace in kawo maka abinci"..tun kafin ta karasa yace"Mummy tace ki kawo ko kuma kikace zaki kawo..wato bazaki fita harkana ba koh?.."a hankali tace"bazan iya fita harkanka ba because i love you"...daga mata hannunshi yayi yana fadin"hold it there...wai how many times do i have to push you away ne?..don't you get tired?.."nan da nan hawaye ya kawo idanunta tace"Uncle Bobby please!..wlh i love y.."still bai bari takai karshe ba yace"who's ur uncle anan?..stop calling me that am not ur Uncle"..ya karasa mgn yana kawar da kanshi daga gareta kaman wanda yaga poopoo...baisan why duk ta ce mishi Uncle Bobby yakejin wani iri ba...duk Miemie ce ta cuceshi tasa mishi wnn sunan shknn yanxu kowa ke kiranshi haka...hatta Sab da yake brother dinshi shima ta koya mishi kiranshi da Uncle Bobby and now wnn super glue din ma ta kama...hannu Rayhan takai ta goge tears dinta...wlh da tanada yanda zatayi ta cireshi daga ranta da tayi ko don sbd wulakancin da yake mata amma bazata iyaba ita kanta ta sani...mikewa tayi bayan ta gama wiping tears din nata tace"zan tafi..amma dan Allah Uncle Bobby ka dinga picking call dina ko sau daya ne a rana please"...baice mata komai ba sai kanshi daya daga ita kuma ta juya a hankali ta fita tana cigaba da share hawaye...Nuru na ganin ta fita ya dawo dakin rikeda empty cup daya shanye juice din ciki...kai tsaye warmers data shigo dasu ya shiga budewa kobi takan Oga Bobby baiyi ba...ya wani lumshe ido yana smelling aroma din abincin hadda su girgiza kai...serving kanshi yayi ya fara cin abincin...su Uncle Bobby dai har yanxun ana zaune dafe da kai feeling extra hot inside. Saida Dr Nuru ya gama cinye abincinshi tas ya kora da juice snn ya dawo da hankalinshi kan Bobby da har yanxun ke zaune kaman statue yace"Man if bakaci abincin nan ba kayi missing wlh..na tabbata wnn handwork din Mummy ne for the food taste good"...banza Bobby yayi dashi dan abunda ya dameshi ma ya isheshi...shi kuwa Nur ya sake zuba juice dinshi a cup snn ya mike yana sipping abunshi ya fita daga dakin...parlon Mummy ya koma ya samu tana sallama dasu Rayhan zasu tafi sai Miemie dake zaune dinning tana cin abinci...karasawa yayi ciki shima ya zauna idanunshi kan Miemie kafin Mummy ta dawo cikin parlon itama...Nur ya gyara zama yana fuskantarta yace"Mummy karan abokina na kawo fa"...juyawa itama tayi gareshi tace"wai Bobby?..meya hadaku kuma?.."saida ya sauke ajiyar zuciya snn yace"akan college ne wlh...malamar da take daukan reproductive health ne ta tafi maternity leave and su biyu dama mukeda a wnn bangaren shi kuma Umar yanada classes da yawa da yake attending shine nace Bobby ya taimaka ya danyi covering yaran ko na 1 week ne before we employ new staff amma sam yace bazaiyi ba..that shi ba lecturer bane kuma Mummy na tabbata ba wanda zai iya koyar dasu kamanshi tunda field dinshi ne amma yaki amincewa and in the next 3 to 4 weeks students zasu fara exam bansan me yakeso su rubuta a course dinba tunda duk wnn semester baifi lectures din 1 month suka samu ba shine naga i have to talk to you ko zakiyi mishi mgn ya taimaka musu plss"...if you see yanda ya karashe mgnr da wani puppy eyes zakayi tunanin mutumin kwarai ne😂Mummy na gama sauraranshi tace"amma Bobby bai kyauta ba gaskia..don't worry zanyi mgn dashi ai bai kamata a bar students a haka sunata wasting time dinsu a banza ba..i'll speak to him"...Mummy na fadin haka ya saki wani murmushi yana shafa kanshi yace"yauwa Mummy thank you...thank you sosai"...murmushi itama tayi tareda gyada mishi kai...Aunty Sumy ta shigo parlon sanyeda dogon riga mara nauyi da alama tayi wanka ne...ta karaso ciki ta zauna tareda umartan Miemie data kawo mata abinci...ba musu ta mike zuwa kitchen tunda ta gama cin nata already...zubowa tayi ta kawo mata snn ta nemi wuri ta zaune kusada Mummy...Aunty Sumy data fara cin abincin tace"Mummy yanxu mukai waya da Hafsa tace zasu dawoda Ilham gobe"...Mummy na gyada kai tace"to Allah ya kaimu goben..nasan da kyar idan ba halin nata tayi musu ba tunda zasu dawo da ita da wuri"...Aunty Sumy tace"nima nayi tunanin haka..ai tama dade wnn karon yau satinta daya fa"...sauke ajiyar zuciya Mummy tayi kafin ta sake fadin"Allah ya kaimu goben toh"..Aunty Sumy tace"Ameen"...Miemie da har yanxun ke zaune kusada Mummy tace"Allah ya kaimu dama na matsu ta dawo wlh..duk gidan ba dadi idan bata nan"..murmushi Nur yayi yana kallonta yace"to mai 'yar uwa"..murmushin itama kawai tayi mishi..shi kuma ya sake kafa idanu a kanta..yarinyar na burgeshi sosai...ana haka Sabeer ma ya shigo parlon sanyeda yadi milk...dogo ne sosai shima dan kusan tsayinsu iri daya dana Bobby saidai Bobby yafishi da kadan...kai tsaye jikin Mummy yayi masauki yana wani kwabe fuskanshi kaman dan yaye yace"Mummy yunwa"..shafa cikinshi Mummy tayi tace"shiyasa nace ka tsayi kaci abinci kafin ka fita amma kaki...nasan ba abincin waje kake iya ci ba..Miemie tashi ki kawo mai abinci"..ta karasa mgnr referring to Miemie dake zaune...batayi musu ba ta mike zuwa kitchen tana kunkuni...itafa ta dena kula Uncle Sab a gidan nan sun kasa fahimta...Nur da yaga yanda Sabeer ke sake lafewa jikin Mummy sai ya saki daria yana fadin"haba Oga ASP da girmanka?..irin wnn shagwaba ai na civilians ne irinmu mu bana officers ba"...cikeda yar kunya ya dago daga jikin Mummyn yana wani shafa kanshi yace"Uncle Nur barka da zuwa..ashe kana nan wlh ban lura da kai ba"...Nuru na girgiza kanshi yace"dama ya zaayi ka lura dani Sab kana irin wnn shagwaba haka..wai kai auta koh?.."daria kawai Sab yayi yana sunkuyar da kai...Miemie ta dawo da abincin nashi ta ajiye tana kokarin zaunawa yace"Mummy kinga bata kawomun spoon ba kuma idan na gama ci wane ruwa takeso nasha?.."kafin ma Mummy tayi mgn Aunty Sumy tabi Miemie da wani kallo tace"haka ake kawo abinci?.."dan turo baki tayi tace"shine fa dazu da safe hadda cemin skeleton"...a fusace Aunty ta sake cewa"sbd ya fada maki haka shine zaki rama yanxu koh?..wai yaushe kika raina Sab ne haka a gidan nan?..abokin wasanki ne shi?.."bata ce mata komai ba sai mikewa da tayi zuwa kitchen da dauko spoon din hade da ruwa ta kawo mishi..ya faki idon su Mummy yayi mata gwalo ita kuma ta kwabe fuska tana duban Mamanta tace"Aunty kinga yanamin daria koh?.."tsaki Aunty Sumy ta saki tareda tura mata plate data gama cin abinci dashi tace"C'mon dauka ki kai kitchen"...da gudu ta mike ta dauki plate din tayi kitchen...tana ajiyewa ta sake fitowa a guje tayi dakinta rai duk a bace kaman zatasa kuka...Mummy ta bita da kallo tana girgiza kai...ta fuskanci wnn rigiman nasu hali ne a kokon rai dole sai sunyi shi...hakan kuma baya hana duk daya baya nan dayan yayita kewar dayan ba...dan ma akwai Bobby da suke tsoro ai da kilan rikicin nasu sai yafi haka. inaso inyi muku wani dan sanarwa plss...wata tamin dm jiya waita biya kudi bansata a group ba kuma nidai baki ta turawa kudinta ba...you people should take note plss...Vip groups dina guda biyu ne kawai daga Dr.Bobby VIPs(a) sai (b) duk wani group apart from wnn ba nawa bane...and ku dinga kula ta wnn number dake kasa kadai zaku sameni kuma dashi zanyi adding dinku a group so dan Allah a kiyaye🙏🏻 Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank.. Sai a tura evidence of payment through 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 06 Suna zaune Bobby ya shigo rikeda waya a hannunshi kai tsaye ya karaso ciki tareda mikama Aunty Sumy wayan yace"Its your call"...ba musu tasa hannu ta amsa wayan tareda karawa kunnenta tayi sallama...a daya bangaren Hafsa tace"wa'alaiki salam Maman Miemie..inata kiran wayanki no answer shine nace bari inyi trying na Bobby in gani sai gashi kuma ya shiga..Ilham ce ta dameni wai tanason mgn daku"..Aunty Sumy ta dan saki murmushi tace"oh Hafsa wai kece?..dama kinada Number Bobby knn?.."Hafsa tace"bani dashi wlh Ilham din ce ta bani wai tunda naki baki dauka shi a kirashi..gata kuyi mgn"..daga haka ta mikama ilham dake zaune kusada ita wayan...yarinyan da bazata haura 8 to 9 years ba ta amsa wayan full of happines tace"Auntyyy"..aunty sumy ta saki daria jin yanda taja sunan nata tace"na'am 'yar gidan aunty ya kike?.."tace"am fine aunty just missing you..i want to come back home"..aunty sumy tace"hope dai ba rigima kikema aunty hafsa ba koh?.."tace"bana rigima aunty kullum sai mun fita yawo..yau ma saida aka kaimu shopping dasu fadeel"..aunty sumy tace"inyee 'yan gidan aunty hafsa..ilham banda fitina kinji?..kuma banda kiriniya banda sa aunty hafsa magana"...daria ta saki sosai kaman wata babba tace"aunty i want to speak to everyone please..where is my Uncle Bobby?.."Aunty sumy tayi putting nata on speaker snn tace"your uncle bobby is here"..cikin excitement ilham tace"my uncle bobby"..yace"yes my mummy how are you?.."tace"am fine uncle bobby ya aiki?.."yace"aiki fine ilham gobe zaki dawo ba?.."tace"yes..kasan me na siyo muku daxu da mukaje shopping?.."yace"sai kin fada mummy"..suna jin yanda ta danyi kasa da murya snn tace"na siyo maka cheesy na siyoma uncle sab sweet na siyoma yaya chocolate snn na siyoma Mummy da aunty biscuits"..dan bata rai Bobby yayi yace" seriously ilham?..of all abubuwan dake wajen ki rasa abunda zaki siyomin sai cheesy?.."daria ta saki sosai tace"to ba kace min kana son cheesy ba..shknn zan sake maka wani yanxu ka bama Mummy da uncle sab muyi mgn"..bai sake mgn ba ya mikama Mummy wayan..nan ma hira suka sha sosai sai kace wata babba snn sab ya karba shima aka sha hiran dashi...miemie ce karshe aka kai mata wayan har daki nan ma suka dora daga inda suka tsaya...Bobby na duban Mummy in a serious tone yace"Mummy nidai kada a sake bari wani daga cikin mutanen nan yazo yace zai dauki yaran nan bana so wlh..after duk abubuwan da suka yi mana yanxub zasu ringa wani zagayowa suna daukan yara sbd mu yadda dasu?.."girgiza kai Mummy tace"kaidai ka fiya riko wlh Bobby..baka manta abu komai qanqantarshi...abun daya faru ya riga ya faru saidai a kiyaye gaba"..aunty sumy tace"kuma Mummy duk abubuwan da suka faru babu ruwan hafsa a ciki..lokacin ma tana england komai ya faru so bazan iya hanata ba muddin ta nuna tanason daukansu koba komai qanwar mahaifinsu ce"..wani kallo Bobby yayi mata yace"sbd tana qanwar mahaifinsu bashi zai daman zuwa koda yaushe tace zata daukesu ba..idan abun da gaske ne meyasa shi baban nasu ya kasa nemansu duk tsayin wadan nan shekarun sai ita?.."dafe goshi kawai Mummy tayi dan tasan kome zaa fada bazai yadda ba tunda ya riga ya dauki zafi haka...itama aunty sumy sanin halinshi yasa taja bakinta ta tsuke tunda it's of no use trying to explain things to him bazai taba fahimta ba..ya mike zai koma flat dinshi Mummy ta kira sunanshi...ba musu ya dawo ya zauna yana fuskantarta...itama tana dubanshi tace"wane magana kukayi da Nuru dazu kace bazaka iyaba?.."da sauri ya kalli Nur da yayi wani kasa da kai sai kace mutumin kirki...wato ma karanshi yazo ya kawowa Mummy sbd yasan ita kadai zata iya mishi dole koh...rai a dan bace Mummy tace"bada Bobby nake mgn bane?.."a hankali yace"Mummy lecturing fa yakeso inje inyi..sbd Allah Mummy ta ina zan wani fara shiga class ince zanyi lecture bayan ba tabayi nayi ba..idan tsakani da Allah ne shi meya hana bazai je ya koya musu da kanshi ba"..yana rufe baki Nur yace"amma kasan da field dina ne ba abunda zaisa ma in tambayeka sbd nasan 6atamun lokaci zakayi..kaine gynaecologist dan haka kai ya kamata ka koya musu ba ni ba"...wani irin daci yaji yana taso mishi tun daga throat dinshi zuwa bakinshi..gaba daya sai ya zama speechless a wurin..nan take Mummy tace yaje ya taimaka musu koda na one or two days ne...as usual ya amsa mata da toh snn ya mike zuwa flat dinshi...Nur ya bishi da kallo yana kunshe daria...sallama yayi dasu Mummy snn ya mike zuwa flat din Bobby ya sameshi kwance kan three seater a parlor idanunshi lumshe yayi pillow da hannayenshi...murmushi ya saki tareda sunkuyawa saitin kunnenshi yace"this is your punishment for making Lamido cry"...Bobby da yaji mgnr kaman daga sama baisan lokacinda ya mike zaune da sauri yana kallonshi ba...mamaki ne karara a fuskanshi jin abunda yace...shi kuwa Nur juyawa yayi ya fita daga parlon yana daria kasa kasa yasan yanxu komai taurin kanshi dole yayi abunda yakeso tunda Mummy tasa baki...Bobby kam sbd tsabar takaici baisan time daya dunkule hannunshi tareda naushin kujeran da yake kai ba yana fadin"Fuck you Nur". Har washegari Saturday ranshi bai dena 6aci kan abunda Nur yayi mishi ba..neman hanyan da zai rama kawai yake amma ya rasa...mikewa yayi daga karshe ya bude wata kofa ta cikin parlonshi sai gashi wajen wani tafkeken swimming pool daga gefenshi kuma gymnasium dinshi ne daya cikashi taf da kayan motsa jiki...kai tsaye gym din ya nufa dan a al'adanshi every Saturday and Sunday sai yayi training kafin yayi komai dan haka yana shiga ya fara training dinshi...ya 6ata lokaci sosai yanayi dan bai baro gym din ba sai da ya hada gumi sharkaf snn ya bude fridge dake ciki ya dauki chilled water ya bude yasha snn ya fito daga gym din yana cigaba da sipping a hankali...direct bedroom dinshi ya wuce bai kobi takan wayanshi da yaga yana haske ba ya fada bathroom...wanka yayi a tsanake snn ya fito yana goge jiki da towel..ya isa gaban mirror yayo shafe shafenshi snn ya shiga closet dinshi ya sako kaya ya fito snn ya isa ga wayanshi da har yanxu bai dene haske ba alamun ana kira knn...missed calls ya gani har 8 biyu na wata Nurse dake Hospital dinshi,biyu na Nuru sai ragowan hudun kuma gaba daya na Rayhan ne...baibi ta kan natan ba ya fara kiran Nurse din..bayan sun gaisa tace"Sir dama da akwai emergency ne kuma Dr Isaac baya nan"..yace"doc Vivian fa?.."tace "itama bata nan Sir".. kmr bazaiyi mgn sai daga baya kuma yace"alright i will be coming".. ta amsa da" ohk sir"..snn ta kashe wayan...suna gamawa ya shiga kiran Nur shima bai dade yana ringing ba yayi picking yana fadin"Bob ina ka shiga naketa kira baka picking?.."ba tareda ya bashi amsan tambayan ba yace"what's the call for?.."da sauri Nur yace"wlh yanxun ake kirana daga Hostel wai wuta tayi spark a wani apartment kuma baa san me yayi causing ba shine naga ya kamata muje mu duba to make sure ba wani babban matsala bane"..shiru Bobby yayi yana sararonshi har ya gama snn yace"yanxun Hospital zanje munada emergency sadai in na gama da can in shigo"..da sauri Nur yace"No problem kana gamawan ka shigo i'll wait for you"..bai sake cewa komai ba ya kashe wayan...karasawa gaban mirror yayi ya sake feshe jikinshi da turaruka snn ya dauki dayan phone dinshi ya fita daga dakin...kai tsaye parlon Mummy ya shiga bai sameta ciki ba dan haka ya wuce bedroom...tana zaune kan sallaya sanye da hijab a jikinta tana azhkar ya shigo...ya nemi wuri ya zauna saida ta gama azhkar din ta juyo tana kallonshi tace"Bobby"..yace"Mummy ina kwana"..tace"lafia lau..in zakaje haka da sassafe?.."yace"Hospital zanje wa there is emergency..daga can kuma zan shiga college amma ba jimawa zanyi ba"..Mummy ta mike daga inda tace"to muje kayi breakfast "..tana rufe baki yace" Mummy am ok plss..bana jin yunwa"..zaunawa tayi kusa dashi tareda kamo hannunshi a hankali tace"wai sbd maganan jiya ne kaketa 6acin rai haka?.."ya dan turo bakinshi yace"Mummy nifa ba ta6a lecturing nayi ba kin sani..kawai sa inje in wani ce su zauna zanyi musu lectures "..murmushi Mummy ta saki tareda gyara zama tace" ko da baka ta6ayi ba am 💯 sure you can do it..besides taimakawa zakayi Bobby dududu baifi kuyi na two or three days ba zaa samu wani..ko kana ganin as the proprietor bazaka iya shiga class ka koyar dasu ba?.."da sauri ya girgiza mata kai yace"that's not what i mean"..tace"to ka kwantar da hankalinka nasan you can do it..and believe me zaka kara qima a idonsu idan sukaga har ka shiga class dinsu da kanka ka koyar dasu so relax"kasa ce mata komai yayi sai dan murmushi daya saki...murmushin itama tayi masa tareda mikewa ta kama hannunshi suka fita zuwa dinning...da kanta tayi serving dinshi baiyi musu ba ya shiga cin abincin...jin shiru da yayi gidan yace"wai duk ba wanda ya tashi?.."Mummy tace"kasan weekend ai dama ba tashi da wuri suke ba..kowa yana ramuwar bacci"...gyada kanshi yayi yace"amma shi Sab ramuwar baccin uban me yake shida ba fita ko ina yake ba?..wai yaushe ne ma zasuyi resuming school?.."tace"nan da two weeks ina tunanin"..yace"Allh ya kaimu..gara ya koma ko don sbd mu huta da rigimarsu da Miemie..kullum cikin cin zalinta yake"harara Mummy ta maka mashi kafin tace"bayanta kake goyo sbd ita 'yarka ce koh?."ya dan saki murmushi yace"aah Mummy gaskia dai nake fada"..tace"to rike gaskiyan naka baa son ji dan bazan bari ka dorama d'ana laifi ba"...murmushi kawai ya sakeyi baice komai ba...saida ya gama cin abincin ya mike Mummy ta rakashi har centarl parlor tana mishi addu'a..yayi mata side hug tareda fadin"Ameen Mummyna..bari inga aunty Sumy kafin na fita"...gyada mishi kai kawai tayi snn ta juya ta koma ciki shi kuma ya nufi flat din yayar tashi...Miemie ce kadai kwance a palor tana kallon wani Series ya shigo..ta mike zaune da sauri tana gaisheshi yace"lafia..bata tashi bane?.."tace"ta tashi tun dazu tana daki"..bai sake mgn ba ya nufi bedroom dinta..zaune ya sameta a kan gado tayi tagumi tareda zubama wayanta dake rike a hannunta ido sai kace zata gano wani abu a jiki...ya karasa ya zauna kusada ita yana kallon wayan nata snn ya kalleta yace"Aunty Sumy lafia kuwa?.."firgigit ta dago tana kallonshi dan batasan ya shigo ba...ta boye wayan hannunta da sauri tana kakalo murmushi tace"yaushe ka shigo?.."maimakon ya amsa sai cewa yayi"lafia wai?..meya faru naga kin zubama waya ido haka?..did somebody called?.." girgiza kai ta shiga yi da sauri tace"b..ba wanda ya kirani"...bai sake cewa komai ba yakai hannu ya amsa wayan daga hannunta..direct call log ya shiga aikuwa yaci karo da wata international number..yayi tsai yana karema number kallo nan take kuma ya gane number England ce...ya dago yana kallonta fuskanshi har ya sauya sbd 6acin rai yace"why did he called?.."murya a sanyaye tace"don't know..maybe sbd kids dinshi"..bata rufe baki ba cikin tsananin 6acin rai yace"but how dare he called you?..a ina ma ya samu numberki koda yake nasan qanwarshi ce zata bashi..wnn shine dalilinda yasa nace maku bana son mu'amala da mutanen nn..idan ba munafurci ba all these years meyasa bai ta6a kira ya tambayi kids din nashi ba sai yanxu?..after all what he's done to us har yanada guts din dazai daga waya ya kiraki?..is he Maddd?.."shiru kawai Aunty Sumy tayi tana kallon yanda ya rufeta da masifa as if shine yayanta..tasan duk wnn abun da yake yanayi ne akan gaskiyarshi and bazata ta6a ganin laifinshi ba..ita kanta kusan mutuwar tsaye tayi da taji voice dinshi ta kuma tabbatar da cewa Ismail nefa da gaske ya kirata after 5 long years...to me zai fada mata?..me xai fada wanda bai fada mata shi a lokacinda zasu rabu ba?...a hankali tace"ka kwantar da hankalinka plss"..bai bari ta karasa ba yace"i will have to deal with him myself"..bata ce komai ba tana gani yayi blocking number snn ya mika mata yace"he might use another number to call..yana kira ki fadamin"..a hankali ta gyada mishi kai shi kuma ya mike ya fita sbd 6acin rai ko mgnr daya kawoshi bai fada mata ba...sauke ajiyar zuicya tayi bayan ya fita ta koma ta kwanta kan gado tana sake sake..ita kanta tasan idan yaji anyi blocking dinshi zaiyi using wani number ya kira..idan ya kira din kuma batasan me zata fada masa ba as gabaki daya kanta a daure yake yanxun..ga kuma Bobby da tasan muddin ya samu labarin ya sake kira din shima ba karamin rikici zaayi dashi ba..she knows how stubborn he can be and ko kadan bata blaming dinshi because duk abunda yakeyi yanayi ne sbd su..tasan yanda yakejin ciwon abubuwan da suka faru a baya shiyasa har yanxun ya kasa mancewa...yanada son 'yan uwanshi sosai shiyasa duk wani abu daya shafesu yake bashi muhimmanci...ta lumshe idonta ta bude data tuna yanda yake dawainiya dasu Miemie tamkar shi ya haifesu..bama su kadai ba hatta ita kanta Bobby shine komai nata a yanxu..tun daga kan Mummy,Sab,Miemie da Ilham zuwa ita kanta shine ya zama tamkar mahaifi a garesu...duk tsawon shekarun nan bai ta6a bari sunyi missing wani abu ba ya zama gatansu sosai...kusan duk neman kudin da yakeyi a kansu yake karewa tunda shine komai nasu...kuma da yake Allah ba azzalumin sarki bane sai yake buda mishi a harkokinshi sosai kuma mishi albarka business dinshi har ya kawo level din da yake a yanxu...tayi nisa cikin tunani har batasan time din da ta fara hawaye ba..tausaya ma kansu takeyi yanda basu da kowa sai junansu a yanxu sai few daga familyn Mummy da suka rage..yanda familyn dad dinsu dana baban yaranta sukayi abandoning dinsu kawai sbd kasancewar Mummy ba bahaushiya ba...yanda sukayita truggling su kadai har Allah yasa suka yanxu...zuwa yanxu kuka takeyi sosai shiyasa bata cika son tana tunawa da past dinsu ba domin yin hakan yana dawo mata da baya gaba ne..gashi duk yanda takai da kokarin dakatar da kanta abun ya gagareta haka taci kukanta sosai ta godema Allah har 6arawon bacci ya lalla6o yayi gaba da ita. Kai tsaye yana fita parking space ya nufa...driver na ganinshi ya mike da sauri yazo ya gaisheshi tareda tambayanshi motan da zasu fita...Bobby bai iya cewa komai ba sai juyawa da yayi yana kallon motocin..idonshi ya sauka kan wata Benz dinshi daya dade bai hau ba dan haka yace a fito da ita kawai..cikin hanzari Mr.Obi yayi clearing motan dukda dama ba wani datti ke gareta ba cox ana yawan wankesu snn ya fito da ita..ya bude back seat da kanshi ya shiga snn driver yaja motar bayan ya gama warming dinta suka fita daga gidan..kai tsaye yace ya fara kaishi Hospital. Bai baro asibitin ba sai after 11 kai tsaye kuma suka wuce College...suna hanya ya kira Nur yace gashi nan zuwa shima yace dama already yana cikin college din shi yake jira...da yake akwai dan nisa tsakanin Hospital da College din basu suka isaba sai 12...bai fito daga mota ba ya kira Nur sai gashi ya fito daga office hihi ma ya da cikin motan nasu suka shiga Hostel din...as always sukayi parking daidai second gate snn suka fito zuwa ciki...daya daga cikin Matrons dake kula dasu tayi musu jagora har cikin apartment da abun ya faru..wutar apartment din ya dauke gaba daya..Nuru yace"amma daga wane room abun ya fara?.."ba musu Matron ta kaisu har cikin dakin..babu kowa ciki kasancewar an riga an sanar dasu cewa Provost zai shigo dan basu san har proprietor zaa zo ba...karema dakin kallo suka hau yi idanun Bobby ya sauka kan gadon Lamido da har yanxun ke shimfide da bedsheets na Man Utd..ya kalli gadon da kyau sai kuma ya ta6e baki cikin ranshi yana mamakin wai mace da football...duk iya dubansu basuga wani alama na wani abu ba har sun juya zasu fita ta fito daga kitchen hannunta rike da plate din indomie tana cewa"Billy you need to taste this..."magananta ya makale sakamakon mutanen data gani a dakin...yau ma dai kaman ko yaushe jessy ne a jikinta fara na Manchester sai wandon jessyn daya tsaya mata iya guiwa...gaba daya tsayawa sukai suna kallonta...ita kanta mutuwar tsaye tayo a wurin don kwata kwata batasan suna cikin dakin ba...juyawa tayi da sauri tana zazzare idanu kaman wanda tayi ma sarki karya...idanunshi ya sauka bayan rigan nata da aka rubuta POGBA da capital letters sai a kasa kuma aka zana katoton number 6...wani haushi yaji ya sake turnukeshi...ita kuma kaman wanda aka tsikara ta bude wardrobe da sauri ta rarumo hijab din Billy ta zura a jikinta...sai a yanxu Nur ya samu baki mgn"Lamifo is this your room?.."tana kokarin kakalo smile tace"yes sir..good afternoon "..yace" afternoon amma garin ya wuta yayi spark a nan?.."tayi kasa da kanta ganin irin kallon da Bobby ke mata tace"muma bamu saniba sir..kawai muna zaune sai mukaji wani kara"..bata rufe baki ba Bobby ya juya ga Matron data rakosu yace"waye dayan wanda suke tare a dakin?.."da sauri matar tace"bari a kirata Bilkisu ce"..daga haka ta fita sai gasu sun dawo tareda Billy da tayi kasa da idanu sbd idanun Dr.Bobby da ko kusa bata kaunar ya zuba mata su...sumi sumi ta karaso cikin dakin tareda tsayawa kusada Lamido da itama nata tun dazun yake kasa...shi kuma ya shiga binsu da kallon da suka tsana ya ganeta sarai itace ta rakata Clinic ranan da ya mata allura..baisan meyasa jikinshi ke bashi akwai dalilin yin spark din ba..kuma as far s Lamido is concern yasan abunda yafi haka ma zata iya aikatawa cox a dan ganin da yayi mata yaga alaman ba karamar fitinanniya bace..cikin voice din daya sake tsoratar dasu yace"now tell me..waye ya kusa haddasa min gobara a building?.."sukayi shiru ba mai kwarin guiwar yin mgn cikinsu...ya daka musu wani tsawa yace"are the two of you deaf?.."jiki na rawa Billy tace"Sir itace ta jona iron ta barshi a jiki"..tana rufe baki itama Aysha tace"Sir karya ne itace ta jona iron din ta tafi tayi bacc.."ragowar mgnr nata ya makale sakamakon idanu data hada dashi...wani irin kulululu taji cikinta nayi kaman zataje toilet..Allah ya zubama idanun nan nashi wani kwarjini na musamman dake sa mutum ya shiga taitayinshi da zaran ya hada ido dashi...shi kuwa Bobby da gayya yayi hakan don yasan duk iskancinta ta kalli cikin idonshi saita saduda...lokaci guda wasu hawaye suka ciko idanun nata gashi har yanxu ya kafeta dasu ko blinking bayayi...hatta Bilkisu da nata idanun ke kasa ji take kaman ana wura mata wuta a cikinta tsabar tashin hankali...maimakon ya dauke idanun nashi sai ya shiga takawa a hankali har zuwa inda take...ya tsaya dab da ita hannayenshi zube cikin pockets dinshi cikin wani stern masculine voice dinshi yace"Now speak"..idanunta ta lumshe hawayen dake ciki suka cigaba da gangarowa cikin ranta ko duk addu'an da yazo bakinta yi take dan yanda taji kaman an daureta da sarqoqi ne an kuma jefata a cikin kurkuku tsabar rudanin data shiga...ganin halin data shiga Nur yayi saurin matsowa inda suke saidai kafin yayi magana Bobby ya daga mishi alaman he shouldn't say a thing..ba yanda ya iya haka ya koma baya tareda rungume hannu yana binsu da kallo. Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank..sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 07 Saida ya sake dinke fuskanshi tsaf snn yace"i said speak"..a hankali tayi kasa da kanta tana fidgeting fingers dinta kuma har yanxu gayyar hawaye basu dena sukuwa kan fuskanta ba tace"Sir bacci ne ya daukeni"..ba tareda ya dauke idonshi daga kanta ba yace"da kika jona iron din sai bacci ya daukeki right?.."a hankali ta gyada mishi kai...a fusace yace"how dare you do that?..qona min building kikeso kiyi?.."tayi shiru kanta a kasa..yace"i said qona min building kikesonyi?.."ba tareda ta dago ba ta girgiza kai alaman aah..shi kuma cikin wani additional 6acin rai da yaji yana saukan mishi yace"Billahi if you dare repeat this again you will see the devil side of me..are you mad da zaki jona abu a wuta snn kije kina bacci?.."ya karasa mgn yana wani huci..shi kanshi baisan daga ina wnn 6acin ran ke saukan mishi ba...Nuru ya karaso tareda kama hannunshi yace"zo mu tafi dan Allah what's done is done saidai a kiyaye gaba kuma"..baiyi masa musu ba ya bishi suka fita daga dakin matron ta bi bayansu...suna fita ya daddage ya fizge hannunshi dake cikin na Nuru snn ya karasa inda motarshi yake ya bude ya shiga...shima Nur karasawa yayi ya shiga snn ya dauko wayanshi ya kira mai gyara musu wuta yace azo a gyara a yau din nan...bayan ya kammala ya juya yana kallon Bobby daketa faman cika yana batsewa yace" Bobby are sure you are alright?.. wnn 6acin ran duk na meye?.."ko kallon inda yake baiyi ba balle yasa ran samun amsa...shima baiyi expecting amsan nashi dan haka yaci gaba da mgnrshi"you shouldn't have acted like that sai kace secondary school?..besides kudi fa suka biya"..tun kafin ya rufe baki ya juyo yana kallonshi da wani irin karaji yace"seriously bayansu kake bi?..yanxu da sun konamin building zaka iya biyana ne?..kuma da suka biya kudi ai ba kudin building dina suka biya ba kudin zama cikin Hostel suka biya so dole inyi mgn idan naga zaayi min 6arna"...shiru kawai Nuru yayi yana kallonshi deep down yasan da akwai abunda ke damunshi...ya tabbata wnn fushin ba iya na an kusa kona masa building bane dole da akwai wani abun a kasa...har suka koma cikin makaranta ba wanda ya sake cewa komai a cikinsu...kafin su fita Nuru yace zai sauka dan bai gama aiyukan da yakeyi ba..babu wasting of time driver yayi parking shi kuma ya bude motar ya sauka snn suka cigaba da tafiya...bayan fitarshi Bobby ya sauke wani numfashi da yake rike dashi tun dazu tareda jingina jin seat din da yake hadi da lumshe idanu...baisan wane irin bala'i bane ya hau kanshi yau din nan...shi kanshi haushin kanshi yaji yanaji bai kuma san dalili ba...har ga Allah maganan da Nuru ya fada yasan its not that far from the truth..bai kamata yayi acting kaman yanda yayi ba amma ko Allah ya san shi kanshi baisan abun da ya hau kanshi ba a lokacin..bai kuma san daga ina duk wnn masifan yayita tahowa gareshi ba...kawai shidai ya tsinci kanshi cikin tsananin 6acin rai which he couldn't control..ya lunshe ido yana sake budewa har yanxun idanunshi basu dena hasko mishi ita sanye da kayan 'yan ball ba...ya saki wani tsaki kuma wai sbd tsabar iskanci shine ta juya musu baya wato tunda sun gama ganin gaba su kalli bayan ma knn...yau ya sake tabbatar da cewa ita din sangartacciya ce..idan ba haka ba why yarinya mace kamarta zaa barata tana supporting wani football club kuma har a gidansu a biye mata ana wani siya mata jessy da gajeren wando tana sawa..wai har bedsheet na Manchester sai kace wata namiji...runste idon yayi yana wani girgiza kai duk a kokarinshi na ya dena ganin pictures din nata saidai to no avail...gaba daya yaji yayi dana sanin zuwa Hostel din ma at the first place..daya sani da Nur ya kirashi kawai yace mishi bazai samu daman zuwa ba da shknn babu shi babu ganin wnn masifa...wnn yarinyar ya rasa wace iri ce ita da take kokarin yi masa kutse cikin rayuwarshi...ya tabbata masifan daya rufeta dashi hadda tsanar da yayi ma 'yan garinsu yasa shi haka...kilan da bai san 'yar Gombe bace bai zama lallai ya aikata abunda yayi ba...jingina ya sakeyi yana kara sakin wani tsakin duk ranshi yabi ya jagule...a daya 6angaren kuma ga wancan mara kunyan da yake kokarin sake kustowa cikin rayuwar 'yar uwarshi again..baisan me yake takama dashi ba har da zai dauki waya ya kirata sbd bashida kunya...sai kuma wnn kaddararren lecture da Mummy tace sai yaje yayima yaran can..shi sam wnn abun bi gamsheshi ba...baima san taya zai fara shiga class ya rike marker yace zaiyi musu lectures ba..baisan ta ina zai fara ba...a takaice har suka kai gida bai dena wadan nan tunane tunanen ba..gaba daya kanshi ya dauki wani zafi kaman wanda ke amfani da wutar lantarki. Tunda suka fita Lamido ta zube nan kasan dakin tana sakin wani marayan kuka...Bilkisu ma batasan lokacinda ta durkusa nan kusa da ita ba suka taru suka hada kai sunata kokawa abunsu...if you see yanda suke kuka zakayi tunanin mutuwa akayi musu...saida sukayi na sama da one hour Billy ta dakatar da nata snn ta shiga rarrashin 'yar uwarta amma a banza...ta kwashi wasu 30 mins tana rarrashi ganin ba denawa zatayi ba ta mike tareda rage kayan jikinta ta fada bathroom...wanka tayo tareda alwala snn ta fito ta gabatar da sallahn azahar da akayi tun dazu basu tashi sunyi ba suna aikin kuka...har ta idar da sallahn Lamido bata dena kuka ba...ta karasa wardrobe dinta ta dauko dan dogon riga mara nauyi tasa snn ta sake komawa gun Aysha data koma kan gadonta ta kwanta tareda lullubewa da blanket...kawai ayyanawa take da ace daddynta irin easy going mutane ne da babu abinda zaisa ta sake kwana a FCNM saidai kawai su ganta a gida...to sanin da tayi kota fada mishi ma ba goyuwa da bayanta zaiyi ba kilan ma saidai ta janyo ma kanta fada yasa ba yanda ta iya haka nan zata hakura tacigaba da zama ko bataso...tun dazun wayanta ke vibration amma ta kasa tashi ta dauka...Billy da ta gaji da jin vibration din ta dauka tareda picking call din ta kara a kunne...a daya 6angaren Hamma Najeeb yace"Maama are you mad anata kiran wayanki bakya dauka?.."cikin voice dinta da bai gama warewa ba Billy tace"Hamma ba ita bace"..da sauri yace"Subhanallah Bilkisu what happened?.. you sound somehow..ina Maaman take? "..a hankali ta juya tana duban Aysha da har yanxun ke kudundune kan gado tace" Hamma gata...kuka takeyi tun daxu"..a dan rikice ya sake fadin"Ya Ilahi meya sameta?..bata wayan muyi mgn"..ba musu ta karasa ta yaye blanket data lullu6e dashi ta saka wayan a speaker snn ta ajiye kusada face dinta tace"Hamma gashi nan na bata"...da sauri yace"Maama can you hear me?..what happened?.. why are you crying?.."da sauri ta mike zaune tareda daukan wayan ta rike a hannunta har yanxun bata dena hawaye ba tace"Hamma bana son makarantan nan please..inaso in dawo gida dan Allah"..hankalinshi duk ya tashi yace"Aysha me yake faruwa ne wai?..me akayi maki?.."tana kuka tayi mish bayanin duk yanda sukai da proprietor daxun...yayi shiru har saida ta gama snn yace"to ki kwantar da hankalinki ina nan zuwa gobe kinji..first thing in the morning zan taho inshaAllah amma ki dena maganan dawowa gida kinsan daddy bazai yadda ba"...ta kai hannu tana goge hawayenta tace"Hamma to nidai kazo dan Allah...i really want to see you"..yace"ba damuwa zanzo inshaAllah..stop crying kinji"...gyada mishi kai tayi kaman yana kallonta...saida ya tabbata ta dena kukan yace"to bari in kaima Ammi zakuyi mgn dama itane tace in kiraki and karki nuna mata wani abu ya faru okay?.."a hankali tace"toh"...bai sake mgn ba ya fita zuwa parlor inda gaba daya suke zaune snn ya mikama Ammi wayan yace"yauwa Ammi gata"..Ammi ta amsa wayan tana fadin"kun gama sirrin naku knn?.."baice komai ba yayi daria ita kuma ta kai wayan kunnenta hade da sallama..a hankali tace"wa'alaiki salaam Ammi ina yini"..tace"lafia lau ya jikin naki?.."tace"naji sauki Ammi..ina Yusra"..Ammi tace"Yusra gata nan..kina jina?.."da sauri tace"inaji Ammi"..."wani mgn kika kira fiddausi kika fada mata?."..lokaci daya Aysha ta wani zaro ido hadda su rufe baki tace"aunty fiddausi wai?..Ammi me zan fada mata ni toh?.."bata rufe baki ba Ammi tace"zakici ubanki wlh..kin kirata kin hadata da 'yar uwarki shine yanxu kike tambayana me kika fada mata?.."ta marairaice tace"wlh Ammi kome Husna ta fada karya take..ya zaayi ma ki yadda na da mgnrta ni da nake babba baki yadda da nawa ba?."dan tabe baki Ammi tayi tace"da kike babba ai ba hankali gareki ba har yanxun..kuma kome kika fada mata maza maza ki kirata yanxu kice mata karya kike dan ba cikakken hankali gareta ba itama fiddausin"..batasan lokacin da murmushi ya dan subuce mata ba tace"kai Ammi maman tawa?.."Ammi tace"Maman taki fa shiyasa duk wani rashin mutuncinta ai kikayi gado..lokacin da muna gida Fiddausi ai ba karamar fitinanniya bace"..batace komai ba sai daria da tayi...Ammi tace"iceko kina kiran daddy ki gaisheshi?.."tace"ina kira Ammi..ko jiya saida na kira ban sameshi ba"..tace"to ki sake gwadawa yau ko gobe..ya danyi tafiya ne amma nasan a yau ko goben zai dawo"..tace"InshaAllah zan kira Ammi..ki bawa habibty mu gaisa plss"..ba musu Ammi ta mikama Yusra wayan snn ta bar parlon...Yusra ta amsa da murnanta saidai kafin tayi mgn Husna ta kwace wayan tareda kaiwa kunnenta tace"to Adda ni da baki nemana sai me?..duk tsiya dai ni kika fara sani kafin Yusran"...wani murmushin Aysha ta saki tanajin yanda lokaci daya duk wnn damuwan data shiga na tafiya tace"kuma dana fara saninki ai ba cewa akayi dole sai nafi sonki ba"...Husna ta wani murguda baki kaman tana ganinta tace"kuma ko Hamma zaizo na fasa biyoshi wlh"..tana gama fadin haka ta ajiye wayan tayi gaba abunta...Yusra ta dauka tana murmushi suka fara mgn...duk abunda suke Hamm na zaune yana kallonsu...lokaci daya Aysha ta mance da wani 6acin ran proprietor sukaita hira da qanwarta...basu suka gama ba saida ya kar6e wayan da kanshi...sai a lokacin ta samu ta shiga toilet tayo wanka snn tazo ta shirya ta sake hayewa kan gadon ta kwanta sbd Billy bata dakin...tana kwanciya sai abubuwa da suka faru suka shiga dawo mata...ta tuna yanda ya daure fuska ya kuma tsareta da wnn shegun idanun nashi mai kama dana aljanu ta bakin na Billy...batasan wane irin magic ke gare idanun nashi ba da yana dora mata su taji kaman an tattaro duk wani rashin nustuwa da tashin hankali na duniyar nan an dora mata su akai...anya kuwa mutumin nan ba wani abu yakema idanunshi ba?..tana cikin tunanin Billy ta shigo dakin ta mika mata wayanta dake hannunta tace"kar6i ki ce masa ya dena kirana dan Allah..haba! tun daxun yaketa faman kira ko yanaso ya shanyemun caji ne?.."ba musu Aysha ta mike zaune tareda amsan wayan daga hannunta taga Lamido's bestie ke kira...dariya ta saki sosai dan har gobe bata dena dariyan wnn sunan da tayi saving number besty dashi..wai Lamido's bestie sai kace wani yace bestienta ne ita...har kiran ya katse wani ya sake shigowa bata dauka ba...Billy data kulu tace"malama idan bazaki dauka ba bani wayata dan Allah"..bata bata wayan ba tayi kokari ta tsayar da dariyan snn tayi picking tareda karawa a kunne...yanajin an dauka yace"Haba my Billy"..Aysha ta wani zaro ido jin abunda ya fada hadda toshe baki tace"besty ba ruwana wlh"..dan dariya shima yayi kafin yace"inata kiran wayanki bakya dauka itama kuma wnn 'yar rainin hankalin sai wani jamin class takeyi taki daukan wayan sai kace saurayinta"..yana rufe baki Billy da taji kaf abinda ya fada ta daga murya tace"Allah ya kiyaye na rasa dawa zanyi soyayya sai kai...kuma a kashe a bani wayana sai ka kira wayarta ku cigaba da shirmenku"..dariya yasa sosai Lamido na tayashi...saida sukayi me isarsu snn yace"besty wai an fasa zuwa saloon din ne?..kin ganni fa tun dazu a bakin gate dinku ina jiranku"..tana dan girgiza kai tace"anya zuwa saloon din nan zai yiwu kuwa besty?..i don't feel like going out"..tana rufe baki yace"kuma shine baki kira kin fadamin ba saida na baro gida nazo?..fadamin me yake damunki da zakice you don't feel like going out?..na sanki da son yawo fa besty"...tayi shiru tanajin yanda 6acin ran dazu ke son dawo mata sabo fil...shi kuma jin tayi shiru sai yace"alright ki fito waje sai muyi mgn..ina bakin gate"..bata ce komai ba ta kashe wayan snn ta mike ta zura hijab tace ma Billy"taso muje"..tayi mata wani kallo tace"je ina?.."tace"wajen besty mana bakiji yace yana bakin gate ba?.."tsaki ta saki tana kokarin hawa kan gadonta tace"sai kin daw.."bata gama mgnr ba ta shiga janta suka fita daga dakin tunda already da akwai hijab a jikinta...har suka fito waje bata dena jan hannunta ba itama kuma bata dena kokarin kwatan hannun nata ba har suka karasa inda yake...ya bude mota ya fito yana kallonsu one by one kafin ya danyi murmushi yace"to a bani labari menene ya faru?.."Bilkisu ta daure fuska tana kawar da kai Lamido kuma tace su fara samun wuri su zauna first... duk basuyi gardama ba suka karasa wani dan wuri da aka zagayeshi da flowers tsakiya kuma cement chairs ne suma aka zagaye wurin dasu suka zauna...suka danyi shiru na wani lokaci kafin Aysha ta bashi labarin duk yanda sukayi da proprietor daxun...shi kanshi baiji dadi ba kuma suma yaga yanda duk Mood dinsu ya sauya dan haka yace ko baza'a je saloon ba shi yanaso ya kaisu wani wuri...Bilkisu ce ta fara cewa bazataje ba kunsan mutumiyar taku😂sai da kyar suka samu suka lalla6ata ta amince ta bisu..daga nan basu koma ciki ba suka shiga motanshi suka wuce..kai tsaye Ten to Ten ya fara kaisu yayi musu ordern abinci mai kyau yace suci dan yasan yau da kyar idan sunyi lunch gaba dayansu...ba suyi musu ba kuwa sukaci dan da gaske ba abinda sukaci tun breakfast... suna barin nan ya kaisu park nan kuwa duk suka ware suna enjoying kansu...bayan sun bar park din suka shiga Ado Bayero Mall sukayi shopping snn sukai branching a gidan grandmother dinshi dake Tarauni...tana zaune parlor tanashan nono da fura suka shigo...ta dago tayi musu kallo daya tareda ta6e baki snn ta cigaba da shan furanta...saida suka karasa ciki suka zauna Sa'eed yace"Hajjaju baki ganni da mutanen naki bane?.."sake ta6e baki tayi ta kur6i furanta kafin tace"ai ni ba ruwana da mutanen nan yanxu...tsakani da Allah suna cikin garin nan yaushe rabon da naga kafafunsu cikin gidana?.."dan murmushi Billy tayi tace"Haba Hajiya kinaso Sa'eed yaji kanmu knn?.."tace"yo jin kai na nawa kuma Bilki?..ai saidai kar a kuma"...Aysha daketa murmushi itama tace"to munji mun dauki laifinmu Hajiya kuma mun bada hakuri inshaAllah baza'a sake ba..daga yanxu duk weekend sai bestie ya kawomu mun gaisheki"...harara mai kyau ta watsa mata tace"sarauniyar 'yan dadin baki..to na hakura dai ba dan halinku ba..ya kuke ya karatun?.."sukace"karatu Alhamdulillah Hajiya..ya gida"..tace"lafia lau..ya wajen iyayen naku?.."Sa'eed dai na zaune yana kallonsu..lokaci guda i hira ya 6arke a tsakaninsu dama hajiya ba daga nan ba akwai labari su din ma kuma ba baya bane...a takaice sai da sukai sallahn magrib suka bar gidan...kai tsaye ya maidasu Hostel kowacce rikeda kayan kwadayin da suka siyo a shoprite..duk wnn kunci da 6acin rai da suka shiga daxun yayi disappearing..besty kam yayi kokari. Wahsegari sunday karfe 7 daidai Bobby ya dannawa Nuru kira...bai dauka ba sai a karo na biyu ya daga cikin magagin bacci...Bobby ya dan ta6e baki jin bacci ma yake yace"kana jina?..ka fadama students din naka zan shigo 8 muyi lectures din..and tell them duk wanda ta wuce 8 batazo ba batada C.A"...yana gama fadin haka bai tsaya jin me zai fada ba ya kashe wayanshi...da mamaki sosai Nur yabi wayan da kallo kafin ya sake danna masa kira...saida ya kusa katsewa snn ya dauka..da sauri Nur yace"Bobby me kake nufi ne wai?..i don't understand"..babu gardama ya sake repeating abunda ya fada daxun..Nur ya wani marairaice yace"amma Bobby ka duba time kuwa ka gani?..this is past 7 yanxu har yaushe aka kira aka sanar dasu su fito gashi yau weekend"..a takaice Bobby yace"that's non of my business.. ba kai kakeso inyi musu lectures ba?..to gashi nan zanyi and wallahi duk yarinyan da ta sake na rigata shiga class din nan tayi loosing c.a so kindly call and ask them to start coming tun kafin 8 din yayi"...still yana gama mgn ya kashe wayanshi...Nur ya girgiza ya shiga neman number Lamido ya samu ya kirata...yasan duk meyasa Bobby ke wnn abun sbd yayi amfani da Mummy ya tilastashi yin abunda baiso ba shine shima yakeso ya rama ta wnn hanyan...yana zuwa kan numberta yayi dialing amma har ya katse bata dauka ba..shi kuma bai hajura ba ya sake kira..yana dab da katsewa ta dauja cikin muryan bacci tace"good morning sir"...yace"Morning Lamido inaso ki sanar da duk 'yan class dinku su shigo college zuwa 8 an samu wanda zaiyi taking over reproductive health dinku"..da sauri ta kalli wall clock dake manne cikin dakin nasu kafin tace"but sir this is 7:15"..yace"i know just try your best..tell them duk wadda batayi attending ba tayi loosing c.a and i want yiu to be fast about it please"..a hankali tace mishi"ohk"..snn ya kashe wayan...Billy dake bacci ta fara tashi tayi mata bayani snn ta dauki wayanta ta kunna data tayi musu bayani ta voice note ta tura a group snn kuma ta dhiga kiran duk wanda tasan zai iya sanar da wasu tana sake fada musu...Billy kuma fita tayi tayi announcing wa 'yan class dinsu dake cikin hostel din...saida ta tabbata ta fadama kowa snn ta koma daki..itama Aysha daidai lokacin ta gama kiran duk wanda zata sanar ma...tana duba agogo tana 7:35 dan haka ta mike da sauri ta fada bathroom tayi wanka sharp sharp tana fitowa itama Billy ta shiga...karfe takwas saura mintina goma suka gama shiryawa..ita tana sanye cikin abaya sky blue tayi rolling mayafin rigan..Billy kuma dogon riga ta saka na atampa ta daura dankwali sai veil dinta a kafada...koda suka fita compound drivern school bus har ya fito dan haka suna gama fitowa suka shiga motan zuwa cikin makaranta...motan na gama parking duk suka fito suka nufi class dinsu makarantan yayi tsit sai few students dake shigowa karatu...mutum 8 kadai suka samu a class din sunzo idan aka hada dasu da suke cijin hostel su 15 sun zama 23 knn out of 38...hankakinta duk yabi ya tashi ta dauki waya tana kokarin sake kiran wasu kiran provost ya shigo wayan...tayi picking da sauri tace"Sir wlh har yanxu da yawa basu karaso ba..mu 23 ne kadai a class din"..yace"no problem ki fada musu suyi sauri suzo before 9 ni zanyi kokari in rike maku shi har zuwa 9 din"...tace"thank you sir"..snn ta katse wayan...group dinsu ta sake shiga tayi announcing cewa an kara musu 30 minutes dan haka kowa yayi sauri ya karaso. Cikin ikon Allah kafin 9 din gaba daya sun hallara...shi kuwa Bobby yana office din Nur time to time yana duba agogo...9 din nayi daidai ya mike duka fito daga office din tareda Nurun...suna haurawa sama ta window ya hangosu zazzaune cikin class din kowa da kalar kayansa sai ya dan dakata da tafiyan yana duban Nur yace"and why are they not in uniform?.."Nur yace"dama lectures din weekend bada uniform suke zuwa ba gaskia..kuma kaima bakace ace musu su sa uniform ba ai"..bai sake cewa komai ba suka karasa class din hannayensu zube cikin aljihu. Masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank..sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 08 Suna shiga gaba daya class suka hada baki suna gaishesu..Nur ne kadai ya amsa musu da "morning class ya weekend?.." suka amsa da lafia yace"well as a result of maternity leave da malaman Reproductive Health dinku ta tafi nasan you people do miss alot a karatunku ga kuma exams dake approaching...Class Rep dinku tazo ta sameni da maganan and our Generous Proprietor here says he will assist you guys har kuyi covering syllabus dinku"..ya karasa mgn da wani killer smile a fuskanshi tareda dan juyawa ya kalli Bobby dake tsaye rungume da hannaye yana sauraronshi...lokaci daya Class din ya dauki tafi jin Proprietor da kanshi yace zaiyi assisting nasu nan kuwa basu san saida aka kai ruwa rana before ya amince ba...Lamido da Bilkisu kuwa kallo daya sukayi masa gaba daya sukayi kasa da idanunsu..Billy dai addu'a take kada Allah ya kawo dalilinda zaisa wnn shegun idanuwan nashi su sauka a kanta..ita kuma Aysha hararan gefen ido take binshi dashi cikin ranta tace"inyamurin banza inyamurin wofi"..daidai nan kuma Nuru ya dubi Bobby yace"to Dr.Bobby bismillah"..daga haka ya koma can karshen class din ya samu wani empty seat yayi zamanshi a wurin...shi kuma Bobby ya dan kalli class din har yanxun yana rungume da hannu thinking from where to start...saida yayi shirun amost 3 mins kafin yace"where do you guys stop?.."daya daga cikin 'yan class din ta fada mishi last topic da sukayi...yana dan gyada kai ya tambayi course outline nan ma suka bashi...saida ya gama studying course outline din snn ya ajiyeshi kan table dake gabanshi yace"well according to the course outline kunada remaining 5 topics to cover before the exams..now zamuyi kokari muyi covering 2 topics the ramaining ones kuma zakuyi dividing kanku into 3 groups..each group su dauki one topic suje suyi studying dinshi sosai zuwa ranan Thursday zakuyi presentation..do u get me?.."gaba daya suka amsa da sun gane...shi kuma ya juya ga board dinsu yaga akwai rubutu a jiki sai ya sake juyawa garesu yace"who's ur class rep?.."gaba daya suka nuna Lamido...shi kuma ya wani daure fuska ganin itace dan lokaci daya incident din jiya ya fado masa a rai...itama daure nata fuskan tayi snn ta mike kanta a kasa..dukda ba kallonshi take ba tanajin wnn shegun idanun nashi a kanta..."come and wipe the board"..ya fada still looking at her...batayi musu ba ta fito tayi wiping board din ta juya zata koma ya sake fadin"da fingers dina kikeso inyi maku rubutun?.."bata juyo ba ta karasa seat dinta ta bude locker dinta ta dakko wani pink marker ta kai mishi snn ta sake dawowa ta zauna...duk wnn abun dake faruwa Dr.Nuru na bayan class din yana kallonsu...murmushi kawai yake yana girgiza kai cikin ranshi yace"zamuga yanda za'ayi wnn lecture"...sunan topic din Bobby ya rubuta jikin white board snn ya juyo yana facing dinsu yace yanaso daya daga cikinsu ta danyi briefing dinsu about the topic before he starts...wajen mutum biyar ne suka daga hannu shi kuma ya shiga binsu da kallo daya bayan daya yanaso yayi choosing mutum daya a cikinsu karaf idonshi suka fada kan Lamido...ya dage gira yana kallonta da kyau hadda sakin wani dan iskan smile cikin ranshi yana ayyana ita zaiyi selecting dukda ba daga hannu tayi ba kawai dai yanaso yana brain dinta da kullum Nur ke cewa she's genius she's this she's that..yau yanaso ya kure brain din nata...daga nan inda yake tsaye yayi pointing dinta da finger dinshi yace"You.."da sauri ta dago idanunta saidai suna sauka cikin nashi ta sake mai dasu kasa...still yana duban inda take yace"fito kiyi briefing namu akan topic din ba kece class rep ba?.."ya karasa mgn still da wani killer smile a face dinshi...ita kuwa qala batace ba ta mike daga seat dinta ta fito...ta juya taga sunan topic daya rubuta snn ta sake juyawa tana facing class din making sure bata kalli inda yakeba don kada ma ya zuba mata wadan nan idanun nashi yasa ta kasa ta6uka komai...bayani ta shiga yi musu dalla dalla kaman ba briefing dinsu yace tayi ba...tunda ta fara dama ya jingina da wall ya wani lumshe ido yana sauraronta sam baiyi tunanin zata iya ba...a yanda take explaining ma sai yakega kaman koshi da yake certified gynaecologist bai zama lallai ya iya yanda tayi ba..sam baiji dadin hakan ba kuma dan so yayi ya kunyatata a gaban Nur da kullum yake kiranta genius...yanxu kam ko da bai yadda she's genius ba tabbas yasan she's brilliant tunda har ta iya explaining abunda ba'a koya mata ba haka..daga yanayin yanda take magana kuma ya fahimci kaman she's used to it dan babu wani alaman tsoro ko rashin sabo a tattare da ita...duk sai yaji ranshi ya fara 6aci all of a sudden...hada ido sukayi da Nur aikuwa ya dage gira irin ya kaga?..shi kuma ya dauke kanshi ba tareda ya kalleta ba yace ya isa haka ta koma ta zauna...6oyayyen ajiyan zuciya ta saki cikin ranta tace"Finally"..sa zahiri kuma batace qala ba ta wuce ta koma seat dinta..shi kuma ya dora daga inda ta tsaya...bayani yake musu sosai shima irin bayanin da bai ma ta6a zaton zaiyi musu ba..suma kuma class din suna participating sosai...nan take yaji ashe yin lectures dinma is not as bored as he thinks...a da kawai gani yake irin boring lectures zasuyi sai kuma yaga ba haka ba baisan ko sbd class din suna participating bane...yana karasa topic din data fara ya shiga yi musu dayan shima kuma suna understanding sosai...a takaice saida suka dauki almost 3 hours kafin su gama...bayan ya gama amsa tambayoyinsu ya sake jaddada musu mgnr presentation da zasuyi ran Thursday snn yayi musu sallama ya fita mai girma provost yabi bayanshi...har ya fara sauka stairs Nur ya bishi da sauri suka shiga sauka tare yace"ko baka fada ba nasan u enjoyed it"...harara kawai ya watsa mashi baidai ce komai ba...shi kuma ya saki wani smile tareda dan lowering voice dinshi yace"and ya kaga brain din Lamido?..hope you are now satisfied?.."tsaki kawai Bobby ya saki yaki kuma kulashi...saida suka fito yace mishi"zamuyi dropping dika ne?.."Nur yace"don't bother nazo da mota kawai dai dan Allah kace ina gaida su pretty idan kaje gida"...bai sakeyi mashi mgn ba ya shiga mota bayan driver ya bude mishi..shima drivern ya zaga ya shiga snn ya tayar da motar suka tafi...shi kuma Nur saida ya shiga office ya dauko wasu files snn ya shiga nashi motan shima ya wuce. Da wuri suka fito daga Class din as a result of message data gani na Hammanta yana ce mata sun karaso...suna fitosa ta hango motanshi ai batasan sanda ta taka a guje zuwa wurin ba...Bilkisu ta shiga girgiza kai tana fadin"Allah nunamin randa zaki girma Lamido"...tun kafin ta karasa duk suka bude mota suka fito...Hamman nata ne da Yusra sai kuma Husna mai cewa ko zaizo bazata zo ba...kai tsaye tana isa ta wani d'ane jikinshi tana dariyan farin ciki...shi kuma ya rabata da jikin nashi yace"ke har yanxun bakisan kin girma ba koh?.."daria ta saki tareda dan kwa6e fuska tace"nidai ban wani girma ba"...murmushi kawai yayi ya girgiza kai yasan Maama will never change...ita kuma sai ta juya ta janyo Husna da Yusra ta rungumesu gaba daya kafin ta dago tana cewa Husna"kikace kuma bazaki zoba?.."murguda baki kawai Husna tayi batace komai ba...a daidai lokacin Billy ta karaso garesu aikam Husna na ganinta ta karasa gareta ta wani rungumeta kafin ta dago tace"nima ga yayata nan"...murmushi kawai Billy tayi tareda kama hannun Husna suka karasa ta fara gaida Hamma...bayan sun gama gaisawa tace ya kamata su karasa daga ciki...kaman jira suke kuwa duk suka shiga mota zuwa cikin Hostel...daidai inda ake parking yayi snn suka bude mota suka fito...yace su shiga ciki dasu Husna shi da akwai inda zaije ya dawo...su Aysha hadda wani marairaicewa akace"amma dai Hamma ba dadewa zakayi ba koh?.."ya saki murmushi ganin wnn shagwa6an nata da bai karewa yace"bazan dade ba Maamata...da wuri zan dawo muyi mgnr daya kawoni garin"..nan dai sukayi sallama dashi ya wuce su kuma suka shiga ciki...direct dakinsu Billy ta bude suka shiga Husna tayi wani irin tsalle ta dire akan gadon Billy tana fadin"nima dai ina candy FCNM din nan taku zance daddy ya kawoni...makarantan ba karamin burgeni take ba"...Aysha data kama Yusra suka zauna kan nata bed din tace"ba wani FCNM da zakiyi yarinya...ni kaina yanxu da za'a cireni so nakeyi dan bakisan yanda take ba shiyasa kike sonta"...tace"koma dai ya take Allah Adda ina sonta"...Billy ta fito daga kitchen dauke da lemuka da ruwa sai Cake dasu meatpie ta kawo musu..ta nemi wuri ta zauna kusada Husna tace"to me kukeso a dafa muku?.."Yusra tace"Hamma yace idan ya dawo zai kaimu eatery ko Adda?.."Aysha tace"yes Billy kawai mu bari ya dawo sai ya kaimu muyi lunch dinmu a waje"..Billy tace"to ku fara cin wnn din"..ba musu su hajia Husna aka sauko aka dauki lemo da cake za'a fara sha sai tace"wai ni ina bestynku ne kam?..tunda mukazo banji wata tayi mgnrshi ba"..dan ta6e baki Billy tayi tace"bestynta dai"...Husna na daria tace"aah Adda Billy hadda ke wlh"...tace"God Forbid"...Lamido dake sauraronsu tana daria itama tace"Husna karki damu anjima kadan zaki ganshi a nan indai besty ne...baima san zakuzo ba nasan da tun daxun yazo"...Husna data fara shan lemo da cake dinta tace"ya kamata yaxo mu gaisa dai gaskia...Yusee bazaki ci cake din ba koh?.."Aysha da kanta ta dauki lemo da cake din ta mika mata itama ta amsa ta fara ci. Karfe daya da wajen rabi Hamman nasu ya dawo...nan ya kirasu a waya duk suka sake shiryawa snn suka fito ya kwashesu suka tafi...basu tsaya iya eatery kadai dan har shopping saida ya kaisu dukda suna ce mishi basu bukatan komai and sun kusa yin hutu Hamma Najeeb bai sauraresu ba saida ya kwasan musu duk wani abu da yasan students kamarsu suna bukata...su Husna kuwa kayan kwadayi sukaita kwasa itada Yusra kaman ba gobe...kan hanyansu na komawa Hostel Husna taga wani sabon cinema a kan zaria road tace"Hamma dama ka shiga damu cinema muyi kallo wlh..kasan inason kallo a cinemas"...shidai baice komai ba sai kai daya girgiza mata...bayan sun koma hostel suka samu wani wuri kaman garden suka zauna su Yusra nata cin kayan da suka siyo shi kuma ya dubi Aysha sosai yace"i hope kin hakura da batun komawa gida koh?.."ta wani rausayar da kai tace"ai nasan daddy bazai yadda ya cireni ba"..yace"good u understand that..yanxu inaso ki zama more careful kan komai da zakiyi..kinga ko a gida dama kinada wnn careless din sai ki jona abu a wuta kice zaki tafi wani wurin ki barshi ko kuma kice kin manta dashi..yanxun da yazo da tsautsayi wuta ya kama dakin fa kinga da gaba daya konewa zakuyi"...tana wani turo baki tace"na dena Hamma"...yace"Good...kema Bilkisu inaso ki kara kisa min ido a kanta sosai...duk kikaga ta jona abu zaka tafi ta barshi ki kira koni ko Ammi ki fada mana"...da sauri Billy tace"inshaAllah Hamma"...daga haka ya mike zuwa mota sai gashi ya dawo da wani da akayi wrapping kaman gift guda biyu...ya mikama Aysha daya itama Billy ya bata daya...Aysha ce ta fara bude nata taga wani hadadden mug fari mai daukeda logon Man United sai wani sbu kaman doll da akayi mishi siffar Pogba yana sanye da kayan ball sai kuma hannunshi rikeda ball din a can kasan abun aka rubuta Man of the Match sai kuma latest jessy dinsu red and black mai daukeda logon Man U itama bayanta kuma sunan Pogba ne da katon number 6 a jikin wandon ma haka...sbd tsabar farin ciki Aysha batasan sanda ta rungumeshi taba daria ba...wnn karon shima rungumeta back yayi yana ganin how happy she looks...dama yasan yanda take son Manchester da Pogba dole ma zataji dadin gift din shiyasa ya siyo mata...saida suka gama hug dinsu snn ya dagota yana kallonta yace"hope u like it"..da sauri tace"i like it mana sosai ma Hamma...kasan tsakanina da Pogba ai"...yace"na sani shiyasa na siyo miki"...tace"nagode sosai Hammana Allah ya saka maka da alkhairi ya baka mata ta gari"...ya dan ja cheeks dinta yana daria yace"Ameen Mamana"...Husna ta hade rai tace"ai dama Hamma munsan zaman da zamuyi dakai...nasan wlh kafi son Adda akanmu"...murmushi kawai yayi yace"Husna kenan"..ya juya ga Billy dake rikeda nata gift din tana kallonsu tana murmushi...yace"if you are done smiling kema saiki bude mana naki mu gani"...ba musu ta dakatar da murmushin da take ta shiga bude nata...komai na ciki iri dayane the only difference shine ita nata na PSG ne madadin Manchester doll din kuma na Mbappe instead of Pogba...sosai murmushin dake fuskanta ya fadada...sai taji itama kanta da d'an uwanta ne ba abunda zai hanata rungumarshi tsabar farin ciki...full of excitement tace"Nagode Hamma Allah ya saka da alkhairi"..yace"Ameen Hajia Bilkisu..yanxu bari muzo mu dauki hanyan kunsan tafiyanmu da nisa"...nan da nan Aysha ta kwa6e fuska tace"Hamma tun yanxu?.."yace"banaso muyo dare ne Maama kuma anjima kadan zakiga Ammi ta fara kira so gara mu tafi sbd mu sauka da wuri"...bata kuma cewa komai ba sai turo baki da tayi...gaba daya suka mike suka fita daga wajen...suna zuwa jikin motanshi kafin su shiga motan Sa'eed ya karaso wurin...yayi parking da sauri ya fito zuwa inda suke yace"Hamma badai tafiya zakuyi ba?.."yace"wlh tafiya zamuyi Sa'eed banaso muyi dare a hanya"..Sa'eed ya juya yana duban su Husna yace"yammata"..tana wani fari da ido tace"sunana Husna Lamido"...yace"to sannu Husna Lamido ya hanya?.."tace"Alhamdulillah Hamma bestie"...ya dan wara ido kafin yace"har yanxu Hamma bestyn nan dai?.."tace"eh mana ba bestie sunanka ba?.."yace"sunana Sa'eed"..ta wani makale kafada tace"oh oh nidai hamma bestie zance"...bai sake mgn ba sai murmushi da yayi...ya karasa wurin Yusra suka gaisa itama tana cewa hamma besty shi kuma yana bayaso...haka dai suka gama gaggaisawa daga nan suka shiga mota suka tafi...Lamido tabi motan nasu da kallo idonta na cikowa da hawaye...Billy ta kwashi gifts dinsu tayi ciki shi kuma Sa'eed ya jata suka zauna yana fadin"haba mana bestie..bakya gajiya da kuka ne?.."ta wani sake tale baki tace"bestie na gaji da makarantan nan wlh..infact am tired of the whole city i want to go home"...murmushi ya saki ganin yanda take mgn sai kace yarinya cikin ranshi yace"gaskia mijin bestie zaisha fama wlh"..a fili kuma sai ya shiga ban baki da bata hakuri har ya samu da kyar ta tsayar da kukan. Koda Bobby ya isa gida Mummy kadai ya samu a central parlor...ya karasa kusada ita ya zauna yana duban illham dake bacci kusada ita yace"Mummy ke kadai?.."tace"wlh ni kadai ne Bobby yanxun Miemie da Sabeer suka fita wai zata rakashi anguwa..Sumayya kuma tana daki tun safe ni bansan meke damunta ba"...da sauri yace"ni nasan abunda ke damunta..Isma'il ne"...da mamaki sosai Mummy ke dubanshi tace"Isma'il kuma?..wane Isma'il kenan?.."yace"Isma'il dai da kika sani baban su Miemie"...idan kaga yanda Mummy ta zaro ido zakayi zaton wani gagarumin abu ya fada...tana shirin bude baki tayi mgn Aunty Sumy ta shigo parlorn...saita dakatar da abunda zatace kawai ta juya tana kallonta har ta karaso ciki ta zauna kaman itace Isma'il din...Mummy tace"are you serious Bobby ko dai wasa kakeyi?.."yace"Mummy am jet serious wlh..nayi blocking number nashi dai ban saniba ko ya sake kira".. yans rufe baki Aunty Sumy tace" ya kira"...gaba dayansu suka juya suna kallonta...tace"yanxun nan ya kira shiyasa ma fito dan in fada maku"...wani salati Mummy ta saki tace"to me yake nema kuma a wurinmu?..me yake ce miki idan ya kira?.."tace"ranan dai ban tsaya naji me zaice ba kawai ina jin voice dinshi na kashe...yau kuma tambayana su Miemie yake kuma wai in taimaka in yafe mishi"...shiru kawai Mummy tayi tana kallonta kaman statue...Bobby kuma ranshi yaji ya 6aci da wnn rainin hankali...idan ba rainin hankali ba yaran da yayi abandoning shekara shekaru bai ta6a kira yaji ya suke ba a matsayin babansu shine rana tsaka yanxu zai wani kira ya tambayesu?..shi har yanxun bai dena mamakin irin guts din Isma'il ba...hannu kawai ya mikama Aunty Sumy yace"bani wayan"..ba musu ta mika mashi..yana kar6a ya zare sim card din gaba daya snn ya mika mata wayan yace"saidai ki hakura da amfani da sim din for a while...idan na shiga ciki zan dakko maki new sim card ki fara using zuwa dan wani lokaci"...batayi masa musu ba ta amsa da toh...ita kanta tasan ajiye sim din is the only way da zai rabata dashi don tasan indai yana nan a Isma'il data sani some years back to bazai ta6a dena kiranta ko zatayi blocking dinshi sau 100 kuwa...idan babu sim din kuma dolenshi ya hakura idan ya kira yaji baya shiga...Bobby dai mikewa yayi ya wuce flat dinshi cikin ranshi yana ayyana kalan rashin mutuncin da zaiyima Isma'il din nan...su kuwa zaman shiru sukayi a parlorn sai kace kurame...suna nan zaune Miemie da Sab suka shigo suna fada kaman ba sune suka fita daxu rimi rimi ba kaman basu ba...Aunty Sumy ce tayi karfin halin cewa"meye haka ne wai?..wane irin iskanci ne wnn zaku shigowa mutane kuna fada?..bakuda hankali ne?.."Sab yace"Aunty wai Miemie sbd batada kawai sbd wani friend dina yace yana sonta saita yadda?.."juyawa tayi tana duban Miemie fuska daure kafin tayi mgn Miemien tace"Aunty na ranste da Allah ba haka bane...ina cikin zamana fa kawai yazo ya fara min mgn shine shi kuma yake cewa wai na kulashi"...tun kafin ta rufe baki Sab yace"karya kikeyi i saw the two of you laughing "...itama ta bude baki zatayi mgn Aunty Sumy ta daka musu wani tsawa tace su 6ace mata a wurin...ba shiri suka kada kafafuwansu suka bar parlon. Masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 09 Ranan Thursday da wuri suka shiga school sbd sunaso su zauna da group dinsu before time na presentation...tun 7 suka hadu gaba daya class suna rehearsing karatunsu...karfe 8 daidai kuma suka fara lectures dinsu...inshort basu fito daga class ba sai around 1..suna fitowa suka nufi cafeteria don cin abinci...a ciki suka hadu da Sa'eed yayi musu reserving table suka karasa suka zauna kowa ya bada ordern abinda yakeso...sunyi shiru kawai abincin sukeci don ko breakfast basuyi ba suka fito...kaman daga sama kawai suka ga mutumi yaja empty kujera dake kusa dasu ya zauna...a tare suka dago kansu duk su ukun suna kallonshi...Tajuddeen ne sanyeda uniform dinshi as always yanata kallon Lamido yana sakin murmushi...Billy taja wani tsaki tacigaba da cin abincinta...shima Sa'eed cigaba da cin nashi yayi ba tareda yace komai ba...a hankali Lamido ta ajiye spoon din hannunta tana dubanshi kaman zata sa kuka tace"what?.."kaman jira yake yace"magana nakeso muyi dake kinata min wulakanci Lamido...dan Allah ki bani dama ko Hostel ne nazo sai mu tattauna a can"...yana rufe baki tace"ba damuwa u can come to the hostel anytime u like...yanxun dai kayi hakuri ka tafi cox muna gama cin abincin nn class zamu koma"...ya danyi shiru yana kallonta kaman bai yadda da abinda ta fada ba yace"U sure?.."cikeda assurance tace"💯Sure...just go we'll talk later"...bai sake cewa komai ba ya tashi daga wurin...sai kuma ya tsaya yana kallonta yace"i love you "...gyada mishi kai kawai tayi ya juya ya bar wurin...yana tafiya Billy kaman jira take ta dago tana hararanta tace" ki tabbata a kunnen Ammi duk wnn maganan da kukayi...shine hadda wani cewa yazo hostel ya sameki sbd tsoronshi kikeji koh?.."girgiza kai kawai tayi ta cigaba da cin abincinta as batada energy din rigima da Billy yanxu sai cikinta ya dauka...bestie dai yana zaune pretending kaman baya sauraronsu har suka kammala ya biya kudin gaba daya snn suka fita...su suka wuce female masjid dan yin sallah shi kuma ya koma class cox ya riga yayi sallah tun daxu...suna idar da sallah kiran provost ya shigo wayanta...ta dauka da sauri tana fadin"Good afternoon Sir"...yace"afternoon Lamido are you guys ready?..proprietor ya shigo tun daxu and in the next few minutes zakuzo Auditorium hope you are all set?.."tace"we are Sir "...yace" alright tell them mu hadu auditorium by 2".. a hankali tace"toh.."suna gama mgn ta ajiye wayan a hankali cikin ranta tana nanata Auditorium kuma?...Common presentation da zasuyi shine sai an kaisu har wani auditorium sbd shegen iyayi...tasan duk wnn ba plan din kowa bane sai na wancan inyamurin mutumin...kawai presentation za'ace su tafi har auditorium sbd neman magana. Karfe biyun kuwa cikin Auditorium din yayi musu...basu jima da zama ba malamai suka shigo su wajen 4 hadda Sir Abdool dinta inji Billy😆..sai shi proprietor din sai provost...daga dan sama kadan malaman suka zauna inda aka tanadar musu kaman high table haka...bayan gaisuwa da dogon bayani daga malaman akace the 1st group should come forward... a yanda suka tsara abun dama ba gaba daya members na kowane group zasu fito ba..each group dunyi selecting mutum uku da zasuyi representing dinsu cox idan akace gaba daya kowa sai yayi bazasu samu gamawa da wuri ba...kaman yanda yake alphabetically group din farko nasu Lamido ne dan haka ba wasting of time suka fita ita da sauran colleagues dinta...first speaker ce ta fara musu bayani tun daga introduction zuwa definition of terms haka..bayan ta gama second speaker itama tayi nata Lamido kuma itace karshe...saida duk suka kammala ta amsa markern dake hannun colleague dinta tareda karasawa jikin white board dake daga gefensu ta zana diagrams dake cikin topic din nasu tayi labelling snn ta fara explanation...sosai Audit din yayi tsit tun daga dalibai har malaman kowa ya nutsu yana sauraronta...da yawa daga cikin malaman dama sun santa tunda akwai wani end of year presentation da sukeyi duk end of session and ko na last year da akayi itace tayi winning...bayan wnn akwai wani tradition da suke dashi a school din at the end of every session ana fitar da overall student for both Nursing and Midwifery departments snn kuma a fitar da Wanda yafi kowa point a gaba daya college din as the overall student of the year...zaayi printing qaton poster mai daukeda pictures na overallers din kowa da sunanshi dana department dinshi sai kuma point dinshi...haka zaa kafe wnn postern kusada general notice board snn a sake kafe wani ta wajen admin block...so da yawa cikin malaman ko basu santa a zahirinta ba sun santa either a wancan poster tunda last year ita tayi overalling a department dinsu ko kuma a end of year presentation da akayi na last year...shi kanshi Bobby yau sai yaji wani abu daban gameda yarinyar...bama ita kadai ba gaba daya class din sun burgeshi sosai coz sunada kokari..cikin ranshi yake ayyana wai haka duk students din nashi suke da kokari ko kuwa iya class dinsu ne haka?..yana cikin tunaninshi yaji Audit din ya kaure da wani irin loud tafi yana dubawa sai yaga ashe sun gama shine ake musu tafi...babu 6ata lokaci group two suma suka fito sukayi nasu followed by group three wanda sune last group...bayan sun gama gaba daya student affairs dinsu ya tashi yana praising dinsu tareda karfafa musu gwuiwa kan karatunsu...bayan ya gama provost ma yayi nashi sai kuma mai gayya mai aiki Alhaji Dr Bobby jikan Waziri lol😃..shima praising dinsu yayi sosai snn ya fadam each group marks din da sukayi scoring wanda dashi zaayi amfani a matsayin c.a dinsu..bayan ya gama malamai suka fara fita followed by students din...kafin su karasa class kiran Sir Abdool ya shigo wayanta...ta dauka tana gaisheshi yace"Lamido can i please see you now?.."ta danyi shiru tana tunanin ne zatace mishi ya sake cewa"ba dadewa zakiyi ba Please!"...ba yanda ta iya haka nan tace mishi gata nan...ta dubi Billy da suke tafiya tare tace"kinji Sir Abdool wai inje...ni kuma na gaji wlh so nake in koma hostel in kwanta"..kar6an text book dake hannunta Bilky tayi tace"yace fa ba dadewa zakiyi ba..kiyi hakuri kije ni zan jiraki a class"..Aysha tayi murmushi tana jinjina wnn so da Billy ke mishi ta juya ta tafi...tazo daidai kofan office dinshi tana shirin budewa Bobby da Nur suka fito daga office din Nurun...ta dauje kanta da sauri sakamakon idanunshi da suka sauka a kanta...ta budr office din da sauri ta shiga su kuma suka wuce don dama tafiya gida zasuyi...tana shiga ya mike daga zaunen da yake tareda dawowa kan soafer ya zauna ya nuna mata kusa dashi itama batayi mishi musu ba zauna...ya tsura .ata ido yana sakin wani shegen murmushi yanajin ina zai saka yarinyar nan ne tsabar son da yake mata...itadai kanta na kasa as batason wnn kallon kasa kasan da yake mata...shi kuwa rasa kalmomin da zai furta mata yayi sai kawai ya kamo both hannayenta yakai su bakinshi yayi kissing kafin ya ajiye yana fadin"i love you"...daure fuska tayi sosai tana dan turo baki ta kalleshi...yasake sakin wani murmushi yana shafa gashin kanshi yace"Ya Allah"...ganin ta sake tsuke baki ya kama ears dinshi yace"am sorry sonki ne yayi min yawa wlh Lamido..so accept my apology inshaAllah bazan kara ba"..batace mishi komai ba sai mikewa da tayi yace"please forgive me"..ta gyada kanta kawai ta fita daga office din. Da dare Hostel suna cin abinci itada Billy kiran Daddy ya shigo wayata...tayi saurin hadiye na bakinta ta sake daidaita nutsuwarta snn ta daga tana cewa"Hello daddy barka da dare"..Daddy yace"sallamanki kenan ba?.."da sauri tace"sorry daddy..salamu alaykum barka da dare"..yace"barka dai ya studies?..hope you are doing well?.."tace"inayi daddy ya aiki"..yace"Alhamdulillah na dawo gida..ba wani matsala koh?.."tace"ba komai daddy"yace"MashaAllah bawa Bilkisu waya"..ba musu ta mikama Billy wayan..itama ta kar6a da sallama tana gaisheshi..yace"inda kika fita hankali knn?..ya karatu fatan ba wani matsala?.."tace"babu komai daddy"..yace"to Alhamdulillah aci gaba da dagewa sosai..Allah muku albarka"..Billy ta amsa da"Ameen mungode daddy Allah ya kara girma"..shima yace"Ameen"..daga haka ya kashe kiran...Aysha ta kar6i wayan tana sauke ajiyar xuciya tace"sai yanxu hankai na ya kwanta..da naga kiran nayi zaton ko wani laifin nayi"...Bilkisu ta girgiza kai tana cigaba da cin abincinta tace"bakida gaskia ne ai shiyasa". Bobby bai samu dawowa gida ba sai yamma likis...su Miemie ya samu a parlor suna kallo..gaba daya suka mishi sannu da zuwa ya amsa idonshi kan Sab da hankalinshi gaba daya ke ga phone dinshi yace"kai yaushe zakuyi resuming school ne?.."Sab yace"next week ne but dan Allah inaso in kara ko one week ne plss"..bai rufe baki ba Bobby yace"C'mon keep quiet..waye zai bari ka kara one week din?..you are deceiving yourself"...daga haka ya kama hanyan parlon Mummy...ga mamakinshi bai sameta a parlon ba sai ya nufi bedroom dinta yana mamakin meye sa bedroom da wuri haka...Allah yasa dai lafiyanta qalau...yana tura kofan ya shiga sai sallaman da yake kokarin yi ya makale a bakinshi sakamakon abunda ya gani...Mummy ce zaune gefen gado tana hawaye Anty Sumy na zaune kusada ita tana hawayen itama...baisan lokacinda ya saki suit dinshi dake a hannunshi ba ya karasa cikin dakin da sauri...gefen Mummy ya zauna ya kamo hannayenta hankali tashe sosai yace"Mummy what is happening here?..why are you two crying?.."damke hannunshi Mummy tayi ta juya tana kallonshi tace"your grandfather Bobby..Waziri..idan bawan Allahn nan ya mutu baisan inda kuke ba bazan ta6a yafema kaina ba Bobby..you need to see his condition..he is seriously.."bai bari ta karasa ba ya rungumeta a jikinshi...itama saitayi lakwas a jikin nashi tana cigaba da hawaye...suka hada ido da Anty Sumy dake kallonsu tana hawaye itama..da ido ya tambayeta me yake faruwa ta buda mishi hannu alaman he has no idea...saida yaji kukan nata ya dan tsagaita snn ya sake dagota still yana rikeda hannayenta yace"Mummy kukan ya isa haka please kar bp dinki yayi rising..besides waya fada maki condition da wazirin ke ciki?..how did you know?.."tace"a news na gani wai ciwon nashi yayi worst har sun daukeshi daga Egypt zasu maidashi india..Bobby he is seriously sick inaso kuje ku dubashi idan ya dawo"..cikin 6acin rai tuno abubuwan da suka faru a baya yace"but Mummy why?..why zamuje dubashi bayan bai damu damu ba..bai damu ko muna raye ko mun mutu ba?.."yana rufe baki tace"because he is your grandfather Bobby..komai girman laifin da yayi he is still the father to your Dad and nobody can change that"..ta kamo hannunshi snn tacigaba"do you think if your Dad was alive zaiji dadin yanda kake treating mahaifinshi?..do you think he would be happy if we choose to hide ourselves from them komai girman abunda suka aikata?.."a hankali ya zame hannunshi daga nata lokaci daya idonshi sukayi jajir sbd 6acin rai yace"but Mummy we didn't hide ourselves from them sune basuga daman su nemi inda muke ba..for five long years Mummy idan suna sonmu meyasa basu nememu ba?.."yana rufe baki tace"because he is sick Bobby..sanin kanka ne tun ranan da mahaifinku ya fadi ya mutu bai sake samun lafia ba"...cikin anger daya fara kasa controlling yace"dukda bashida lafia if he really love us..if he really want to see us he could've at least ask one of his selfish and wicked sons to look for us but he didn't and do you known why?..because he hates us..he despise..."bai kai ga karasawa ba yaji saukan kyakyawan mari a cheeks dinshi...ya dafe cheek din da sauri yana duban Mummy dake kallonshi rai a 6ace itama...Anty Sumy ta taso da sauri ta kama hannun Mummy hawaye na wanke fuskanta tace"Mummy take it easy please..kinsan condition dinki Mummy kar wnn abun yasa bpnki yayi rising please"..ta karasa mgnr tana kuka sosai...Bobby da yayi suman wucin gadi sai yanxu ya dawo hayyacinshi...tun da yake zai iya counting sau nawa Mummy ta dakeshi but now she slapped him sbd azzaluman mutanen can..wasu hawaye yaji suna cikowa idanunshi amma ya dake bai bari sun zubo ba ya dora kanshi a shoulder dinta murya can kasa yace"am sorry for hurting you Mummy amma kinsan gaskia nake fada fa..mutanen nan basu ta6a kaunarmu ba Mummy..kema basa sonki amma meyasa kikeso mu sake kai kanmu inda suke bayan duk laifukan da sukayi?.."dago kanshi tayi tareda cupping fuskanshi tace"because they are your relatives Bobby..they are your Family and Family will always be considerd as Family nor matter what..so try to understand me please"...shiru kawai yayi yana yanajin yanda maganganunta suke neman kashe mishi jiki...Anty Sumayya dai na zaune tana kallonsu..itama Mummy ganin tasirin da maganganunta sukayi ta sake yin kasa da murya tace"try and understand Bobby please..ko bamu nemesu yanxu ba dole watarana dalili zai sa mu nemesu shiyasa nakeso mu daidaita dasu tun kafin zuwan wnn lokacin.."shiru ya sakeyi idanunshi lumshe yana sauraronta...ita kuma Mummy ta dan saki murmushin cin nasara snn tacigaba"kaga watarana Aurenku ne zai taso kuma nasan kasan duk dunia babu inda mutum zaije neman aure a bashi ba tareda dangin mahaifi ba..and gaba daya ku ukun babu wanda keda aure gara Sumayya ta ta6ayi hadda yara amma kai da Sabeer baku ta6ayi ba Bobby..dole kuma watarana lokaci zaizo da zamu bukaci suzo su nema muku aure"...sake daure fuska yayi jin ta fara zancen aure yace"indai wnn mutanen ne zasu nemamin aure Mummy wlh na gwammace har in mutu banyi aure..Anty Sumy da Sab kuma duk wanda bazai kar6i aurensu a wurina ba saidai ya hakura"..ta bude baki zatayi mgn ya dora finger dinshi kan bakinta yace"enough talking about them please..yanxu ki samu ki kwanta kina bukatan hutu sbd bp dinki..maganan zuwa dubiyan Waziri kuma Allah ya dawo dashi lafia sai muje"...lokaci daya murmushi ya mamaye fuskanta tace"da gaske zakuje Bobby?..tasan indai ta samu ta shawo kanshi ragowar basuda matsala dama Bobbyn shine mai taurin kain...yace"anything for you Mummy..yanxu dai ki samu ki huta sosai"..da sauri ta shiga gyada mishi kai tace"Allah ya muku albarka"..yace"Ameen Mummy"..Anty Sumy ce ta taimaka mara ta kwanta shi kuma ya juya a hankali ya fice daga dakin zuwa nashi...a gurguje yayi wanka tareda alwala ya fito ya tayar da sallah tubda an idar a masallaci...ya dade zaune yana addu'a kan Allah ya mantar da Mummy mgnr zuwa dubiyan nan dan fa shi har yanxu baiji zai iya daukan kanshi ya kai Gombe ba..har abada gani yake bazai ta6a iya mace kalan rashin imani da suka gwada musu ba har shi wazirin daya kasance kakansu...da kyar ya samu ya mike daga wurin da yayyi sallahn ya fada kan gado ya kwanta...ya runtse idonshi da karfi yana jin duk wani abu daya faru na daow mishi kaman yanxu yake faruwa...bayason yana wnn tunanin amma ya kasa dakatar da kanshi. ASALIN LABARI... Our free pages sun kusa karewa fa..keep on subscribing before kuji diff kaman an dauke wuta😹 Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 10 ASALIN LABARI... Lokacinda Attahir wato mahaifin Bobby yakai ma mahaifinshi Wazirin Gombe mgnr yanason Auren Nadia daya hadu da ita a kano kai tsaye yace bai amince ba sbd kasancewarta ba bahaushiya ba...hankalinshi ya tashi sosai ganin da gaske waziri naso ya rabashi da matar da yafi kauna a dunia..ya jema mahaifiyarshi da mgnr itama ta nuna batada taimakon da zata iyayi masa har tunda mahaifinshi yace ya hakura da ita kawai ya hakura...bai hakuran ba yacigaba da lalla6a waziri yana nusar dashi illar nunama wanda ba yarenku daya ba banbanci...ya kuma nusar dashi cewa har tunda ta kasance musulma kuma yar Nigeria yana ganin ko addini bai haramta mishi aurenta ba...ran waiziri ya 6aci sosai ya kuma ce matukar shi ya haifeshi bazai ta6a amince mishi ya auri inyamura ba...wnn mgn ba karamin daga hankalin Attahir yayi ba...step brothers dinshi da suke ganin waziri ya fifitashi a kansu nan suka samu damar shiga suna cigaba da ingizashi kan kar ya yadda ya amince ya hada jini da inyamurai wnn zuga kuma yayi tasiri a wurinshi sosai...Attahir da yaga bashida wani mafita kuma bazai iya hakura da Nadia ba kai tsaye yaje ya samu kakarshi mahaifiyar waziri knn yayi mata bayanin duk abunda ke faruwa nan kuma ta goyi bayan lallai sai an aura mishi matar da yakeso...hakan ba karamin 6ata ran waziri yayi ba amma ya hakura ba don yanaso ba ya tura aka nemo masa auren yarinyar har Enugu state bisa umarnin da mahaifiyarshi ta bashi kan lallai lallai ya aurama Attahir matar da yakeso idan baiyi haka ba kuma itama zata tsine masa kmr yanda yayi ikirarin zai tsinewa nashi dan. Cikin lokaci kankani akayi bikinsu aka gama...sbd sanin da yayi cewa yan uwanshi da mahaifinshi ba son auren suke ba sai ya nema mata gida a kano ta zauna itama tacigaba da karatunta...tsakaninshi da Gombe saidai yaje ya gaisa dasu ya dawo kanon ma kuma bai cika zama ba sbd a lokacin yana aiki a Delta state...tun bayan aurensu kuma ko mutum daya baizo daga cikin 'yan uwanshi da sunan yazo ganin matarshi ba...a haka suka dauki tsawon shekara daya bata ta6a ganin wani nashi a inda take ba..a lokacin ta damu sosai da rashin zuwan nasu shi kuma saidai ya bata hakuri yace mata komai zai wuce...ana haka ya samu kira daga waziri kan lallai ya tattaro ya dawo Gombe da zama a cewarshi wai matarshi ke hanashi zuwa ziyararsu yanda ya kamata...baiyi nasa musu ba ko kadan as baison ya sakeyin laifi a wurinshi haka ya tattarata kaman yanda wazirin yace suka koma gidanshi dake cikin Gombe...da farko Nadia taji dadin komawan nasu sbd tana ganin idan tana kusa da yan uwanshi zasufi saurin kar6anta a matsayin suruka sai kuma daga baya ta gane mutanen nan bazasu ta6a kaunarta ba...kyara da tsangwama ba kalan wanda bata gani ba a wurinsu abun har ya kai ko taro sukeyi bata isa ta shiga cikin matan brothers dinshi ba dan zasu yita jifanta da munanan kalamai suna cewa ita inyamura ce..hatta yaransu sunan da suke kiranta dashi knn inyamura...a lokacin data samu cikin Sumayya tayi farin ciki sosai sbd tana ganin kilan idan ta haihu zata iya samun soyayyar waziri dana sauran 'ya'yanshi ko dan sbd abunda zata haifa...mahaifiyar mijinta dama bata ta6a samun matsala da ita ba hakama Munubiya..kawai dai basa iya sakewa su nuna damuwa da ita sosai sbd gudun 6acin ran waziri...duk wnn abun da ake Attahir bai ta6a daga baki yace zaiyi mgn ba sbd yasan ko yayi ba amfani zaiyi ba tunda goyon baya suka samu wajen waziri...'yan uwanshi da dama tuni yasan basa kaunarshi sbd soyayyan dake tsakaninshi da waziri shiyasa suke amfani da wnn damar suna rura wutar tsanarshi cikin zuciyar babanshi...yana sane sarai suke tunzurashi yake aikata duk abubuwan da yakeyi shiyasa bazai taba bude baki yayi complain ba fatanshi daya Allah ya rabashi da mahaifin nashi lafia. Lokacin da aka haifi Sumayya Attahir yayi farin ciki sosai hakama qanwarshi mahaifiyarshi sun tayashi murna matuka saidai babu daman nunawa sbd waziri...lokacin da ya dauketa ya kai masa ita ko kallonta baiyi ba yace ya fitar mishi da ita a wurin...wnn abu ba karamin 6ata ranshi yayi ba...yana ganin ko arniya ya aura bai kamata ace his own father yayi treating yarinyarshi irin haka ba..abun ya 6ata ranshi matuka...wnn dalilin yasa baiyi shawara dashi kan sunan da zaa sama yarinyar ba kamar yanda sauran 'yan uwanshi sukeyi duk wanda matarshi ta haihu shi ke za6an sunan da za'a sa...baiyi shawara da kowa ba yasa mata Sumayya sunan qanwar Nadia da bata dade da rasuwa ba a lokacin...aikam taji dadi sosai dan bata ta6a zaton zaisa sunan yar uwarta ba. Haka rayuwa yacigaba da tafiyan musu yau dadi gobe babu har Sumayya ta fara wayo..a lokacin itama sai aka fara tsokanarta da inyamura ko kuma su kirata da 'yar inyamura..wnn abu ba karamin daga hankalin mamanta yake ba amma ba yanda ta iya haka a koda yaushe take bata hakuri tareda fada mata cewa watarana komai zai wuce wnn dalilin yasa ko ina bata zuwa kullum tana gida nane da mamanta idan mahaifinta na gari kuma tana nane dashi...duk wnn abun dake faruwa Nadia bata nuna mishi damuwarta sbd yanda yake iya bakin kokarinshi yaga basuyi lacking komai ba itada 'yarshi. Bayan Sumayya saida ta dauki tsowon shekaru hudu kafin ta samu wani cikin...farin cikin da Attahir yayi da jin labarin cikin har mamaki ya bata...da dadewa tasan yanada son yara tunda tana ganin yanda yakeji da Sumayya amma yanda yake farin ciki da cikin ko wanda bai ta6a haihuwa ba sai haka...wnn dalilin yasa yake kulawa da ita yanda ya kamata...duk yake gari da kanshi yake kaita antenatal idan baya nan kuma tayi driving kanta...a kullum cikin godema Allah take sbd yanda mijinta har yanxu kiyayyan mahaifinshi dana brothers dinshi baisa ya canxa mata ba..ga kuma budi da Allah ke kara mishi a kullum. Lokacinda haihuwa yazo mata sai akayi rashin sa'a baya gari...daga ita sai Sumy a gidan gashi tanata kiran wayanshi bai shiga as dama ya fada mata zasu shiga jeji she might not reach him sbd network issue...ba yanda ta iya haka ta kira number wani brother dinshi tayi mishi bayanin halinda take ciki yace mata baya gari saidai ta kira wani...bata hakura ba ta sake kiran wani shi kuma yace zai turo matarshi amma shiru har kusan bayan awanni bai turo kowa ba..gaba daya ta fita hayyacinta as ciwon kara gaba yakeyi sosai gashi kuma batada number wani cikin brothers din nashi sai su biyu ga kuma sumayya daketa faman kuka tun daxu ganin halinda mamanta ke ciki...tayi kokarin kiran munubiya a waya itama bata sameta ba..a karshe dai dole sai sumayya ta aika tayi mgn da wata neigbour dinta ba bata lokaci matar tazo ta taimaka mata suka tafi asibiti...lokacin wajen karfe 9 na dare...suna zuwa aka kar6eta akayi labour room da ita..midwives kusan uku ne kanta suna kokarin taimaka mata amma har gabannin asuba bata haihu ba ga dan karen wahala da takesha...sun kira doctor da yake on call sun mishi bayani yace zaizo kawai ayi masa Cs kafin doctor din yazo kuma sai ta fara fitting(jijjiga)..hankali tashe one of midwives dake kulada ita ta sake kiran doctor ta fada mishi tana fitting yace gashi nan kan hanya ya kusa zuwa...dama tunda suka fada mishi yanda blood pressure dinta yayi rising yasan da kyar idan baiyi leading to preeclampsia ba. Doctor na karasowa basuyi wasting time ba suka shiga da ita theatre...neighbor dinta data kawota asibitin na tareda Sumayya da aka samu tayi bacci da kyar sbd jiya bata samu tayi sosai ba...before a shiga da ita theatre din kiran mijinta ya shigo wayanta dake hannun matar data kawota...nan tayi picking ta kumayi masa bayanin halinda ake ciki...hankalinshi ya tashi sosai ya kuma ce gashi nan tahowa Gombe yanxun nan...suna gama mgn ya wuce airport ya taki sa'a kuma ya samu flight din Kano nan ya sayi ticket ya zauna jiran lokacin tashi yayi. Bai samu isowa Gombe ba sai around 10...daidai lokacin kuma ake fitowa da ita daga theatre..baisan time din da hawaye ya cika idonshi ba ganin yanda aka turota kan trolley bed an rufeta da wani green kyalle kaman babu numfashi a jikinta...shiyasa tun jiya yakejin hankalinshi ba kwance ba ashe halinda suke ciki knn. Kai tsaye akayi moving nata Amenity dake female surgical ward...wanda suka kawota suka dagata daga kan trolley bed snn suka dorata kan bed din dakin suka fita...Nurse din da tayi resuscitating baby ta mika mishi babayn ya amsa da sauri itama ta juya ta fita..ya rage dagashi sai Sumayya a dakin dan matar data kawota kin shogowa tayi tace mishi zata koma gida...yayi mata godia tareda kyauta mai tsoka snn ta tafi...a hankali ya karasa kan wani kujera ya zauna har yanxun yana rikeda babyn a hannunshi...ya sauke idanunshi kan babyn da a kallon farko yaga tsantsan kamannin da yakeyi dashi...lokaci guda wani murmushi da bai shirya mishi ba yayi escaping lips dinshi...soyayya babyn yaji yanaji sosai har cikin jininshi..haka suka hada kai shi da little sumayya sunata kallon babyn daketa mustu mutsu abunshi. Lokacinda Anaesthesia ya saketa ta tashi daga bacci sai yaga hawaye a idonta...hankalinshi yakai kololuwar tashi ya kuma ce dole ta sanr dashi damuwarta...itama din ba yanda ta iya duk yanda take kokarin 6oye mishi abubuwan da suka faru kasawa tayi saida ta fada mishi...6acin ran da ta gani a fuskanshi bata ta6a ganin irinshi a tattare dashi ba..yanxu kiyayyan da suke masa har yakai ga suyi abandoning matarshi tana labour wanda ba dob taimakon neighbor dinsu ba da kilan yanxu ya rasa matarshi da kuma babyn data haifa..zai iya yafe komai amma banda wnn cin kashin da sukayi masa..wnn dalilin yasa ya yanke shawaran da zaran ta warke zai daukesu su bar Gombe gaba daya tunda baiga amfanin zaman nasu ba. Haka yake jinyar matarshi shi kadai sai neighbors dinta dake yawan xuwa kullum wasu har suyi girku su kawo...mahaifiyarshi ma bata taba zuwa ba sbd waziri daya hana amma munubiya zuwanta biyu shima duk wazirin bai sani ba take zuwa...saida ta samu sauki sosai yace ta fadi sunan da takeso a sa ma babyn nan take kuma tace sunanshi takeso yasa sbd tana ganin duk dunia yanxu batada wanda ya kaishi sai 'ya'yanta...baiyi mata musu ba yayi mishi hudu ba da sunan Attahir tace zasu ringa kiranshi Bobby. Daga asibiti ko gidansu basu koma ba suka wuce kano...bayan kwana biyu suka bi flight zuwa delta state inda a nan suka cigaba da rayuwa tareda yaransu. Bayan shekara biyu suka koma Lagos sakamakon transfer da akayi mishi ya koma Lagos din da aiki...lokacin Sumy nada 6 years Bobby kuma nada 2...tsahon wadan nan shekarun kuma basu sake zuwa Gombe ba saidai yaje shi kadai ya dawo...ana haka Allah yayiwa mahaifiyarshi rasuwa...wnn karon kam gaba daya suka tafi kuma basu dawo ba sai bayan kwana bakwai...har zuwa lokacin kuma daga waziri har sauran siblings dinshi babu wanda ke kaunar matarshi da yaranshi...haka akwa kwashi tsahon shekaru babu jituwa tsakaninsu wanda hatta yaran dukda ba wasu shekaru sukeda ba sunsan akwai matsala tsakanin iyayensu da familyn babansu especially Bobby da yafi 'yar uwarshi riko da kuma zafin zuciya. Sbd wnn matsalan yasa ko auren qanwarshi da zaayi bai samu labari ba sai gab da bikin...yaji ciwon hakan sosai sbd ganin cewa yarinyar nan batada kowa yanxun daga wazirin sai shi da suke ciki daya da ita tunda mahaifiyarsu ta rasu...haka sukaje Gombe suka dawo bayan kammala bikin. Bayan shekara goma Nadia da yaranta ke kira Mummy ta sake haifan namiji wnn karon yaron yaci sunan waziri Adam suke mishi laqabi da Sabeer. Zaman Lagos na musu dadi sosai don basuda damuwan komai kuma babu wanda ke kyamansu unlike Gombe da ko zuwa basu sonyi sbd yanda 'yan uwan Dad dinsu suke treating dinsu. Bobby nada 17 years ya gama secndary school Sumayya kuma already ta fara karatu a University of Lagos shi kuma Sab yana primary school...zuwa wnn lokacin mahaifinsu yayi kudi sosai dan yana matakin deputy controller General na Nigerian Custom...kai tsaye ya tura Bobby America dan yacigaba da karatunshi a can. Sumayya na kammala karatu aka aura mata isma'il da suka fara soyayya tun a university aka mikata gidanta dake Kanon dabo...unluckily itama mother inlow dinta bata sonta...dama Isma'il kadai ne danta namiji sauran duk mata ne suma kuma ba son nata suke ba...bayan shekara daya da biki ta haifi Miemie da aka sama sunan grandma dinta ta wajen uba wato Maryam ake kiranta Miemie...har zuwa wnn lokacin basa jituwa da sisters din mijinta dama mamansu gaba daya..kullum cikin nuna mata kiyayya suke kawai sbd ba ita sukeso ya auraba snn kuma da kasancewar Mum dinta igbo...wai Isma'il ya gur6ata musu family tunda ya hada musu jininsu dana inyamurai...haka aka cigaba da tafiya har ta sake haifan Ilham...ita kuma sunan Mummy aka sa mata Nadia ake ce mata ilham...wnn maida suna ba karamin tada rigima yayi tsakinshi da familynshi ba..wai don me zai sama yarinya sunan inyamurai...Sumayya da bata ta6a tanka duk abunda suke mata ba wnn karon kasa hakura tayi saida ta wanke su tatas ta kuma ce duk wanda ya sake izgili ga sunan mahaifiyarta sai sun kwashi 'yan kallo dashi...labari na zuwa ga Isma'il mahaifiyarshi ta sanyashi gaba da kuka wai matukar yana sonta sai ya saki Sumayya tunda batasan darajanta ba tayi mara rashin kunya...da sukaga bazai saketa ba sai sukasa ya sake auran 'yar sister din mamanshi sbd a kuntatawa Sumayyan...sunyi nasara kuma domin duk son da mijinta ke mata saida ta fara ganin canji tattare dashi...ya fara mata abubuwa wanda da ba haka yakeyi mata ba...gaba daya ma sai rayuwarshi ta koma 6angaren amaryarshi ita kuma ko oho don ko inda take bai cika zuwa ba...wnn abu yayi matukar daga hankalinta sosai tana ganin ko don yaranshi ai bai cancanci yayi abandoning dinta haka ba...daga karshe datayi kokarin nuna masa rashin dacewar abunda yakeyi sai yace taje ya saketa saki daya...bata sake wasting time ba kuwa ta hada kayanta ta wuce Abuja sbd a lokacin Daddynsu na matakin Controller General na Nigerian Custom so sun koma Abuja da zama...lokacin Ilham tana da shekara uku...haka suka cigaba da zama tareda iyayenta da kuma yaranta basu da matsalan komai...after a year Bobby ya kammala karatunshi a America lokacin shekaranshi kusan 9 a can...gaba dayansu suka shirya suka tafi America sukayi witnessing convocation dinsu snn suka dawo tareda shi Bobbyn da yakeda 27 years a lokacin...Sab kuma yanada 17 years kuma shima ya kammala secondary school. Bayan kaman sati biyu da dawowanshi suka tafi kano wani taro da akayi inviting Daddy sai yace suje gaba daya...suka sauka nan gidanshi dake garin shi kuma ya wuce inda zasuyi taronsu...duk tsahon wnn shekarun daga Bobby har siblings dinshi babu wanda ke marmarin zuwa Gombe sbd cikinsu ba wanda baisan kalan hatred da sukeyi ma Mummynsu da su kansu ba...Bobby kuwa a lokacin ko mgnrsu ma baisonji...wani lokaci sai Daddy ya kira waziri ya waya ya hadasu su gaisa amma kowa zai kar6a shi kuma sai ya kirkiri wani abun ya tashi ya bar inda suke...Mummy duk tana lura dashi ta kuma san baya kaunarsu ne sam amma ko kusa batajin dadin hakan...tanaso ace ya samu kyakykyawan mu'ala da dangin mahaifinshi ko don sbd nan gaba ba wanda yasan me zai faru sai Allah. A ranan bayan sun tashi daga taron shima ya wuce gida tareda zugan securities dinshi...misalin karfe 4:16 na yamma kiran wani brother dinshi ya shigo wayanshi...bayan ya dauka yake sanar dashi cewa waziri ne ba lafia kuma tun jiya yake cewa a kirashi yazo yanason mgn dashi...hankalinshi tashe sosai yace gashi nan zuwa Gomben yanxun...ba yanda Mummy batayi dashi kan ya bari da safe ba tunda yamma yayi amma yace sam bazai iya kwana while mahaifinshi nacan babu lafia kuma yana son ganinshi ba...babu yanda ta iya haka tabishi da addu'a...before ya fita ya shigo cikin gidan ya samu Miemie da Sab sai Sumayya a parlor nan yace musu zaije Gombe ya dawo suma suka mishi addu'an sauka lafia...yana shirin fita Bobby ya shigo parlorn rungume da Ilham da tayi bacci a hannunshi...shi kanshi yana ganinshi all dressed up yasan da akwai inda zaije...bayan ya fada mishi Gombe zaije ga mamakin dukkaninsu da shi kanshi Bobbyn yace zai rakashi...Daddy yayi mamaki sosai don sarai yasan duk yaran ma babu wanda yafi tsanan Gombe kamanshi amma yau shi da bakinshi yake cewa zai rakashi...bai yadda ya bishi ba yace zai tafi da driver shi kuma yanada bukatan ya zauna ko don ya kula da Mummy da sauran yaran...haka nan ya hakura amma har cikin ranshi baiso haka ba...shi kanshi baisan dalilinda yasa yau yaji yanason bin mahaifin nashi zuwa Gombe ba...duk abunda ke faruwa Mummy na zaune tana kallonsu itama bason tafiyan nashi takeba especially da yace dagashi sai driver zasu tafi bazai tafi da securities dinshi ba...a takaice bai samu ya bar gidan ba sai around 5...kaman yanda ya fada dagashi sai driver din nashi sukashiga mota suka kama hanyan Gombe...suna dab da shiga garin dan sun wuce Azare kawai sai ganin babban mota suka from no where tayo kansu gadan gadan...a kokarin driver na ya kaucewa motan sai kan motan ya kwace daya hannunshi gaba daya...daga nan kuma basu sake sanin inda suke ba sai ganinsu sukayi a Hospital...yana bude idanunshi yaci karo da waziri dake rikeda hannunshi idonshi yayi jajawur sbd tsabar rudun da yake ciki...ga kuma wasu daga brothers dinshi suma zaune a wurin...cikin tsananin ciwon kan dake addabarshi yayi kokari ya rike hannun mahaifinshi dake rikeda nashi...idonshi na zubda hawaye yake neman mahaifin nashi da ya yafe mishi...shima kanshi wazirin kaman zaisa kukan yace ya yafe mishi dunia da lahira..shima kuma yana rokon yafiyanshi kan duk abubuwan da ya aikata wa iyalinshi...shi kanshi yasan bai kyautawa abunda yake amma sam ya kasa denawa...yanxun kuma daya ganshi kwancs cikin jini sai duk wnn tsanar da aka sa yake mishi ya 6ace 6att sai tarin kaunar da yake mishi tun can baya suka shiga dawo mishi...lokacinda su Mummy suka karaso gaba daya ba wanda ke cikin hayyacinshi...kuka kawai suke har suka karaso inda yake...idanunshi ya shiga zagayawa akansu yanajin kaman kallon karshe yake musu...ya kalli Mummy da idanunta sukayi suntum sbd kuka sai Sumayya da har yanxu bata dena kukan ba...can gefe kuma Sab ne da Miemie suma rungume da juna suna nasu kukan sai kuma Bobby dake rikeda hannun ilham idanunshi a kasa sbd bayason suga yanda idanunshi suka sauya sbd kuka...hannu kawai ya mika mashi alaman yazo gareshi...cikin karfin hali ya saki hannun ilham tareda karasawa kusa dashi ya zauna ya kama dayan hannunshi da yake free...murmushi sosai yaga yanayi dan haka shima sai shiga kakalo murmushin yana kallonshi...cikin muryanshi da ko fita baiyi sosai ya nuna su Mummy dake jere suna faman kuka yace"na bar maka su amana...inaso ka kulamin dasu fiyeda yanda nakeyi...inaso ka zama gatansu...ko kusa kar ka bari suyi kukan rashina Bobby...they are now your responsibility"...kukane sosai ya kwace ma Bobby ya kasa cewa komai sai kai kawai da yake girgiza mishi...shi kuma ya sake kallon Mummy cikeda wani irin rauni yace"Your Mom...batada kowa Bobby...banaso tayi kukan rashina make sure ka kulada ita yanda ya kamata"...wnn karon ba Bobby kadai ke kuka ba gaba daya sauran ma kukan suke wiwi...suka hada ido da Sabeer shima ya mika mashi hannu yazo nan suka hada kai da Bobby sunata kuka abunsu...waziri dake zaune yana kallonsu bai ta6a jin ya tsani kanshi ba kaman yanda yaji a yanxu...kallonsu kawai yakeyi tunda suka shigo yanda ba wanda yabi ta kanshi a cikinsu...ya fuskanci akwai soyayya sosai tsakin yaran snn kuma yayi mamakin ganin yanda sukayi girma gaba dayansu...sai yakejin wani ciwo na rashin sakewa jikokin nashi da har Sumayya tayi 'ya'ya biyu bai taba ganinsu ba...ya kasa dauke idonshi daga kan Bobby sbd tsantsan kaman da yakeyi da Attahir dinshi...gaba dayansu ma sai yaji wani soyayyansu na daban na shiganshi...yaji gaba daya suna wani burgeshi gasu gaba dayansu tubarkallah dasu akwai kyau...hakika ya aikata kuskurenda shi kanshi baya tunanin zai iya yafema kanshi...bayan like an hour doctor yazo yace su barshi ya samu hutu...haka suka fita daga dakin sukayi cirko cirko a waje...Waziri dake waiting room yana hangosu sai ya fita daga dakin yace ace musu su shiga daka ciki su zauna...basuyi mishi musu ba suka shiga cikin dakin shi kuma ya kowa wani tareda yaranshi guda biyu da sukayi mishi rakiya...suna nan zaune akazo aka sanar dasu rasuwar drivern da suke tare dashi...hankalin kowa ya sake tashi masu kuka suka cigaba da gashi. In summary dai shima Daddyn cikin dare Allah yayi mishi cikawa...fadan tashin hankalin da suka shiga 6ata baki ne...Mummy kuwa dama ana fada mata ta fadi wurin a sume...har wahegari bata farfadoba ga kuma bp dinta da yayi rising sosai dole aka bata alluran bacci. Daga nan direct Gombe suka wuce dashi...lokaci daya mutuwan nashi ya watsu a gari kusan ko ina...karfe goma na safe akayi jana'izarshi aka kaishi gidanshi na gaskia(ubangiji kasa muyi kyakkyawan karshe)...shina waziri tun a wnn lokacin ya fadi dan ko jana'iza ba'ayi dashi ba...mutuwan ya dakesu ne sosai ba kadan ba...su Mummy kuwa gidanshi dake nan Gombe aka bude suka shiga itada yan uwanta da abokan arziki. Ranan da akayi kwana bakwai rigima ya 6arke tsakaninsu brothers din Daddy suka dage kan lallai bazasu fita daga Gombe ba tareda anyi rabon gado an fiddama mahaifinsu kasonshi ba...a cewarsu tunda mahaifinsu nada gado suma suna dashi wai idan suka yadda suka bari Gombe ba'a raba ba suna iya yin sama da fadi da wasu abubuwan...kasancewar Waziri na kwance tunda akayi rasuwar sai baisan abunda yake faruwa ba...tareda Bobby sukaita yawo duk inda kadarorinshi suke ya kaisu suka gani snn aka shiga kotu akayi rabo aka fitarma waziri da rabonshi kaman yanda yake a addinance...a ranan da aka gama a ranan ya tattara su gaba daya suka bar garin ba tareda ko waziri sunje sun duba ba...duk yanda Mummy tayi dashi kan suje suga jikinshi snn suyi mish sallama kin yadda yayi dan shi gani yakeyi ma kaman da wazirin aka hada baki aka kashe musu mahaifi tunda kira akai aka ce shine bashida lafia amma da sukazo sai sukaga akasin haka. Abuja suka koma direct sukayi parking abunda zasuyi parking...ya sai musu sabon gida a kano kuma bai yadda wani cikin 'yan uwan Daddy sun saniba snn ya sake daukosu suka dawo...gaba daya saida yabi ya canxa musu sim card dukda dama ba wani communicating sukeyi da yan uwan daddyn ba amma still saida ya canxa musu dan kwata kwata baison sake ganin kowa a cikinsu...su barsu suji da ciwon kashe musu mahaifi ma da sukayi...ko Sab da ba wani contact dinsu yakeda ba saida Bobby ya amsa layinshi ya bashi new one...Mummy dai bada son ranta yake abubuwan nan ba amma ko yaya tayi mgn sai taga ranshi ya 6aci fiyeda tunani...da farko ma cewa yayi sai yayi bincike if ya samu da akwai sa hannun one of them a accident din Daddy then bazai ta6a hakura ba saiya mgnr court...da kyar da sidin goshi Mummy ta samu ta taushe shi ya hakura da zancen...itadai har zuciyarta bata zargin akwai sa hannun wani a cikinsu...kawai tanaga ai duk kiyayyan da suke mishi bazasu iya aikata wnn danyen aiki especially akan dan uwansu...a lokacin abokan mahaifinshi da yawa suna kokarin taimaka mishi ya samu aiki amma yace shi sam bazaiyi aikin force ba infact bazai ma iya aiki under government ba...da taimakon wani uncle din Mummy wanda ya kasance likita ya bude katon Hospital dinshi mai suna Freedom Specialist Hospital...ya dauki ma'aikata sosai kuma most of them yare ne as gaba daya yanxu ya tsani hausa fulani because yana ganin kaman duk halinsu daya da 'yan uwan daddy...snn kuma ya tsani Gombe ya tsani duk wani abu daya fito daga garin...bayan shekara daya Allah yasa mishi albarka sosai dan ya kusan ninka abunda ya kashe a iya wnn shekaran...daga nan sai yayi tunanin ya bude Nursing and Midwifery College snn ya bude primary da secondary school duk a nan cikin kano...da yake kudi ne suke aikin in no time ya samu fili ya siya aka fara mishi aiki...a shekara na biyu ya bude Freedom College of Nursing and Midwifery Kano da kuma Freedom Science Academy Kano...nan ma yayi employing staff sosai suma kuma daga igbo sai yoruba sai kuma sauran tribes amma bai dauki bahaushe ko daya ba...a lokacin ya damqa Freedom Science Academy a hannun Aunty Sumy cox 6angaren data karanta knn shi kuma College din ya damqashi hannun abokinshi Dr.Nur...da shawarwarin Mummy dana sauran mutane abubuwa suke tafiya yanda ya kamata...cikin shekaru kalilan ya samu kudi fiyeda tunanin mai karatu...ya cire Miemie da ilham daga school da suke zuwa ya maidasu freedom shi kuma Sab ya nema mishi admission a Nigerian Police Academy Wudil as yana matukar son ya zama Police sbd it was his Dad's ambition. In summary cikin shekara biyar Bobby ya zama hamshakin mai kudi a kano state...tuni ya gina musu very big mansion a can airport road inda babu mutane sosai...gaba daya rayuwarshi yanxub bai cika son mu'amala da mutane ba especially hausawa cox yana ga kaman suma zasuyi treating nasu some how sbd kasancewar Mummy inyamura...gidane mai kyau da girman gaske inda babu wanda zai takurama wani a cikinsu...a takaice dai yana kulawa dasu sosai sosai kaman yanda yayima Daddy alkawari...cikin shekarun nan kuma ya sake bude another College of Nursing and midwifery a Lagos sai kuma Freedom College of Health Sciences and Technology shima a Lagos...da yake a can ya girma har yayi primary da secondary school so yanada mutane a can sosai da suke handling mishi Colleges din as bai cika samun time yana zuwa sosai ba saidai yana providing musu duk wani abu da suke bukata...bayan nan kuma ya bude Freedom Medical College Gwagwalada Abuja...itama ba karamin kawo mishi kudi takeyi ba and a wata baifi yaje sau daya ba wani lokaci ma sai yayi two months baije ba sbd aiyuka da suke mishi yawa...haka rayuwansu yacigaba da tafiya har zuwa yanxub da Mummy ke son dawo mishi da duk pain da agony da suka fuskanta a baya. Inaga gobe zaku jini shiru sbd zan danyi tafia...sai zuwa jibi in Allah ya kaimu💞🌸 Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidencs of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 11 Bayan sati hudu... Yau tuesday Aysha na zaune cikin dakinsu kan study table ta dora macbook dinta akan table din tana kallon wasan Manchester United da Liverpool live...sai ihu takeyi tana nishadi duk ta cika dakin nasu da ihu sbd best player dinta Pogba gana performing well...yana ta6a ball zata hau ihu yanxu ma daddagewa tayi ta kwalla wani uban kara tana fadin"Goaal..yes yes..go on senior Man..go ahead"...Billy data fita karatu tun daxun sbd exams da suka fara jiya ta shigo dakin rungumeda katon text book dinta a kirji...ta karasa ta ajiye text book din kan shelve snn ta shiga rage kayan jikinta tana hararan Aysha tace"duk kinbi kin cikama mutane daki da ihu sai kace a kanki aka fara kallon ball"...Aysha da gaba daya hankalinta ke ga abinda take kallo ta saki wani smile tace"bazaki gane bane Billy wani hadadden ci Ronaldo yayi yanxun nan...and kinsan waye yayi assist?.."sake ta6e baki Billy tayi tana daura towel a jikinta tace"ya wuce Martial ko Rashford...ko kuma wnn gantalallen Lingard din"...tace"to duk basu bane Pogba ne..kuma gaskia kika sake cewa Lingard dinmu gantalalle za'aji kanmu dake a hostel din nan"...sake ta6e baki Billy tayi tareda shiga bathroom...har ta fito daga wanka hajia indo na nan inda take tana kallon ball dinta...ihu kuma ba fasa yinshi tayi ba saidai Pogba bai ta6a ball amma sai tayishi...Billy tayi banza da ita ta gama shiryawa abunta snn ta shiga kitchen ta hado corn flakes ta fito...tana zaune tana sha wayanta yayi kara...ta dauka ganin one of colleagues dinsu dake cikin hostel ne...tambayanta yarinyan keyi yaushe zasu fita karatu dan duk aka fara exams suna haduwa suyi karatu gaba saya su 'yan class dinsu dake cikin hostel din su 15...Billy ta amsa da bata sani ba su tambayo Lamido...tana tsaka da kallonta mutum biyu suka shigo dakin...daya daga cikinsu tace"Lamido ya mgnr karatun mu na yau ne?..kowa yana Common Room fa ku biyu kawai ake jira"...san juyowa tayi tayi musu kallo daya duk hankalinta naga kallon da take sam bataso a wuceta tace"safiyya dan Allah kuje ku fara da Billy ana gama wasan nan zan zo"..tana rufe baki Billy tace"babu wani farawan da zamuyi kawai idan bazaki koyawa mutane ba ki fada musu ba sai kima hanya hanya ba"...ta fada tana wani basarwa tasan tunda ta fadi bazata iya cigaba da kallon ba dan a dunia ta tsani mutum yace tayi mishi wulakanchi taki koya mishi wani abu...harara sosai ta sakarwa Billy kafin ta juya tana dubansu tace"ku bani 5 minutes plss ana tafiya half time zanzo"...Billy ta juyar da kai tana kunshe daria dama tasan maganinta knn...kaman yanda ta fada ana tafiya half time din ta mike ta fita hajia Bilkisu tabi bayanta...gaba daya sauran sun taru a Common Room din su biyu kadai ake jira...dakin yanada girma sosai snn da akwai expensive set of kujeru masu kyau a ciki hadda su tv da fridge da standard ac inshort dai babu abunda babu ciki har su curtains da center table like normal parlor dai sosai...each apartment sunada Common Room dinsu da bama wani zama ciki sukeyi ba sai idan abu ya kama irin haka...bayan sun zauna Billy tace"to yanxu da wanne ya kamata mu fara"...da sauri wata tace"mu fara complicated midwifery dan Allah...daxun dana daukoshi zan fara karatu har wani hazo hazo naga ina gani sbd tsabar bana fahimta"...gaba daya sunyi na'am da haka dan haka suka fara da shi din...course outline dinsu suke dauka sunabi one by one suna explaining snn duk wanda yakeda tambaya ya fada a amsa mashi...suna gamawa dashi sukayi other course din da shima zasuyi exam dinshi gobe snn suka watse. Washegari bayan sun fito daga exam Aysha ta shiga kiran Sa'eed da tun safe bata ganshi ba...yana dauka tace"bestie where are you?.."yace"ina downstairs...kun fito daga exams?.."tace"eh..bari muzo downstairs din"...tana kashe wayan ta dubi Billy tace"muje yana kasa"...Billy ta wani hade rai tace"wai me zaiyi miki ne da kiketa nemanshi tun daxu?.."Aysha bata ce mata komai ba taja hannunta suka sauka kasa...can wajen wasu flowers masu kyau suka hangoshi yana zaune da wata class mate dinshi da alama yana koya mata abu ne...karasawa wurin sukayi suka zauna shi kuma ya sallami yarinyan da suke tare snn ya shiga kallonsu with a smile yace"so how was the exams?..Aysha tace"exam Alhamdulillah besty ya naka?.."yace"it was fine"...kallon Billy dake duba littafin hannunta yayi yace"so Bilkisu ya exams?.."tace"lafia lau"...ya kalli Aysha suka hada ido snn ya sske cewa"sai wani hade rai kikeyi sbd kin ganni...ki kwantar da hankalinki munayin counsil bazaki sake ganina ba"...ya karasa mgnr kaman wani abun tausayi...lokaci daya sai Billy ta dago tana kallonshi...idan akwai abunda ta tsana bai wuce yayi mentioning counsil exam ba duk sai taji jikinta yayi wani sanyi...ganin yanda ta kura mashi ido suka sake hada ido da bestyn shi sukasa daria...bayan sun gama yace" my Mom will be coming tomorrow.. hope zakuje ku gaisheta?.."da sauri Aysha tace"of course zamuje mana bestie..Allah ya kawota lafia...and yauwa bestie zaka kaimu lalle ranan Thursday idan mun fito daga exams...kasan cikin week din nan zaa fara bikin Adda Ruky"...yace"na sani besty amma baki ganin zaku samu matsala idan aka ganku da lalle?..nasan kinsan cikin ethics dinmu hadda kin applying wadan nan abubuwan"...tace"i know besty amma bansan ya zanyi bane...tun Thursday fa zaa fara bikin kuma ni bazan samu zuwa ba sai friday kaga banida time din yin lalle da sai na bari idan mun koma muyi...besides nafi son lallen kanawa yanxu..yafi namu kyau"...bai sake cewa komai ba kawai ya girgiza kai dan yasan tunda tasama ranta sai tayi lallen nan duk abunda zai fada ma ba changing mind dinta zatayi ba. The following day kaman yanda suka tsara bayan sun fito daga exams suka koma hostel sukayi changing kaya snn ya kwashesu zuwa Tarauni gidan kakarshi...suka samu Mom dinshi zaune a parlor da Hajia sai dan autansu Mahmud...suka karasa ciki suka zauna snn suka gaisheta...ta amsa musu da fara'a tana tambayan su ya karatu...suka amsa da fine...tace"ga bestie ga Bilkisu koh?.."Sa'eed dake sauraronsu yace"Mom ashe baki manta ba"..tace"ya za'ayi na manta tunda kullum cikin zancensu kake"...Hajia tace"nima nan haka yake damuna da zancensu..magana daya biyu zaice besty tayi kaza ko kuma Billy tace kaza"...daria sukayi gaba daya jin yanda Hajia ke immitating mgnrshi...yana dan hararanta ta gefen ido yace"yanxu Hajia haka nake mgn?.."tace"oho kai ka sani"...sister dinshi ce ta fito daga daki waya kare a kunneta...tana ganinsu tayi hanging call din ta wani karasa cikin parlon da gudu ta fada jikinsu...Sa'eed yac"Lubna meye haka?..karya min su kikeso kiyi ne?.."ta daga jikin nasu tace"sorry yaya..nayi farin cikin ganin kawayena ne...kawayena da basu damu dani ba"..ta karasa mgn kaman zatai kuka...Mom tace"to sai ku shiga daki ku karasa mgn dan naga kaman they are not comfortable here"..Lubna ta mike tsaye rikeda hannayensu tace"yanxu kuwa Mommy"..daga haka ta jasu zuwa dakinda ta fito Sa'eed ya bisu da kallo har suka shige...Hajia dake ankare dashi tun dazu tace"mutum dai yayita yaudaran kanshi da sunan kawance..watarana kana zaune wani zaizo ya dauke ya barka da cizon yatsa"...juyawa yayi yana kallonta yace" me kike nufi?.."tace"me kuwa nake nufi daya wuce kana son mace kana yaudaran kanka wani wai kuna kawance..idan bakayi da gaske ba kana zaune zata auri wani ta barka wlh"...yace"to ke waya fada miki inason wata a cikinsu?..we are just friends "..tace" shine nace kacigaba da yaudaran kanka Sa'eedu"...bai sake mgn ba ya juya yana kallon Mom dinshi sai yaga daria take musu..zaiyi mgn tace"babu ruwana tsakaninku ne wnn".. Suna shiga daki suka zauna suna sake gaisawa...Lubna tace"da gaske mutanen nan baku damu dani ba..ko nemana fa ba wanda yakeyi a cikinku"...Billy tace"wlh abubuwan ne sai a hankali Lubna amma inshaAllah daga yanxu zumunchi sai kince ya isheki koba hakaba Lamido?.."da sauri tace"sosai ma kuwa..daga yanxu mun kulla knn har sai mun isheki"..tace"nikam ba wani dadin baki da zakuyi min dan bazan taba yadda ba sai naga kunzo har kd bikina snn zan yadda daku"..Billy tace"u mean an kusa bikinki?.."tace"in the next three months inshaAllah"..Aysha tace"Allah ya kaimu ya sanya alkhairi...amma besty bai ta6a fada mana ba wlh"..Billy tace"shine nima nake mamaki ai..koda yake kadan knn daga aikin Sa'eed"...nan kuma hiran nasu gaba daya ya koma kan bikin Lubna da irin shirye shiryen da zasuyi...if u see yanda suka sake da juna suna labari zakayi zaton tasowa sukai tare tun kuruciya nan kuwa basu dade da sani juna ba shima ta dalilin Sa'eed wani lokaci da tazo ta dade a kano ya kaita hostel dinsu shknn suka kulla kawance...basu fito daga dakin ba saida yazo da kanshi yace su fito ya maidasu snn suka fito...sukayi sallama da Mom da Hajia da har yanxu suke parlor...Mom ta basu dambun nama da tayoma Sa'eed da Hajiyarta cikeda wani flask aikam sukaita godia snn suka tafi har Lubna data dage zatayi musu rakiya...kaman yanda ya saba duk ya fita dasu sai ya siya musu kayan kwalama yake maidasu yauma haka ya tsaya a grand square ya sai musu su chocolates da sweets snn yayi dropping nasu a hostel su kuma suka koma tareda Lubna. Washegari Thursday suna zaune a premesis kafin time din shiga exam dinsu yayi motan Proprietor ya shigo makarantan...Ayshata wani hade rai dan tana gani ta gane motanshi ne...ko gama parking motan baiyi ba securities da some of staff da sukaga shigowanshi sukayi inda motan yake kaman yanda suka saba...tana daga zaune tana ganin yanda suka bude mishi kofa ya fito sunata wani washe mashi baki hadda masu risinawa suna gaisheshi kaman wani ubansu...Billy ce ta fara lurada ita sai tace"are you okay?.."ta saki wani tsaki tana fadin"mutanen can ne suke bani haushi wlh...dubi yanda sukema inyamurin mutumin can kaman zasuyi mishi sujada...kawai dan mutum nada kudi sai kuyita kaskantar da kanku a wurinshi da yawa daga cikinsu mafa sun girmeshi"..girgiza kai Billy tayi tace"to ke ina ruwanki...kuma an fada maki ba inyamuri bane har yanxu kin ki yadda koh?.."ta maka mata wani harara tace"wai wnn mutumin zaki kalla kice ba inyamuri bane haba Billy.."Sa'eed daketa sauraronsu yace"da gaske ba igbo bane shi besty..ance dai Mom dinshi igbo ce amma babanshi bafulatani ne fa"...da sauri Billy tace"tell her...bafulatanin ma kuma dan garinku"...da sauri ta daga kai tana kallonta tace"what do u mean?."Billy tace"ina nufin dan Gombe ne shi mana"...tun kafin ta rufe vaki tayi spitting tana binta da wani disgusting look tace"God forbid...how could such a heartless person come from Gombe?..gaskia i doubt that kilan dai bakuji daidai ba...and wether u accept it or not mutumin can inyamuri ne kuma na tabbata yana daga cikin masu assasa yakin Biafra sbd tsabar mugun halinshi"...daria suka sa mata gaba dayansu aikuwa ta cika tayi fam har ta mike zata bar wurin Billy ta janyota da sauri tace"to shikenan Sa'ees tell her mun yadda inyamuri ne shi"..da sauri yace"eh mana kuma a cikin inyamuran ma yana daya daga cikin masu assasa yakin Biafra so are we good now?.."murguda musu baki tayi tana hararansu...ganin time din exam ya gabato duk suka mike zuwa classes dinsu. Karfe biyu da wani abu ya daukesu suka tafi lalle kaman yanda suka tsara...Lubna ce tace tasan wani gidan lalle a Na'ibawa sun iya lalle sosai dan haka kai tsaye can ya nufa dasu. Basu suka baro gidan lallen ba sai after six kowacce da rangadeden lallenta mai kyau har Lubna da tace bazatayi zuwan banza ba dan haka dole akayi mata itama...tun da suka fito yake yabon lallen nasu amma wai na bestynshi yafi kyau...Lubna tace"Yaya wnn dai son zuciyarka ka fada gaskia"..Billy tace"ai kadan ma kika gani daga aikin Sa'eed"...Lamido dai dariya take sai kuma ta dan rausaya kai tana dubanshi tace"yanxu besty hostel zamu koma knn?.."yace"eh mana you guys have exams tomorrow "..tace" mun riga mun gama karatu wlh besty dan Allah ka kaimu yawo kaji"...ya dan harareta yace"wani wai kun gama karatu sai kace yin karatun kike"...tace"nidai dan Allah muje yawo pllss ko Billy "..dagowa tayi ta watsa mata harara yace" then we are definitely going back to hostel tunda hajia Bilkisu bata yadda ba"...da sauri Lubna tace"Billy kice kin yadda plss"...kmr bazata ce komai ba sai can tace"shikenan amma we won't stay long"..Aysha tace"hakanma mune da godia hajia bilkisu"...daria kawai Sa'eed yayi yace"to ina zamuje yanxu?.."da sauri Aysha tace"mu fara zuwa mudassir da akwai veils da nakeson siya"..yace"besty da shopping"...tace"ba haka bane besty kaga ko ban siya a nan dole ina sauka Gombe inje in siya kasan fa gobe ne kamun adda ruky"..jinjina kai kawai yayi sarai yasan halin kayarshi da shegen son biki...suna isa mudassir din gaba daya suka fita zuwa ciki...ta kwashi veils wajen guda four snn ta dauki shoe da bag...Billy ma ta dauki nata sai Lubna da suka tilasta mata ta dauki mayafi itama...sunzo wajen biyan kudi Aysha ta mika card dinta..Sa'eed ya watsa mata wani kallo yace"and what's that?.."tace"besty kullum fa kai kake biya yau daya dai ka bari na biya plss"..bai sake ce mata komai ba ya amsa card dinta daga hannun mutumin snn ya bashi nashi...ana gama cire kudin suka fita daga wurin rikeda ledojin kayan da suka siya...daga nan Chicken Republic suka wuce suka samu table suka zauna snn aka kawo musu menu kowa yayi ordern abinda yakeso...suna nan zaune kafin a kawo abincin sukaji sallama kusa dasu gaba daya suka juya inda sukaji sallaman...wani mutumi ne da akalla zaikai iri 50 to above yana nuna empty seat dake wurin yace"may i?.."Sa'eed ne yace mishi"Bismillah"...a hankali yaja kujeran ya zauna snn ya mikama Sa'eed hannu suka gaisa yace"sorry i interrupt you guys...wlh tun daga kabuga na biyoku har nan wajen"...mamaki sosai ya bayyana a fuskokinsu jin tun daga kabuga yake binsu...ganin kallon da suke mishi sai ya saki murmushi ya nuna Aysha da finger dinshi yace"because of her"...wani mamakim ya sake kamasu jin abunda ya fada...shi kuma ya saki murmushi yana duban Sa'eed da yayi tunanin ko yayansu ne yace"can i please talk to her in private?.."shiru Sa'eed yayi ya juya yana kallonta sai yaga tana wani blushing kanta a kasa cikin ranshi yace"dama nasan za'ayi haka wlh..besty da shegen son sugar daddies"...jin har yanxu baiyi mgn ba mutumin ya sake fadin"only 5 minutes plsss"..yaja plss din da har saida ta dago ta kalleshi...a hankali Sa'eed yace"Sure u can"..mutumin yace"thank u so much..you are a life saver"...daga haka ya mike tsaye yana mata wani kallon kasa kasa yace"Ma'am"...batayi mgn ba ta mike tabi bayanshi zuwa wani table a can gefe...da kanshi yaja mata kujera ta zauna snn shima yaja ya zauna yana facing dinta yace"Allah yasa dai banyi laifi ba"...ta danyi murmushi hadi da girgiza mishi kai...shi kuma yayi mata kuri da ido kamab ya samu tv...saida suka hada ido ya sauke wani numfashi tareda cewa"u are very beautiful...shiyasa ina kallonki naji komai nawa ya tsaya..naji bazan iya hakuri ba har saida na biyoki...Allah yasa ban kawo kaina inda za'a wahalar dani ba"...still murmushi ta kara saki tana girgiza kai...yace"my name is professor Ahmad Abdu Kurawa and i think i have fallen for you"...shiru kawai tayi tana kallonshi sai taji ya burgeta sosai...this is exactly why she loves sugar daddies cox they are straight forward ba wani kwana kwana a tsarinsu...snn ga iya handling mace da nuna mata so da kauna...shiyasa duj ta shirya yin aure batada burin da ya wuce ta samu sugar daddynta ta aura yanda zata yita zabga shagwa6a son ranta ana lallashinta...jin batace komai ba ya wani rausaya voice dinshi yace"dan Allah say something plss..wlh i love you..i love you so so so much"...murmushi ta kara saki tana rufe fuska da hannayenta sai ya saki murmushin shima kafin yace"ohk i guess i have to give u some time to think right?.."da sauri ta gyada mishi kai..yace"alright then you take your time...amma plss kiyi min mgn inji sai in tabbatar da banyi zuwan banza ba"...still smiling tace"sunana Aysha Ahmad Lamido"...yana gyada kai yace"your name suits you...dama ina ganinki naji a jikina wnn beautiful soul din must be Aysha..thank you so much Aysha for giving me your time...yanxun zan wuce sbd na bar yaro a mota kema kuma naga 'yan uwanki suna jiranki"..batace komai ba sai murmushi shi kuma ya zaro card dinshi ya ajiye mata yana cewa"ga card dina nan saiki kirani or better still bani number dinki cox i can't the risk of loosing you"...batayi musu ba ta amsa wayanshi tasa number dinta...saida yayi dialing yaga ya shigo snn ya katse tareda mikewa tsaye yana kallonta yace"to ni zan wuce beautiful Aysha..zan kiraki inshaAllah and Allah yasan baza'a bani negative news ba"...tace"inshaAllah"...yace"alright bye"...itama tace mishi"bye"snn ya juya ya fita itama ta mike ta dauki card dinshi daya ajiye ta koma inda suke..Lubna tace"so har kun daidai knn?.."itadai tayi murmushi tareda fara cin abincinta...Billy tace"ai bama saikin tambaya ba Lubna wlh nasan da kyar idan batayi accepting dinshi ba..Lamido da shegen son sugar daddies"...shidai besty yana jinsu baice musu komai ba...suna gamawa suka bar wurin time din dare ya farayi sosai yayi dropping nasu a hostel su kuma suka wuce Tarauni. Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ 🤍Dr.BOBBY🤍 By Aysha Rano✨ Wattpad@aysharano22 I dedicated this whole page to my darling small mom🥰❤️Hajia Fiddausi Musa Kibia aka Mrs MD aka Maman Mufeed da Mufeedah🥰❤️Ina roqon Allah ya biya maki dukkanin buqatunki na alkhairi Aisha Indo loves u so much🥰❤️ 12 Washegari Friday zasuyi final paper na first semester level two knn..zasuyi hutun two weeks snn su tafi clinical posting...tun wajen 7 suka baro hostel zuwa cikin makaranta..daga ita har Billy murna suke zasuje gida dan ko weekend sun kwana biyu basu je ba...kafin time din exam yayi provost ya kira wayanta yace tazo yanason ganinta...babu wasting of time kuwa taje office dinshi yace list din yan class dinsu yakeso ta bashi yanxun nan...ta juya zata fita ya dawo da ita ya mika mata pen da paper yace ta zauna nan ta rubutasu yasan zata iya tunda ba wani yawa garesu ba...ba musu ta amsa ta zauna ta fara rubutawa shi kuma Nur yacigaba da aiki a Laptop dinshi...a hankali Bobby ya turo office din ya shigo...idanuwanshi basu sauka ko inaba sai hannun Lamido da lallenta yayi wani moroon yanata shinning abunka da farar fata...ranshi yaji ya 6aci sosai like how dare this girl apply henna a hannunta bayan tasan baya cikin ethics... har ya karaso cikin parlon basu sani ba sai kawai sukaji yace"keh.."a gigice ta dago tana kallonshi..fuskan na sarari yace"bakuyi professional ethics bane?.."voice dinta na dan cracking tace"mun...yi"yace"then why did you apply this rubbish a hannunki?.."tayi shiru kanta kasa tana 6oye hannunta...Nur dake kallon abokin nashi da mamaki yace"C'mon Bobby ni banga wani abu anan ba..maybe kafin su tafi clinical posting ya baje so relax "...a fusace ya juya yana kallonshi yace" amma kai kanka kasan duk wayan nan abubuwan is prohibited a profession dinta koba a clinical area bane"...shiru kawai Nur yayi yana kallonshi..baisan why he easily gets angry when it comes to her ba..he remember yanda yayi acting ranan da sukaje hostel...ita kuwa Aysha daure fuskanta tayi tana dan turo baki har yanxun kanta kasa dan ko a mafarki batason sake hada idanu dashi...(note:nasan wayansunku will be like ya zaayi a hanata yin lalle sai kace a secondary school..well duk wanda yayi health institution yasan banbancinsu da secondary school dan kadan ne coz sunada strict dokoki snn kuma akwai ethics so ba yanda zaayi mutum yazo yana yin anyhow a irin wnn makarantun sbd suna dealing da lives of many people..da akwai rules da dole mutum sai yabi while in school ko kuma clinical area..na farko dai applying lalle is prohibited especially during clinical posting..snn ba'a sanya kayan ado musamman duk wabi abu da zai dauki hankalin patient ta hanyar sound dinshi ko wani abu shiyasa ake sanya uniform and ko takalmi bada kowanne ake zuwa ba dole sai preferred wanda aka za6a..irinsu zobe su agogo da sauransu suma duk are prohibited sbd suna iya daukan hankalin mara lafia shiyasa ake fara training mutum ya saba tun a school kafin ya tafi clinic..so i hope u understand dan nasan wasu zasuce wnn ta cika tsanani da yawa ko kuma ace tana rubuta abunda ba haka bane bayan haka tsarin kudan duk wani health institution yake saidai wasu sufi wasu tsanantawa)...karasawa yayi cikin office din ya tsaye nan inda take zaune snn yace"a ka'idar wnn abun da kikayi suspension za'a baki kuma bazaki dawoba har sai ya baje amma yanxu tunda you are going for holiday punishment dinki shine bazaki rubuta exams dinki na yau ba"...a rikice ta dago tana kallonshi idonta har ya ciko da hawaye...kallon nata yakeyi shima aikam nan da nan tayi kasa da nata don bazata iya daukan wnn kallon nashi ba...Nur ya taso daga seat dinshi ya zagayo inda yake yace"Bob me kakeyi ne haka pls?..meyasa bakajin mgn?.."a fusace yace mishi"ita why bazaka tambayeta meyasa batajin mgn ba?..meyasa ta cika fitina duk wani abu da tasan zai ja mata matsala bazata hakura dashi ba"...shiru gaba daya sukayi suna kallonshi...shidai Nur har yanxu bai dena mamakin wnn behaviour din nashi ba...shi kuwa ganin kallon da yake mishi ya karasa ciki ya dauki wani file akan table dinshi snn ya juya ya fita daga office tunda dama abunda ya kawoshi knn...kaman jira takeyi ya fita ta saki wani kuka mai ciwo...Nur ya dawo kusada ita da sauri yana kallonta a hankali yace"Lamido stop crying plss...dont cry"..girgiza kai kawai take as tasan idan daddy yaji an hanata rubuta exam sbd lallen da tayi applying fada ne zata sashi kilan ma saiya hada da duka..sam ba mai daukan iskanci bane shiyasa take mugun tsoronshi...ganin yanda take kuka Nur ya sake kwantar da murya yace"dan Allah stop crying kinji...duk wnn abun da kikaga yanayi baikai zuciyanshi ba...yanxun kije can office din nashi ki bashi hakuri"...yana rufe baki ta dago a razane tana kallonshi...sai kuma ta hau girgiza kanta tace"Sir bazan iya zuwa ba...inajin tsoro"...yace"don't be..ba abunda zaiyi miki inshaAllah believe me...kawai idan kinje ki kwantar da muryanki kice yayi hakuri dan darajar Mummy da Daddy na tabbata idan kika fadi haka zai hakura"...shiru kawai tayi tana kallonshi kaman bataji me yace ba...saida ya sake mata mgn snn ta fita daga office kaman mara lafia...secretary dinshi na ganinta tace ta jira ta fara mishi mgn...landline dinshi ta kira ta fada mishi yanada bakuwa kai tsaye yace a barta ta shigo...saida ta gama goge tears dinta snn ta shiga office din kai a kasa kaman munafuka...kanshi na sunkuye yana signing wasu papers so bai ga wanda ya shigo ba...ta karasa gaban table dinshi ta tsaya gabanta sai aikin faduwa yake...batasan why take tsoron bawan Allahn nan ba dan duk yanda takai da son ta bude baki tayi mgn kasawa tayi...kawai imagining take ta koma gida daddy ya samu labarin an hanata exam sbd tayi lalle...duk wnn abun da take baisan tana tsaye kanshi ba saida ya gama signing papers din ya dago...mamaki ya kamashi sosai dan baisan itace bakuwar ba...idanunta rufe suna fitar da hawaye sai bakinta daketa motsi kaman tanaso tace wani abu...kallonta ya tsaya yayi da kyau irin kallon da bai ta6a yima wata mace a dunian nan ba...tun daga kan idonta da suke rufe har zuwa kan lips dinta dake shinning as a result of hawaye daya wankesu har yanxun kuma basu dena motsi ba...haka nan yaji wani irin sanyi na rufe mishi jikinshi...irin internal sanyi da mutum keji idan yana fever...ya dauke kanshi da sauri sai kuma yaji hadadden zafi yana maye gurbin sanyin daya faraji...ranshi ya 6aci sosai jin yanda temperature dinshi ke raina mishi hankali...yanxun nn yakejin sanyi after a minute kuma ya farajin zafi...ita kuma har yanxu taki bude ido tana tsaye tana karanta mishi Yaseen cikin zuciyarta wai ko Allah zai dorata a kanshi ya janye abunda ya fada...ganin bayan sauyin temperature har mood dinshi ma ya fara sauyawa gata kuma ta wani yi mishi tsaye a kai kaman wata soldier ya sake dinke fuskanshi tsaf snn yace mata"keh.."a hankali ta bude idonta ta dora kanshi sai kuma ta sauke da sauri tana kwa6e fuskanta irin yanda babies keyi idan zasuyi kuka ganin wnn kallon data tsana yakeyi mata...kirjinta har bugawa yakeyi dan tsoro ta rasa wane irin magic mutumin nn keyi dake sanya mata tsoronshi haka...shidai Bobby baki da hanci ya saki yana kallon ta6ara iya ta6ara...yanda tayi da face dinta dama kana gani zakasan sanrgatacciya ce ta ajin farko ma kuwa...ranshi yaji ya sake 6aci dan a dunia ya tsani shagwa6abbun yara wlh...ya tsani yaga an zubama yaro ido yana zuba iskanci son ranshi baza ayi mishi fada ba sunan wai ana sonshi...can kasan makoshi yace"spoiled brat"...a fili kuma komawa yayi yayi relaxing kan kujeranshi still yana kallonta yace"leave my office if u don't have anything to say"...da sauri ta shiga girgiza kai cikin stammering tace"Sir...am...sorry"...wani kallo yake binta dashi before yace"what did u said?.."ta dan turo baki tace"i said am sorry"...tana rufe baki yace"sorry for yourself..now leave"...shima yana rufe bakin ta hade hannayenta alaman roko tace"Sir dan Allah...dan annabi..dan darajar Mummy da Daddy kayi hakuri"...shiru yayi yana kallonta totally speechless as ta fadi biggest weakness dinshi...in his entire life bashida weakness daya wuce parent dinshi likewise his strength especially Mummy that is still alive...ko ba'a fada ba kuma yasan aikin Nur ne wnn and he will definitely have to deal with him...ganin yanda yayi shiru ya kurama spot daya ido ta sake karya muryanta tace"Sir Please!.."wnn kallon dai data tsana ya watsa mata kafin ya nunata da finger dinshi strictly "but this should be your last...i promise duk na sake ganinki dashi you'll face the consequences"... tun bai rufe baki ba tace" nagode Sir..thank you so much"...bai sake cewa komai ba sai kofa daya nuna mata...ta dan ta6e baki tana goge tears dinta snn ta juya ta fita cikin ranta tace"inyamurin banza". Taci sa'a tana zuwa aka fara raba question papers ta karasa seat dinta da sauri ta zauna...Billy daketa baza ido taga shigowanta tun daxu ta saki ajiyar zuciya dan sam hankalinta bai jikinta ganin har za'a fara bata shigo ba. 11 daidai suka fito daga exam hall...already Hamma Najeeb na zaune cikin mota yana jiransu dan haka suna fitowa suka nufi inda suka hango motanshi...shima yana hangosu ya bude motan ya fito...suna karasowa ta wani kwa6e fuska kaman zatasa kuka snn ta kama hannunshi ta rike idonta na cikowa da hawaye...hankali a dan tashe yace"what happened again?.."ganin taki mgn ya juya yana duban Billy yace"me akai mata?.."Billy ta buda hannu alaman bata saniba...shi kuma ya kama hannunta suka kan wasu cement chairs dake gefe still hannunta cikin nashi yace"Maama plss talk mana..waya ta6amin Mamana?.."tana turo baki tace"Hamma i don't want to come back to this college kayi mgn da daddy plss"..yace"but Maama why?..did something happen again?.."tace"Proprietor ne...Hamma wlh ya tsaneni..kawai daxu yayita min wulakanci hadda cewa bazanyi exam ba sbd nayi lalle..nidai i don't want to come back plss"...kamo dayan hannunta yayi yana dubanta da kyau yace"Maama kinsan daddy bazai ta6a yadda ba tunda ke kika dage sai an kawoki nan...but i think i have to talk to Proprietor din naku ya bar takura maki kawai"...tana goge hawayenta tace"there is no need..idan kaje ma wulakanci zai maka na sani...Hamma inyamuri ne fa..ko cikakken hausa bai iyaba"...yace"to indai bakiso inje in sameshi ki bar kukan nan haka..yanxun ku debo kayanku mu wuce amarya nata kirana wai inyi sauri in kaiku da wuri"..da sauri ta karasa goge hawayen nan da nan kuma saiga murmushi a fuskanta tace"laaa Hamma kasan har na manta wlh...Billy taso mu tafi nasan yanxu ana can ana shirye shiryen kamu"...girgiza kai kawai Billy tayi tana mamakin halin Lamido da shegen son biki..yanxun nan fa take kuka sha6e sha6e amma daga jin mgnr biki ta wartsake...kayansu kawai suka dakko daga wani class don dama basu fito da shirin komawa hostel ba..suka zuba su cikin booth snn suma suka shiga motan Hamma yaja suka tafi...basu samu yin sallama da Sa'eed ba as har time din yana exam hall bai fito ba..dama ba lokaci daya suka shiga ba so sun rigashi fitowa. Saida suka fara tsayawa Bauchi suka ajiye Billy snn suka wuce Gombe bayan tayima Lamido alqawarin zata zo gobe ayi bikin da ita yau dai tanaso ta huta gajiya...suna shiga cikin Gombe murnanta ya kasa 6oyuwa dan ba karamin missing gida tayi ba...kai tsaye GRA suka nufa inda a nan Estate dinsu yake...Estate ne babba inda ciki duk wani wanda ke amsa sunan Lamido yake.. a nan ciki gidansu yake tun daga kan 'ya'ya da jikokin Lamido maza baya bari suyi nesa dashi mata ne kadai suke fita shiyasa ake yima Estate din laqabi da LAMIDO'S PALACE...horn yayi jikin tangamemen gate din shiga Estate din wanda daga can samanshi aka rubuta THE LAMIDO'S in capital letters..masu gadi sukazo suka bude mishi yasa kan motar ciki...tsayawa fadan haduwan ciki ma bata baki ne kawai dai is one of the biggest and beautiful Estate i have ever seen...ya tsaru ne iya tsaruwa snn yana daukeda gidajen da ni kaina bazance ga adadinsu ba don sunada yawa sosai...layi na uku ya shiga by his right side snn yayi parking motan a daidai kofan gidan daya kasance shine na uku layin...tun kafin ya kashe motar ta bude kofa ta fita da gudunta ta fada cikin gidan...bata ga kowa a parlor ba dan haka ta wuce zuwa dakin Ammi...a gaban madubi ta isketa zaune tana daura dankwali ta karasa da saurinta tayo hugging nata ta baya tana fadin"Ammi nayi missing diki wlh"...a hankali ta juyo ta zame hannunta daga jikinta snn ta daure fuska tana kallonta tace"bakida hankali kou?..wnn shine sallaman?.."rungume hannu tayi tana turo baki tace"Ammi nayi kewarki nefa sosai shiyasa amma kiyi hakuri"...juyawa Ammi tayi tacigaba da daurinta tace"zakici ubaki ne"...sake turo baki tayi tace"yanxu Ammi ko gaisawa fa bamuyi ba"...Ammi data gama daura dankwali tana kokarin sa wayanta cikin hand bag dake hannunta tace"ni kike jira in gaisheki ai tunda ke kika haifeni"...kaman bata son mgn tace"Ammi ina yini..ya gida"...tace"lafia lau ki wuce kije kiyi wanka ana gama ma su Husna make up kema ayi miki ku taho..tun daxun ake tafiya sbd ke nace su jira ku wuce tare"...tace"to bari inje Ammi..amma Aunty Fiddausi bata zo bane?.."tace"bazata samu zuwa ba Mufid ne ba lafia wai...yanxun mu fara zuwa ku gaisa da daddy sai kije kiyi wankan"...tare suka fita daga dakin bayan Ammi ta yafa mayafinta...tayi kyau sosai cikin coffee lace daya amshi skin clour dinta sosai snn kallo daya zaka mata kaga tsananin kamar da Lamido takeyi da ita...a zahiri kuma bazaka ta6a cewa ta haifeta ba dan yanda suka jero sai sukayi kaman kawaye...a palor suka samu daddy zaune yana yin waya...suka karasa ciki Ammi ta zauna kusa dashi ita kuma malama A'ee ta zauna a kasa tana wani irn nutsuwa kaman mutumiyar kirki...bayan ya gama wayar ya dubi Ammi da tayi mishi kyau kwarai yace"har kin gama?.."tace"na gama daddy zuwa zanyi Najeeb ya ajiyeni a hall din kafin ya fita..su kuma idan sun kammala sai Idris ya kawosu"..gyada kai yayi yana fadin"ohk"..snn ya maida kallonshi ga Aysha da take zaune tsumu a kasa kaman ba ita ba..cikin sabuwar nutsuwar data aro ta yafawa kanta tace"daddy barka da yamma"..yace"yauwa Aysha an dawo?.."tace"mun dawo daddy"...yace"Maa sha Allah ya exams?.."tace"daddy Alhamdulillah"...yace"to Alhamdulillah ya ban ganku tareda Bilkisu ba?.."tace"sai gobe zatazo daddy"..ya gyada kai yace"Allah ya kaimu..sai kije ki fara shiryawa kar suzo suna jiranki"..a hankali ta amsa da"toh.."snn ta mike ta bar parlon...itama Ammi mikewa tayi da bag dinta a hannu tace"nima bari in wuce daddy lokaci na kara tafiya"..kama hannunta yayi ya zaunar da ita yace"ki bari in kaiki da kaina mana...irin kyau da kikayi ya kamata ace sai na gama gani zaki tafi"..murmushi ta saki tana girgiza kai tace"daddy bakada dama wlh...inaga sai kaga mun aurar da Aysha snn zaka gane girma ya fara zuwan mana"...yaja dogon hancinta yace"ke girma ya fara zuwan ma bani ba..kuma ko mun aurar da Aysha ni babu abinda zai canxaki cikin zuciyata"..daria ta saki tana jin kaunar mijinta ta ko ina a jikinta snn ta sake mikewa tace"to nidai ayimin uzuri in wuce ba don ni ba..nasan yanxu ana can ana menana wlh"...bai sake yunkurin hanata ba yace"sai kin dawo Allah ya kiyaye"..ta amsa da"Ameen"..with a smile snn ta fita daga parlon...a main parlor ta samu Najeeb na jiranta dan haka yana ganinta ya mike suka fita tare..dukda cewa hall din da suke bikin cikin Estate din yake yanada nisa sosai da baza'a iya zuwa a kafa ba. Aysha kuwa tana shiga dakinsu ta iske Husna zaune ana mata make up din Yusra kuma na kwance kan gado...saida suka gama rungume rungumesu itada Yusra as usual Husna nata faman ta6e baki tana binsu da harara snn ta fada bathroom tayo wanka sharp sharp ta fito...lokacin am gamawa Husna an farama Yusra...ita kuma ta tayar da sallah bayan ta idar ta dauki kayanta da yake iri daya dasu Husna har dinki ta saka snn ta zauna zaman jira. Karfe biyar da wani abu suka shigo cikin hall din...dukkaninsu suna sanye cikin atampan ankonsu dark blue da adon sky blue a jikinta...kaman yanda na fada dazu hatta dinkinsu iri daya ne haka daurin dankwali da akai musu shima iri daya ne..takalmi da jakansu ne ya bambamta amma duk color daya ne...hall din ya cika makil da mutane banda sautin waka ba abunda ke tashi a ciki...amarya na zaune high table tareda angonta...Aysha na hangota ta fara zuwa inda take kawai suka rungume juna cikin rada tace"adda ruky kinga kyan da kikayi kuwa?.."amarya data kasance cousin dinta domin diyar yayan daddy ce tace"duk kyauna ban kaiki ba Lamido"..ta matsa daga jikinta tana dan turo baki tace"kema Lamidon zakice?.."itama amarya komawa tayi ta zauna snn tace"yes koba sunanki bane?.."tace"sunana ne kaman yanda kema yake sunanki..so daga yanxu duk kika kirani da Lamido kema da Lamidon zan kiraki"..murmushi kawai tayi mata ita kuma ta juya ta tafi..can inda ta hango da yawa daga cousins dinta ta nufa wanda duk yawancinsu age mates dinta ne suma duk suna sanye da anko...nan suka hau rungume rungume suna farin cikin ganinta. Daga wnn page na kawo karshen Free pages dina sbd haka inayina kowa fatan alkhairi...wayanda sukayi patronizing a big thank u to all Allah ya saka da khairan🙏🏻 Masu bukatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment ta 07063800556. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344...sai a tura evidence via 07063800556. 13 Basu suka baro hall din nan ba sai after seven...lokacin duk an gaji su hajia Aysha a gajiye aka dawo gida sbd rawa da aka tika wajen...kai tsaye ta fada bayi ta watsa ruwa a jikinta snn ta fito tasa kayan bacci tareda hayewa gado ta nade kaman wanda zatayi bacci...sai yanxu ta tunada wayanta data bari a school bag din daxun...shaf ta mance data dawo bata fito dashi ba ta mike da sauri zuwa inda ta ajiye jakan ta zaro wayan snn ta sake komawa gado...missed calls ta tarar guda 46 aikuwa ta wara ido sosai tana kallonsu..biyu daga ciki na Billy ne sai guda hudu na Besty sai kuma wata bakuwar Number mai sauran 40 din...ta danyi shiru tana nazarin number lokaci daya kuma sai ta wara ido tana sakin murmushi data tuna mai number...wnn sugar daddyn ne da suka hadu a Chicken Republic ranan...Allah sarki bawan Allah shine yayita jera mata missed calls haka?..tayi mamaki ma da bai ta6a kiranta ba sai yanxu...har ta danna zatayi dialing number dinshi sai kuma taga bari ta fara kiran Billy da bsty tukun dan kar ta fara kiranshi ya cinye mata time bata kirasu ba...Billy ta fara kira suka gaisa tareda yima juna ban gajia snn Billy ta jaddada mata tana nan zuwa gobe inshaAllah...suna gamawa ta kura bsty shi kuma korafi yaketa yi wai basu tsaya sunyi sallama dashi ba suka wuce ita kuma tayita aikin bada hakuri har ya hakura...bayan sun gama ta wani sake lafewa kan pillown da take kwance tana lumshe idanu tayi dialing number dinshi da yanxun nn tayi saving as Prof...yana shiga kaman jira yake ya dauka sai ya sauke wani wawan ajiyan zuciya before saying"baiwar Allah laifin me nayi ake ignoring calls dina haka?.."tana smiling tace"sorry bana tareda wayan ne"..yace"hankalina duk ya tashi na fara tunanin kodai ban samu kar6uwa bane"..murmushin ta kara saki tace"sam ba haka bane..bikin cousin dina akeyi shine na manta ban tafi da wayan ba"...yace"to shiknn hope ban takura maki ba?.."tace"not at all"..tana jiyo sautin smile dinshi kafin yace"to yanxu ya zakiyi dani?..inaso in ganki gaskia"..tace"bana Kano yanxu..na dawo gida"..yace"ohh ba kano kikeba?.."tace"yea Gombe"..ya wara idanunshi da kyau kafin yace"no wonder kikeda kyau..dama an fadamin gaba daya 'yan Gombe kyawawa ne"..tayi murmushi kawai..shi kuma ya sake yin kasa da murya yace"to nidai inason ganinki and if kin bani dama har Gomben zan iya zuwa"..tace"haba da akwai nisa fa"...yace"bakiji ance garin masoyi bai nisa ba?..nifa da gaske nake sonki Aysha bada wasa ba..ban ta6a tunanin zan iya auren karamar yarinya ba sai a kanki..so please inaso a bani dama"...shiru tayi tana tunanin me zatace mishi...tadai san ko ta fara shaye shaye bazata fara kawoshi gidansu ba dan Lamido najin labari zaice ta fito da miji a nata aure tunda tara samari take..besides shi kanshi daddy won't take it likely idan yaji ta kawo saurayi gida ba tareda ya nemi izini ba snn Ammi ma ba rufa mata asiri zatayi ba dan bakinsu daya itada daddyn..amma yanxu ya zatayi da wnn bawan Allah data farajin itama kaman tana sonshi...idea ne ya fado mata dan haka da sauri tace"to ka bari mu gama biki zuwa Sunday sai mu hadu a Bauchi"...yace"but why Bauchi?..ba kince Gombe ne garinku ba?.."tace"nan ne garinmu amma bazan iya kawoka gidaba sbd mahaifina zaiyi fada"..yace"zan iya turowa a nemi permission dinshi if kin amince cox banso da girmana in hadu da yarinha baa gidan iyayenta ba..it's not proper ko 'yata aka yima haka bazanji dadi ba"...ta dan shagwabe muryanta tace"nidai banaso kazo yanxu plss and Bauchin fa ba gidan wani zamu hadu ba gidan small mom dita ne..qanwar mamana"...shiru taji yayi for a while da alama yana tunanin yiwuwar hakan ne...kafin yayi mgn ta sake narke murya kaman wadda ke shirin fashewa da kuka tace"shikenan dama nasan ba damuwa kayi dani ba"...da sauri yace"subhanallah baby why zakice haka?.."tace"gashi nan sbd nace mu hadu a Bauchi kanaso kace ka fasa zuwa"..yace"alright ok don't cry plss...kawai ina ganin rashin dacewar hakan ne a matsayina na babba bai kamata na biye miki ba amma zanzo kinji?..zanzo inshaAllah"...lokaci daya ta saki smile tanajin dadin yanda yake mata tace"shknn Allah ya kaimu...ranan sunday inshaAllah"..yace"no problem Allah ya kaimu i can't wait to see you"..tayi daria tana feeling kanta kaman a sararin samaniya..wnn shine exactly dalinda yasa take son sugar daddies...tayi shagwa6arta son ranta babu wanda zaice don me..dan Allah ya sani tana son taga ana pampering dinta ita dai sai kuma Allah bai bata irin wann parents din ba don daga Ammi har daddy ba masu sangarta yara bane..itama din da takeyi kawai don abun yana jininta ne amma ba shagwa6ata suke ba shiyasa wani lokaci Ammi takan ce"wnn yarinya da shagwa6aki muke Allah kadai yasan iskancin sa zaki mana a cikin gidan nan"...sun dauki lokaci mai tsayi suna waya tanata zuba shagwa6arta yana biye mata aikam farin ciki kaman ta zuba ruwa kasa tasha to dama abun nema ne ya samu wai matar driver ta haifi mota😂. Washegari around 11 Billy ta karaso gidan...if u see yanda suka rungume juna sunata murna zakayi tunanin dadewa sukayi basu hadu ba nan kuwa jiya jiyan nn suka rabu...bayan sun gama hoge hogensu suka je ta gaisa da daddy da Ammi snn suka shiga daki...Billy take bala labarin yanda sukai da Sir Abdool wai ya kai karanta ta dena daukan wayanshi...Aysha ta wani cunno baki tace"wai bama fada miki abunda yayimin ba?.."Billy tace"and so what dan yayi pecking hannunki?..Lamido nifa banga wani abu a nan ba kawai kina nema kiyi complicating abubuwa"...da mamaki tace"seriously?..yanxu ke a wurinki ba komai bane namiji ya kama hannunki yayi kissing?.."Billy tace"of course ba wani abu bane mana indai da soyayya...kema fa da kina sonshi nasan wlh bazaki damu da hakan ba kawai dan bakya sonshi ne"...tace"Alhamdulillah da kika gane bana sonshi...ke ban fada miki ba jiya bakiga wayan da mukasha da wnn mutumin ba wlh..Billy he is so romantic nima harna fara sonshi wlh..gobe ma zaizo mu a hadu gidan Aunty fiddausi"...harara Billy ta buga mata tace"au yanxu har daman zuwa zance ma kika bashi mutumin da bakisan halinshi ba Lamido?..ba gara Sir Abdool din ba tunda shi munsan wayeshi?.."Aysha ta ta6e baki tace"ba dama ayi mgnr arziki sai kice Sir Abdool...nidai dan Allah ki taimaka ki roki Ammi kice zan rakaki gida sai muje tare plss"...a kufule Billy tace"bazanyi ba"..tace"C'mon Billy dan Allah fa nace?.."Billy tayi mata banza bata kulata ba. Da yake event din ranar na dare ne basu suka fara shiri ba sai after magrib...yauma kaman jiya har gida make up artist tazo tayi musu wnn karon hadda Billy...Lace ne a jikinsu yellow da black flowers a jiki sai aka daura musu black head dinkin straight gown daya zauna jikin kowaccen su...karfe takwas da wani abu Hamma Najeeb ya kwashesu zuwa hall da zaayi event din...wurin yayi kyau sosai hakama Amarya da maids dinta tamkar a sacesu a gudu sbd kyau...Amminsu ma yau ba'a barta a baya ba dan make up akayi mata light wanda baikai nasu ba sai ta fito tayi das abunsa kamar yammata...biki dai yayi biki domin anci ansha anyi ruwan kudi snn an dirki rawa kaman ba gobe...su Aysha basu koma gidaba sai after twelve..wanka kawai sukayi suka kwanta bacci. The next day ringing din wayanya ya tadata daga bacci...ta mike zaune a hankali tana murza ido takai hannu ta dakko wayan nata..Prof taga ke kira kaman yanda tayi saving dinshi..ta saki smile sai a lokacin ta lura duk su Billy ashe sun rigata tashi sun ma fita daga dakin...tayi picking da sallama..a daya 6angaren yace"my beautiful baby girl..hope bani ma tasheki a bacci ba"..ta wani narke tace"ka tasheni mana"..yace"eyya am sorry baby pardon me plss..am eager inji voice dinki ne that's why amma am sorry kinji?.."tana murmushi tace"baka laifi ai"..cikin excitement yace"Really?.."tace"Sure.."yace"baby gaskia inason ganinki sosai..i feel like coming to Gombe right now"..tayi kasa da murya sosai tace"no ka bari yanda muka tsara plss..anjima kadan zamu wuce Bauchi inshaAllah"..yace"shknn sai anjima..i have to barki kiyi wanka kiyi breakfast koh?.."tace"yea..ba bye"..shima yace"bye"..snn suka ajiye waya...ta sauka daga gadon tana sakin murmushi one after the other ta shiga bathroom...brush kadai tayi snn ta fita zuwa parlor...a dinning ta iskesu gaba daya suna breakfast except daddy da Ammi da normally sukafi yin breakfast dinsu a parlon daddyn...karasawa tayi taja kujera ta zauna tace"shine duk kuka fita baku tasheni ba"...Billy tace"yo kina can kin wurgar da bakinki akan me zamu tasheki?.."Husna tasa daria tace"kai Adda Billy meye wurgar da baki kuma?.."Billy tace"mutum ya kwanta yana bacci mana"...Husna ta sake sa daria...itadai Aysha bata kulasu ba ta fara serving kanta...saida suka gama Hamma Najeeb ya shigo yace suyi serving dinshi...Husna ce tayi serving su kuma sauran suka koma parlor. karfe hudu da mintina aka fito da amarya zaa kaita gidanta dake Bauchi...hajia Aysha dai ta samu da kyar da sidin goshi Ammi ta barta zuwa kai amaryan tace daga nan ma ta biya gidan Fiddausi ta duba mata jikin Mufid idan tazo gobe saisu dawo tare...murna wurinta kaman bata ta6a zuwa Bauchi ba har saida Ammi tayi zaton ko wani abun zai kaita sai kuma ta waske tacema Ammin ba komai...basubi motan kai amarya ba Ammi ta hadasu da driver ya tafi dasu...kai tsaye gidan aunty Fiddausi ta nufa ko hanyan gidan amarya basu nema ba...lokacin karfe biyar ya kusa...suna shiga ciki suka gaisa da Auntyn nata dake nan mai kamada Ammi sak snn Aysha tayi mata bayanin zatayi bako dan yanxu haka ma yana kan hanya...kallonta ta shiga yi tace"Adda bata saniba koh?.."da sauri Aysha tace"Aunty kinsan idan na fada mata bazata barni inzo ba..tama ce gobe idan tazo duba Mufid sai mu wuce tare..Aunty ya jikin nashi kuwa?.."tace"yaji sauki dama malaria ne yake fama dashi amma yanxu ya warke yana ciki yana bacci"..tace"to Allah kara sauki amma ya banga Mufida ba".."Mufida na islamiyya..yanxu me za'a dafama bakon naki?.."Aunty ta tambayeta kai tsaye...ta danyi shiru tana nazari kafin tace"kawai Aunty a dafa mishi koma menene..nasan ya kusa karasowa yanxu haka"..mikewa auntyn tayi ta nufi kitchen tace"to bari in fada musu suyi mishi abu mai sauri tunda lokaci ya kure"...cikin jin dadi tace"yauwa Aunty na"...Billy dai na sauraranta ko uffan batace ba as haushinta takeji for accepting wnn mutumin kuma wai harda bashi dama yazo su hadu...da farko ma cewa tayi ita gida zata tafi sai da kyar ta samu ta shawo kanta kan ta bari su tafi tare gobe. Prof bai samu shigowa Bauchi ba sai after five...yabi address data tura mishi sai gashi kofar gidan Aunty Fiddausi...ya kirata a waya yace mata ya iso ita kuma tacema nai gadi ya bude mishi ya shigo...tana tsaye jikin window tana ganin shigowanshi...da kanta ta fito cikin black abaya da yayi nata kya sosai ta shiga dashi dakin baqi...ko zama ya kasayi kallonta kawai yake yanajin tamkar ya dagata yayita juyi da ita cikib parlon sbd tsabar kyau da tayi mashi...duk yasa ta farajin wani iri wlh..da kyar ta samu ya zauna itama ta zauna suja fara gaisawa...ya kasa dauke idonshi daga kanta kona second daya...mikewa tayi ta shiga ciki ta kawo mishi drinks da snacks kafin a gama abinci...har ta zuba lemo ta mika mashi bai bar kallonta ba..ta dan daure face tana turo baki tace"Prof mana...banason kallon nan wlh"..a hankali ya dauke idonshi yana sauke wani gwauron ajiyan zuciya yace"na dena my baby..just know that i love u so much"...dan murmushi ta saki for the first time itama tac mishi"i love u too"...ya wara idanu sosai yana kallonta full of excitement yace"Really?..da gaske kina sona baby?..thank u so much baby Allah ya miki albarka"...ta wani sake karya muryanta tace"Ameen Ameen my Baby Boo"...wani irin dadi yaji ya sake lullu6eshi...shikam baisan inda zaisa kanshi ba duk ranan da akace ya mallaki wnn zandadediyar yarinya..she's like 100 percent kaman ita tayi kanta..she's like a complete package da kowane namiji zaiso samunta as his wife...hira sosai suka shigayi irin na masoya inda mutumiyarku keta zu6a shagwa6a shi kuma yana tarairayarta...bayan an gama girki Billy ta kawo mishi snn ta zauna suka gaisa...Aysha tayi introducing nata as her best friend shima tayi introducing nashi as her baby boo...wani takaici Bilky taji ya isheta jin wai wnn tsohon take kirada baby boo..bata wani jima suna hira ba tayi excusing kanta ta fita su kuma suka dora daga inda suka tsaya...har akai sallahn magrib basu gajiba yaje sallah ya dawo suka cigaba da gashi...in short Professor bai bar gidan nan ba sai da aka kira sallahn isha..ta rakoshi har mota suna jin kaman bazasu rabu ba sukayi sallama ta kima ciki shi kuma ya tada mota ya wuce yasan kwanan Bauchi ya kamashi dole tunda dare yayi saidai da safe ya koma...a labarin da sujayi ne ya sanar da ita bashida mata domin tun bayan rasuwar matarshi tsahon 3 years bai sake aure ba amma yanada yara uku mata biyu namiji daya...babbar macen tana aure a Abuja with a son mai binta kyma ba'a dade da bikinta ba ita kuma tana kd sai karamin cikinsu Muslim yana karatu a Malaysia. Washegari wajen 10 suka tafi gidansu Billy kafin Ammi ta karaso...ta gaisa da Ummansu Billy da abbansu sai wajen 12 ta koma gidan Aunty...lokacin kuma su Ammi sun jima da zuwa tareda Yusra da Husna...nan suka zauna sunata faman hira amma koda wasa Aunty Fiddausi batayi mentioning zuwan bakon Aysha wa yayar tata ba dan tasan idan ta sani har ita kanta zata hada ta wankesu tatas shiyasa tayi shiru da bakinta..wnn dalilin yasa kullum Ammin ke cewa bakinsu daya da Aysha dan nasu yazo daya sosai zaiyi wahala aji kansu snn kuma Aysha bata ta6a zuwa hutu ta koma ba tareda tazo Bauchi gidan Auntyn nata ba...suna shiri sosai da ita unlike Husna da basa jituwa kwata kwata...saida sukayi sallahn asr snn suka nata sallama suja tafi...Aysha duk sai tajita wani iri ita dama su barta ko sati ne tayi a Bauchin. Kano... Yana kwance cikin dakinshi yayi wani coiling a kan gado yana bacci Ilham ta shigo...tun daya gama gymming dinshi yayi wanka ya kwanta shine har yanxun bai tashi ba don sai yamma zai shiga Hospital...ta karasa kan gadon tana hargitsa uban gashin kanshi mai santsi takai bakinta saitin kunnenshi tace"Uncle Bobby wake up"...a hankali ya bude ido snn ya sake maidasu ya rufe...Ilham ta sake hargitsa gashin nashi tace"Uncle Bobby wake up mana..Mummy said i should call u"..wnn karon gaba daya ya bude idanun nashi yana kallonta...sai kuma ya mike zaune yana gyara gashinshi data hargitsa yace"Ilham bakida hankali kou?.."tace"Sorry Uncle Bobby Mummy tace a kiraka"..sauka yayi daga gadon snn yace mata"kice am coming"..Ilham bata sake mgn ba ta mike ta fita..shi kuma ya shiga bathroom yana jin haushin katse mishi bacci da akayi...ya tabbata da ba Ilham din suka turo ba duk wanda yazo ya tadashi a baccin nan sai anji kansu dashi amma Ilham favorite dinshi ce shiyasa ko fada bai fiye yi mata ba...brush yayi ya wanko face dinshi ya fito don bai dade da yin wanka ba...ya dauki wayanshi kan mirror snn ya fita...a Central parlor ya samesu zazzaune...Mummy ce da Aunty Sumy sai wata mata da bai gane wace ba...ya karasa kusada Mummy ya zauna snn yace"Mummy gani...lafia dai koh?.."da igbo tace mishi"lafia ka gane wnn?.."ta nuna matar dake zaune...ya girgiza kai alaman aah...tace"Sunanta Hafsa kuma qanwar Isma'il ce"..ai tun kafin ta rufe baki ya wara ido sosai yana kallonta fuskanshi har ya sauya sbd 6acin rai...bata damu da sauyin face din nashi ba tacigaba"zuwa tayi tanaso ta tafi dasu Miemie su dubo grandmum dinsu da batada lafia"...bata rufe baki ba cikin zafin rai still da igbo yace"babu inda zasuje Mummy...basu bukatan wayan nan mutanen a rayuwarsu"...shiru Mummy tana ganin yanda yakeson kunyata ta gaban baiwar Allahn nan..dukda bada hausa yayi mgn ba tasan zata iya fahimta sbd yanda ranshi ya 6aci all of a sudden...Aunty Sumy kam dama she expect this to happen shiyasa she's not surprised...ita kuma bakuwa Hafsa kanta na kasa tana sauraronsu...dukda bata gane me yake cewa ba har ga Allah ko hanata daukan yaran sukayi bazatayi blaming dinsu ba tunda tasan duk wulakancin da sukama uwar yaran har ma dasu kansu yaran a baya so bazataji haushinsu ba ko kadan...Bobby da yaji zuciyarshi na kara haurowa sama mikewa kawai yayi ya fita daga parlon cox idan yaci gaba da zama zai iya causing scene din da he might end up regretting dan haka yake ganin it's better he leaves...Mummy da taji kunyan abunda ya fada ta bishi da kallo kawai har ya shige flat dinshi snn ta dawo da kallonta ga Hafsa tace"don't mind him Hafsa inshaAllah tare zaki tafi dasu..amma ayi kokari a dawo dasu gobe sbd kar suyi missing school"...da sauri Hafsa tace"in Allah yadda za'a dawo dasu Mummy...nagode sosai Allah ya saka da alkhairi"...Mummy ta amsa da Ameen snn ta juya ga Aunty Sumy da ita kanta bataji dadin hukuncin da Mummyn ta yanke ba tace taje ta hada kayan Ilham ta kawo itama Miemie ace ta shirya nata kayan ta fito...haka ta mike jiki ba dadi ta shiga flat dinta...dakin Miemie ta fara tsayawa ta fada mata ta dauki kaya set daya zasuje gidan grandma dinsu da Aunty Hafsa...itama ranta baiso ba amma ba yanda ta iya ta dauki set dayan kaman yanda tace ta saka a jaka snn ta fita...itama Aunty ta fito da na Ilham a hannunta. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 sai a tura evidence of payment via 07063800556. 14 Miemie ta amsa kayan ilham din ta hadashi da nata cikin bag din data dauko snn ta samu wuri ta zauna...Hafsa ta mike tana duban Mummy tace"Mummy to bari muje in Allah ya kaimu gobe da kaina zan dawo dasu..nagode sosai da sasai Allah ya saka da alkhairi ya kara girma"...Mummy tace"ba komai Hafsa Allah ya bata lafia"..ta amsa da Ameen snn ta rike hannun Ilham zasu fita Mummy tace"Ilham ba sallama?.."juyowa tayi tana murmushi tace"ba bye Mummy mun tafi yawo"...murmushi na daria tace"to a dawo lafia"..daga haka suka fita Aunty Sumy da Miemie sukabi bayansu...kafin su karaso har ta bude mota sun shiga..suna zuwa Miemie ma ta bude ta shiga ita kuma Aunty Sumy tace"to shknn Hafsa sai goben koh?.."Hafsa tace"eh inshaAllah...ina godia fa Maman Miemie Allah ya bar zumunci"..Aunty Sumy tace"Ameen"..snn ta dagama ilham hannu alama bye itama ta daga mata...Miemie dai na zaune back seat duk rai a 6ace..sam batason zuwan inda matar nan wlh..dukda ba wani girma gareta ba time din she can still remember yanda sukayi treating nasu kaman ba family dinsu ba...bayan sun gama sallama Hafsa taja mota ta tafi ita kuma Aunty Sumy ta koma gida. Basu zarce ko ina ba sai gidan kakarsu dake Kabuga...tana gama parking ta bude motar ta fita tareda kama hannunsu gaba daya su biyun suka shiga cikin gidan a haka...kakarsu na kwance parlor tana jiran karasowarsu...tana ganinsu ta mike zaune da kyar ta kama hannayensu kawai sai ta rushe da kuka..ba ita kadai ba hatta Hafsa saida ta tayata kukan...ko baa fada ba tasan tanajin ciwon raba Sumayya da Isma'il tunda gashi nan tun bayan rabuwarsu ta kasa gane kan danta...matar data aura mishi ma bai dade da rabuwa da Sumayyan ba ya saketa shi kuma ya tattara ya koma London da zama sbd baqin cikin rashin Sumy...kuka takeyi sosai tana cewa su taimaka su yafe mata snn su roki mamansu ma ta yafe mata...Ilham dai tayi tsuru as kwata kwata bata san inda zancen ya dosa ba...Miemie kuwa sarai ta fahimci me take nufi amma tayi gum da bakinta dan bataji zata iya yafewa ba itadai...ta dauki tsohon lokaci tana kuka tana su yafe mata ganin kamar numfashinta zai dauke suka rabata da hannuwan yaran da kyar snn suka dauketa suka maidata daki itada autarsu mai suna Safiyya...Hafsa na fitowa daga dakin ta dannama dan uwanta video call don yace tana daukosu ta kirashi vid call yanaso ya gansu...yana ganin kiran nata ya dauka tana murmushi tace mishi"to Yaya ga 'ya'yanka dai yau na kawosu wajen Umma"...yace"kin kyauta sosai Hafsa..dan banisu mu gaisa plss"...ba musu ta mika musu wayan tace"speak to ur Dad"..Miemie ta wani hade rai snn ta karbi wayan...kallonsu ya shigayi sosai idonshi na cikowa da hawaye...it's been six long years rabonshi da ganinsu..yanxun kuma daya gansu sai yakejin wani irin kewa da sonsu na sake shiganshi...murya can kasa yace"Mamana"...Miemie ta dan tsuke baki kafin tace"na'am ina yini"...yace"lafia mamana ya school?.."a takaice tace dashi"fine.."kallonshi ya maida ga Ilham da tayi tsit tana kallonshi dan ba saninshi tayi ba...shima saida yaji wani kuka ya taho mishi da yaga kallon da take masa...ko ba'a faa ba yasan kallon rashin sani ne wnn..wai ace yana matsayin mahaifinta amma ta tashi bata sanshi ba...shi kam ina zaikai zunubin yaran nan dana uwarsu?..itama murya a sarke yace mata"Maman Aunty"...ta sake yin zuru tana kallonshi dan bata gane me yake nufi ba..Miemie dai ta gane don bazata manta ba lokacin tana jaririya haka yake kiranta Maman Aunty ita kuma Miemien ya kirata da Mamana..itama Aunty tacema Miemie Maman daddy snn tacema Ilham Mamana...yayi kokari ya maida hawayen dake idonshi yace"baki sanni ba right?.."da sauri ta daga mishi kai...yace"i am ur father"..yarinyar ta wara ido sosai hadda su rufe baki tace"Uncle Bobby ne babanmu ai"...yace"yea he is ur dad but ni na haifeku"...idon ta sake budewa cikeda mamakin abunda ya fada tace" dama maza suna haihuwa ne?.."diff yayi kamar ruwa ya cinyeshi..sai can kuma yace"sunayi mana kinga ni din nan nine babanku..shi kuma Uncle Bobby uncle dinku ne shiyasa kuke kiranshi da uncle"...kafin Ilham ta sake mgn Miemie tace"sai anjima"...tana kokarin kashe kiran yace"don't hang up plss..i missed u guys alot ko ganinku bazaki bari nayi ba?.."tayi shiru ba mgn shi kuma yace"ya Mamanku?.."ta sake cewa"she is fine.."shima ya danyi shiru na tsahon lokaci kafin yace"i know u are upset with me Miemie but believe me wlh nayi regretting komai dana aikata dan haka please inaso ki yafemin snn ki tayani rokon mamanki ma ta yafemin"...kallonshi Miemie tayi for like two minutes snn tace"toh.."daga haka bata jira me zaice ba ta kashe kiran..sam ta gaji da jin wnn maganganun nashi...ita har taso ta manta kamanninshi ma wlh..ilham kuwa dama bata sanshi ba so bata dauki abunda ya fada serious ba...haka suka kwana gidan duk basu wani sakewa dasu duk kuwa da yanda yan gidan suke kokarin jansu a jiki kin sakewa sukayi. A can gida kuwa Bobby baisan tare dasu Hafsa ta tafi ba saida ya dawo daga Hospital around 9 na dare ya tambayesu Aunty Sumy tace sun tafi da Hafsa...wani hadadden kunchi yaji yana sauko mashi..yanxu knn Mummy saida ta tura yaran nan suka tafi?..bayan duk abubuwan da suka aikata a baya still take kokarin patching things up dasu?..ranshi gaba daya yaji ya 6aci..kawai ya wuce Flat dinshi...karfe goma da wani abu Mummy ta zuba abinci ta dauka da kanta ta nufi Flat din nashi...yana kwancen can kuryar gado ya juyama kofa baya..ta karasa ta ajiye abincin hannunta kan table snn ta isa gefen gadon nashi ta zauna...a hankali takai hannu ta zare hannunshi daya rufe fuskanshi dashi...ha dago yana kallonta snn ya mike zaune da kyar kaman mara lafia...sake kama hannun nashi tayi ta rike tana kallonshi da igbo tace mishi"so u are upset with me right?.."a hankali ya girgiza kai alaman aah...tace"you are lying nasan fushi kakeyi...kana jin haushi sbd na bari Hafsa ta tafi dasu koh?."kasa yayi da kanshi baice komai ba...Mummy tace"Bobby you won't understand..bansan ya zanyi maka bayani ba..kawai dai banaso ka nesantasu da yan uwan mahaifinsu kaman yanda ka nesanta mu da gaba daya yan uwan mahaifinku..ni kadai nasan how am feeling duk na tuna cewa grandfather dinku na nan da rai amma baisan inda kukeba tsawon shekara biyar...inaji a jikina bamu kyauta ba sam kuma nasan Allah bazai yafe mana..."bata karasa ba ya rufe bakinta tareda matsowa sosai ya rike hannayenta...idan ya bari tacigaba da magan nn tsaf zata kashe mishi jiki tasa ya farajin kaman shima bai kyauta din ba...ga kuma jininta da zai iya hawa idan bata bar wnn damuwan ba...yana kallon cikin idonta yace"Mummy ba laifi bane...ba laifinmu bane...laifinsu ne da basu ta6a yunkurin nemanmu ba...su kuma su Ilham nasan ke da kanki kinsan meyasa banso suje inda mutanen nan sbd ba sonsu sukeyi ba"...hawaye suka shiga sauka fuskanta tace"duk abunda in the past bai kamata mu bari yayi affecting future dinmu ba...we are all Humans Bobby and we all make mistakes...nasan abunda da sukayi is uncalled for amma ya zamuyi?..dole haka zamuyi hakuri dasu tunda sunyi nadama...zumunchi ba karamin abu bane Bobby banaso Allah ya kamamu da laifin yanke zumunta a ranar gobe kiyama"...tana karasawa wasu tawagar hawaye suka sake biyo fuskanta Bobby baisan sanda ya matsa tareda rungumota jikinshi ba...kuka takeyi sosai da alama dama ta jima tana neman inda zatayi kukan...bai hanata ba saida ta dakata dan kanta snn yace"Mummy to kukan ya isa haka plss and we shouldn't talk about them again..am not angry anymore"...ta saki dan murmushi tana share hawayenta tace"then tashi muje kaci abinci"...baiyi musu ya mike ya koma kan sofa ya zauna snn ya janyo table data ajiye abincin akai ya fara cin kayanshi...itama mikewan tayi ta dawo kusa dashi ta zauna snn tace"and mgnr zuwa duba Waziri"...a takaice yace"yana nan Mummy..idan ya dawo zamuje gaba daya mu dubashi..are you happy now?.."sake gyada mishi kai tayi tana murmushi...shi kuma yacigaba da cin abincinshi amma deep down yasan abunda ya fada karya yake...ko kusa baijin zuciyarshi zai iya mance tarin munanan abubuwanda Waziri da iyalanshi suka aikata musu har yaje inda suke..sam hakan ba mai yiwuwa bane ya fada mata ne kawai dan ta dena damuwa amma baida intension din zuwa ko ina..shi a yanda yakeji mafa ko rasuwa waziri yayi saidai suje za'aziyya kawai su dawo amma ba wani zaman makoki da zasuyi tunda bai ta6a daukansu a matsayin Family ba. Gombe... Tsaye take a kitchen tana suyan Pancake fuskan nan a tamke kaman wanda aka aikoma da sakon mutuwa...daga gefe kuma Ammi ce tana kokarin hadama Daddy breakfast dinshi a kan tray sai kuma mai aikinsu dake juya pepper soup a kan gas...bayan ta gama hadawa ta dauki tray din kafin ta fita ta dubi Aysha dake faman tura baki tace"kuma wlh idan bakiyi sauri kin gama ba har Lamido ya fita bakuje kun gaisheshi ba zakiga yanda zanyi dake a gidan nan"..mai aikinsu mai suna Asabe tace"da kin barta hajia zan karasa wlh..ita taje tayi shiryawanta"...Ammi tace"bazan barta ba Asabe na lura tunda ta dawo gidan daga kallo sai chatting ta iya bata tsinana uwar komai ko dakinsu saidai Husna ta share..anjima ma ita zaku bawa suyan fried rice tayi ai ba bayi ta ajiye dan sunayi mata girki ba"...tana gama fadin haka ta fita daga kitchen din...ita dai Aysha na tsaye tana aikin gabanta ko juyawa batayi ba amma fuskan nan kaman zatasa kuka...ko Allah yasan ba mai son girki bace ita...gara a bata duk wani aikin gida zatayi amma ta tsani girki shiyasa ko a makaranta Billy keyi musu girki...Asabe na ganin Ammi ta fita ta kashe gas din gabanta snn ta matso inda Aysha take tana amsan spoon din hannunta tace"kawo in karasa kinji indo...ki tsaya daga nan ki huta idan mukaji zata dawo saiki kar6a kicigaba"...nan da nan kuwa ta sakin mata shi tareda matsawa gefe tace"nagode Baaba"...Asabe tacigaba da suyan Pancake ita kuma ta rungume hannu tana kallonta...wayanta dake aljihun jean dinta ne ya fara ringing...ta zaroshi da sauri tana sakin wani smile ganin Prof ke kira tasan yanxu zaiyi flushing wnn 6acin ran da take ciki...saida ta gama kwa6e fuskanta tayi readyn shagwa6a snn tayi picking...a daya 6angaren Professor yace"my baby girl"...ta wani cunno baki sai kace yana ganinta tace"umhhm"...yanajin yanda tayi replying yasan akwai matsala...if u see yanda ya gigice zakasha namaki...fadi yake"my baby please what happened...waya ta6amin ke?.."ta sake narkewa tana tale baki tace"baby Ammi ne"...yace"Subhanallah me Ammi tayi maki?..hope ba dukanki tayi ba?.."tace"cewa tayi sai nayi suyan Pancake...kuma ni baby banason girki fa"...tana iya jiyo sautin dariyarshi kafin yace"eyya sorry my baby gaskia Ammi bata kyautamin ba..why zata turamin mata kitchen?.."tana sake narkewa tace"shi na gani nima baby..aidai in munyi aure bazaka na sani girki ba koh?.."yace"wane ni in saka princess dina girki...duk abunda mukeso ordering zamu dingayi ko mu dauko chefs su dafa mana"...lokaci daya ta wage baki tana smiling tace"yauwa my Professor..my very own baby durling"...saida ya lumshe ido daga can inda yake ya wani dora hannu kan chest dinshi yace"ohhh that sounds sweet baby...i love u"...tace"i love u more baby"...mai aiki dai na aikinta tana sauraron yanda take zuba shagwa6a tana murmushi...ko su da suke aiki gidan sun san Aysha mai son shagwa6a ce duk kuwa da cewa iyayen nata ba shagwa6ata suke ba...haka taciga da wayanta har aka gama suyan Pancakes din snn ta dora wormern da aka zuba kan tray ta fita dashi parlor...dining ta karasa ta ajiye snn ta nufi parlorn daddy...as usual suna zaune dinning suna karyawa shida Ammi...ta karasa ciki bayan ta nutsu snn ta gaisheshi ta bar parlon...tana fita ta samu su Husna a dinning itama ta karasa ta zauna suka fara breakfast...Ammi da daddy suka fito tare bayan sun kammala suma...Ammi na rikeda briefcase dinshi zasuje gaida Lamido shi da yaran daga can kuma zai wuce Abuja wurin aikinshi...su Aysha na zaune parlor suma sun gama nasu breakfast din kowacce sanyeda katoton hijab sbd zaaje gaida Lamido...Daddy ya kalli yanda sukayi reras a parlon kowa tasha hijab kawai ya girgiza kai yasa daria...ya lura har wani nutsuwa na musamman sukeyi duk zasuje wajen Lamido snn kaf jikokinshi ba wadda take zuwa mishi ba tareda hijab ba dan fada yake sosai...bayan ya gama dariyan ya kallesu one by one yace"are we good to go?.."suka hada baki wajen fadin"yes daddy"..snn yace"to ku tashi muje"...gaba daya suka mike suka fita...shima suka fita tareda Ammi...har jikin mota ta rakashi ta bude mishi kofa da kanta ya shiga snn ta ajiye briefcase dinshi..suma su Aysha nasu motan suka shiga tana kallon Ammi tana sallama da mijinta cikin ranta tace" muma dai muzo muyi auren nan wlh..haka zanje inta yima babyna yana lalla6ani"...Yusra dake jikinta tace"Adda me kika ce?.."ta saki murmushi tana shafa kan Yusra tace"ba komai habibty...bance komai ba"...motan daddy ne ya fara fita daga gidan snn nasu. Kofar gidan Lamido motocinsu sukayi parking...daddy ya fara fitowa suna biye dashi zuwa ciki...katoton parlon Lamido dake daukeda two sets of kujeru suka shiga...yana zaune kan one of kujerun sai wasu mutane biyu zaune a kasa suna gaisheshi...karasawa ciki sukayi daddy ya zauna kasa ta right side dinshi su kuma suka zauna his left side...kyakkyawan bafulatani da a kallon farko da kayi masa zaka gane attajiri ne snn kuma yanada dattako...kamanninsu daya da daddy saidai haske da daddy zai nuna masa shima ba sosai ba...bayan ya sallami mutum biyu dake zaune ya juya yana duban daddy yace"Ahmad har an fito?.."cikeda respect daddy yace"na samu fitowa Baffa...barka da safiya"..yace"barka dai ya iyalin?.."kai a kasa yace"suna nan lafia Baffa...tace a mika mata gaisuwa kafin ta shigo"..gyada kanshi yayi yace"to mashaAllah"...sai kuma ya juya ga su Aysha ya dan saki murmushi yace"mutanen Lamido"...da ladabi suma suka dukar da kai suka gaisheshi...ya amsa tareda tambayansu makaranta sukace Alhamdulillah...idonshi ya tsayar kan Aysha kafin yace"ke saura wata nawa ki gama karatun ne Aisha?.."tace"ba watanni bane Lamido saura shekara daya da rabi"..gyada kai yayi yace"to ba laifi Allah ya kaimu..Allah yasa a gama lafia"..sukace" Ameen Ameen"...sun dan jima suna hira har wani qanin daddy ya shigo shima da 'ya'yanshi...suka gaisa dashi snn daddy yayi salama da mahaifin nasa suka fita...kai tsaye ya shiga motanshi suma suka shiga nasu bayan ya sallamesu suka koma gida shi kuma suka fita daga Estate din. Kwanci tashi abun ba wuya har sun cinye sati biyunsu cif sun fara shirin komawa makaranta...tunda satin komawa ya shigo Aysha take kunci tana baqin ciki sam batason komawa wlh especially idan ta tuna wnn dan rainin hankalin inyamurim Proprietorn nasu...sam bata kaunarshi wlh...neman hanyan da zata sanar da Ammi kawa take amma ta rasa dan haka ta tsiri 6ace 6acen rai sai ta zauna a parlor da gayya tayi tagumi wai tanaso Ammo ta tambayeta abunda ke damunta ta fada mata amma Ammi tayi biris da ita kaman batasan tanayi ba...abu daya dake dan yaye mata wnn damuwan shine Prof dinta...zuwa yanxu soyayya sukeyi sosai sai kace wanda sukayi shekara da shekaru a tare...yana mugun shagwa6ata kaman yanda takeso ita kuma tana sake falling mishi. Kaman kullum yau ma tana zaune ta buga uban tagumi a parlor wai ko Allah zaisa Ammi ta tambeyi meke damunta saidai abunda bata sani ba shine Ammi ta rigada ta ganota tasan duk wnn attitude da take displaying kilan sbd komawa makaranta ne shi yasa taki kulata...Ammi ta shigo parlon waya kare a kunneta tana mgn da Aunty Fiddausi...bayan ta gama ta dauki remote tana kokarin kunna tv Aysha da taga still bazatayi mata mgn ba ta dan marairaice tana dubanta tace"Ammi.."ba tareda ta bata attension dinta ba tace"na'am"...sake narkewa tayi tace"Ammi bazaki tambayi meke damuna ba?.."dan juyawa Ammi tayi tana kallonta kafin yace"what's wrong..are u sick?.."sake marairaicewa tayi ta koma kalar tausayi tace"Ammi dan girman Allah ki cema daddy bazan koma makaranta ba plsss"...fuska daure Ammi tace"sbd me?.."tace"bana sonta wlh kuma yanxu ba wani karatu akeyi ba sai shegen takurawa mutane"...gyada kai Ammi ta shiga yi tace"dama nasan karshen zancen knn...kilan kinje kinyi laifi anyi miki fada shine zakizo kice mana bazaki komaba kuma kike tunanin zamu yadda dake kaman bamusan halinki ba koh?..to bari kiji in fada maki babu fashi komawa makarantanki gobe idan kuma kika sake kika sake min mgnr nan sai kinci ubanki wlh...daidai nake dake ai kinsani"...nan da nan ta fara hawaye tana cewa"nifa Ammi Allah na gaji da Kano inaso in dawo gida...kuma Proprietor dinmj inyamuri bashida mutunci wlh"...Ammi mikewa tayi zata bar parlon tace"ur problem not mine..nidai na gama mgn kuma Allah yasa kar ki dena kukan nan kiga yanda zanyi dake a gidan nan...shashasha kawai"...daga haka Ammi ta wuce dakinta...ita kuma hajia indo ta rungumi pillow tana sake rushewa da kuka. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 15 Yau Sunday tun around ten Hamma ya tafi maidasu bisa umarnin daddy ya maidasu da wuri shima ya samu ya dawo gida da wuri kafin dare...karfe daya a cikin Hostel yayi musu...Hamma bai tafi ba saida ya tabbatar ba abunda suke bukata snn ya musu sallama ya wuce su kuma suka shiga area classes don duba Posting dinsu...gida biyu akayi dividing class dinsu first 19 aka turasu Freedom sauran 19 din kuma aka turasu Kinana...gaba daya ran Aysha taji ya 6aci itadai Allah ya sani ba son Freedom din nan takeyi ba...tasan ko baa fada ba Dr.Bobby mugun takurawa mutane zaiyi sbd yana ganin Hospital dinshi ne...ita kuma harga Allah yanxu batason abunda zai sake shiga tsakaninta dashi yazo yana mata rashin mutunci tunda ta fuskanci dabi'arshi ne...kallon Billy tayi tace"Billy zo muje muyi mgn da provost ko zaisa baki a canxa mana posting din nan...na tsani zuwa Freedom wlh"...Billy tace"but why?..asibitin yanada kyau fa Lamido..besides ko kinje wajen provost ma i don't think zasu canxa maki cox ba'a ta6ayima mutum posting kuma daga baya a sake mishi ba..kawai ki hakura dashi nasan muna fara zuwa zakiji kina enjoying"...girgiza kai ta shigayi bayan Billy ta gama mgn tace"nidai dan Allah ko rakani ne kiyi plss...Allah bazan iya zuwa Hospital din nan ba haka nan da kayi small mistake Proprietor yace zaiyi maka rashin mutunchi"...daga kafada Billy tana cewa"Fine tunda bakiji shawara na ba...nima kuma babu inda zan rakaki sai kije ki dawo ina jiranki a nan"...hararanta tayi ganin itama zata mata wulakanci kawai ta juya ta tafi ita kadai...kafin ta shiga office din secretary dinshi tace baya nan amma yace idan anzo nemanshi ta kira ta sanar dashi dan haka tayi dialing number dinshi yana dagawa tace"Sir Lamido tazo nemanka"...daga other side din yace"kice ta sameni office din Dr.Bobby"..tana kashe wayan tace mata"yace kije office din Dr.Bobby yana can"...Aysha ta wani zaro ido jin ta ambaci Dr.Bobby tace"tsaya..waye Dr.Bobby?.."dan murmushi Secretary din tayi kafin tace"Proprietor mana"...wani irin diff tayi kaman wuta ya dauke mata...tabbas da tasan inda yake knn da bata bari an kirashi bama in the first place bare har yace taje can ta sameshi...itafa ta tsani abunda zai hadata da inyamurin nan ko kadan..sam batason hada sabga dashi sbd ta lura ba karamin mara mutunchi bane...gashi kuma Secretary ta ambaci sunanta da wlh bazata jeba sai tayi wucewarta ta dawo daga baya amma yanxun tunda yaji sunanta tasan zuwa ya zama mata dole ko don posting da takeso a sake mata tunda gobe zasuyi reporting...ganin tana 6ata lokaci a banza ta juya ta fita daga wurin tayi hanyar office dinshi tana sake sake cikin ranta sai kuma taji haushin kanta for tsoron wnn inyamurin...kawai ma gara taje inyaso ta dake ta fadi abunda ya kawota tasan duk tsiya dai bai isa yasa hannu a jikinta ba...da wnn sabon courage ta isa zuwa office din...bayan an bata permission din shigowa ta tura kofar a hankali ta shiga kai a kasa...yana zaune kan kujera yayinda Dr.Bobby shima ke zaune kan office chair dinshi...ta karasa ciki ta tsaya snn tacema Nur"good afternoon sir"...yace"Afternoon Lamido ya holidays" ...ta dan kakalo murmushi tace"Alhamdulillah"..yace"to bismillah zauna inji meke tafe dake?.."tace"thank u ba saina zauna ba Sir...akan mgnr posting ne dama"...yace"Posting?..meya faru?.."saida ta hadiyi saliva trying very hard not to look at Bobby da zata iya rantsewa taji wann shegun eyes din nashi a kanta tace"Sir...banason inda akayi posting dina shine nace in maka mgn ko zakasa a canxa min?.."Nur dake kallonta yace"No problem ina akayi posting dinki?.."ta sake hadiye wani yawun snn tayi qundunbala tace"Freedom"...da mamaki sosai Nur yake kallonta yace"amma why bakison Freedom din?..naga students da yawa har so sukeyi ayi posting dinsu can"...kai tsaye tace"Sir kawai nidai banaso"...saida ya danyi shiru na wani lokaci kafin yace"shknn kije zanyi mgn da Isaac sai muga yanda za'ayi"..nan da nan ta saki smile tana fadin"thank u so much Sir..nagode"..wani mamakin ya sake kamashi ganin how happy she is kawai sbd xaa canxa mata posting...lallai bata son Freedom din kuwa kaman yanda ta fada...Dr.Bobby yayi shiru yana kallonsu saida suka gama yace"ba wanda za'a canxama posting"...a tare Nur da ita suka juya suna kallonshi...ganin kallon da suke mishi ya sake tamke fuska yana cewa"don me za'a canxa mata posting bayan ba haka akeyi ba...who did she think she is?.."Nur yace"amma..."bai bari ya karasa ba ya katseshi da fadin"if she can't stay..she leaves"...mamaki sosai ya kama Nur kawai yayi sakato yana kallonshi...ita kuwa Aysha right now ji take kaman ta kwada masa mari...dan rainin hankali har ita zai wani ce she leaves?..wlh da daddynta zai amince da daga office din nan ko Hostel bazata koma ba zatayi gida saidai Bilkisu ta taho mata da kayanta amma she won't sbd tafi kowa sanin halin mahaifinta...rai a matukar 6ace ta juya zata fita yace"dawo.."tsayawa tayi cak da tafiyar ita bata juyo ba kuma bata cigaba da tafiya ba...shi kuma ganin ta wani yi tsaye ta juya musu baya saiya tuna ranar da sukaje Hostel dinsu ma haka tayi musu...a kausashe yace"i said come back here...are you deaf?.."juyawa tayi ta koma gaban table din fuska a tamke...Dr.Nur dai relaxing yayi yana kallon wnn rigima nasu...ya shiga binta da wnn kallon da bata kauna snn ya nuna hannunta da fingers dinshi yace"remove those things"...a rikice ta dago tana kallonshi sai kuma ta dauke kan da sauri jin wnn abun da batasonji duk ya kalleta..hannun nata ta kalla zobuna ne na gold guda biyu ajiki kwata kwata mantawa tayi bata ciresu kafin ga bar gida ba...ta dan rage murya tace"Sir..."kasa karasawa tayi sbd wnn idanun dai daya zuba mata...bata sake yunkurin mgn ba takai hannu ta zarosu daga fingers dinta snn ta ajiye kan table din ta juya a fusace ta fita daga office din..shi kuma ya daukosu daga inda ta ajiye ya bude wani drawer dake kusa dashi ya watsasu ciki ya rufe...duk abunda yake idanun Nur na kafe a kanshi yana kallon latest behavior dinshi...mamakin ta yanda har ya lura da akwai zobe hannunta yake dan koshi da suke mgn da ita bai lura akwaisu a hannunta ba saida ya fada...wani murmushi ya saki yana shafa beard dinshi yace"Dr.Bobby tell me plss..do u love this girl?.."wani kallo Bobby ya bishi dashi kafin yace"what the hell...are you insane?.."Nur ya daga shoulders dinshi yace"no am not..kawai dai inaso in san ta yanda akayi ka lura da akwai rings a hannunta bayan koni da nake mgn da ita ban lurada hakan ba"...tsabar haushi kasa mgn yayi sai ido kawai daya zuba mishi yana mishi kallon da shi kanshi yasan zaiji ajikinshi...ilai kuwa Nur din ya dan yatsine fuska yace"C'mon stopping looking at me that way plss?..sbd kasan tasirin idanunka shiyasa kakeso kayita tsatstsare mutane dasu don kasa sunajin somehow..nidai stop looking at me plss tunda mgnr ne bakaso an barshi"...murmushin cin nasara ya saki tareda komawa yayi relaxing kan kujeranshi...Nur yace"dole kayi smiling mana tunda ka cuceni"...baice mishi komai ba sai shoulder dinshi daya daga. Washegari Monday kowa zaije yayi reporting a Hospital da aka kaishi...kaman kullum karfe 8 school bus dinsu ya kwashesu zuwa Freedom Specialist Hospital...daidai lokacinda suka isa Hospital din shima Dr.Bobby yazo..bayan bus dinsu yayi parking duk suka fito shi kuma bai fitoba sbd waya da aka kirashi...daga nan inda yake ya hangota suna mgn da Billy baidai san me suke cewa ba yaga sun nufi wurin wata mota...suna fitowa Aysha da tun shigowarsu taga motar babynta a parking space tace ma Billy"wlh Billy shine ba gizo yakemin ba..dama yace yau ko office bazai iya zuwa idan baizo ya ganni ba"...Billy da zuwa yanxun ta dan fara sakewa dashi tace"ikon Allah..kinga har ya rigamu zuwa"..Aysha daketa blushing tace"ai Allah kadai yasan tun yaushe yake a nan...zo muje kar ya gaji da jira"..ba musu Billy ta bita zuwa inda yake...tun kafin su karaso ya bude mota ya fito idanunshi kan Aysha yanajin kaman ya rungumeta ga jikinshi tsabar kewarta da yayi...suna karasowa Billy ta gaisheshi ya amsa da tambayan ya baby girl dinshi tace"wnn baby girl din taka fa sai kai...bazan iya da fitinanta ba"...yayi daria yace"anya kuwa zan yadda dake Billy?.."itama tayi dariyan tace"ai dama bazaka yadda ba na sani...nidai bari na shiga ciki sai anjima"..yace"to shknn Bilkisu ina godia sosai"..bata sake cewa komai ba ta bar wurin..shi kuma ya bude front seat yana kallonta yanajin kaman ya maidasmta cikinshi...ba musu ta shiga ya rufe kofa snn ya zagaya shima ya shiga...kallon juna kawai sukeyi kowa yanajin soyayyan dan uwanshi na karuwa cikin zuciyarshi...a dan zamansu dashi Aysha ta fuskanci zurfin da yayi a karatun boko baisa ya zubar da addininshi ba...yanada addini sosai dan tunda suke bai ta6a yi mata anything dirty ba..ko dirty talk bai ta6ayi mata haka kuma bai ta6a kama koda hannunta ba...wnn dalilin yasa sonshi ke karuwa cikin ranta..tasan matukar ta aureshi tayi dace da salihi kuma muminin namiji...shi kam ganin time na tafiya and baiso ta makara ya dan saki smile yana cewa"i missed you"..ita kuma shagwa6e fuska tayi kaman wata baby tace"i missed you more baby"..yayi murmushi tareda dauke kanshi dab yanda tayi da face dinta yasa yaji kaman yayi hugging dinta...yanason yarinyar nan to the moon...hira suka dan ta6a kadan snn yace mata zai wuce amma su shirya itada Billy da yamma zaizo ya kaisu shopping...ta wani lankwasa murya tace"baby u shouldn't bother munada komai wlh"...hade rai yayi yace"banason musu baby..idan kuma ban isa ku amsa abun hannuna bane fine"...da sauri tace"to kayi hakuri na dena...zan fada mata inshaAllah"...yace"yauwamy little baby girl...yanxun ki shiga ciki kar suga kin dade baki shigo ba"..ba musu ta bude mota ta fita ta sunkuyo ta window suka sake yin sallama snn ya tada motar ya tafi ita kuma ta shige ciki...duk wnn abun da suke kan idanun Bobby daya gama wayan da yake tun daxu amma ya kasa fitowa daga motar...tunda yaga ya bude mata mota ta shiga da kuma yanda yake hango murmushinda take daga nan inda yake yasan confirm wnn boyfriend dinta ne...haka nan yaji wani irin haushinta ya kamashi cikin ranshi yace"she isn't only a spoiled brat she's also a flirt"...har saida yaga ta fito daga motan snn shima ya bude nashi ya fito...driver dinshi da tunda sukazo ya fito waje ya mika mashi briefcase dinshi ya amsa snn yasa kai cikin building din. Tana zuwa ta samu colleagues dinta office din Chief Nursing Officer inda daga nan akayi posting dinsu various wards...Billy tana Antenal Clinic Aysha kuma tana cikin Labour Room...ranta duk ya 6aci an rabata da qawarta snn kuma an kaita maternity da bata kauna...sam batason aikin labour room sbd azabar wahala...aikine sosai suke yinshi kmr ba gobe shiyasa duk dunia ba ward da take son aiki kaman ANC ko Family Planning Unit...su aikinsu nada sauki and ba'a shifting amma yanxu tasa a labour room da kyar idan ba'a sata shifting ba...tanata 6ace 6acen rai suka fita daga office din..Billy ta wuce ANC tareda sauran da akayi posting dinsu tare itama Aysha suka wuce Maternity. Karfe goma daidai Dr.Bobby ya shiga Maternity don yin ward round...wata Midwife dake zaune Nurses Station tana cike Register tazo da sauri ta gaisheshi snn ta koma ta fara harhada files din patents...ta dorasu gaba daya kan trolley snn ta turama Aysha data fito daga labour room yanxu tace"Aysha dan je kuyi ward round da Dr in samu in karasa cike Register nan"...ba yanda ta iya haka ta tura trolley din tayi gaba...yana tsaye kusada bed din wata patient da sukayima cs last two days yana mata tambayoyi Aysha ta karaso wurin...ta daure fuskanta sosai tana sunkuyar da kai kasa dan ko Allah yasan batason hada idanu dashi...tunda tazo wurin yaji zuwan nata amma yanda yayi zaka rantse babu wata hallitta a kusa dashi...hankalinshi gaba daya yana kan patient da yakema tambaya ko kallon bayanshi da yasan tana tsaye baiyi ba...tana fada mishi sunanta Aysha ta shiga nemo file dinta cikin tulin files dake kan trolley kawai sai ya kai hannu ya janyo trolleyn zuwa gabanshi ya dauki file din nata snn yacigaba da aikinshi...wani sabon takaici taji ya lullu6eta...meyasa mutumin nan keyi mata haka ne wai?..meyasa bashida kirki ko kadan?..ganin ya tura trolleyn da kanshi zuwa next bed itama ta ta6e baki cikin ranta tace"ka wutar dani nima"..ta juya ta koma ciki...midwife din da taga ta dawo tace"ya kika dawo kuma?.."kai tsaye tace"shi yace in dawo"...mikewa tayi daga inda take zaune ta fita zuwa inda yake..ita kuma Aysha ta zauna inda ta tashi tacigaba da cike nata register...bayan ya gama ward round har zai fita tace mishi akwai wadda ya kamata ya duba cikin labour room dan haka ya juya zuwa labour room din...Aysha na zaune tana aikin gabanta ko kallon inda suke batayi ba...sun shiga ciki suka samu matar dake ciki tanata fama har kan baby ya fara fitowa sukayi kanta da sauri...ganin harta jigata ranshi ya 6aci sosai...ita waccan zaman uban me takeyi da har patient ra kusa haihuwa bata sani ba...midwife da suke tare tana kokarin taimakawa matar ya dakatar da ita...tace"Sir babyn zaisha ruw..."bata karasa ba yace"call that useless da take zaune ta kyaleta ita kadai"...da sauri ta fita ta kira Aysha...yana ganinta ya sake dinke fuska yace"are u mad?..bakida hankali zaki wuce ki bar patient ita kadai cikin wnn situation din?..are u sick or something?.."dan turo baki tayi tace"ai ni bansan ta kusa haihuwa ba...kuma Register nake cikewa"...sbd tsabar takaici kasa ce mata komai yayi...yana nuna patient din yace"go and attend to her and make sure u did not make any mistake cox you'll regret knowing me"...cikin zuciyarta tace"ai ko a yanxu i regret knowing u wlh...me za'ayi da sanin masifaffen mutum irinka"..karasawa tayi inda matar ta shiga taimaka mata...yana tsaye rungume da hannu yana kallonta kaman bai ta6a ganin yanda ake kar6an haihuwa ba...so yake yaga tayi mistake komai kankantarshi yaci mata mutunchi amma baiga tayi mistake din komai ba...wato dai ba brain kadai takeda ba har skills tana dashi...sam baiji ta wani burgeshi ba duk abunda take...ta kar6i haihuwan successfully ta gama ta kuma yi duk wani necessary abu daya kamata tayima matar da babyn sai a lokacin ya juya ya fita..ita kuma ta bishi da harara kaman idonta zasu fado tace"duk wani baqin hali dai a gun inyamurai ya kare...har abada basu son a zauna lafia". Around 5:30 suka gama shiri suka fito dan zuwa shopping da Prof kaman yanda suka tsara...bakin gate dinsu sukayi ido hudu da Sa'eed dake jingind jikin motanshi yana kokarin kiran one of them a waya...Aysha ta wara idanu tana kallonshi smilingly tace"my bestyyy"...dagowa yayi yana kallonta sai kuma ya daure fuska yana hararanta...ta karasa kusa dashi da sauri tana cewa"haba my besty...hope ba fushi kakeyi dani ba"...hararan nata ya sakeyi kafin yace"ba wani your besty...ni da aka manta dani"...da sauri tace"oh C'mon besty kaima dai kasan ba wanda ya isa ya mantaka..jiya fa na kira wayanka ban samu ba Allah"..kafada ya daga yace"baki damu ki ganni ba ai..ni da na damu ai gashi nazo har inda kuke"...kaman zatasa kuka tace"besty wai meye haka plss?..kanaso Billy tayi mana daria koh?.."juyawa yayi ya kalli Billy dake tsaye tana kallonsu ya wani kwa6e fuska irin yanda bestyn tashi keyi idan abubuwan suka motsa yace"Billy hadda ke ma koh?..kikaje kika biyewa besty kuka manta dani..is that fair?.."murmushin da bata shiryaba ta saki ganin yanda yayi da face dinshi...ta buda hannaye tace"ni babu ruwana da tsakaninku...kawai inzo in shiga anjima ku bani kunya"...murmushi shima ya saki yana kallonsu with smile yace"nayi missing dinku da gaske...sai nakeji kaman nayi tsuntsu naje Bauchi da Gombe"...murmushin suma suka kara saki Aysha tace"da gaske munyi missing dinka muma...yasu Mom da Lubna"..yace"they are all fine..amma ina zakuje ne haka?.."Aysha ta saki wani qayataccen murmushi kafin tace"wlh Baby ne yazo wai zai kaimu shopping.. muje kayi dropping namu bakin gate nasan yana can yana jiranmu"...kallonta Sa'eed yayi cikeda mamaki kafin ya juya yana kallon Billy yana neman karin bayani..ta daga kafada tana dan smiling dan ta gane me yake nufi tace"ai soyayya ya dade dayin nisa...bakaji har baby ma ake cemishi ba?.."Yace"shine nima nake mamaki ai..but when did this happened banida labari?.."tace"gaka ga bestynka ai"...juyawa yayi ya kalleta kafin yayi mgn tace"besty mu shiga mota idan mun tafi zanyi maka bayani"...baiyi mata musu ba ya bude motar suka shiga..yana gama warming dinta yayi reverse suka dauki hanyan fita hostel din...basuyi nisa ba yace mata"umhum ina sauraronki"...a nuste ta bashi labarin duk yanda sukayi dashi...saida ta gama yace"amma kina ganin ba matsala besty?..i mean kin tabbata mutumin kirki ne shi?.."da sauri tace"sosai mutumim kirki ne wlh besty...ask Billy ta fada maka tunda muke dashi bai ta6a min wani abu da bai kamata ba..he really is a gentle man"..gyada kai Sa'eed yayi yace"to Allah yasa..but still ya kamata muyi bincike a kanshi..i don't want you dating a wrong guy kar azo a samu matsala"..murmushin jin dadi ta saki kafin tace"i trust you completely my besty...kayi duk binciken da kaga ya kamata"...dan juyawa yayi ya kalleta sai ya saki murmushi yace"za'ayi min dadin baki a cuceni"...tana daria tace"ba wani dadin fa..it's the truth"..sake gyada kai yayi baice komai ba...Billy dama tana back seat tana chatting dinta so ko sauraronsu batayi...suna fitowa main gate suka hango motarshi parke daga gefe..saida ya karasa har kusada motan nashi snn yayi parking...suka bude mota suka fita shima ya fito daga cikin nashi motan...Sa'eed ya karasa ya bashi hannu suka gaisa kafin yace"Hope dai za'a bani aronsu for just an hour?.."yana murmushi yace"of course..Allah ya kiyaye hanya"..Prof ya amsa da"Ameen"snn sukayi sallama Sa’eed ya shiga motanshi ya wuce suma suka shiga na Prof suka wuce. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 16 Shopping sosai Prof ya shiga yi musu Aysha tun tana cewa ya kyaleshi haka har ta hakura kawai ta zuba mishi ido...ta lura ba karamin money spender bane shi..baijin kashe kudi sam..yanda yake musu siyayya ko shekara guda zasuyi a school sai haka...Billy dama batayi mgn ba kallonshi kawai take...saida ya dauki duk wani abu da students kamar su suke bukata snn ya wuce counter...bayan yayi payment akai musu packaging wani messenger ya dauki kayan yabisu dashi mota...ya zubasu nan cikin booth suma suka shiga suka wuce...a hankali Aysha ta juya tana kallonshi tace"Babyy.."ya dora hannu kan lips dinshi yace"shushsh ba sai kince komai ba pls"...shirun tayi bata sake mgn ba kaman yanda ya bukata...saida ya tsaya Pizza Hut yayi musu takeaway snn suka wuce Hostel...a bakin gate dinsu yayi parking Billy ta bude mota ta fita bayan ta mishi godia...Aysha kuma sake juyawa tayi tana kallonshi da cutest eyes dinta cikin shagwa6an da yake mutuwar so tace"Baby u shouldn't have done this...i told u munada komai da komai fa"...kallonta yayi for like 5 mins kafin ya dauke kanshi yana sakin murmushi...this girl is damn cute..bai ta6a ganin wanda shagwa6a yakema kyau kaman ita ba..she is just different..sake turo baki tayi hadda bubbuga legs dinta a kasa tace"Baby manaa"...daria ya saki sosai har jikinshi na dan jijjigawa yana daga hannu yace"ohk am sorry...amma ke din ce bakiji baby girl...idan har am important to u zakiyi accepting kayan nan and azaki sake kokarin hanani siyan maki wani abu ba"...turo baki tayi tana kallonshi kaman zatasa kuka...kallonta kawai yake yanajin kamar yakai hannu yaja dan bakin da take turo mishi...tace"shikenan nima daga yanxu duk abunda na gani na siyan maka sai kayi accepting ka yadda?.."gyada kanshi yayi yace"na yadda"..nan da nan ta saki murmushi har dimples dinta suka lotsa...sun dan ta6a hira kadan kafin yayi mata sallama ya wuce ita kuma ta kwashi kayan da suka siyo ta shiga ciki...bata samu Billy a dakinsu ba dan haka tana ajiye kayan ta fita zuwa room 2b da ta jiyo hayaniyarsu a can...tana shiga wata daga cikinsu mai suna Rahma tace"yauwa ga Lamidon nan ma tazo"...karasawa tayi ciki ta zauna tana kallonsu tace"meya faru ake neman Lamido?.."Rahma ta sakw cewa"mgnr bikin Aneesa ne wlh...kinsan munyi mata alqawarin zamuyi selecting music mai dankaren dadi muyi training sbd muyi performing ranar dinner dinta?.."gyada kai Aysha ta shigayi tace"inaga shine dalilin da yasa take nemana...ko daxu naga missed calls dinta ina tareda Baby"...Rahma tace"yauwa to shine mukeso ki za6o mana latest music mai dadi snn ki koya mana rawan da zamuyi tunda dai kaf Hostel din nan ba wanda ta iya wani rawan kirki idan bake ba"...dan murmushi Aysha ta saki kafin tace"to ku da kuketa wnn lissafin Aneesan tace muku 'yan class dinsu baza suyi bane?..kunsan fa 'yan Nursing din nan da shegen iyayi"...wnn karon Billy ce tace"yo Lamido kamar bakisan 'yan class din nasu bane?..babu abinda zasu iya wlh shiyasa itama Aneesan ta nememu kuma bai kamata mu watsa mata qasa a ido ba...dukda ba department dinmu daya ba year dinmu daya and tanada kyakyawan relationship damu sbd haka ba wanda ya kamata ya fitar da ita kunya idan ba mu din ba..koya kukace Midwives?.."da sauri suka hada baki suna fadin"Zancenki dutse hajia Bilisu"..sauke ajiyar zuciya Aysha tayi tace"shikenan sai mu fara this weekend...amma wane time kuke ganin zamuyi selecting evening ko night"...Rahma tace"kam night ai sai yafi sugar Lamido..yanda zamusha sha'aninmu babu wani takura"...gaba daya sukayi na'am da wnn shawara dan haka suka tsaida mgn kan zasu ringa dance training dinsu every Saturday and sunday around karfe 8 na dare. Tun daga wnn rana suka fara training dinsu kaman yanda suka tsara...every weekend suke taruwa suyi abunsu ba wanda ya sani...a haka suka cinye satin farko na clinical posting dinsu suka cinye na biyu...a cikin sati na uku ne za'ayi bikin and sun gama training dinsu tsaf daidai da anko duk cikinsu ba wadda batayi ba...duk tsawon wnn lokacin Aysha bata sake haduwa da Dr.Bobby ba a Hospital kuma yana shiga ward dinsu Allah ne kawai baisa sun sake haduwa ba shiyasa take cewa Allah ya amsa addu'anta dan koshi yasan yanda ta tsani ganinshi shiyasa suke samun sa6ani dashi. Yau Saturday za'ayi dinner Aneesa gashi evening duty take kuma ta rasa wadda zata kar6an mata aikin zuwa gobe...jiyama Allah ne ya taimaketa wata daga cikin staff din dakin ta kar6i evening din tayi mata ita kuma tayi mata morning sbd event din jiya kamu ne so tana tashi daga Hospital din ta koma Hostel suka shirya suka tafi...event din yau kuma na dare ne gashi bata san wanda zai rike mata aikin ba...tun daxun take zaune gefen gadonta tana daure da towel sai tufka da warwara takeyi...tsoro takeji kar ta tafi biki wani matsala ya faru ayi blaming dinta...sai wata zuciyar tace mata tayi tafiyarta kawai ai bai zama lallai ita kadai take evening ba so dayar zata rike dakin...da wnn shawara na zuciyarta ta yanke hukuncin zuwa bikinta kawai dan Allah ya gani bazata iya hakura da zuwa dinner nan ba...yanda sukayi training idan bataje ta baje kolin rawan nan ba matsala za'a samu ta sani...Billy data fito daga wanka ta kalleta ganin tayi nisa cikin tunani tace"to ya muke ciki ne Lamido?..kin samu mai rike miki aikin?.."sauke ajiyar zuciya tayi a hankali tace"ashe bani kadai zanyi evening din bama..da akwai wata staff kuma nasan bazaki zuwa ba"...Billy da har ta fara shiryawa tace"har naji dadi wlh dan Allah ya sani idan bakije bikin nan ba bazamu ji dadinshi ba muma...yanxu ki karasa shiryawa kisa kayanki nasan wnn dan rainin wayon bestyn naki ya kusa zuwa...kuma dai kinsan make up da zuwa da wuri mukayi ba bazamu samu mai kyau ba"...wani murmushi Aysha ta saki tareda mikewa zuwa wardrobe dinta tace"tsakanin keda bestyn za'aga waye dan rainin wayo a cikinku...ke kice mishi dan rainin wayo shima ya kiraki da haka..duk zaku gaji da munafurcinku ne ma ku dawo kan hanya"...cak Billy ta tsaya da kokarin saka skirt da takeyi tace"what are u insinuating?.."Aysha ta fashe da daria itama ta fara zura kayanta tace"nothing ooo...am just talking to myself "...tsaki kawai Billy ta saki taci gaba da shiryawanta...ko ten minutes basu kara ba suka gama shiryawa kowa ta dauki abinda take bukata suka fita inda Sa'eed ke jiransu...yana daukansu direct sukayi Zoo road inda za'ayi musu make up. Mummy ce ta Aunty sumy suka fito compound din gidansu kowacce sanye cikin lace dinta na alfarma sunyi kyau sosai da gani kasan gidan biki zasuje...sai Ilham da Miemie dake sanye cikin nasu lace din suma iri daya da yayi matukar amsarsu Sab kuma ya dade da komawa makaranta...aunty sumy har ta bude motarta da zasuje bikin da ita Mummy tace" sake kira min Bobby Sumayya...wlh idan baije bikin nan ba sai naci mutunchinshi"...aunty sumy murmushi tayi kafin ta sake dialing number Bobby ta mika mata wayan...saida ya kusan katsewa yayi picking Mummy ko jira yayi mgn batayi ba cikin igbo tace"wato ka rantse dai bazaje bikin nan ba ko Bobby?..haka daxu kiri kiri kaki zuwa daurin aure shine yanxu dinner ma kace bakazo ba?.."saida ta bari ta kai aya snn yayi kasa da murya yace"Mummy ina Hospital fa..wlh aiyuka ne a gaba na idan baki yadda ba ga Nur ki tambayeshi"...a takaice tace"bawa Nur din waya"...ba musu ya mika mishi wayan...shima yana amsa before yayi mgn Mummy tace"kana jina Nuru?.."yace"inaji Mummy"...tace"tell him duk ya sake muka bar wurin dinner nan baije sai yaga 6acin raina wlh...kan wane dalili zaiki zuwa bayan yasan yanda nake da uwar yaron nan...snn shima abokinshi ne amma sbd iskanci ya mishi yawa ya wani cemin yana aiki a gabanshi"...Nur yayi kasa da murya sosai yace"kiyi hakuri Mummy zamuzo tare inshaAllah...Allah ya huci zuciyarki"...bata sake cewa komai ba ta kashe wayar...suka shiga motar aunty sumy gaba dayansu suka fita daga gidan...shi kuwa Bobby dafe goshinshi yayi yana dan murzawa a hankali...duk yaji maganganun da Mummy ta fada and baiji dadin musun da yayi mata ba sam...ya mance when last Mummy tayi mishi mgn cikin fushi haka...kuma shi kanshi yasan bai kyauta ba...angon abokinshi ne sosai dan lokacin suna lagos shine babban abokinshi...Mom dinshi kuma aminiyar Mummy ce itama tun a Lagos suke zumunchi har zuwa yanxu basu dena ba shiyasa ma take kokarin hadashi aure da qanwar angon Rayhan shi kuma baya sonta sam...kafin Nur yayi mgn ya dauki car keys dinshi tareda mikewa yace"muje ka rakani wajen bikin nan plss..nasan yau idan banje ba mai rabani da Mummy sai Allah"...Nur daria ya dan saki shima ya mike tsaye suka fita daga office din snn yace"nima dai banga dalilinka na kin zuwa ba...angon nan fa abokinka ne kuma yayan matar da zaka aur..."Bobby bai tsaya jin karshe ba ya kara gudun tafiyarshi ya barshi a baya dan bayason ji sam...baisan meyasa ya tsani a hadashi da wnn Rayhan din ba wlh...he hates her with passion...saida suka tsaya nan gidansu Bobby sukayi wanka kowa ya sake shiri snn suka tafi wurin dinner a motan Nur...lokacin har anyi sallahn isha dan haka sukavfara tsayawa masallaci auka gabatar da nasu snn suka wuce...suna isa hall din amarya da ango na isowa...basu bi takan brides maida da sukaga anata faman jerasu ba wai da sunan zasu shiga da amarya kai tsaye suka shiga hall din...duk iya wulla idonsu basu hangi Mummy ko su antu sumy ba coz hall din nada girma sosai dan haka kawai suka karasa wani table suka zauna Bobby sai faman cika yake yana batsewa dan ko Allah yasan shi ba maison zuwa biki bane...sam bayason hayaniya shiyasa duk wani abu indai ya hada da taron jama'a shiga bai sonshi sbd tsabar rashin son mutane irin nashi...a can waje kuwa saida su Aysha suka shirya kansu tsaf snn mc yace ma dj ya sakar musu waqan shigowa da amarya...dj kuwa yasa waqan da sukace sunaso snn suka fara shigowa a hankali suna dan bin waqan hade da rawan da yayi matching song din sosai...Aysha ce a sahun farko sai Rahma a gefen ta su Billy kuma suna bayansu wasu kuma suna bayan amarya da ango ma'ana sun sanya su a tsakiya knn...tunda suka shigo hall din gaba daya kallo ya koma kansu gaba daya lace sukayi anko sea green har head dinsu ma sea green sai dinki kawai daya bambamta...su Aysha ansha make up sosai dam idan ka kalleta zaiyi wuya ka ganeta sbd tsabar kyau da tayi...Nur ne ya fara ganeta aikuwa ya wara ido sosai yana kallonta sai yaga almost gaba dayansu ma students dinsu ne...to me ya kawosu nan kuma?..bai samu amsar tambayan shi ba saida ya ga amaryar itama yaga student dinsu nan take ya saki murmushi yana fadin"No wonder...Bobby kasan yaran can gaba daya students dinmu ne...amaryar ma ai Nursing takeyi na ganeta a year two take"...Bobby da gaba daya hankalinshi ke kan wayanshi dan dagowa yayi a hankali yana kallonsu and idanunshi basu fada ko ina ba sai kan Lamido dake tikan rawanta hankali kwance tana smiling da gani tana enjoying abunta...wani irin haushi yaji ya turnukeshi...baisan meyasa these days yake yawan haduwa da ita ba...ya tsani ganinta wlh sbd duk ya sauke idonshi akanta yana sashi tunowa da abubuwanda ya faru dasu a baya...abun takaicin kuma duk yanda yaso dauke idonshi kansu kasawa yayi har suka raka bride and groom suka zaune snn sukayi dividing kansu into two wasu suka tsaya side din amarya wasu side din ango suna cigaba da rawansu...gaba daya hankalin kowa na hall din na wurinsu dan ba karamin burgewa sukayi ba...daya bayan daya sukw fitowa kowacce ta taka mutane suka fara zuwa suna musu liki abun dai dai wanda ya gani...Dr.Bobby kuwa haushi ne cikeda zuciyarshi yana mamakin yanda iyayen yaran nan suka bari suka fito biki haka gansansan dasu ko mayafi babu...saida suka gama rawarsu snn suka zauna nan kuma mc ya fara kodasu yana yabon irin rawar da sukayi...har zuwa yanxu basu hangi su Mummy ba bayan amarya da ango sun fito fili aka kira Maman ango snn ya gansu sun fito suna ma bride da groom ruwan kudi har su Miemie da suke kanana...suna hada ido da Mummy tayi musu alaman suzo da hannunta...ba musu suka mike zuwa inda suke shidai Bobby fuskan nan a daure kaman wanda aka aikoma sakon mutuwa...suna zuwa Mummy ta zaro bundle na 500 daga jakanta ta mika musu wai suyi liki dashi...Bobby ya dan dauke kanshi tareda zaro wanda ya fito dasu daga aljihunshi ya shiga likama amarya da angon...shima Nur ya zaro nashi ya fara likin...bayan sun gama ango ya mika musu hannu suka gaisa tareda congratulating dinshi suka bar wurin amarya dai kanta na kasa tana mamakin a ina mijinta yasan provost da proprietor dinsu...su Aysha kuwa suna zaune inda aka tanadar musu dan haka ba wanda ya lura dasu a cikinsu...biki yayi biki yayinda wayanta dake cikin bag dinta keta vibrating alaman ana kira ita kuma da gayya daki dauka dan tasan Prof ke kira ita kuma fushi takeyi dashi...saida taga ba dena kira zaiyi ba ta koma can bayan hall din inda ba hayaniya sosai ta samu seat ta zauna snn ta zaro wayan daga bag dinta tareda sliding takai kunne...ta wani cuno baki taki cewa komai kaman yana ganinta...a hankali taji yace"baby girl fushi kikeyi koh?.."saida ta murguda masa baki snn tace"nidai na dena kulaka"...yace"subhanallahi baby idan kika dena kulani ya zanyi?..kinaso kiyi kisan kai koh?.."sake murguda bakin tayi tace"to ba kaine ba...cewa fa kayi bazakazo in ganka ba"...yace"wlh ni kaina ina son ganinki baby girl amma baa wurin biki ba...haka nan sai in kama biyoki wurin biki niba karamin yaro ba"...ta wani tale baki kaman zatasa kuka tace"haka ma kace kou?..to wlh idan bakazo yanxu ba baka kara ganina sai mub gama Clinical Posting"...da sauri ya wara idanu sosai yace"Subhanallah baby how could u do this plss?..ai abun bai kai nan ba gani nan tahowa yanxun amma bazan shigo ciki ba zan kiraki ki fito kinji?.."nan da nan ta saki kasaitaccen murmushi har dimples dinta suka lotsa tace"that's my baby boo..ina nan ina jiranka plss and don't keep me waiting"..yana murmurshin shima yace"wane ni?..am coming right away inshaAllah"...tace"ohk bye sai kazo"..shima yace mata"bye snn suka ajiye waya...ta mike daga wurin tana kokarin maida nata wayan cikin jaka idonta ya sauka a kanshi ya wani hakimce kan seat yana kallonta with his big eyes...gabanta taji ya fadi tayi saurin kawar da kanta tana salati...meya kawo wnn mutumin nan wurin kuma fisabilillahi?..sake dagowa tayi still taga idanunshi a kanta yana mata wnn kallon dake sata nutsuwa ko batayi niyya ba...sunkuyar da kanta tayi ta hadiye wani yawu da taji ya cika mata baki snn ta juya a hankali ta bar wurin fatanta Allah yasa baiji abunda take fada ba...ko wane irin asiri yakema idanunshi oho?..batasan ko kowa yanajin wani abu idan sun hada ido ba amma ita dai Allah ya gani tsoronshi ma takeji...ta tabbata ba karamin mara imani bane dan ko a fuska baiyi mata ruwan mutanen kwarai ba uwa uba kuma gashi inyamuri...duk dunia a ganinta babu azzalumin qabila kaman inyamurai shiyasa sam bata son tana hada harka dashi dan a cewarta da kyar idan baya daya daga cikin masu assasa yakin biafra.😆 Shima a nashi bangaren kallonta kawai yake yana mamakin gangancin da yasa iyayenta suka turota karatu wani gari bayan sunsan halinta...duk mgnr da tayi a kunnenshi tayi su ya kuma tabbatar da cewa bayan sangarta dake damunta hadda rashin tarbiyya ma...idan ba haka ba why zata ringa behaving haka?..yanxu dubi yanda ta taho biki ko mayafi babu snn ta fito da gashi waje ga kayan jikinta sun matseta sbd tsabar rashin sanin darajar kai...ya saki wani hadadden tsaki shi baisan dalilinda yasa wasu matan ke neman maida kansu wawaye ba wlh..shi sam bazai iya auren mace mai irin halinta ba...macen da bata ajiye komai ba sai shegen shagwaba da rawar kai ai yanaga idan ya auri mai irin halinta kilan kullum sai yayi mata dan iskan duka sbd kular dashi da zatayi...tsakin da ya saki ne ya dawo da hankalin Nur daketa faman danna wayanshi kanshi...yace"hope lafia kake sakin wnn tsak haka?.."harara ya watsa mishi mai kyau ba tareda yayi mgn ba...kawai haushin kowa da komai ma yaji yanaji and he doesn't know why...Nur da yaga kallon da yayi mishi sai yaci gaba da abunda yake cikin wayanshi yana fadin"easy dude ai bani na kar zomon ba and ko rataya ba wanda ya bani"..wani hararan Bobby ya sake maka mashi duk yaji zaman wurin ma ya gundureshi...mikewa yayi zuwa wurin da ya hango Mummy ya samu ya lalla6ata wai yanaso yaje gida ya huta sbd zai fita aiki da safe gobe...bata hanashi ba tace suma sun kusa tahowa gidan...yana barin wurin kai tsaye ya wuce waje dan ko second daya baison karawa nan ciki dan wani irin haushi yakeji from no where...text ya turama Nur yace ya fito su tafi snn ya karasa jikin motar nashi ya jingina dashi...har bayan 20 mins Nur bai fito ba ran Bobby duk ya gama 6aci na barinshi da yayi a tsaye cox key yana hannunshi balle ya bude mota ya shiga...yana kokarin sake dialing number dinshi wani mota yayi parking kusada nasu...baisan meyasa a kallon farko da yayiwa motar ya ganeta ba...it was the same car da suka shiga itada mutuminda yakeda tabbacin saurayinta ne ranan da sukayi reporting a Hospital dinshi...wani tsakin ya kara saki yanajin haushin Nur for not coming out har wnn mutumin yaxo ya sameshi a wurin...yayi kaman zai koma cikin hall din idanunshi suka hango mishi ita ta fito daga ciki ana tafiya kaman baza'a taka kasa ba...fuskan nan daukeda murmushin dake sa dimples dinta fitowa sosai dan yana iya ganosu daga nan inda yake tsaye..da yake inda yake babu haske sosai har ta karaso wurn bata lura dashi ba shi kuma baisan dalilinda yasa ya kasa dauke idonshi akanta ba duk kuwa da yanda yaso yin hakan...as usual tana karasowa ya bude mata mota ta shiga snn shima ya shiga ya rufe kofa...Bobby ya runtse ido yanajin wani zafi sosai a jikinshi...shi baisan wnn masifa ba da babu dama yaga yarinyar nan sai ranshi ya 6aci kuma duk laifin Nur ne dan daya fito sun wuce tun daxu yasan babu yadda za'ayi yaga wnn kayan takaicin...gaba daya yaji yanajin haushinsu daga ita har saurayin nata...wai babban mutum dashi ya rasa inda zai kare sai akan wnn fitsararriyar yarinyar sangartacciya ma da bata ajiye komai ba sai dan banzan shagwa6a...ganin time na sake kurewa Nur bai fito ba ya danna mishi kira...yana dauka yace"malam you should have told me if u are not going to leave now ba wai ka shanyani waje inata faman jiranka ba"..da sauri Nur ya mike daga inda yake zaune yace"wai kana nufin kana waje?.."tsaki kawai Bobby ya saki tareda kashe wayarshi...shi kuma Nur fitowa yayi dan sam bai lura da message daya tura mishi ba...yana karasowa ya bude mota suka shiga snn yayi reverse suka fita daga wurin fuskan nan na Bobby a dinke tsaf kaman wanda bai san me ake nufi da daria ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 17 A bangaren love birds kuwa musayar kallo aka shigayi bayan an shiga motar...sai daga baya Prof yayi breaking silence din da fadin"baby girl kinyi more than kyau..i don't how to put it but u look extraordinary gorgeous"...murmushi jin dadi ta saki tanata juya ido dan ba karamin dadin compliment din taji ba shiyasa ma ta dage mishi yazo dan bazata so tayi asaran duk wnn kwalliyan a banza ba tareda ya gani ba...sai kuma ya dan hade rai yace"amma baby haka kike yawo ko veil babu a jikinki?..look at yanda kika fito da gashinki kowa yana kallo this is not fair mana"...murmushi ta kara saki kafin tace"baby sbd biki nefa"yace"next time ko bikin wa akeyi banson ana ganinki a haka...banaso"...hannu takai tayi saluting dinshi still tana smiling tace"yes sir..ur wish is my command"...daria yasa sbd ganin yanda tayi itama tana tayashi...bayan sun gama daria kuma sai hira ya 6arke a tsakaninsu...labari sukesha sosai dan har ta mance da wajen biki suke tanata buga love abunta...yana fada mata zaiyi tafiya zuwa malaysia gobe ta dinke fuskanta tsaf kamar ba ita ke daria a while ago ba...shima nashi fuskan ya marairaice mata yace"baby bafa dadewa zanyi ba and believe me kullum zamu kasance tare a waya"...a takaice tace dashi"how many days?.."shiru yayi yana kallonta kafin a hankali yace"four weeks"...ganin zata fara mishi kuka yayi saurin matsawa kusada ita yana cewa"C'mon baby kar kimin kuka please...nima fa baa son raina bane ya zama dole ne shiyasa zanje but Allah kadai yasan how am going to miss u"...goge hawayenta tayi tana turo baki tace"kuma shine baka fadamin da wuri ba"..yace"am sorry kukan nan ne banaso amma am sorry kinji..pardon my manners"...sake turo bakin tayi wnn karon hadda dan murgudashi tace"kuma na dena kulaka"..ya saki murmushi yace"kicigaba da murgudamin bakin nan baby duk abunda ya biyo baya don't blame me"...sake turo bakin tayi tana taleshi kaman zatasa wani kukan yayi saurin dakatar da ita da fadin"ohk ohk yi hakuri da wasa nake..am sorry okay?.."to cut it short Aysha daga nan ko cikin hall din bata koma ba bayan sun gama hiransu ta kira Billy a waya ta fito suka tafi...as usual yayi musu takeaway na kayan kwadayi snn yayi dropping nasu a hostel. Dr.Bobby kuwa Nur na ajiyeshi a gida ya shige ciki ko sallama bai tsaya sunyi dashi ba...kawai gaba daya jinshi yake wani iri shiba mai lafia ba kuma shi ba mara lafia ba...wanka kawai ya sakeyi ya kwanta amma duk kokarinshi na ganin yayi bacci abun gagaranshi yayi...har su Mummy duka dawo bai runtsa ba...yanajinsu yaji fitowa yasan suma sunyi tunanin yayi bacci shiyasa basu nemeshi ba shi kuma bacci kiri kiri yace bazai daukeshi ba...har dare ya raba bai samu baccin ba haka yayita juyi kan gado yana faman tunanin abunda sam bai shafeshi ba sai can wajen 3 baccin ya lalla6o yayi gaba dashi...rashin samun bacci da wuri yasa ya makara sallahn asuba dan time din daya tashi an idar da sallah sai a gida yayi nashi snn ya sake kwanciya amma still baccin bai daukeshi ta dadin rai ba saida ya gama ja masa aji...can cikin baccin ringing din wayanshi ya tasheshi...a fusace yakai hannu ya dauko wayan yayi sliding yakai kunnenshi ko sunan mai kiran bai tsaya dubawa ba...daga can 6angaren Rayhan tace"uncle bobby"...ya runtse ido yanajin wani irin haushinta na lullu6eshi...yanxu dama duk uban kiran nan da ake jera mishi wnn yarinyar ce?...yana kokarin kashe wayarshi dan yasan yana bude baki mgn zai fada mata mara dadi yaji ta sake cewa"uncle bobby kayi hakuri plss...na kasa hakura ne...jiya Mummy ke cemin kaje wurin dinner kuma har ka tafi ban karaso ba...a wurin make up ne aka 6ata mun lokaci amma naso haduwa dakai sosai"...shiru ya sakeyi yanajin kaman yakai hannu ya kwada mata mari ta cikin wayan..he is just trying to control his temper sbd idan ta kaishi bango bazataji da dadi ba...jin shiru bai still baice komai ba tace"uncle bo..."bata karasa ba ya katseta da fadin"ke hold it plss..how dare u call me at this time of the day?..are u insane?..bakisan safiya bane ko bakisan i might be sleeping ba?.."kwantar da muryanta tayi sosai tace"kayi hakuri dan Allah..naga 8 ya wuce so i taught kana Hospital..am sorry"..tsaki ya saki bayan ya duba wall clock din dakin nashi yaga it's 8:36 dan haka ya kashe wayan kawai tareda jan duvet ya lullu6e har kanshi dashi...kawai shidai gashi nan ne amma sam dadin jikinshi at all..wani irin weakness yakeji all over him ga kuma zuciyanshi da bai mishi dadi shima...haka nan ta kama kiranshi da sassafen Allah sai kace batada aikin yi...shi tunda yake bai ta6a ganin mayyar mace kaman Rayhan ba wlh...ace mace kaman chewing gum duk wulaqancin da yake mata har yanxu taki rabuwa dashi...haka yacigaba da juyi a kan gado shi bai koma bacci ba kuma shi bai tashi yayi abunda ya kamace shi ba...daga karshe dai da kyar ya iya mikewa yasa sport wears dinshi ya shiga jym wai ko zai dena tunanin abunda bai kamace shi ba. Karfe uku dot yayiwa Aysha a Freedom Specialist Hospital...yau ko jiran bus bata tsaya yi ba besty ya kawota sbd tanaso ta wanke laifinta na jiya shiyasa ta fito as early as possible...tana shiga ward din taci karo da incharge na gaba daya maternity matron Salamatu sai midwife data rike mata aiki ranan da taje biki sai kuma wasu staff guda biyu da take ganinsu a eclamptic ward sai kuma alhaji Dr.Bobby dake tsaye hannayenshi zube a aljihu yana sauraronsu...wani irin dum taji gabanta ya fadi dan tasan taron bana lafia bane...Matron salamatu ceta fara ganinta dan haka tace"yauwa ga yarinyar nan doctor"..juyawa yayi a hankali ya kalleta sam baiyi mamakin ganin itace na sbd jikinshi ya bashi babu mai iya aikata wnn danyen aikin sai ita...gashi kuma hasashenshi ya zama gaskia..Aysha dai kasa tayi da kanta da sauri tana karanta lailaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimun a cikin zuciyarta...har yanxu heart beat dinta bai dawo daidai ba...saida matron ta sake yi mata mgn snn tayi karfin halin daga kafarta ta karasa ciki...daga gefe ta tsaya kanta kasa tana karanto duk abunda yazo bakinta...idanunta lumshe tasan ko bata gani ba idanunshi ke yawo a kanta dan taji wnn hadadden tsoro da firgici da take shiga idan ya kalleta...Matron ce ta fara jifanta da tambayan da ya kusa sata sakin fitsari sbd tsoro.."meya hanaki zuwa aiki jiya?.."tayi shiru tana tunanin karyar daya kamata tayi...matron ta sake cewa"kinsan asarar da kika janyo mana kuwa?..kin tafi kin bar daki ba kowa snn ga patients duk babu mai kula dasu har daya daga cikinsu ta rasu sbd carelessness dinki"...a razane ta dago tana kallon matron din abunda ta fada..she can't believe wata ta mutu sbd rashin zuwanta aiki jiya..."innalillahi wainna ilaihi rajiun mena janyoma kaina haka?.."ta fada cikin zuciyarta...lokaci guda hawaye suka ciko idonta yanxu hakan na nufin tayi kisan kai knn?...Dr.Bobby da tunda ya dora idanunshi kanta bai sauke ba ya daka mata wani tsawan daya sake firgita ta ganin yanda tayi banza da mutane kaman bada ita ake mgn ba...yace"bakida baki ne?.."da sauri ta shiga girgiza kai alamar tana dashi...ya sake tamke fuska snn yace"oya speak up..tell us exactly why u left them all alone har kika janyo mukayi asarar rai"...bakinta ta shiga motsawa tanason tace wani abu amma ta kasa...ta sai san ko kwaya takesha bazata yi karyan batada lafia ba tunda ya ganta jiya a wurin dinner... ganin batada mafita kawai ta shiga yarfa hannayenta hawaye na turereniya kan cheeks dinta tace"am...sor..ry"..Matron tace"ko dan gaba baa yin irin haka a asibiti..da kikasan bazaki zoba sai samu wata ta rike maki amma ba ki tafi ki bar patients on their own ba sbd ba wanda zaiyi tunanin su kadai ne...ba don Allah ya taimaka wadan nan sunzo jiyan ba da kilan asarar da zamuyi sai yafi haka"..kuka kawai takeyi tana gyada mata kai...Bobby ya zaro kudi a aljihu ya mikama mutum biyu da suka taimaka suka rike dakin snn yayi musu godia suka wuce...Matron da taga yanda ranshi ke 6ace tace"ayi mata uzuri dr kaga yarinya ce..zanyi mata fada inshaAllah bazata sake aikata makamancin haka ba"...bai ko kalleta ba bare tasa ran zai amsa idanunshi kan Aysha da har yanxu bata bar kuka ba yace"wuce muje"...a rikice ta dago tana kallonshi...ya zuba mata idanun nan nashi aikuwa ba shiri ta wuce gaba tana cigaba da kukanta...haka suka fito daga ward din tana gaba yana binta a baya har zuwa office dinshi...karasawa yayi seat dinshi ya zauna fuskan nan ba sarari yace"sbd bakida hankali kika wuce kika barmin patients su kadai dan bakisan aikinki ba koh?..anya kuwa bada malpractice kikayi passing Clinical skills dinki ba?.."dukda halin da take ciki mgnrshi ba karamin kular da ita yayi ba...wato ita yake nufi tana satan amsa amma Allah ya isanta wlh...cikin daga murya yace"are u deaf ina miki mgn zakimin shiru?..are u sick?.."runste idonta tayi sabbin hawaye na sake gangaro mata...itadai yau ta shiga uku da masifan wnn mutumin...sai ihu yakeyi mata kaman ita tajs ta shaqe matar ta kasheta...shima runste nashi idon yayi yana murza goshinshi trying very hard to control his temper don idan ya biye ta zuciyarshi yana iya gaggaura mata mari sbd haushin datake bashi...what did she think of herself da zai ringa mata mgn tana banza dashi...ganin bafa shiru zatayi ba ya buga table din gabanshi cikin karaji yace"kin rufemin baki ko sai na gaura maki mari a wurin...are u even alright da zaki sani a gaba kina min kuka?..are u mad?.."ya karasa mgnr cikin tsananin 6acin rai...sbd tsoratan da tayi batasan time data hadiye kukan nata tana toshe baki da hannayenta ba...shi kuma yacigaba da fadin"from today onwards aikinki ya dawo office dina...ke zaki dinga cleaning min office kullum kina wanke toilet dina...snn duk wani aike na office dina ke zaki dinga zuwa zan sallami cleaner da messenger dina har zuwa lokacin da zaki gama punishment dinki...if u like ki tafi gidan biki ku hadu da saurayinki kiqi zuwa aiki kiga yanda zanyi dake lazy fellow kawai"...har yanxun idanu a lumshe take sauraronshi...wato ma itace zata zama mishi cleaner kuma messenger sbd bashida imani...kuka kawai takeyi har yanxun batace mishi qala ba...shi kuwa kallonta yake har yanxu yana ganin yanda dimples dinta ke fitowa as a result of kukan da takeyi...ya sake daure fuska snn yace mata"go to the Nurses Station kice ina kiran Zarah"...ba tareda ta bude idon ba ta juya ta fita a office din...saida ta tsaya ta gama clearing face dinta dukda tasan a banza dan ana ganinta za'aga alamun kuka tattare da ita snn ta wuce nurses station din...tare suka fito sa nurse din zuwa office dinshi...Aysha taja gefw ta tsaya tana daure fuska dan a ganinta sbd tana mishi kuka ne yasa yake raina mata wayo...Zarah ta karasa bayan ta gaisheshi yace"how many files do we have?.."tace"they are many sir.."yace"ohk kuje da ita ki bata ta kawo and kina iya tafiya gida u are done for today"...nan da nan ta washe baki hadda risinawa tace"thank u sir"...Aysha ta maka mata wani harara a kan idon Bobby dake kallonta ta gefen ido...cikin ranta tace"azzaluma ba dole kiyi godia ba"...saura kadan daria ya subuce mishi sbd ganin yanda tayi hararan kaman idonta zasu fado kasa...tare suka sake fita Zarah ta hadata da uban files na patients din da zai gani yau snn ta koma office din nashi ta kai mishi da kyar take iya dauka sbd nauyinsu...ta ajiye mishi su nan gabanshi snn taja baya ta tsaya tareda rungume hannunta...yace"zo kiyi arranging files din according to their numbers"...sake daurw fuska tayi ta matsa ta janyo kujera zata zauna yayi saurin dakatar da ita da cewa"and who ask u to seat?.."shiru tayi tana kallonshi yace"C'mon get started before i loose my temper with u...ba dai aikinki tafia gidan biki kina barin patients su kadai ba?..as small as you are har kinsan ki hada Ap da saurayi ya sameki wani wurin sbd ba gaban parents dinki kike ba kou?..i know exactly how to deal with people like u..now start what i asked u see the other side of me"...a hankali ta matsa gaban table din ta kai hannu ta janyo files din gabanta...har zata fara dubawa ta tuna batasa glasses dinta ba dan haka ta mike zuwa inda bag dinta ke ajiye ta dauko glass din ta saka snn ta sake komawa ta fara abunda ya sata...shidai yana zaune yayi crossing hands dinshi a kirji yana kallonta...Allah ya taimaketa gaba daya files din a jere suke according to numbers dan haka ta dago tana kallonshi tace"Sir a shirye suke"...without looking at her yace"call the first person"...cikeda haushi sosai take kallonshi jin abunda yace..ta kalli bell dake gabanshi dannawa kawai fa zaiyi patients din su fara shigowa amma bazai iyaba sbd dole sai ya bata wahala...ganin wasu hawayen na sake ciko idonta ta dauki file din farko tareda juyawa ta fita sai gasu sun dawo ciki da me file din...ya nuna mata wuri ta zauna ita kuma Aysha ta kwashi files din gaba daya zata fita dasu yace"where do u think u are going?.."ba tareda ta juyo ba tace"waje.."yace"su kuma files din suyi mene a wajen?..and ke kanki waya baki permission din zuwa waje?.."saida ta hadiye tears dinta snn tayi qundunbala ta juya tana kallon tsakiyar idonshi trying so hard ta 6oye tsoronshi dake cikin nata idanun tace"sai nacigaba da turosu daga waje"...kallon tsakiyar nata idanun shima yayi kafin yace"zo ki ajiyemin files and if u dare step out of this office sai na baki mamaki wlh"...sauke idonta qasa tayi tareda lumshe su allowing tears dake ciki fitowa kan cheeks dinta...ai ita tasan ta gama yawo tunda ta fada hannun wnn azzalumin...bata damu data goge hawayen ba ta maida mishi files din gabanshi kaman yanda yace snn ta koma gefe ta tsaya tana cigaba da hawaye...hankalinshi ya maida kan patient dinshi yana mata tambayoyi...Aysha tayi mamaki sosai yanda taga yana interacting da patients din nashi sam batayi zaton haka daga wurinshi ba...gani take ko patients din ma zare musu ido zai ringayi yana daure musu fuska amma sai taga ba hake yakeyi ba sam...mgn yakeyi dasu full of attention da kuma concern kamar dai ba arrogant and wicked Proprietor dinsu ba...haka yacigaba da attending patients dinshi tana tsaye saidai idan ya gama yace ta kira next patient and ba yanda ta iya haka tayita sintiri from office dinshi zuwa waje...legs dinta har sun fara mata ciwo sbd tsaiwa ga wnn kai kawon da takeyi shima ba karamin wahala ne dashi ba...ga patients din da masifan yawa dan gani take kaman ma karosu akeyi ace tun dazu suna abu daya amma har yanxun sunki karewa...har aka kira sallahn magrib basu kammala ba...zuwa yanxun karfinta ya gama karewa tass neman wanda zata saukema kukan dake cinta kawai takeyi amma babu dan haka ta jingina da bango tareda kai hands dinta ta rufe fuskanta dasu ta shiga rera kukanta a hankali...Bobby na jinta baice komai ba har ya sallami wadda take gabanshi snn ya mike zuwa bathroom yayo alwala ya fito ko kallon inda take baiyi ba ya fice zuwa masjid...tana jin ya fita ta zauna nan kasa zaman dirshan ta dora hannu a kanta tana rushewa da wani matsanancin kuka...kuka take sosai dan idan ka ganta zaka ranste da Allah wani gagarumin abun akayi mata...saida ta shafe kusan minti goma tana abu daya kafin ta mike da sauri kaman wanda ta tuno wani abu ta dauki bag dinta tana goge hawayenta ta bude office din ta fita...a bakin kofa sukayi karo dashi yana tsaye ya zuba mata ido kaman yasan abunda take niyyar yi yace mata"waya baki permission din tafiya?.."takai hannu ta goge tears dinta ta bude baki da kyar sbd kukan da taci tace"Sir...dan..Allah...inje gida...wlh na gaji...kaina namin ciwo"...kallonta kawai yake yanda tayi mgn dama tun ba yanxu ba yasan sangartacciya ce so baiyi mamaki ba sam...baice komai ba yakai hannu ya bude kofar office din yana binta wnn kallon da bataso cikin stern voice dinshi yace"get in.."yarfe hannu ta farayi tana dan bubbuga legs dinta a kasa da alama abun ya motsa cikin shehssheka tace"Sir dan...Muhammdu...Rasulillahi...dan darajan..."kasa karasawa tayi sbd ido daya tsareta dasu...haka nan ta juya ta koma office din sabbin hawaye na sake antayowa fuskanta...shima shiya yayi ya maida kofan ya rufe snn ya karasa seat dinshi ya zauna...ya duba sauran files da suka rage mishi yaga guda uku yasan idan yace ta kirasu 6ata mishi time zatayi dan haka ya danna kararrawa ba dadewa wanda yake kan layi ya shigo...wuri ya nuna mata ta zauna snn ya shiga attending dinta...Aysha dai har yanxun tana tsaye tana kuka kaman wanda akama dan banzan duka...ganin bafa dena kukan zatayi ba daya sallami ta gabanshi sai ya juya yana watsa mata harara yace"ke kinada hankali kuwa?..office din nawa zaki maida wurin iskancinki are u insane?.."banza tayi dashi tana cigaba da kukanta...ya daka mata tsawa yace"are u deaf"...ai batasan lokacin data hadiye ragowar kukan ba sbd tsabar tsoratan da tayi...ya nuna mata wani seat dake kusada ita yace"seat down and keep shut...idan kika sake na sake miki mgn you will see the other side of me"...ba musu ta zauna kan kujeran tana kunshe kukanta...haka tayita zaune har ya karasa ganin patients din snn ya mike ya tattara kayanshi ya dau keys da wayoyinshi ba tareda ya kalleta ba yace"leave my office immediately..and make sure gobe ki fito da wuri kimin clearing office idan ba hakaba zakiga yanda zanyi dake"...tun kafin ya karasa ta bude office din ta fita da sauri tana sakin kukan da take rike dashi tun daxu. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 18 Parking lot ta zauna tacigaba da rusa kuka kaman wadda aka aikoma saqon mutuwa...tana nan zaune taga fitar motanshi aikam tabi motan da harara kamar idanun zasu fadi...saida tayi me isarta snn ta daga waya ta kira besty dan yazo yayi picking dinta...yana dauka ko mgn kasawa tayi kawai ta rushe mishi da kuka...a rikice sosai Sa'eed ke tambayan abunda ya sameta amma ko uffan batace ba sai azabar kuka take...daga karshe sai ya kashe wayan kawai snn ya dauki hanyan Hospital dama he is near by so within few minutes ya iso...da sauri ya karasa inda ya hangota zaune tana kuka shima ya zauna nan gefenta hankalinshi duk a tashe yace"besty dan Allah what is it?..why are u crying like this?..are u sick?.."girgiza mishi kai tayi meaning she is fine...yace"then what happened?..why are u crying?.."kuka tacigaba dayi kaman bazata yi mgn ba sai can daga baya tayi kokari ta tsayar da kukan nata snn tayi mishi bayanin duk abunda ya faru tun shigowarta asibitin zuwa yanxu...sauraronta yake saida ta gama tsaf snn yace mata"yanxu dai kiyi hakuri ki fara mikewa mu wuce kinga dare na karayi sosai...shi kuma proprietor kiyi mishi addu'a Allah zai saka maki kinji kou?.."gyada kanta tayi tareda mikewa a hankali suka nufi inda yayi parking...if u see how she is walking u will think irin tayi shekara da shekaru tana ciwon kafa...a haka suka isa inda motan yake ya bude mata ta shiga shima ya shiga suka fita daga asibitin...koda suka isa hostel saida ya kira Billy a waya wai tazo ta shiga da ita ciki aikuwa ta fito a rikice dan tana tunanin wani mugun abun ne ya faru da ita...mamaki ya kamata ganin yanda idon 'yar uwar tata yayi ja sosai face dinta duk yayi red sbd kukan dataci kafin ma ta tambaya Sa'eed ya labarta mata abunda Ayshan ta fada mashi ya faru...jikinta yayi sanyi kalau ita kanta tausayin Ayshan takeji...tasan haduwa irin wnn da proprietor ba abun alkhairi bane mutumin da ko idanu ka hada dashi sai kaji a jikinka inaga kuma ace ya tsareka da a gaba yana suburbuda maka masifa...ai dole ma Aysha ta jigata wlh..ko ba don zirga zirgan da tayi ba ko zama at the same roof da wnn mutumin kadai ya isa yasa mata zazza6i balle kuma ga wahalar da ita da yayi...Allah kadai yasan adadin sau nawa cikinta na kadawa sbd wmn matsiyacin kallon nashi...a hankali ta kamata suka shiga hostel din shi kuma Sa'eed ya juya kan motarshi ya wuce gida...suna shiga ciki ta hada mata warm water ta taimaka mata zuwa bathroom snn ta dawo ta shiga kitchen ta hado mata thick tea shima mai zafi ta jiye mata kan study table...ta dauko pcm da ruwa shima ta ajiye mata nan kusada tean sai kuma ta bude wardrobe dinta ta dauko mata jessy dinta as usual na Man Utd fara qal da wandonta duk ta jiye mata su kan gado...tana fitowa ta dauki kayan ta saka snn tasha tea da magani snn ta nannade kan gado tana sauke ajiyar zuciya...kawai imagining take yanda zatayi spending three whole weeks tareda wnn azzalumin mutumin da baida imani da tausayi ko kadan. Washegari da wuri ta tashi duk da ba wani baccin kirki ta samu ba amma she woke up as early as possible sbd gudun sake yin wani laifin...a gurguje ta shiga bathroom tayi wanka snn tazo ta shirya suka fita tareda Billy ko breakfast ta kasa tsayawa tayi sbd tsoron kar tayi latti ya samu daman ci mata mutunchi. 8:17 suka shigo Hospital ko sallaman kirki bata tsaya sunyi da Billy ba ta wuce sbd tsoron abunda zai iya mata...saida ta tsaya ta gama jero addu'o'inta a bakin office dinshi snn ta tura kofan ta shiga a hankali da sallamanta ciki ciki...yana zaune kan office chair dinshi sanye da suit as always yana filling wani file dake kan table dinshi...ko kallon inda take baiyi ba balle har tasa ran zai amsa sallaman da tayi..itama hakan bai dameta ba ta karasa inda ta tsaya jiya ta tsaya kanta a kasa...wayanshi ne keta ringing yana ciki file din amma yayi banza dashi kaman bashi ake kira ba...saida ya gama snn yayi sliding tareda putting nata on speaker da igbo yace"Sab bakada hankali kou?..why kaketa jeramin missed calls haka?.."daga daya bangaren Sab ya amsa mishi cikin igbo shima saying yanason mgn dashi ne...Aysha dai na tsaye tana jin yanda suke mgn da igbo dagashi har wanda ya kirashi a wayan...dukda ba fahimtan language din takeba for sure tasan masifa yake sbd yanda yake daga murya...can kasa kasa tace"duk wani inyamuri dai ya iya masifa..kilan abun a jininsu yake"...tayi nisa cikin tunaninda take har batasan ya kammalan wayan da yake ya dawo sa hankalinshi gareta ba...yana kallon yanda dan bakinta ke motsawa as a result of zancen zuci da take kawai sai yaji gabanshi ya fadi...ya lumshe ido yana karanta innalillahi cikin ranshi...ya dauki tsahon lokaci idon nashi a rufe har saida yaji heartbeat dinshi ya daidaita snn ya bude..still kuma idanun kanta suka fada this time around sai ya kasa dauke idanun daga kanta...he just keep staring at her like mirror...har yanxun bakinta mosti yake and he wonder what she's saying da bakin ke motsawa haka...a hankali yayi sama da eyes dinshi zuwa forehead dinta da black thick hair kenan a kwance luf kaman na jaririya har zuwa sajenta da kuma dimples dinta da ko yaya cheeks dinta yayi motsi sai ya fito...sake lumshe eyes dinshi yayi yana dan murza goshinshi feeling somehow...baisan meya sameshi yau ya kasa dena kallonta ba and it's not as if she's beautiful kawai dai baisan dalili ba...wnn karon yana bude idon itama ta bude nata aikuwa idanunsu suka sarke cikin juna...Aysha da dauke nata da sauri sbd wnn abun dai da takeji duk ya zuba mata golden eyes dinshi a kanta...turo baki tayi murya can kasa tace"nidai Allah ya isana wlh..haka nan ya dinga zubama mutane idanun nan nashi sbd yasan ba'aso"...daure fuska yayi kafin yace"ke what are u saying?.."da sauri ta maida bakinta normal tareda kokarin daidaita face dinta kai a kasa tace"ba komai Sir...good morning"...bai amsa ba sai nuna forehead dinta da yayi yace"baki iya daura dankwali bane?..ko duk cikin rashin sanin darajar kai ne yasa kike yawo da gashi a waje?.."hannu takai ta dan janyo hijab din zuwa goshinta dukda ba rufe gashin yake ba dan kome zatasa sai ya fito shiyasa ma take barinshi..cikin ranta tace"na rasa a ina inyamurin nan yaji hausa wlh..he speaks like jakin kano"...kallon forehead din nata yayi yaga still gashin na nan waje kuma wai da sunan ta rufe kawai sai ya girgiza kai tareda sakin tsaki...mikewa yayi ya dauki phone dinshi snn ya kama hanyan fita yace mata"follow me"...ba musu tabishi a baya kaman body guard...eclmaptic ward taga ya nufa...ya jima suna mgn da wata nurse da doctors guda biyu kan wata patient da zasu shiga da ita theathre yanxu...after like ten minutes aka fito da matar zuwa theatre sauran doctors din suma duk suka shiga don shiryawa...shine karshen fitowa shima ya kama hanyan theatrn Aysha ta bishi a baya...daga bakin kofa ta tsaya ta dan daga murya yanda zai jiyota tace"Sir in koma knn?.."juyowa yayi yana kallonta da mamaki yace"go back where?..ba cewa nayi ki biyoni ba"...ta dan marairaice tace"to Sir naga zaku shiga theatre nefa"...ya daure fuska snn yace"C'mon come inside and get ready dake zamu shiga ai"...ta wani zarw idanu tana kallonshi hadda dora hannu a chest dinta tace"dani kuma?.."yace"ke don't waste my time here.. i said dake zamu shiga kiyi resuscitating baby and don't let me repeat myself"...hannu ta fara yarfewa zata kwaso magiya kawai ya zuba mata idanunshi yana yi mata irin kallon da yasan duk iskancinta bata isa ta sake yi masa musu ba...hakan ne kuwa ya faru dan kasa cewa uffan tayi..tayi kasa da kai cikin ranta tana mamakin tasirin da eyes dinshi suke dashi a kanta...kofa ya nuna mata yana kallonta alaman she should enter...ba musu balle gardama ta shigo ciki a hankali kaman mara lafia...changing room ya nuna mata ba tareda yace komai ba haka ta shiga ciki tanajin kaman ta dora hannu a kai tace wayyo Allah...bayan ta shiga shima ya shiga doctors changing room yayi changing zuwa theater outfit dinsu snn ya fito zuwa main theatre...matar tana kwance masu anaesthesia sun fara aikinsu a kanta sai doctor faith da doc gabriel da zasuyi aikin tare...ganin har zasu fara bata fito ba ya fita zuwa dressing room din...a tsaye ya sameta ta gama sa kayan sai kallon kanta take tana ganin yanda kayan sukayi mata yawa...tana turo baki tace"kayan ma over size n..."bata karasa idanunta ya sauka cikin nashi sai tayi saurin daidaita kanta da sauri tana cewa"am sir..d..dama yanxun..zan fito"...kallonta yayi from head to toe snn ya tsayar da idon nashi kan gashinta datayi parking a tsakiyar kai ta saki jelar yanata yawo tsakanin wuya da shoulders dinta...da sauri ta dauki hijab dinta ta rufe kan nata dashi baki a tunzure tana fadin"to babu hula fa"...baice mata komai ba ya karasa cikin dakin ya bude wani drawer ya zaro mata one of huluna da suke ciki snn ya wurga mata...saida ta daure fuskanta tsaf snn ta dau hulan ta saka cikin ranta tana zaginshi sbd cilla mata hulan da yayi...hanya ya nuna mata ba musu ta shige gaba yabita a baya...a bakin main theater suka tsaya ta zura wnn gunduma gunduman takalman snn suka shiga ciki...itadai a tsorace take dan bata ta6a shiga theatre ba..tsananin tsoronta ma bazai bari ta shigaba dan ko Allah ya san batason ganin ana yanka mutum sam...amma yau wnn inyamurin ya sanyata dole ta shiga dukda rashin son nata...saida suka gama shirya komai tsaf snn kowa yasa nose mask dinshi suka fara aikinsu...Aysha dai na tsaye tana faman runste ido don bazata iya gani ba wlh...Bobby dayaga yanda take runtse ido sai yayi mata alama da ta matso kusa...ta shiga yarfa hannu har ta fara hawaye shi kuma ya tsareta da ido yanda baza tayi mishi gardama ba...haka ta matsa inda ya nuna mata tana cigaba da hawaye har doc Gabriel nayi mata daria...kafin ta sake kulle idon yace mata"if u dare close those eyes again zakiga yanda zanyi dake wlh..and i mean it"...bata rufe din ba kuwa ta zuba idanu kawai tana kallon abunda sukeyi...kirjinta har sama da kasa yakeyi bata ta6a sanin tanada tsoro har haka ba sai yanxu...hankalinta bai sake tashi ba saida taga sun fara yanka matar...taga yanda suke cutting skin dinta layer by layer kawai sai taji wani hadadden jiri ya fara daukanta...kokari tayi ta rike gefen gadon gam still kuma taki kulle idon sbd kar yayi mata masifa...tun tana iya bakin kokarinta wajen ganin jirin baiyi tasiri a kanta ba har yakai limit din da bazata iya controlling dinshi ba kawai sai gani tayi dakin yana juyawa da ita...ta saki gadon da sauri tareda kai hannu ta dafe head dinta dashi idanunta a rufe still bata dena ganin jirin ba daga karshe ma sai ji tayi ta tafi luuu kaman zata fadi Allah ya taimaka akwai wani gado a bayanta kawai saita fada kanshi ji kake timm...a tare gaba daya doctors din suka dago suna kallonta don sunyi nisa a aikinsu that ba wanda ya lura da abunda ke faruwa da ita sai faduwan nata sukaji...dukda ta fadin kuma jirin bai dena daukanta ba har yanxun tana dafe da kanta hawaye na fitowa idanunta murya can kasa take fadin"wayyo Ammina..wayyo dadyna..wayyo Allahna"...gaba daya doctors din saida sukayi daria banda Bobby da baiga anything funny a nan ba...basubi ta kanta ba suka cigaba da aikinsu that last for 40 to 45 mins kafin suka gama...doc faith ce tayi resuscitating baby su kuma suka karasa duk wani necessary abu da zaa yima matar snn wanda zasu fita da ita sukazo suka dorata kan trolley sukayi waje da ita babynta kuma already an mikashi wa relatives dinta...sauran doctors din suma duk fita sukayi shi kuma Bobby bayan yayi sanitizing hannunshi ya nufi kan gadon da take thinking ko bacci take mishi a theatre and to his biggest surprise sai yaga ashe sumewa tayi...mamaki ne ya kamashi hade da daria at the same time...wato duk iskancin dan iska akwai abunda yake tsorata shi har ya sashi suman dole...shi tunda yake bai ta6a ganin Midwife irinta ba...wai matar dake dealing da kar6an haihuwa itace zata suma sbd Caesarean section "what a shame!.."ya fada trying to control his laugher cox he still can't believe sumewa tayi...wato duk rashin jin nan nata she has this phobia of blood ne ko of the operation din ne gaba daya ma bai sani ba...saida ya gama dariyarshi snn yasa aka kawo ruwa ya watsa mata...ta mike a gigice idanunta kulle take fadin" dan Allah no...i don't want to see it plss i beg u...wayyo Allah besty,Billy,baby come help me plssss"...ta karasa mgn new tears na rolling kan fuskanta...Dr.Bobby still can't believe this...knn da gaske suma tayi sbd abunda ta gani...lallai kuwa tanada aiki a gabanta...a very huge one ma kuwa...a hankali ta bude idonta sai taci karo da smiling face dinshi aikuwa ta wara idanun da kyau tana kallonshi to make sure she is not dreaming...tadai san idan ba mafarki ba ba yanda za'ayi inyamurin nan yayi daria for it's something she never seen..shi kuma ganin kallon da take masa sai ya dinke fuskanshi tsaf tareda matsawa daga inda yake yace"C'mon get dawn before i slap u lazy girl kawai...a haka zaki zama midwife kina painting sbd caesarean?..u are deceiving ur self"...goge tears dinta tayi ta sauko daga gadon tana fadin"ai ni ba ta6a gani bane shiyasa"...harara ya watsa mata yace"shiyasa nace u are deceiving ur self...now ki wuce ki jirani office and if u like kije wani wurin kiga idan na dawo banyi maganinki ba"...wucewa tayi tana sake turo baki sai kuma ta juyo zatayi mishi mgn yace"i said leave"...ba gardama ta sake juyawa ta fice daga wurin...duk jikinta ma wani iri take jinshi kaman na mara lafia...shiko Bobby bayan yayi changing zuwa normal outfit dinshi ya fita zuwa office...zaune ya sameta kan one of sofas dake nan ciki tayi wani dai dai kaman tana office dinta yana shigowa ta mike da sauri tana rarraba ido kamar munafuka...baice mata komai ba ya karasa gaban table dinshi ya dauki stethoscope ya rataya a wuya snn ya juya zai fita ya sake ce mata"Follow me"...banza tayi dashi tana binshi da harara har ya fita snn ta mike itama ta fita tana kwaikwayon mgnrshi" wani wai follow me...sai kace ajiyeni yayi in dinga yi masa bauta...mugu kawai"...ta karasa mgnr da guntun hawaye a idonta...ita dai zataga ranar da zatazo asibitin nan ta tafi bai sa tayi kuka ba...kullum burinshi ya sata yin abunda bataso ko ya wahalar da ita kawai sbd small mistake data aikata bayan ba kanta aka fara ba...Post natal ward suka je ya fara ward round ita kuma tana biye dashi a baya...data gaji da tsaiwa sai ta faki idonshi ta samu wuri zata zauna taji yace mata"zo kimin taking vital signs din wnn"...kamar ta kwada masa mari haka taji amma ba yanda ta iya haka ta mike ta fara taking vital signs din...a takaice ita ta dauki vital signs din duk patients din dake ward din shi kuma yana dubasu...kafin su gama kuwa jikinta yayi laushi liss kaman an nakada mata shegen duka...yau ma kamar jiya da kuka ta fita daga office dinshi bayan ya sallameta. Haka kwanaki sukayita tafiya kullum Aysha na shan baqar wahala a wajenshi dan ba ranan da zatazo ta wuce bai sata kuka ba...gashi ita kuma ta kasa sabawa da wahalar da yake bata kullum idan ta gani bata ma sanin yaushe kukan ke zuwa...a haka suka kwashe two weeks suna abu daya har suka shiga sati na uku wich is their final week daga shi zakuyi resuming school...if u see how she is happy zakayi zaton graduation ne zatayi gaba daya...nan kuwa murna take sbd Allah ya kawo karshen wahalar da takesha hannunshi dan ko makiyinta bazata yi mishi fatan ya shiga hannun dr bobby ba dan bashda kyau ko kadan...cikakken mara mutunchi ne na gidan gaba shiyasa take addu'a idam sun rabu a nan Allah yasa rabuwarsu knn dan ko a College bata fatan ko hanya su sake hadawa dashi...laf cikinsu ita kadai ce batayi rotating wards ba sbd yanda ya makaleta a office dinshi amma su sauran kusan wards uku kowacce taje...ita Billy daga ANC ta koma Family Planning Unit daga nan kuma taje Ante Natal Ward duk tayi two two weeks a wurin amma ita duk yabi ya takureta a wuri daya ya hanata gaba ya hanata baya sbd baqin hali irin nashi...ita har yanxu tana mamaki idan akace mata musulmi ne dan har ga Allah wnn baqin halin nashi ba idabi'an musulman kwarai bane..ko da yake shima kilan musulmin ne kawai amma bana kwarai ba...shiyasa dole ma tayi murna Allah zai rabata dashi ta huta da ja'iba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitar min dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 19 Yau Thursday Aysha na zaune office dinshi ita kadai as shi tunda ya fita sallah bai dawoba dan haka ta bararraje abunta tana ta faman waya da Babynta da har yanxun bai dawo daga tafiyar da yayi ba...bayan sun kammala wayan tayi dialing number Ammi dan da gaske so take taje gida weekend amma Hamma yace wai ta bari ba yanxu ba...ringing biyu Husna ta daga wayan tana cewa"Addah.."tace"na'am ina Ammi?.."Husna ta dan turo baki tace"ke Adda bakida kirki wlh..daga daga wayan zaki wani ce ina Ammi ko gaisawa bazaki bari muyi ba?.."dan murmushi ta saki tana gyara zamanta tace"to sannu Husna ina yini..ya gida ya studies?.."daria Husna tasa jin yanda take gaisheta tace"kai Addah"...itama tana cigaba da smiling tace"to ai naga ba'a iya maki ne shiyasa na gaisheki"...Husna tace"umh to ina nan lafia ya posting?.."da sauri kaman wadda aka tsikara tace"posting dai yazo karshe ki tayani murna wlh..gobe Allah zai rabani da inyamuri in huta da azaba"...daria Husna ta sakeyi tace"nifa Adda har yanxu daria kike bani idan kika kirashi inyamuri..ina laifin ma kice dr bobby"...ta6e baki Aysha tayi tace"ki zauna saina kirashi dr bobby...mutuminda kowa yasan inyamuri ne shi..ranar bakiji wayan da naji yanayi da wani ba kilan dan uwanshi ne sukata inyamurancinsu abunsu"...sauke ajiyar zuciya Husna tayi tace"to congratulations Allah zai rabaki dashi gobe..amma zaku iya haduwa a cikin college fa"...tun kafin ta rufe baki Aysha tace"bakinki ya sari danyen kashi..nidai kiba Ammi waya inyi mgn da ita..where is my habibty?.."tace"yanxun nan suka fita da Hamma...Ammi kuma tana daki tace bacci zatayi kar in tasheta"...Aysha tace"karya kikeyi dan Allah ki kai mata it's urgent plss pls plss..kinji 'yar kanwata"...kafin Husna tayi mgn ta jiyo voice din Ammi tana cewa"Husna daukan min waya kikay kou?.."da sauri ta mika mata wayan tace"dama Adda ce ta kira gashi"...batayi mgn ba tasa hannu ta amsa wayan...Aysha ta wani narke kamar tana gaban Ammin tace"my Ammi"..tsaki Ammi taja tace"zakiyi mgn ko bazakiyi ba?.."ta sake narkewa tace"Ammi zanyi...amma fa nayi missing dinki sosai wlh...wai yanxu Ammi ni ko dan pampering dina sbd bana gida bazakiyi ba kuma fa nice fisrt love dinki tunda ni kika fara haif..."bata karasa ba Ammi tace"Aysha zakici ubanki wlh...abokiyar wasanki ne ni da zakina fadamin such maganganu..wato sbd kinga kwana biyu kinata zuba rashin mutuncinka na kyaleki kou?..to zaki dawo gidan nan ki sameni zany maganinki"...da sauri tace"Ammi am sorry dan Allah...kiyi hakuri ban karawa"...wani tsaki Ammi ta kuma ja tace"naji...yanxun zaki fadi ur reason for calling ko kuma iskancin naki zaki cigaba dayi?.."ta wani marairaice kaman abun tausayi tace"zan fada...Ammi dama fa so nake nazo gida weekend shine hamma wai ba yanxu ba...dan Allah Ammi kice yazo ya daukoni kinji..wlh ina missing dinku"...kai tsaye Ammi tace"saidai kuwa kiyi hakuri dan gobe muma zamu wuce Abuja nasan shiyasa yace ki hakura..amma idan muka dawo ai zakizo so stop worrying urself"...da sauri tace"Ammi me zakuyi a Abuja kuma?.."tace"wani taro ne nasu daddynku akayi inviting dinmu and daga ni sai Najeeb zamu tafi banda su Husna dan nasan yanxun xaki ce an tafi dasu baa tafi dake ba...nasan sbd irin wnn halin naki dadyn ma yace a kyalesu a gida"...ba kunya har wani ajiyar zuciya ta sauke dan wlh da zaaje dasu itama daga hankali zatayi sai an biyo an tafi da ita...yanxu kuwa da taji babu su sai taji hankalinta ya kwanta..zuwa weekend dinma ta hakura idan suka dawo din sai taje...a hankali tace"to shikenan Ammi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya"...Ammi ta amsa da"Ameen"snn sukayi sallama...tana ajiye wayan idonta ya sauka kan Bobby dake zaune yayi relaxing kan seat dinshi yana kallonta...ta zare idanu sosai hade da dora hannu a kirji cikin tsananin tsoron ko yaji abubuwanda ta fada a kanshi tace"Na shiga uku"...saura kiris daria ya su6uce mishi amma ya fuske...instead sai ya daure fuskanshi yace"so abunda kikeyi min a office knn idan bana nan kou?..yayi miki kyau"...hadiye wani yawu tayi da kyar cikin karfin hali tace"Sir..dan Allah am sorry...kaji"...ko kallonta baiyi ba ya mika mata hannunshi yace"bani wayan"..a razane tace"wich one?.."yace"ur phone"...nan take ta sake tsurewa duk a tunaninta yaji gulmanshi da sukayi tace"Sir dan darajan su Mummy kayi hakuri"...kallonta kawai yayi hade da girgiza kai yacigaba da aikinshi bai sake cewa komai ba...ita kuwa daukan wayan tayi ta turashi cikin jaka tana addu'an Allah yasa baiji wayan da sukayi da Husna ba...karfe uku ya sallameta as usual tana fitowa suka hadu da Billy da sauran 'yan hostel suka karasa inda bus dinsu yake duk suka shiga sai Hostel dinsu. The following day duk da wuri suka shigo sbd friday gajeren rana ce and kowa tanaso a sallameta da wuri sbd su samu su wuce...lokacinda ta isa office dinshi yanata attending patients sai ta nemi wuri ta zauna kamar yanda ta saba tana sauraron discussion dinsu..wasa wasa tayi learning abubuwa da dama zaman da tayi office dinshi don sata gaba yake idan yana interacting da patient yace idan sun gama zaiyi mata tambayoyi dan haka take bude brain dinta da kyau tana kwashe duk abunda yake fadi..haka duk prescription din da yayi saiya nuna mata nan ma idan sun gama ya shiga mata tambayoyi iri iri so he've learned alot and ko ba komai ta wnn fannin dai zatace yayi abun kirki...da yake patients din ba masu yawa bane around 12 ya gama dasu snn ya fara shirin tafia sallahn jumu'a...before ya fita ya bata log book dinta da yayi signing already snn ya nuna mata kofa yace"A sauka lafia"...wani kayataccen smile ta saki da har both dimples dinta suka bayyana cikin tsantsan farin cikin zata rabu dashi tace"nagode sir"..daga haka ta fice daga office din bobby ya bita da kallo irin na mamaki...tunda yake da ita bai ta6a ganin such smile kan face dinta ba...yanxun duk wnn excitement daya gani kan face dinta na rabuwa dashi ne ko kuwa there is more to it?..kai ai daga gani ma wnn na rabuwa dashi ne...haka nan kuma sai yaji baiji dadin yanda tayi ba.."am i this bad?.."ya fada a fili kaman he's asking someone...ganin yana wasting time dinshi a banza kawai ya fita zuwa parking lot driver na ganoshi ya bude mishi mota ya shiga suka fita daga asibitin. Ita kuwa Aysha office din da aka fara posting dinsu taje nan ta samu sauran colleagues dinta a wurin kowacce an sallameta an kuma yi mata signing... daga nan aka basu certificate shknn aka sallamesu kowa ta kama gabanta...ita da Billy tare suka fito zuwa parking lot amma basuga motan Sa'eed da yace zaizo daukansu ba...suna kokarin zama sai gashi nan ya karaso dan haka suka karasa inda yayi parking...ko a hanya Aysha kasa 6oye excitement dinta tayi Billy sai tsokanarta take wai daga yanxu tanayi mata laifi zata hadata da proprietor tunda shine maganinta...ita kuwa sai hakilo take bestynta na tayata...yana ajiyesu a hostel suka shiga ciki shima ya wuce. Around 5 pm suna zaune room 3a gaba daya sai labari suke suke darawa...they are all happy sun gama Clinical Posting dinsu lafia...wayan Aysha data bari cikin dakinsu nata ringing bata ji ba sbd hayaniyan da sukeyi...wata da tazo wucewa taji ringing din shine ta dauka ta kai mata dakin da suke...tana duba screen taga Baby boo jiki sai ta mike da sauri ta fita daga dakin tana fadin"my husband is calling"...Rahma tabita da kallo tana daria tace"Billy wai ina mgnr Sir Abdool ya kwana ne naga Lamido har tayi mishi kishiya sbd wulakanci"...Billy tace"ki bari kawai wlh tunda nake ban ta6a ganin mace kaman Lamido ba...she is indirectly rejecting him for that sugar daddy"...gaba daya daria suka saka kafin wata tace"nima dai ina mamakinta wlh..ta samu mutum kmr sir abdool da yake bala'in sonta wai ta kyaleshi for someone else..she is kind of different"...nan kuma akalar hiran nasu ya koma kan Lamido and her love for sugar daddies kowa yana fadan albarkacin bakinshi...tana fita ta fada room dinsu hadda rufe kofa snn tayi picking...before she says anything yace"My baby am back"...wani ihu data saka saida ya janye wayan daga kunnenshi...lokaci daya kuma ta toshe bakinta tana zaro ido feeling so ashamed of herself for behaving like this...sam batasan sanda ihun yayi escaping bakinta ba wlh..she is just super excited he's back dama ga farin ciki rabuwa da inyamuri ga kuma another good news...shi kuwa Prof daria ya saki sosai jin tayi diff kaman ruwa ya cinyeta yace"baby girl why are u quite?."kamae zatasa kuka tace"sorry...ban san yaushe ya fito ba wlh..am just happy u are back"...murmushi ya kara saki yace" don't worry yanxun dai ki samu ki fito waje in ganki"...idanu ta sake budewa tace"wait..u mean kana hostel dinmu?.."yace"komai bazan iya yi ba har sai na ganki"...ai bata jira ya karasa ba ta kashe wayan da sauri ta rarumi hijab din Billy dake nan kan bed dinta ta dora kan jean da shirt dake jikinta ta zura takalma ta fita...a bakin gate din nasu kuwa ta ga motanshi batasan time data saki murmushi tana karasawa wurin ba...bude mata motan yayi ta shiga snn ta rufe ta juya tana kallonshi...kallon nata shima yakeyi yanajin tamkar bai ta6a missing wata halitta ba kaman yanda yayi missing dinta...ita kuwa banda murmushi ba abunda takeyi...a hankali taji ya kira sunanta"Ayshaa.."ta sake dagowa tana kallonshi don tunda suke bata ta6a jin ya kirata da Aysha ba...before she says anything yayi adding"Baby girl am tired plss...am tired of this hide and seek i really want to meet ur dad..i need to talk to him about us..about our marriage am not a small boy da zanyita wasting time dina ina soyayya a waje"...shiru tayi tana sauraronshi thinking of what to tell him...har ga Allah ba wai batason aurenshi bane no kawai dai tafiso ta fara kammala karatunta then sai ayi mgnr aure amma ta fuskanci he won't let that happen...his last statement yasa ta dan kwa6e fuskanta kaman zata fashe da kuka tace"wato wasting time dinka kakeyi ma kou?..soyayya dani shine waste of tim..."bata karasa na ya katseta da fadin"No baby that's not what i mean...ina nufin am tired..i want to marry you plss"...batasan time din da ta saki murmushi sbd yanda yayi da face dinshi ba...tana dubanshi tace"baby saurin me kakeyi ne?..xaka aureni inshaAllah.."zai sake mgn tace"Please mana..k ganinka ban gamayi ba ka fara wani mgn daban..nidai allow me to look at u sosai inyaso daga baya sai muyi mgnr auren"...murmushi ya saki yana girgiza kanshi sarai ya ganeta..wai shi yarinyar nan zatayi ma wayo...bai sake cewa komai din ba kuwa sukaita kallon junansu kaman wanda suke staring competition...har tafiya ta hanashi wai bata gaji da kallonshi ba...haka yayita zaune har sai da aka fara kiran magrib snn ta kyaleshi ya tafi ita kuma ta koma hostel. Washegari saturday Bobby tunda ya gama gyming dinshi yayi wanka ya fito suke zaune parlor tareda Mummy da aunty sumy sai labari suke...Nur ne ya shigo parlon da sallama Bobby ya wani hade rai yana kallonshi...yasan tunda yazo gidan nan fita yakeso suyi shi kuma baida intention na zuwa ko ina yau...he wanted to stay home yayi enjoying weekend dinshi like any other person amma it’s like Nur yana baqin ciki da haka...har ya iso cikin parlon ya zauna baice mishi qala ba yanaji suna gaisawa da mummy da aunty sumy sai yayi kaman bai jinsu ya shiga danna wayarshi...bayan sun gama gaisawa Nur ya daga kanshi yana kallon Bobby yaga yanda ya hade giran sama dana qasa kawai sai ya dan girgiza kai yana murmushi...yasan duk wnn attitude da ya fara displaying sbd baison fita ne and shi kuma ya ranste yau din nan sai ya fita dashi sai suga yanda za’ayi...hankalinshi ya mayar kan mummy ya wani tattara gaba daya nutsuwa da kamun kanshi yace"mummy alfarma nazo nema a wajenki dama"...mummy tace"to ina sauraronka Nuru"...yace"ai kinsan ana gina new apartments a college hostel koh?.."Mummy ta gyada kai alaman ta sani...yace"to wlh mummy tun last week mukayi mgn da engineer nan yace ya kamata muje da akwai abunda zai nuna mana amma bobby sam yaki zuwa...yanxun ma da kika ganni kirana yayi yace yana can site din yanaso mu hadu sbd gobe zaiyi tafia kuma zai iya daukan lokaci bai dawoba shiyasa na fito..nasan kona fada masa ba yadda zaiyi ba shiyasa nace gara in biyo ta wajenki"...murmushi kawai mummy tayi tana kallonshi kafin ta juya tana kallon Bobby da har yanxun ran nan a hade yana 6a66ata rai...daria ta saki sosai tana kallonsu...wnn draman nasu ba yanxu aka fara ba...shi Bobby nada taurin kai da kafiya shi kuma Nur akwai naci shiyasa duk irin haka ya hadasu kai tsaye yake zuwa wurinta dan yasan itace kadai zata iya sanyashi ya aikata abu ko bayaso...aunty sumy ma dake zaune tana kallonsu daria take...mummy ta sake juyawa tana duban Bobby tace"ai kaji me abokinka ya fada kou?.."da sauri yace"mummy don’t mind him dan Allah makaryaci ne kawai...babban burinshi yaga ya fitar dani daga gida kuma yasan bai isaba shine zai biyo ta hannunki"...juyawa ta sakeyi tana duban Nur shima ya kwaso rantsuwa yana fadin shi wlh da gaske yake...itama kuma taga alama da gasken yake dan haka ta dubi Bobby tace"yi hakuri kuje kaji?..ai nasan ba dadewa zakuyi ba ko Nuru?.."da sauri yace"eh wlh mummy nan da few minutes zamu dawo"...tace"to kaji bazaku jima ba ka daure kuje kaji?.."fuskan nan ba sarari ya mike zuwa Flat dinshi...shidai ko Allah yasan baiyi niyyam fita yau ba wlh amma shi Nur idan yaso abu kaman d’a yaso fitowa daga cikin mahaifiyarshi...kayan jikinshi yayi changing zuwa tracksuit blue ya debi wayoyinshi snn ya fita bayan ya sake feshe jikinshi da perfumes...Nur na ganin ya fito shima ya mike yayi sallama da su Mummy snn yabi bayanshi dan already har ya kusa kaiwa kofa...suna fita compound ya juya yana kallonshi fuska a cunkushe yace"sai kaje dauko motanka muje dan ni yau na sallami driver na"...Nur na sakin smile yace"dama da shiri na nazo ai..motan yana waje"...harara Bobby ya watsa mai kafin ya kama hanyar wajen...Nur yabi bayanshi yana kyalkyala daria...suna fita ya bude motan suka shiga snn ya tayar da ita ya kama hanyan college...karfe 5 saura suka shiga college amma basu karasa cikin hostel din ba sai after five...a gate din female hostel yayi parking tunda engineern yace mishi yana nan ciki...ya bude mota ya fita shima Bobby ya fito har yanxu fuskan nan a hautsine kaman wanda akaima mutuwa...shidai Nur baice dashi komai ba ya shiga ciki...basu damu da sanar da students shigowansu ba sbd ba cikin apartments dinsu zasu shiga ba dan haka kai tsaye suka zagaya ta backyard inda new apartments din suke...tun kafin su karasa suke jiyo sautin kida na tashi daga wurin amma basu kawo komai ba suka cigaba da tafia...daidai bayan apartment C suke jere kusan su goma kowacce sanye da dogon wando da t shirt amma banda Aysha dake sanyeda wata ash color jessy na manchester da wandon jessyn daya dan haura guiwarta da kadan shima ash ne da ratsin red a gefe da gefe sai kuma number 6 dake can kasan wandon...kanta ba dankwali dogon gashinta gaba daya ya sauka zuwa gadon bayanta ta maida hankalinta sosai kan rawar da take koya musu tana miming...wani kullutun abu Bobby yaji yazo ya tokareshi ya hanashi ko hadiyar yawu...duk yawan nan nasu idonshi bai sauka akan kowa ba sai a kanta nan take kuma yaji wani mashahurin kunchi yana mamayeshi...ya lumshe ido ya bude yana son yasan dalilin da yasa idonshi idon yarinyar nan sai ranshi ya 6aci...baisan meyasa kusan komai nata yake kular dashi ba...yanxu dubi yanda ta dage tana koya musu rawa kaman abunda aka turota yi makarantan knn...and the most annoying this is yanda kowa na sanyeda kayan kirki banda ita...kan kowa da akwai hula amma banda nata...gashin kowa a rufe amma banda nata snn wandon kowa har qasa ita nata sbd tsabar tsageranchi a guiwarta ya tsaya...ba kuma wanda ke sanye da kayan yan ball sai ita...shi tunda yake bai ta6ajin ya tsani kayan yan ball ba sai a kanta...sam ya rasa dalilinda yasa ya tsani ya ganta cikinsu...ji yake da yanada hali har supporting man u dinma sai ya hanata wlh sbd ba dabi’a ne mai kyau ba...Nur da tun dazu yake mishi mgn amma yaga hankalinshi bai jikinshi sai ya rungume hannunshi a chest yana kallon inda yake kalla sai yaga Lamido...murmushi ya saki yana sake kallon Bobby still yaga idanunshi kanta ko blinking bayayi kawai sai ya wuce abunshi yana daria...shidai yasan da matsala domin tun ranan da ya kwace zobuna a hannunta jikinshi ke bashi akwai gagarumar matsala amma bai nuna ba...Bobby kuwa a halin yanxu gani yake ko wanda ke prison bai kaishi baqin ciki ba...baisan meyasa ba amma tabbas yasan yana jin wani irin kunchi da 6acin ran da bai ta6a samun kanshi a ciki ba...su kuwa gaba daya ba wanda ya ganshi da haka suketa dirkan rawarsu cikin nishadi sunayi sunabin waqan...baice komai ba ya juya zuwa gidajen matrons yaci karo da wata student din yace taje ta kira mishi one of metrorin dake hostel din babu wasting of time kuwa suka dawo tareda ita...fuskanshi a gimtse muryanshi na nuna tsananin 6acin ran da yake ciki ya nuna mata su Aysha da har yanxun basu bar rawa ba yace"what’s this?..a building dina kuka barsu suke wnn lalatan babu mai tsawatar musu?.."jikin matar har ya dauki rawa tace"yalla6ai ayi hakuri za’ayi musu mgn InshaAllahu..kayi hakuri"...baice mata komai ba ya rungume hannu yana mata nuni da taje ta kirasu aikuwa ta wuce da hanzari zuwa inda suke...tana isa kai tsaye mp da suka kunna kidan dashi ta dauki tayi disconnecting nashi nan take gaba daya suka juya suna kallonta...kafin wani cikinsu yayi mgn ta nuna inda Bobby ke tsaye murya a dan kasa tace"yace a kiraku"...gaba dayansu ba wadda bata tsorata ba ganinshi a tsaye yana binsu da matsiyacin kallo especially Aysha da takejin kaman ta saki fitsari a wando don tsoro...tana daga idanunta suka hada ido dashi aiko ba shiri tayi kasa da nata tana fadin"la’ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minzzalimeen"...cikinta har wani sauti qululu ya bada sbd tsabar figici...batayi aune ba taga gaba dayansu sun nufi inda yake tsaye hankalinta ya sake tashi idonta har kawo kwalla tace"to ko hijab bazamu dauko ba?.."matron tace"wane hijabi kuma bayan ya riga ya gama ganinku a haka"...a haka suka karasa wurinshi saidai ko kallonsu baiyi ba ya juya ga matron yace mata"ki tabbata ko mutum daya bata gudu ba a cikinsu...suzo su sameni ranan monday a office dina by 4"...yana gama fadan haka ya kama hanya sabon apartment din su kuma kowacce ta bishi da kallo baki bude...masu sallallami nayi masu zaginshi ma duk sunayi haka suka mike kowa ta dauki hanyar hostel dinsu...Aysha dai ko kusa bata cikin hayyacinta dan tana ga duk cikinsu ba wadda tasan muguntarshi kaman ita shiyasa tafi kowa tsurewa a cikinsu...yanxu idan yace ya basu suspension me zata cewa Ammi da Daddy ita Aisha?...bama haka ba yanxu idan yace zai basu punishment kaman yanda ya wahalar da ita a Freedom fa?.."yanxu menene abun yi?.."ta tambayi kanta kamar tana jiran wani ya bata amsa...karashen ranar nan dai gaba daya bataji dadinshi ba dan ko baccin kirki batayi ba...Billy tun tana bata baki har ta hakura ta kyaleta. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 3208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 20 Ranan monday kiri kiri tayi kwanciyarta a hostel taki shirin shiga school din wai ita batada lafia bazata je ba...ba yanda Billy batayi da ita kan ta shirya su fita ba amma sam tace ita bata zuwa sbd tasan idonta idon proprietor ci mata mutunchi zaiyi...haka Billy ta hakura ta rabu da ita sauran da ya kamasu suna rawa tare ranan suka tambayi Billy why bata shigo school ba Billy ta amsa da batada lafia...sam basuyi tunanin da gayya tayi hakan ba so ba wanda ya sake daga maganan saidai kaf cikinsu ba wadda ba a tsorace take da kiransu da proprietor keyi musu ba..duk tsoronshi sukeji sbd bai daya daga cikin masu sakin ma yara fuska balle har suga damanshi...gashi kuma yanada wani irin kwarjini da kowane yake iya resisting idan yana tare dashi ba..yanada wani irin huge spirit dake sanya ma mutane shiga taitayinsu idan suna tare dashi...sai kuma uwa uba eyes dinshi da kowa ke fadarsu wajen nutsar da fitinanne. Karfe biyar da wani abu ya shigo college din dan saida ya gama da Hospital snn ya taho...don ma zuwan ya kamashi dole ne amma da baiga dalilinda zaisa yashigo college monday ba tunda ba ranan shigowanshi bane...kawai ji yake idan baiga yarinyar nan yaci mata mutunchi ba bazai samu nutsuwa ba..sam bazai samu ya huce takaicin data kunsa mashi na ganinta da yayi tana rawa ba...ba ita kadai ya gani tana rawan ba amma ba na wanda ya tsaya mishi a rai kaman ita baisan meyasa hakan ba...ko don sbd tafi kowa zakewa ne oho...har yanxun ya kasa mance scene din...ya tuna ranan dinner wan Rayhan ma itace sahun gaba a masu rawa and yanada yaqinin suma itace ta koya musu...mamaki yake why yarinya kamarta take da shegen rashin ji haka..tanada fitina that yake ganin sam yafi karfin shekarunta...dukda ba sani age dinta yayi ba yasan tayi wuta takai 20 maybe ma bazata fi irin 19 ba haka...shidai da shine yake da ‘ya kamarta ko zata mutu bazai kaita karatu wani garin ba wlh sbd fitinanta yayi yawa...she is so stubborn that yake ganin aurar da irinsu kawai ya kamata ayi a huta...kai tsaye office din Nur ya nufa ya samu zai fita daga office din sbd meeting da yake dashi da entire college staff din yanxu...da mamaki sosai yake duban Bobby dan zai iya tanstewa bai ta6a ganinshi cikin college a irin wnn time din ba kuma ranar monday...komawa ciki yayi yana sake kallonshi yace"mazaa hope everything is fine?..meya kawoka college at this time?.."ta6e baki Bobby yayi yace"yaran nan na hostels zakasa a kiramin"...wara idanu Nur yayi cikeda another mamaki yace"ban gane yaran hostel ba?..wane yaran?.."tsaki Bobby ya saki cikin fara gajiya da questions dinshi yace"wadanda suka maidamin building club mana?..or are u tryinyto tell me baka gansu suna rawa ranan da muka shiga hostel din ba?.."shiru kawai Nur yayi yana kallonshi yasan definitely da akwai abu a qasa...idan ba haka ba why zaice a kirasu kawai sbd yaga suna rawa a hostel...ya bude baki zaiyi mgn Bobby ya katseshi da fadin"hold that to ur self plss...kawai kasa a kirasu kaima ka wuce meeting dinka...u are wasting our time"...wrist watch dake hannunshi ya duba yaga fa time na tafia and yanaso suyi meeting din nan dan haka ya fita daga office din yasa a kira mishi su kaman yanda yace snn shima ya shiga meeting dinshi bayan ya kudurce a ranshi sai yaji dalilin wnn abubuwan da yake. Yana zaune office din after like 10 mins suka shigo gaba dayansu...idonshi na kansu har karaso ciki duk suka durkusa nan gabanshi yace su mike tsaye...bayan sun mike ya sake baza idanu yana son ya hangota amma sam bai ganta ba..yasan kuma zaiyi wahala idan ba da gangan tayi haka ba...bai tambayesu itaba ya shiga yi musu nasiha a nuste...gaba dayansu mamaki sukayi da sukaji ba masifa zaiyi musu kaman yanda sukayi tunani ba...nasiha ce yake musu mai ratsa jiki wanda da yawa daga cikinsu basu san there is this side of him ba sai yanxu...gaba daya kallon wanda bai san komai ba sai masifa suke mishi amma yayi proving dinsu wrong at this very moment...ya nuna musu illan da jin kida da rawa ke iya haifarwa especially gasu da suke mata snn yayi musu na killace jikinsu koda a cikin hostel ne domin kuwa ko babu maza hostel din bazaa rasa aljanu ba and gaba dayansu sun san aljanu da son mata mussaman masu kyau kyau dan haka suka dauki nasihan nashi da muhimmanchi...godia suka hau mishi bayan ya gama tareda alqawarin zasu kiyaye gaba inshaAllah...dadi sosai yaji wanda har hakan ya nuna a face dinshi ta hanyar dan murmushi daya saki and da yawa daga cikinsu was like"wow!..ashe haka smile ke mishi kyau shiyasa yakeda tsada a wurinshi?.."shidai bai sake ce musu komai ba har suka juya zasu fita...kasa hakura yayi ya dan dakatar dasu da fadin"are u sure gaba dayanku ne nan?.."wata daga cikinsu that is already crushing him tace"no sir akwai guda daya batazo ba..tana hostel batada lafia"..kanshi kawai ya iya gyada musu nan suka juya suka fita...mikewa shima yayi ya fita a office din cikin ranshi yana ayyana yanda zaiyi da yarinyar nan duk ya hadu da ita...baisan meyasa duk ta tsaya mishi a rai ba...sam ya kasa mancewa da ita duk kuma kokarin da yakeyi na ganin yayi hakan...deep down yasan ko rantsuwa yayi tana sane taki zuwa baizaiyi kaffara ba cox he is 100%sure kin fitowa tayi sbd gudun haduwa dashi...shi kanshi kuma baisan why yakeson punishing nata kan laifin da bashi ta aikawa ba...ba kuma shi zai samu matsala ba idan ma aljanu sun shafeta as result of abun da tayi...sam ya kasa gane kanshi these days...abubuwanda he don’t use to care about sun fara damunshi yanxu...sam da ba haka yake ba...yana ganin ko a titi zai ganta tana rawa bai zama lallai ya dameshi ba amma yanxu a cikin hostel dinsu ne and abun ya dameshi fiyeda tunanin mai karatu...yana karasowa ya bude mota ya shiga driver yaja ta suka fita a harabar makarantan. Wahegari saida yayi da gaske snn ya iya hana kanshi zuwa college din don ji yake kawai idan bai ganya yaci mutuncinta ba bazai samu nutsuwa ba...amma haka ya hakura sbd gudun tarin tambayoyin da zaisha wajen Nur wanda for sure yasan bayada amsarsu...tun daga wnn ranan bai sake shigowa college ba sai ranan Thursday that is normal days daya saba shiga dama...around seven something motanshi ya shigo premises din and yana shigowa yayi nasarar ganinta zaune kan wasu chairs itada qawarta da wani da yake tunanin kilan saurayinta ne shima tunda yaga ba wai kamun kai gareta ba...daga ganin yanda suke mgn suna daria zakasan hira ba karamin dadi yayi musu b...sai Allah Allah yake suyi parking sbd ya tura a kirata yanda bata isa tayi escaping ba amma kamar ance ta juya idonta ya sauka kan motanda a kallon farko ta gane nashi ne...bata tabbatar da cewa nashin bane saida ya wuce ta gabansu taga plate number din Dr.Bobby 5 ai batasan time data mike daga wurin ta nufi classes dinsu da wani mahaukacin sauri ba kaman zata tashi sama...ta jikin mirror yake kallonta yaga yanda take ta faman sauri har tana hadawa da gudu kawai sai ya girgiza kai yana kallonta...kafin su karasa parking ya bude mota ya fito har ta shige ciki dan haka direct kawai ya wuce office dinshi...11 da wani abu ya samu call daga hospital that ana buqatarshi da gaggawa haka ya fita ba don yanaso ba driver ya daukeshi zuwa hospital din...emergency theater suka shiga and basu suka fito ba sai around 1...sallah kawai ya tsaya yayi masjid dake nan asibitin snn ya shiga mota driver yaja suka dauki hanyan college. Daya da mintina bakwai Motan daddy ya shigo cikin haraban makarantan...wani taro ne ya kawoshi kano shine yaga before ya wuce Gombe ya kamata yazo ya ganta dan ya kwana biyu bai zo ba..ko sanar da ita zuwanshi baiyi ba sbd yanaso yaga how she’s doing a school din...dama duk zai zo bai ta6a sanar mata ba saidai kawai ta ganshi kwatsam yazo...dagashi sai driver dinshi da security guda daya...bayan sunyi parking yace da security yaje bakin gate ya tambayi masu gadi ko zasu santa dan yanata kiran wayanta bai shiga gashi kuma baiga student ko daya a premises din ba ba mamaki suna clesses dinsu...da hanzari security ya tafi bakin gate kamar yanda aka umarce shi ya tambaya ko sunsan Aysha nan sukace mai basu santa ba and abun bai sani ba shine idan zai shekara yana tambayan Aysha zasuce mishi basu santa ba because ba wanda ya santa da Aysha a cikinsu...ko yan class dinsu mantawa suke sunanta Aysha sbd yanda sunan ya 6ace 6att kowa yake kiranta da Lamido...komawa yayi ya sanar dashi sunce basu ganeta ba dan haka daddy ya bude mota ya fito yana karema premises din kallo still trying her number wai zaici saa ya sameta yanxu...daidai wnn lokacin motan Bobby ya shigo haraban school din...gefen motan daddy driver yayi parking nashi snn ya bude mishi mota ya fito...tun daga cikin mota yake kallon wnn mutumi that kana ganinshi zaka gane babban mutum ne kuma mai dattako yana tunanin me yazoyi college dinshi kuma?...har zai wuce office dinshi yaga kaman bai dace ba..bisa ga dukkan alamu mutumin wani yake nema duba da yanda yaga yanata kokarin kiran waya kuma bata shiga...juyawa yayi zuwa inda suke yana tafiya a nutse kaman yanda ya saba har ya karasa inda suke...fuska dauke da murmushi dan haka nan yaji mutumin ya mishi wani irin kwarjini yace"sorry to interrupt sir..are u looking for someone?.."murmushi daddy ya saki tareda mika mashi hannu alaman suyi musabiha yace"yarinyata nazo gani wlh kuma inata kiran wayanta baya shiga"...Bobby da yaji nauyin ya bashi hannu su gaisa yace"if babu damuwa mu karasa office dina sai insa a nemo maka ita"..daddy ya fadada smile dinshi lokaci daya yaji yaron ya kwanta mishi a rai yace"ba damuwa muje"...Bobby ya wuce gaba shi kuma yabishi baya..security dinshi zai biyosu yayi mishi alaman he should stay...suna zuwa office din ya bude suka shiga still yana murmushi ya nuna mishi sofa yace"Bismillah sir"..ba musu daddy ya zauna yana sakejin yaron na burgeshi sosai...shi kallon sani ma yake mishi sai yaga kaman ya ta6a ganinshi a wani waje...Bobby ya bude fridge ya dauko ruwa da lemo ya ajiye mishi kan table snn ya zagaya seat dinshi ya zauna ya dauki landline dinshi yace"ya sunan yarinyar da za’a kira sir?.."daddy bai maji me yace ba as hankalinshi gaba daya yana ga katon picture din Bobby dake manne a wall din office din...fuskanshi dauke da suprise look ya juya yana kallonshi yace"u mean kai son din Col Attahir ne?.."Bobby yayi shiru yana kallonshi da mamaki shima...daddy ya sake juyawa ya kalli pic din snn ya kuma juyowa gareshi har yanxun cikeda mamaki yace"ina nufin Col Attahir Waziri na Gombe..are u his son?.."a hankali Bobby ya gyada mishi kai alaman yes...wani irin bright smile ya gani shimfide kan fuskan daddy wanda ke nuni tsantsan farin cikin haduwa dashi...juyawa ya sakeyi ya kalli hoton then back to Bobby kafin yace"ikon Allah...kasan mahaifinka shine sanadiyyar matakin da nake kai a yanxu?..he was a very good and generous man..my mentor...har yanxun banida wani abun kwaikwayo kamanshi...he was a very kind hearted person..a very responsible person.."ya karasa mgnr da wnn bright smile kan face dinshi sai kuma eyes dinshi dake nuni da tsananin kewarshi da yaji sakamakon tunawa da mutuwarshi da yayi...Bobby dai mutuwan zaune yayi sai kallonshi kawai yakeyi kaman statue...wani irin qima yaji mutumin ya sakeyi a idanunshi...kawai yaji yana sonshi sbd wnn maganganu da yayi kan dad dinshi...a rayuwa yanason ya hadu da mutumin da yasan babanshi ba don komai ba sai don kawai yayita bashi labarinshi yanajin dadi amma banda familyn dad din nashi...su wadan nan ko zasuyi me bazai iya yadda wani alaqa ya sake shiga tsakaninshi dasu ba...bayan few minutes of silence daddy yacigaba da cewa"no wonder tun a kallon farko da nayi maka naga kaman na sanka...its because kana kama da dad dinka sosai and ba iya kamanninshi kawai ka dauko ba harda halayenshi...kawai daga gani na kaji ya kamata ka taimakamin har ka kawoni office dinka without knowing who i am and wnn na daya daga cikin halayen mahaifinka...bai ta6a ganin wani na bukatar taimako bai taimaka mishi ba...ubangiji Allah ya jikanshi yasa yana aljannah"...Bobby ya lumshe ido sbd dadin addu’ar da yaji a hankali yace"Ameenn"...daddy ya zuba ruwa a cup yasha snn yace"kasan sa akwai alaqa ta sarauta tsakanin shi mahaifinmu Lamido da kakanka Waziri..wnn dalilin ne yasa dana fara aikin Custom aka hadani da mahaifin naka"...kallonshi kawai Bobby keyi yanajin dadin labarin...shi daddy yacigaba da fadin"kacigaba da irin wnn habit din yanada kyau kaji?..Allah ya maka albarka”...yana murmushi ya amsa da"Ameen..nagode sir"..daddy yace"no thanks a tsakaninmu...u are like a son to me"...sake murmusawa Bobby yayi yana shafa kanshi...tunda yake bai ta6a cin karo da mutumin da ya kwanta mishi a rai ba kaman wnn mutumin ba..da ganinshi mutumin kirki ne and he ha so much respect for him..baisan ko sbd yasan dad dinshi bane oho amma yaji yana ganin girmanshi sosai...saida ya sake daukan landline snn yace"Sir baka fadi sunan yarinyar ba"...murmushi daddy ya kuma saki yace"kaga har na manta da ita sbd tunowa da Mentor na da nayi...May his gentle soul continue resting in peace"..sake lumshe ido Bobby yayi tareda cewa"Ameen Ameen"..daddy yace"sunan yarinyar Lamido...Aysha Ahmad Lamido"...idanu a waje sosai Bobby ya dago yana kallonshi jin sunan daya ambata...he can’t believe wnn responsible mutumin shine zai haifi wnn fitinanniyar yarinyar...ganin irin kallon da yake mishi daddy yace"do u know her in any way?.."da sauri ya shiga girgiza kai yace"ah no sir..bari insa a nemota"...daga haka ya kira secretary dinshi using the landline...tana dauka yace tazo yana son ganinta...bayan ta shigo yace mata"did u know a girl called Lamido?.."secretary ta danyi shiru for the mean time kafin tace"yea na santa sir..mai kukan allura kou?.."banza yayi kaman baiji me tace ba yace"kije midwifery section ki nemota..tell her that her father is here waiting for her"..secretary ta amsa da"ohk sir"..snn ta juya ta fita daga office din...daddy ya bita da kallon jin tace mai kukan allura...knn hakan na nufin Aysha har a nan dinma kukan alluran take?..kawar da tought din yayi ya juya ga Bobby yace"kanada sister sumayya koh?.."gyada kai Bobby yayi yace"yes my elder sis"...murmushi daddy ya kuma saki yace"a lokacin bazan manta ba inajin sunanta a bakinshi...yanaji da kids dinshi sosai dan koda yaushe cikin mgnrku yake...and kanada brother mai sunan Waziri kou?.."nan ma kai ya sake dagawa yace"Sabeer"...daddy na cigaba da murmushi as old memories rush back yace"ina tunawa da sunanku ai..he was man of the people shiyasa duk na kasa dashi suke sonshi sosai"...gyada kai kawai Bobby yake yana murmushi...he doesn’t want the conversation to end. Secretary na fita kai tsaye midwifery section ta nufa kaman yanda yace mata...duk wanda ta tambaya Lamido zaice baisan inda ta tafi ba...har class dinsu taje bata nan and gaba daya yan class din suna ciki suna lectures ita kuma ba wanda yasan inda take...gajiya tayi da neman nata ta sauka kasa ta sake dubawa nan inda classes din Nurses yake amma ba Aysha ba alamarta...tana fita daga wurin ta hangota can bakin gate ta shigo makarantan hannunta niki niki da ledoji kaman wadda taje kasuwa...da sauri ta karasa inda take tace"kece Lamido koh?.."kai tsaye ta gyada mata kai alaman eh...secretary tace"kizo office Dr.Bobby na nemanki"...Aysha ta wara idanu kaman taga abun tsoro tace"what!..ce mishi kikayi kin ganni?.."secretary bata sake cewa komai ba ta juya tace"nidai na fada miki..idan kuma inje ince mishi baki zuwa ne toh"...da sauri tabi bayanta tana turo baki tace"muje..ai dai duk abunshi bazai gutsuri naman jikina yayi pepper soup dinshi yaci ba..iyaka ya balbaleni da masifa wnn kuma shi ya sani"...secretary dai tafiyarta tayi bata ma jin abunda take fada sbd ciki ciki tayi mgnr...saida ta fara ajiye kayan dake hannunta nan kofar office din nashi snn ta tura kofar a nutse ta shiga bayan ta gama hade rai wai sbd kar ma yaga fuskanta a sake yace zai rana mata hankali...bayan ta shiga ciki ta juya tareda closing kofar tayi taking one step forward kafin idonta ya hango mata wanda ke zaune cikin office din...zare idanu sosai tayi looking at him kaman taga dodo dan har ga Allah ta dauka gizo yake mata...hannu takai ta murza idanunta sosai tana tunanin kodai sbd batasa glasses dinta bane ta fara gane gane kuma...bata tabbatar da gaske shine nan zaune ba saida taji voice dinshi na fadin"ni ne nan zaune ba daydreaming kike ba"...lokaci daya gabanta yayi wani irin faduwa irin wanda bai ta6a yin irinshi ba...juyawa tayi ta kalli Bobby taga shima idonshi a kanta snn ta sake juyowa ga daddy still shima kallonta yake fuska daure...nan take wani irin zufa ya fara keto mata...taya akai daddy yazo office din mutumin nan?..bata samu amsan tambayan ta ba ta sakejin daddy yace"ni kike jira in taso in gaisheki knn kou?.."da sauri ta karasa inda yake ta zube kan guiwoyinta murya a matukar nutse tace"daddy..barka da z..."bai bari ta karasa ba ya katseta da fadin"daga ina kike?.."wani yawu ta hadiye da kyar zufa na kara keto mata tayi qundunbala tace"da..daga class nake"kallonta yakeyi rungume da hands dinshi yace"really?..wato daga class kike?.."kai ta sake dagawa tareda cewa"eh.."sai kuma tayi saurin girgiza kan ganin irin kallon da yake mata tace"aah.."fuskanshi ba alamun wasa yace"kince eh kince aah..wanne zan dauka knn?.."hawaye na cikowa idonta tace"daddy wlh abinci naje na siyo"..yace"abinchi?..bakuda cafeteria ne cikin makarantan?.."tana girgiza kai tace"da akwai"...yace"then menen dalilinda zaisaki fita waje siyo abinci lokacinda students yan uwanki suke class..wato har yanxu baki dena irin wnn halayen ba koh Aysha?..kina ganin kaman tunda kina nesa damu you are free to do duk abunda kikaga dama kou?.."da sauri ta shiga girgiza kai tana hawaye sosai tace"daddy wlh ba haka bane...dan Allah kayi hakuri wlh Billy ce batada lafia tace in siyo mata shine na fita amma ba haka nakeyi ba wlh"...kallonta kawai daddy keyi baice komai ba...Bobby kam kusan suman zaune yayi sbd mamaki...bai ta6a tunanin haka takejin tsoron mahaifinta ba dan hasali ma shi kallon sangartatta yake mata ashe abun ba haka bane..ya tabbata da sangarta ta ake babu yanda zaayi ta shiga tashin hankali haka sbd ganin babanta...wnn kadai ya isa ya nuna cewar sam ba sangartata akeyi a gida ba kilan dai kawai halinta ne haka...amma kam albasa batai halin ruwa ba...jin kukanta ya fara cika office din daddy yace"ke denamin kuka a nana..ai bakisan da kukan ba kike aikata abunda kikaga dama sbd kinga bama ganinki kou?.."girgiza kai kawai takeyi tana kokari tsayar da kukan nata ko uffan ta kasa cewa...a dan fusace yace"bazakiyi shirun ba knn"...tun kafin ya rufe baki tayi diff kaman anyi ruwan sama an dauke...still fuskanshi a daure yace"ina Bilkisun take?.."da sauri tace"tana hostel.."yace"kun kaita asibiti ne?.."ta gyada kai tace"da safe muka kawota..an bata drugs da injections yace inshaAllah zuwa gobe zataji sauki"...gyada kanshi yayi alaman ya gamsu kafin ya sake dan hade ranshi yace"idan kin koma ki hadani da ita awaya and wlh wlh Aysha idan kika sake na gani ko naji labarin kin aikata abunda bashi kenan ba a cikin makarantan nan ko a waje Allah sai kinyi mamakin matakin da zan dauka a kanki tunda na fuskanci har yanxu akwai sauran rashin ji a tare dake..just dare me kiga abunda zai biyo baya"..kai a kasa taba matsar kwalla tace"inshaAllah zan kiyaye daddy..kayi hakuri"..baice mata komai ba ya juya yana kallon Bobby da yayi relaxing kan seat dinshi yana kallon su kaman movie..kawai mamakin yanda such a responsible and reasonable person kamanshi zai haifi tantiriyar yarinya kamar Lamido...ga dukkan alamu kuma yana iya bakin kokari kan tarbiyyarta kunnen qashi ne kawai Allah ya hore mata...muryan daddy ya dawo dashi daga duniar daya tafi da yace"son alfarma nake nema a wajenka"...wnn karon Aysha ce mai mamakin sbd sunan da taji daddy ya kirashi dashi"son dai?.."ta fada cikin ranta...murmushi Bobby ya saki cikeda girmamawa yace"ai babu alfarma tsakanimu sir..kawai ka fadi buqatarka"...shima daddy ya saki smile din jin dadi snn ya nuna Aysha da har yanxu ke zaune kan guiwoyinta yace"so nake kasamin ido a kanta plss..tanada fitina sosai..she is so stubborn that saida mahaifi na yasa baki before in amince ta taho karatu wani garin..batajin mgn sam kuma tun tana karamarta haka take...na yadda da tarbiyyarka shiyasa zan dora wnn responsibility din a kanka and inada tabbacin u can do it...i want u to put eyes on her idan kaga zata aikata abunda ba daidai ba kayi stopping dinta snn duk lokacinda kace tayi wani abu batayi ba just give me a call zakaga hukuncin da zanyi mata..i hope u can do that for me"...gyda kai Bobby yayi yace"inshaAllah sir"...murmushi daddy ya kara saki tareda mikewa ya isa gaban table dinshi ya mika mishi hannunshi yana cewa"thank u so much son..ubangiji Allah jikan mahaifinka"...Bobby da kunya ya hanashi mika nashi hannun yace"Ameen sir"...kamo hannun nashi dady yayi tareda shaking da nashi still smiling yace"we’ve already became family so meye na makale hannun?.."murmushin dai ya kara saki kanshi kasa ya kasa hada ido dashi...hakan da yayi ya sake burge daddy sosai ya kuma tabbatar da cewa ya damka amanar Aysha a hannun daya dace domin yasan har abada jinin Attahir bazai ta6a kasancewa bata gari ba..ya aminta da tarbiyyar yaron dari bisa dari...bayan ya saki hannun nashi ya zari card dinshi daga aljihu ya ajiey kan table dinshi tareda fadin"here is my card ka kirani da wuri sbd inyi saving numberka"..Bobby ya dauki card din yana fadin"InshaAllah sir..thank u so much"..daddy yace"always welcome son..will like to meet u again"...yace"inshaAllah Sir..Allah ya tsare"..daddy ya amsa da"Ameen"..kafin ya fita daga office din...hajia Aisha kuwa suma ne kawai batayi ba tsabar mamaki...har yanxu ta kasa fahimtan ta inda wnn sabon alaqa ya 6ullo tsakanin daddy da inyamurin mutumin nan..sam hakan bai gamsheta bane..dr Bobbyn da ba kaunarta yake ba shine yanxu zaa ba amanarta aikam tasan ta gama yawo..takura dai iri iri zata sha a wurinshi kuma batada bakin complain tunda umarnin mahaifinta ne...ficewa tayi itama yabi bayan daddy...yana dab da shiga mota ta cimmasa dan haka ya dakata tareda juyawa gareta ya zaro kudi masu yawa daga aljihun babban riganshi yayi dividing kudin into two tareda mika mata daya yace"ga naki"...ta amsa tana godia snn ya sake bata dayan yace"wnn kuma na Bilkisu..saura kuma ki bari inji labarin ya saki ko ya hanaki wani abun kinki yi zakiga yanda zanyi dake"...kasa cewa komai tayi kanta kasa...security dinshi dake tsaye ya nunama ya dauko mashi wani abu a mota nan da nan ya bude motan ya dauko wani bag mai kyau ya mika mashi...daddy ya amsa tareda mikawa Aysha dake tsaye kai a kasa yana cewa"take.."da sauri tasa hannu biyu ta karba tareda dan risinawa tace"Allah ya saka da alkhairi "..a hankali yace"Ameen"..snn ya shiga cikin mota...ta matsa jikin window tana dubanshi tace"daddy Allah ya kiyaye hanya..ina gaida su Ammi"..yace"zasuji inshaAllah..ki koma ciki"...a hankali tace"toh.."tareda barin wurin...tana kallo motan nashi har ya fita daga makarantan ta sauki ajiyar zuciya tareda dafe kirjinta da har yanxu bai dena bugawa ba...taso komawa ta dauko kayan data bari a kofar office dinshi amma bazata je ba haka kawai yayi ram da ita a wajen...yanda yake neman tan nan tasan ai idan suka hadu rashin mutunchi ne zata sashi musamman yanxu da daddy yace wai yasa mata ido...wucewa tayi class dinsu cikin ranta tana ayyana wai ita daddy zaice a sa mata ido sai kace wadda take aikata wani aikin ashsha. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 21 Tun daga wnn ranan bata sake yadda ta hadu dashi ba har tsahon sati guda shima kuma bai nemeta ba...gashi duk sukayi waya da daddy sai jaddada mata tayi mishi biyayya and ta ringa zuwa tana gaisheshi time to time ta amsa mishi ai already tana zuwa...gaba daya haushi takeji that daddy zai dinga hadata da wnn mutumin...ko a inama ya sanshi har ya yadda dashi haka oho?. Yau Thursday suna zaune class dinsu tana koya ma wasu assignment kiran daddy ya shigo wayanta...excusing kanta tayi tareda daukan wayan tana gaisheshi..bayan ya amsa yace mata"where are u now?.."tace"ina class daddy"..yace"kinje kin gaida Attahir?.."shiru tayi tanaso ta gane waye Attahir yace"ur proprietor"...da sauri tace"eh..aah banje ba..amma zanje sai mun tashi daga class"..yace"to idan kinje ki hadani dashi a waya"..bai jira cewarta ba taji ya kashe wayan...tabi wayan nata da kallo tana mamakin abunda yace..tadai san bai yiwuwa ace har yanxu Bobby bai kirashi don akan idonta ranar yace yanaso ya kirashi a wuri so dole yanada number dinshi amma why zaice ta hadasu a waya?.."so yake ya tabbatar da kina zuwa gaidashi ko bakiyi"..cewar wani 6angare na zuciyarta..ta kuwa yi na’am da haka don dai tasan zaiyi wahala ace kiran wayanshi yayi bai shiga ba...komawa tayi suka karasa assignment din kafin lecturer dinsu ya shigo ta nufi office dinshi don tasan idan bata hadasu kamar yanda daddyn yace ba then zasu samu matsala gagaruma...tana isa bakin office dinshi kafin ta shiga secretary dinshi ta bita da wani irin kallo tace"wai ke me kike zuwa yi office din nan ne?.."wani kallo Aysha tabita dashi irin na rainin hankali kafin taja tsaki ta wuce...da sauri ta mike daga inda take tana fadin"ki bari a fada sanar dashi zuwanki kafin ki shiga"...ai ko tsayawa sauraronta batayi ba ta banka cikin office din itama tabita da sauri...tana shigowa secretary din itama ta shigo da surinta...Bobby dake zaune seat dinshi ya daga idanu yana kallonsu..ganin yanda kowacce ke huci yace"bakuda hankali ne?..why zaku shigomin office kai tsaye haka without my permission?.."da sauri secretary dinshi tace"Sir cewa nayi ta jira in fada maka idan kace ta shiga sai ta shigo shine taki tsayawa ta shigo ciki"..juyawa yayi yana kallon Aysha data wani hade rai yace"kan wane dalili zaki shigomin office kai tsaye?..are u mad?.."sake daure fuska tayi tana turo baki tace"raina min hankali zatayi shine kawai na shigo"...tsaki ya saki tareda juyawa ga secretary dinshi yace mata"u can leave"...ba musu ta juya ta fita daga office din...shi kuma ya maida dubanshi gareta fuskanshi cunkus yace"wato ke bazakiyi hankali ba kou?..duk wani abu da bai kamata ba bazaki dena yi ba kou?.."turo baki ta sakeyi tace"Sir ni me nayi?.."kallonta kawai yake yace"oh tambayana ma kike?..to bari na kira mahaifinki na sanar dashi shi sai kiyi masa bayani"...ai tun kafin ya karasa ta karasa kusa dashi da sauri tace"aa dan Allah kayi ban karawa"..harara ya watsa mata bai sake cewa komai ba...ita kuma taja kujera zata zauna yayi saurin katseta da fadin"who asked u to sit?.."ta wani marairaice tace"Sir dan Allah..daddy ne yace in hadaku a waya"...still bai sake cewa komai ba ita kuma ta zauna snn ta fiddo wayanta tayi dialing number daddy...yana fara ringing tasa a speaker snn ta mika mishi...ya kar6a ya wani 6alla mata harara tareda cirewa daga speaker snn yakai kunnenshi..tana ganin yanda har wani sunkuyar dakai yake yayinda suke gaisawa da daddyn...ta lura he have so much respect for him and hakan ko kadan bai burgeta ba don gani take duk ladabin kura ne...saida suka kammala wayan snn ya mika mata abarta yana hararanta yace"wato ce masa kikai kina zuwa gaisheni koh.."sake turo baki tayi tace"ai daga yanxu zan fara zuwa"...ya wani ta6e baki yace"kiyi zamanki bana bukata..now tashi ki bar min office"...mikewa tayi ta sake hade rai fa fita cikin ranta tana ayyana shegen son office inda kasan kanshi aka fara zaman office...komai sai ya wani ce office din,my office sai kace wani yace ba office dinshi bane...batafi 10 mins da fita ba Nur ya shigo office din...ya karasa ciki ya zauna yana duban abokin nashi yace"maza yane?.."Bobby yace"normal..kwana biyu..ya aikin"..yace"aiki fine yanxu ma mgnrshi ne ya kawoni"...Bobby yace"umhum inajinka"..."kan batun Festivities din nan ne"...gyara zama Bobby yayi before saying"ina sane dashi ai..next week za’a fara kou?.."Nur yace"yea and yanxun nayi receiving message daga social department that suna buqatar additional money for the preparations"...buda hannu Bobby yayi yace"then ka basu mana"...Nur yace"dama in fara mgn da kai ne..if kace a basu sai a basu"...wani kallo Bobby ya shiga binshi dashi kafin yace"seriously?..haka ka daukeni dama?..kenan har yanxun ban wuce wnn matsayin a wurinka ba?.."shafa kai Nur yayi yace"sam ba haka bane..kawai dai naga bai kamata in fara amsan kudi without permission dinka ba"..yana rufe baki Bobby yace"gaskia bakayi min adalci ba idan har yanxu baka bar irin wnn tunanin ba..now tashi ka bar min office"...dan murmushi Nur ya saki saying"abun hadda kora kuma?.."Bobby yace"yes tunda baka daukeni bakin komai ba ai banga amfanin zamanka nan ba so kindly leave"..gyara zama Nur yayi hade da fadin"to kayi hakuri ya wuce"...harara ya sake 6alla mishi shi kuma yasa daria yace"da gaske bazan karaba mana..sorry". Ranan Friday akayi pasting result dinsu na first semester wurin ya cika fam da jama’a kowa na kokarin duba nashi wanda sukayi passing mata murna while masu resitting suna jimami...Aysha dai na kwance a hostel dan ko fitowa batayi ba sai Billy ce tayi kokarin duba musu da taimakon Sa’eed sbd turereniya akeyi sosai a wurin...bayan ta samu fitowa daga hayaniyar ta samu waje ta zauna tareda dialing number dinta...cikin muryan bacci ta daga da fadin"Hello"..Billy tace"so u are still sleeping"..tace"eh mana ban dade ma da kwanciya ba"...cikin excitement Billy tace"anyi pasting results yanxun nan and gues what?.."a hankali tace mata"what?.."da sauri Billy tace"as usual ke kikayi overall..and this time around bestynki ma yayi abun kirki"...daria ta saki dukda baccin dake idonta tace"kema dai kinsan my besty is always intelligent kece dai kawai baki ganin haka"...ta6e baki Billy tace"oho ku kuka sani..am hanging up now"..da sauri Aysha tace"wait..baki fadamin naki ba ai"...wani murmushin Billy ta saki kafin tace"congratulations to me..inada 4.55"..tun kafin ta rufe baki Aysha ta saki wani ihu tana fadin"are u serious Billy?..gaskia am very happy bari in kira besty this calls for celebration"...murmushi Billy ta kara saki tana jin yanda take farin ciki ko nata result din bataima wnn murnan ba koda yake idan da sabo ai ya kamata abun ya zaman mata jiki dan tun shigowarsu college din bata ta6a scoring below 5 points ba...kafin ma ta jira jin ta bakinta tayi hanging kiran and for sure tasan bestyn nata zata kira kamar yanda ta fada. Bobby da bai samu shigowa college din da wuri ba sai after jumu’at prayer motanshi na shigowa ya hangi crowd din dake wajen sai ya tuna ashefa Nur ya fada mishi cewa yau zasu kafe result...daga dan gaban inda aka kafe result din ya hango katon banner da suke kafewa duk shekara na best students of the year kowa da grade dinshi da department sai kuma picture dinshi a jiki...driver bai karasa inda ya kamata yayi parking ba yace ya saukeshi nan wurin..ba musu yayi parking daga gefe kafin ma yazo bude mishi kofan ya bude ya fita...inda aka manna babban banner ya nufa...haka nan yaji yanason ganin da akwaita a jiki ko babu...aikam yana karasa yayi ido biyu da pic dinta tana sanye da uniform da glasses dinta a ido...qasan pic din nata ya kalla baisan time daya wara idanu yana sake kallon points din nata ba...gani yake kaman karya ne bazata iya scoring wnn points din on her own ba...hoton su biyu ne kadai a jikin banner daga ita sai Sa’eed da yayi overall a Nursing department...dukda baisan yaron ba amma ya jinjina mashi sosai dan points ba kadan ba shima yakeda...ita kuwa nata har yanxun bai gama yadda ita taciyoshi da kanta ba...bayan ya gama kallon ya shiga takawa a nutse zuwa office dinshi saidai kafin yakai office din kusan mutum uku sukazo suna gaisawa dashi snn suka nufi office din tare...deep down wani irin feeling yakeji...like gaba daya sai baiji dadin ganinta da yayi jikin banner ba...not because yana mata bakin ciki but because yana ganin yin hakan kaman talla ne akeyi da ‘ya’yan mutane tunda yasan yanxu duk wanda ya shigo college din sai ya gani and hakan will make her popular da bai zama lallai parent inta su so haka ba..especially ita da dama ba wani cikakken nutsuwa gareta ba...ya fuskanci kanta na rawa shiyasa ko mahaifinta baya sassauta mata...har ya isa office dinshi bai bar tunanin ba and yanaso yayi ma Nur mgnr kuma yanajin tsoro kar yazo yayi misquoting dinshi amma seriously baiji dadi ba sam...sai yakejin kaman yaje ya yageta daga wurin amma ba hali...hakura yayi da yima Nur mgnr saidai ya kudirce a rai kafin next year zai samu yayi mgn dashi kawai a hakura da banner ma gaba daya...sam baiga amfanin yin hakan ba...dukda ba yanxu aka fara ba amma wnn karon kam abun baiyi mashi dadi ba. Shirye shirye sukeyi sosai for the upcoming Annual Festival da ake gabatarwa cikin college din every year...shiri ba daga 6angaren students ba ba kuma daga 6angaren social department ba...week guda suke cinyewa suna abu guda and wnn year din ma kaman ko wacce shekara sun gama tsara duk yanda festivities din zasu kasance...ranan farko daya kama Monday zasu gabatar da dramas da wasu daga cikin students din zasu gabatar..da akwai English drama sai Hausa drama...rana na biyu kuma zasuyi cultural activities rana na uku ne ake inviting mawaqa daban daban suzo suyi performing a wurin sai rana na hudu wich is Thursday zasuyi Public Lecture and Fun Walk ma’ana za’ayi picking one among cututtuka da suke damun mutane a wnn lokacin sai daga cikin doctors da ake inviting zuwa wurin suyi fashin baqi akan cutan bayan an gama sai su fita fun walk dasu police bands da masu dj suna tafe suna waqa da rawa zasubi ta cikin gari har zuwa state road snn su dawo college din a qafa...ranan Friday wich is the last day of the festival sukeyin sport activities such football,volley ball,table tennis,snooker,basket ball dama sauran wasanni na maza dana mata. Ranan Monday wich is the first day if the festival wurin 10 na safe auditorium dinsu na cike da students,doctors da kuma manya manyan baqi from every angle na kano da akayi inviting dinsu...kowa yana zaune a respective wurin da aka tanadar musu...mike na hannun mc yanata welcoming baqi tareda sanarwa cewan a jira wanda zasu gabatar da drama zasu bayyana in few minutes time...daga can waje masu yin draman ne a tsatsaye suna mgn da wani daga cikin organizers na festivals din...ba anko sukayi ba amma kowa cikin yayi kyau in his own way...saida ya gama musu karin bayani kan abunda zasuyi snn yace su shiga audit din...suka jera kansu a layi snn dj yasa musu waqa suka fara shiga wurin...Aysha na tsaye a gaba tana rikeda katon sign board da aka rubuta day 1 English and Hausa Drama...suna shigowa wurin ya kaure da sowa da tafi kowa sun burgeshi...Dr.Bobby dake zaune inda aka tanada domin shi a hankali ya dago idanunshi ya kallesu...as always idanunshi ita suka fara hango mishi...tana sanye cikin riga da straight skirt na atampa red da touches din black leaves a jiki...ta daura dankwalinta irin daurin da ake cewa Zara Buhari ta fito da gashinta ta qasan daurin snn ta kalmasheshi ya tsaya a wuyanta...daga bayan skirt din nata an dan tsagashi kadan ta kasa sbd yayi mata dadin tafia...takalmin kafanta flat ne sosai black sai veil dinta da tasa a kafadanta shima black...sai wrist watch da dankunnenta suma black...batasa sarqa ba dan haka fair wuyanta yana nan sai daukan ido yake...a hankali take takawa tana rikeda sign board a hannunta sai murmushi take dimples dinta na fitowa...wani irin abu yaji ya taso tun daga kwakwalwarshi yazo ya tokare mishi maqogaro shi bai tafi ba kuma shi matsa ya bashi sararin maqogaron ba...tunda yake bai ta6a tsintar kanshi cikin 6acin rai irin wnn ba..har wani zafi yaji yana rufeshi duk kuwa da sanyin ac dake wurin...lokaci daya kanshi yayi wani mugun sarawa kaman zai tarwatse..har yanxun kuma ya kasa dauke idonshi daga gareta har suka karasa suka zauna...lumshe idanunshi yayi yana karanta innalillahi a cikin ranshi wai ko zai samu sassauci...kai tsaye kuma yace ga abunda ke damunshi bazai iya ba dan shi kanshi bazaice ga dalilin wnn sudden change din nashi ba...sam baisan yaya zai misaltashi ba...kokari yayi sosai yayi kokarin danne abunda ke taso mishi ganin har za’a fara taron...yana kallo aka fara kiran sunan wanda zasuyi draman kawai ya runtse ido yana addu’a Allah yasa babu ita a ciki saidai kamar jiran addu’an nashi akeyi yaji mc na kiran "Aisha Ahmad Lamido"...sake runste idanun yayi yanajin wnn kuncin da yaketa kokarin 6oyewa yana sake neman hanyar dazai fito amma bai bashi dama ba dan kara dakewa yayi sosai wnn karon har yana dan muzurai snn ya bude idon...baisan ko shi yake kai idanunshi gareta ko kuma idanun ne ke kai kansu gareta ba dan yanxun ma ita ya sake gani bayan ya bude idon...karasawa sukayi suka zauna inda aka tanada domin yin draman...acting zasuyi itada Sa’eed matsayin mata da miji Billy kuma kishiyarta a cikin sauran kuma akwai yara snn akwai set of another couple da dai sauransu...cikin kwarewa da nutsuwa suka fara gabatar da draman nasu na English knn...wurin sai yayi tsit banda voices dinsu ba abunda akeji...gaba daya sun saki jiki suna acting dinsu sosai dan babu wanda zai gani yayi tunanin ba gaske bane sai wanda ya sani...dama kuma sunyi rehearsal sosai shiyasa basu samu wani problem ba...Bobby kuwa tunda yake bai ta6a sanin da akwai kunchi irin wnn yakeji a yanxu ba...kallon yanda suke acting itada Sa’eed kadai yasa yaji kaman zazzabi na neman kamashi...baisan meyasa yake feeling what he’s feeling ba...baisan why zai damu da rayuwar yarinyar nan ba..."sbd amanarta da mahaifinta ya baka"..cewar wani sashe na zuciyarshi...babu wata wata kuwa yayi na’am da wnn amsa don yasan da gaske kuwa ba abunda ya hadashi da ita bayan wnn...da wnn amsa na zuciyarshi ya dan samu sauki kadan daga cikin abubuwanda ke damunshi...haka yacigaba da daurewa yana kallonsu har wani murmushin yake yakeyi sbd kar mutane su dago halin da yake ciki...draman nasu ya dauki kusan one hour kafin su gama...wanda zasu gabatar da na Hausa akace su zama ready kafin mc yacigaba da surutanshi...sauran kuwa tafi aka shigayi musu sosai dan ba wanda basu qayatar ba a wurin Bobby kam shi kadai yasan halinda yake ciki...bayan lokaci mai tsayi masu draman Hausa suka shigo and to his biggest suprise wnn karon ma da ita a ciki...lokaci guda face dinshi ya sauya yana kokarin mance jarumtar da yace zai nuna...wnn karon kuma matsayin budurwar wani ta fito hakan kuma ya 6ata masa rai fiyeda tunaninshi...haka nan ya sake daurewa ya kalla har suka gama amma fa kafin a gama ya saki tsaki yafi cikin carbi...6acin ranshi kuwa ya ninka na dazu ninki ba ninki...gaba daya yaji zaman wurin ya gallabeshi burinshi kawai a tashi ya samu yarinyar can ya zabga mata rashin mutunchi...kwata kwata baisan dalilinda yasa bayason ganinta cikin irin wadan nan abubuwan ba...bayan sun gama masu jawabi duk suka tayi sukayi kayansu...wanda zasu bada kyauta ma duk suka bayar and Lamido na daya daga cikin wanda suka samu kyautar 50k da wani attajirin mutumi ya bayar...ran Bobby idan sun kai dubu duk a 6ace suke...ji yake inama yanada hali ya kar6e kudin daga hannunta gaba daya sai yaga ta gidan uban da zatayi amfani dashi dan yaga sai wani fara’a take tana jujjuya ido ita bata yadda ba celebrity...InShot har aka tashi daga wajen Bobby baisan ina kanshi yakeba...a zafafe ya koma office dinshi ya dauki waya da niyyan kiran secretary dinshi tasa a nemo mashi ita nan take kuma wani tunani yazo masa..."to idan na kirta ince mata me?.."ya fada a fili kaman he’s talking to someone...nan take kuma ya shiga girgiza kai yana fadin"no yanxu idan na fadi wani mgn tana iya misquoting dina ma tunda ba hankali gareta ba"...ya sake fadama kanshi...can kuma yace"amma ai sbd babanta zanyi hakan kou?.."yayi shiru kaman yana sauraran amsan da zuciyarshi zai bashi kafin yace"No I won’t talk to her...wai ma ina ruwana da ita taje taita haukanta mana is not as if i care"...ya fada yana daddaure face dinshi kaman tana zaune nan kusa dashi...da wnn shawara yayi amfani don bai kiratan ba a cewarshi wai baison raini...haka yayi dakon bakin cikin daya kwasa ya kaishi gida su Mummy sukaita aikin fama.😹 The next day kasa fitama yayi da wuri sbd tunanin abunda zuwan nashi zai haifar...yadai san a yanda take da shegen rawar kai yanda tayi performing a komai na jiya yau din ma zaiyi wahala idan batayi performing ba..shi kuma baisan meyasa yakejin abunda yakeji ba and Allah ya sani bazai iya kiranta ya hanata ba sbd kar tayi tunanin wani abun daban...da yanada ikon hana kanshi jin abunda yakeji da ya aikata hakan wlh ko don ya samawa kanshi salama amma bayada damar hakan...wnn dalilin yasa bai samu fitowa ba har saida yaga Nur ya fara kiranshi a waya and yasannshi da shegen naci haka zaiyita jera mishi kira idan har ba fitan yayi ba. Wani daki ne kusada auditorium dinsu inda daya wanda zasuyi performing suke ciki kowa yana karasa shiryawa...cultural dance suka shirya na Hausa,Fulani,igbo da kuma yoruba...and kowa daga cikinsu yana sanye cikin traditional attire na tribe da zaiyi representing...Lamido sarkin rawa zatay participating kusan gaba daya sbd ita koya musu rawar...da farko cewa tayi only Fulani da Yoruba zatayi sai hod na social department dinsu yace tayi participating gaba daya...Hausa Dance shine na farko dan haka koda mc ya kira iya wanda zasuyi hausa dance din ne suka fita daga dakin...as usual itace a gaba tana rikeda sign board kaman najiya saidai shi an rubuta day 2 cultural activities...wata kuma daga cikinsu ta rike wani da aka rubuta Hausa Dancers a jiki...waqa aka sakar musu ta hausa mai dadi yayinda suke shigowa cikin wurin...gaba dayansu suna sanye cikin normal dogon riga na atamparsu iri daya kowacce ta daura dankwalinta babu mai mayafai cikinsu...bayan sun karasa dance floor sun tsaya dj ya samo waqar hausa ta gargajiya yayi playing snn suka fara dancing...yau ma Bobby yana zaune mazauninshi na jiya and gaba daya tunda ya dora idonshi a kanta ya samu gagarumar matsala don komai nashi tsayawa yayi cak banda zafi ba abunda yakeji har cikin heart dinshi...lumshe idanunshi yayi yana salati dan abunda yake jin yaji jiya was nothing compared to what he is feeling right now...ji yake kaman yaje ya dauketa ya fita da ita daga wirin...haka nan yakejin ciwon kallon da mutanen wurin zasuyi mata tana rawa kamar batasan ciwon kanta ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 22 Ranshi bai sake 6aci ba saida yaji yanda gaba daya wurin ya kaure da tafi da sowa ana hailing dinsu..nan take yaji wani abu yazo ya tokare masa wuya...abun bai tsaya haka ba har liki mutanen da akayi inviting suka fara tasowa suna musu...bayan sun gama aka kara tafa musu sosai snn suka fita mc yacigaba da zance kafin next dancers su fito...dakin da suka shirya suka koma nan kuma suka fara arranging next dancers da zasu fita wato Yoruba Dancers...Lamido ce kadai tayi changing dress dinta zuwa na yoruba snn ta shiga cikin sauran suka koma ciki...suma dai da tafi da sowa akayi welcoming dinsu...Dr.Bobby yana zaune sam baiyi mamakin ganinta ba dan yasan dama hakan zai faru saidai bai saniba ko zai iya cigaba da jure abunda yakeji har su gama...yau dai ya rantse kome zai faru sai yayi mata mgn saidai idan taga dama misquoting din nashi he no longer cares..kawai haushi yakeji that gaba daya festival din ma ya fita daga kanshi kuma ya rasa wnn masifa da akan yarinya guda daya yana neman rasa sukuni da nutsuwarshi...suna isa dance floor aka sa musu waqan yoruba suka fara dancing...tafi da sowa kam sun shashi kaman ba gobe ga kuma ruwan kudi da suka samu daga mazauna wajen...lokacin da suka fito zasuyi na igbo Bobby kasa dauke ido yayi a kanta sai yaga kaman duk kayan da ta saka ba wanda yayi mata kyau kamansu...baisan ko don shi ya kasance igbo din ba amma kayan sun amsheta kaman itama igbo din ce...sai yaga kaman idon kowa na wurin a kanta yake sbd kyawunda tayi...bata sake bashi mamaki ba saida suka fara rawar...sunyi kokari matuka kaman dama inyamuran ne su...har yanxu kuma wnn zafin da yakeji yana nan wanda shine yasa gaba daya baya enjoying zaman wurin...Fulani dance shine na karshe and lokacinda suka shigo Bobby baki da hanci ya saki yana kallonta...tunda yake bai ta6a tsaywa ya kalleta irin na yau ba...tayi mishi kyau fiyeda yanda bakinshi zai iya fada..shi baima ta6a ganin kyanta kaman na yau ba tunda ya santa...haka akasa musu waqar fulani sukayi rawa sosai yanda ya kamata...and again an watsa musu naira snn wani babban mutumi dake wurin yayi musu kyautar kudi masu yawa...wani kuma daga cikin baqin shima yace ya bawa Aysha kyautan sabuwan waya Smsung Galaxy...farin ciki sosai takeyi har hakan ya kasa 6oyuwa dan sai murmushi takeyi Bobby kuma kamar bala’i idanunshi suna kanta yana ganin yanda dimples dinta ke fitowa as a result of smile da take...kasa cigaba da zaman wurin yayi kawai ya mike kaman wanda yakeda mutanen 6oye ya fita daga hall din kusan gaba daya mutane suka bishi da kallon mamaki...Nur ne ya mike da sauri yabishi a baya yana dab da shiga office dinshi ya iskeshi yace"Bob are u alright?..lafia naga ka tashi ana taro ko wani abun ya faru ne?.."juyawa yayi a fusace yana kallon Nur din snn ya nunashi yatsa yace"Fuck you"..daga hakaya bude office dinshi ya shiga ciki tareda bugo kofar da karfi...Nur mutuwan tsaye yayi a wurin yana kallonshi da mamaki...to meya sameshi haka?..kodai wani saga ciki guests din yayi mishi abu?..duk kokarinshi na yaga yayi pointing finger kan dalilin tasowarshi daga wurin ya kasa...baiyi yunkurin binshi cikin office dinba kawai ya juya tareda komawa can wurin still yana tunanin abunda akai mishi. Bobby na shiga office din ya zauna tareda dora kanshi kam table yana sauke numfashi da sauri kaman wanda yayi race...ko kusa baya son wnn sabon al’amari dake kokarin kunnowa cikin rayuwarshi..bayaso sam...baisan kan wane dalili zai dinga jin haka akan yarinyar da bai hada komai da itaba...shi tunda yake ma bai ta6a samun kanshi cikin yanayi irin wnn ba sai yanxu...gaba daya yarinyar nema take ta zame mishi tauraruwa mai wutsiya...ciwo yakeji sosai na raye rayen da taje tayi a bainan nasi..kuma sbd rashin sanin darajar kai ko dan mayafi bata yafa ba ballantana ayi mgnr hijab..gaba daya ya kasa gane wace irin yarinyace ita?..duk sai yaji kaman bai kyautawa babanta daya damka amanarta a hannunshi ba...kaman wanda akama allura ya mike da sauri ya fita daga office din...can inda audit din yake ya nufa yana shiga premises din wurin yaga Billy ta fito daga ciki tana waya tana ganinshi tayi saurin kashe wayan da takeyi tana kallonshi a tsorace...voice dinshi a cunkushe yace mata"where is ur friend?.."da sauri ta nuna auditorium din tana cewa"tana..ciki"..."go and call her"..ya fada hands dinshi zube cikin aljihu...ba musu Billy ta juya da sauri ta koma ciki...can tsakiyar dance floor ta hangota bayan sun gama performance dinsu aka sakar musu kida suka fara rawa gaba dayansu...haka Billy ta kutsa ta cikin mutane zuwa inda take kawai sai ji tayi ta kamo hannunta ta shiga janta...Lamido ta kwace hannunta tana turo baki tace"Billy rawa nakeyi dan Allah"...harara me kyau Billy ta watsa mata before tace"to kicigaba da rawa ai ga Proprietor can yana nemanki"..bata rufe baki ba Aysha ta zaro idanu tana fadin"dan girman Allah da gaske?.."kama hannunta Billy tayi suka fita daga wurin snn tace"Allah da gaske nake..yana can a waje fuskan nan kaman bai ta6a daria ba dan wlh har tsorata nayi dana kalleshi"...nan take hankalin Aysha ya fara tashi tace"na shiga uku meyasa yake nemana kuma?.."Billy tace"indai kinsan bakiyi laifin komai ba ki kwantar da hankalinki..kiyi addu’a kije ki sameshi in Allah ya yadda ba abunda zai miki"...girgiza kai kawai Aysha keyi tace"zo muje ki rakani dan Allah"...Billy ta kwalo idanu waje tana fadin"Ni?...rufamin asiri Lamido in mutu maza su kaini ba mata ba...haka nan inje yayita zazzaro idanun nan nashi yasani sakin fitsari a wando"...dukda tashin hankalin da take ciki saida mgnr Billy ya sata daria...sai kuma ta marairaice fuskanta tace"na shiga uku tsoron zuwa nakeyi wlh...nasan yanxu abu karami yake jira ya hadani da daddy"...Billy tace"ba fada miki inshaAllah ba komai kedai kawai kije kiji mezai fada idan ba so kike ki kara wani laifin ba"...jiki a sanyaye ta gyara mayafinta snn ta fita daga wajen...bata sameshi nan waje ba dan haka ta wuce office dinshi...tana shiga ya dago fuskanshi da yayi murtuk kaman na marasu imani kawai ya mika mata hannunshi murya a cushe yace"bani wayarki"...mika masa wayar tayi da sauri tareda sunkuyar da kanta kasa tana wasa da fingers dinta...shi kuma yana amsan wayan yasa digits dinshi snn yayi dialing...wayanshi dake ajiye kan table dinshi yayi ringing alaman kiran ya shigo snn yayi quitting call din tareda ajiye wayan a kusada nashi...Aysha dai har yanxun kanta na kasa tana kwararo mishi addu’a cikin zuciyarta...tsoronta Allah tsoronta kada ace wani laifin tayi ya kira daddy ya fada masa...shi kuwa kallonta yakeyi yanajin tamkar ya kwada mata mari don haushi..dubi dai yanda ta wani nustu a gabanshi kaman mutumiyar kirki amma dazu taje ta gama bayyanar da jikinta wa mutane suka kalla...ko rantsuwa yayi yasan da kyar babu wanda bata burgeba a cikin wadanda suke wajen...kawai ciwo yakeji that a gaban idonshi abun ya faru and he couldn’t do a thing...cikin muryan daya kusa sanyata fitsari yace"wato ke bakida hankali kou?..sbd bakisan ciwon kanki ba kikaje kina rawa gaban mutane kina musu tallan jikinki kou?.."dan dagowa tayi ta kalleshi kafin ta mayar da kan nata da sauri dan tsoro idanun ma suka bata...saida ta dan marairaice snn tace"tallan jikina kumah?.."a fusace yace"if u dare say another word a wurin saina kwada maki mari...tambayana ma kikeyi sbd bakida kunya kou?.."shiru tayi tana turo baki...yace"well let me call ur Father and tell him all you’ve been doing"..yana karasa mgnr ya dauki phone dinshi dake nan kan table ai batasan time din da ta kama hannun nashi ta rike gam ba sbd tsoro...cikeda tashin hankali tace"Sir dan Muhammadu rasulillahi kar ka kirashi..i beg of u please"..ta karasa mgnr hawaye ba zubowa kan cheeks dinta...Bobby dake kallon yanda ta rike mishi hannun yace"how dare you?.."sakin hannun nashi tayi da sauri tana cewa"am sorry...Sir dan girman Allah ka rufamin asiri karka fada wlh fada zaiyimin"...sake daukan wayan yayi yana searching contact din daddy yace"da kina tsoron fadan ai bazaki aikata abunda ba daidai ba"...wnn karon hannayenta ta hade waje daya in a pleading tone tace"Sir na rantse da Allah ban karawa kayi hakuri plss"...ajiye wayan yayi yana kallonta..dama baida intension din kira yayi haka ne kawai dan ya tsoratata tunda already yasan yanda take tsoron mahaifinta...idonshi a kanta yace"fadamin meyasa bakijin magana?.."tana cigaba da hawaye tace"am sorry"...yace"ba wnn na tambayeki ba..i said meyasa bakyajin mgn?..why kikeda fitina?.."shiru tayi tana goge hawayenta sai can kuma tace"nima ban saniba"...tsaki ya saki tareda daukan wayanta yana mika mata yace"leave my office immediately..and if u like gobema kizo kiyi abunda kikayi yau kiga idan ban sanar dashi ba"..kar6an wayan tayi tana turo baki ta juya ta ta fita daga office din..tana ganinta a waje ta sauke wani ajiyar zuciya a fili ta furta"kuma Allah ya isana wlh..inyamurin banza"...shi kuwa sai daga baya duk haushin kanshi yabi ya kamashi...wai ma ina ruwanshi da rayuwarta ne at the first place...mamakin kanshi yakeyi shi that ya tsani Fulani especially na Gombe amma wai shine har yake kokarin protecting yarinyar da yasan asalin ‘yar Gombe ce?..baisan ko don sbd mutuncin mahaifinta da yake gani bane...abu guda daya sani shine dukda kasancewar babanta bafulatani kuma na Gombe yana matukar ganin kima da darajarshi and shine mutum na farko daya faraji ya kwanta mishi a rai bayan sanin cewa shi din bafulatanin Gombe ne...kilan sbd kyawawan maganganun da yayi kan Dad dinshi ne amma maganan gaskia mutumin yayi mishi dari bisa dari...itama kuma ‘yar tashi yasan sbd mahaifinta yakejin abunda yakeji and nothing more. The next day which is Wednesday ranan ne ake inviting mawaqa from different states suzo suyi performing a makarantan...Bobby na kwance tun safe a daki ko parlor ya kasa fitowa...kawai jin jikinshi yakeyi wani iri that har yake tunanin kilan hakura zaiyi da shiga college din nan kawai...dukda yayi mata mgn jiya and yanada tabbacin ta tsorata sai yakejin kaman yayi zamanshi a gida or better still ya tafi Hospital dinshi kawai ba sai yaje ba balle yaga abunda zai 6ata mishi rai...haka yayita kwance a daki bai fito ba saida Mummy ta aiko a kirashi...yana saukowa daga gado ya fada bayi yayi wanka snn ya fito ya shirya kanshi cikin wata armless shirt da wando three qtr snn ya nufi parlor...parlon Mummy ya samesu zaune gaba daya as aunty sumy na gida itama ranan bataje aiki ba Miemie ma bataje sch ba sbd fever data kwana dashi ita kuma ilham tun 1 aka tashesu...karasawa yayi ciki ya zauna da igbo ya gaida Mummy itama ta amsa da igbo snn tayi adding da"yau baka fita ne naga har yanxu baka shirya ba?.."dan ta6e baki yayi yace"i just don’t feel like going out..i think zamana zanyi a gida in huta"...Aunty Sumy tace"aikam bai kamata kaki zuwa ba Bobby..remember it’s a Festival week and abune wanda yake taking place once in a year sai nakega kaman bai dace kaki zuwa ba ko don sbd guests dinku"...Mummy ma na gyada kai tace"sumayya gaskia ta fada Bobby"..shiru yayi cikin ranshi yana ayyana bazaku gane bane...abun kaman hadin baki kawai sukaji sallamr Nur a parlon...Bobby ya kulle ido tareda fadin"the fool is here..nasan yanxu ko banida intention din fita saina fita ko don nacinshi"...daria Mummy sa aunty sumy suka saka jin abunda yace...Nur daya karaso ciki ya zauna ya shiga gaisawa dasu Mummy shima cikin igbo...aunty sumy tace"wlh har mantawa nake Nur yanajin igbo sbd bai cikayi ba unlike abokinshi da mgn daya biyu sai ansa igbo a ciki"...murmushi Nur yayi yana shafa kanshi yace"wlh ni kaina ina manta inajin yaren aunty...gaba daya hausawa sun janyeni"...daria suka sake yi Mummy tana ai dole hausawa su janyeshi tunda yake zaune a kano...bayan sun gama Nur ya juya yana kallon Bobby kafin yayi mgn Bobbyn ya mike yana cewa"ba saika 6ata bakinka ba nasan meya kawoka..ka bani just 5 mins zan shirya in fito"...daria gaba daya suka kara sawa Bobby ya wuce flat dinshi...aunty sumy tace"Nuru kai kadaine maganin Bobby gashi tun kafin kayi mgn an tafi shiryawa"...dariyan shima yasaka yace"kinsanshi baya son naci ai..ni kuma indai inason yayi abu bana barinshi har saina samu abunda nakeso"...bayan 5 mins ya fito a shirye kaman yanda ya fada...Nur na ganinshi ya mike yana sallama dasu Mummy Ilham tace"uncle bobby inaso inje plss"..kallonta bobby yayi sai kuma yace"no kiyi hakuri sai gobe kuje tareda su aunty kinji"..makale shoulder dinta tayi tana fadin"oh oh inaso inje yau"...kallonta kawai yakeyi totally speechless..shi ba son zuwan nan nasu yakeba wlh..ko gobe da aunty sumy tace zasuje suji lecture da za’ayi ba so yakeyi ba...Nur da yaga tana shirin sakin musu kuka yace"zamuje dake baby don’t cry"...nan da nan ta washe bakinta tana tsallen murna..."uncle Nur"..yaji Miemie ta kira sunanshi...a hankali ta juya yana kallonta sai yaga tayi narai narai tana kallonshi...murmushi ya saki dan ya gane mgn take mishi a haka..so take taje itama and tana tsoron furtawa sbd Oga Bobby kada ya hana...saida ya dan saci kallon Bobbyn snn ya dubeta yace"kema zakije kou?.."daga mishi kai tayi da sauri..yace"to je dauko mayafinki"..da sauri ta mike zuwa dakinta ta dakko veil da phone dinta ta fito...Bobby da haushi ya isheshi ya bude baki zai fara masifa Mummy tace"don’t say anything plss..kuje dasu su gani ai ba dadewa zaayi ba"..gum ya maida bakin nashi ya tsuke ba tareda ya fadi abunda yayi niyya ba...sallama sukayi musu suka fita Bobby ya shiga motanshi tareda driver da kuma ilham shi kuma Nur ya dauki Miemie a nashi motan suka tafi. Tsaye take gaban mirror dinsu tanata kallon kanta kaman bata ta6a ganin mirror ba...straight gown ce a jikinta na wani lace mai kyau..dinkin yabi jikinta ya kwanta luf luf hakan kuma ya baiyanar da beautiful figure dinta...daurin dankwalinta Zara Buhari as usual gashinta ya leko ta karkashin daurin..gaba daya ranta ba dadi duk ma tasan ba jin dadin yau din zatayi ba sbd Bobby..duk ta tuna kashedin da yayi mata jiya na idan tayi wani abu zai hadata da daddy sai taji kaman tasa kuka wlh...yanxu haka yakeso taje tayi zaune a wurin tayita kallonsu knn ita bazatayi rawa ba...da yasan yanda take kaunar rawa da baiyi mata haka ba wlh..kawai rawan yakema bala’i jiya kaman zuwa tayi club ta kwana...Billy ta shigo dakin tana sanye cikin kayanta irin na Aysha sak har dinki da daurin dankwalinsu iri daya...batace mata komai ba ta karasa cikin dakin ta dauko veils dinsu da suke zube kan bed dinta ta hada da wayoyinsu snn taja hannun Aysha suka fita daga dakin...binta kawai takeyi har suka isa compound snn ta saketa ta mika mata veil da wayanta ba musu ta kar6a ta yafa itama Billy ta yafa nata snn tace"nasan in muka daka ta taki zamu iya kwana nan ciki baki gama kallon madubi ba..na fada maki idan kika kiyaye babu abunda ya isa ya maki amma har yanxun kinki kwantar da hankalinki”..juyawa Aysha tayi tana kallonta kaman zatasa kuka tace"yandu fisabilillahi saidai inje inyi zaune kaman gunki ni bazanyi abun arziki ba?..ai wnn rashin imani ne wlh"..ta karasa mgn hawaye na cikowa idonta...daria yaso kufcewa Billy amma ta gimtse suka fita daga wurin...inda Sa’eed ke tsaye suka nufa kafin su karaso ya bude musu mota Aysha ta shiga gaba Billy kuma baya snn shima ya shiga ya tayar da motar suka tafi...a hanya ya dubi bestyn tashi yaga fuskan nan cunkus sai ya kallo Billy ta mirror yace"waya ta6amin besty ta?.."daria Billy ta saki tace"akan mgnr jiya nefa"..dan murmushi shima ya saki yana kokarin controlling dariarshi yace"besty har yanxu mgnr rawan ne dai?.."a fusace ta juya tana kallonshi tace"malam ba ruwanka dani tunda biyewa Billy kake kunamin daria...kawai sai inje inyi zaune ni bazanyi rawa ba sbd rashin imani"...ta karasa mgn hawaye na sake ciko eyes dinta...wnn karon kasa 6oye dariar sukayi dan dagashi har Billyn basu san sanda ta fito ba...daria sukeyi sosai sai kace ta6a66u Aysha kuma ta shaqa iya shaqa kawai sai ta rufe fuska da hands dinta ta wani rushe da matsanancin kuka...ganin kukanda take sai darian ya sake zuwa musu aikam sukaita yinshi knr sabbin kamu saida sukayi me isarsu snn suka bari...Sa’eed ya dan juya yana kallonta with a little smile yace"besty dan Allah kiyi hakuri kinji..nifa bake nakewa daria ba"...yana rufe baki Billy ma tace"nima na ranste ba dake nake ba dan Allah ki bar kuka"...ai kaman ma sunce tacigaba don kara sautin kukan tayi hadda su buga kafafu a kasa ba shiri Sa’eed ya gangara gefen titi yayi parking...juyawa yayi yana kallonta ya wani marairaice yace"yanxu besty dan girman Allah bazakiyi shiru ba?..nace fa am sorry kuma da gaske ni ba dake nake ba"...banza tayi dashi tana cigaba da kukanta...yana mata ciwo idan ta tuna saidai kawai taje wurin a matsayin hoto bazatayi rawa ba...gashi ance hadda favorite mawaqinta aka dauko Ado Gwanja kuma ace bazatayi rawa ba ai wlh an cuceta...wayanta dake ajiye kan dashboard ne ya fara ringing Sa’eed yakai hannu ya dauka ganin yanda tayi banza da wayan...Baby boo ya gani kan screen din dan haka ya juya screen din yana nunawa Billy..da sauri tace"yauwa dauka kace masa yazo ya rarrashi kayarshi tunda mu taki ta sauraremu"...ba musu Sa’eed yayi sliding tareda sawa a speaker...on the other side Prof Ahmad yace"my baby girl"...hada ido Sa’eed sukayi da Billy suna kunshe daria kafin ya maze yana cewa"ahm ba ita bace sunana Sa’eed"...Prof yace"ai besty zaka cemin yanda zanfi ganewa"...Sa’eed ya kara sakin murmushi before yayi adding"besty ce dama tun daxu take kuka wlh kuma munyi iya bakin kokarinmu taki tayi shiru"...hankalinshi har ya fara tashi yace"wait voice dinta ne nakeji tana kuka yanxu?.."da sauri Sa’eed yace"itace wlh...mun rasa yanda zamuyi da ita"...Prof yace"bata waya muyi mgn"...ba musu Sa’eed ya ajiye wayan kan laps dinta...voice dinshi taji yana fadin"hello baby girl"...dan dakatar da kukan tayi tana goge tears dinta tace"umhum"..yace"why are u crying baby girl..waya ta6amin ke?.."saida ta sake goge tawagar hawaye da suka biyo fuskarta tace"ba komai"...yace"no ban yadda ba baby kodai inzo ne?.."girgiza kai tayi tace"aah.."yace"then promise me u will stop crying inba haka ba kuma am coming"...a hankali tace"I promise"...yace"yauwa my little baby girl i love u kinji?..and zanzo da daddare sakin fadamin wanda yasa babyna kuka"...kai take gyadawa kaman yana ganinta kafin tace"toh.."yace"ohk bye"...itama tace"bye.."snn ta ajiye wayar...Billy da Sa’eed hanci da baki suka saki suna kallon ikon Allah ganin har ta dea kukan kaman ba itane suke roki ta dena ba amma taki...bata kalli kowadaga cikinsu ba ta maida kanta jikin window...suma basuce mata komai ba as suna tsoron su sake mgn ta kuma langabe musu Sa’eed ya koma seat dinshi ya zauna snn tada motar suka karasa cikin makarantan. Wucewa sukazo yi ta daidai inda suke tsaye da alama wani suke jira...Bobby rikeda hannun Ilham Miemie kuma na tsaye kusada Nur don ko kadan batason hada ido da Bobby data tabbatar haushinta yakeji for following them...Bilkisu da Sa’eed ne suka fara tahowa suna zuwa inda suke gaishesu snn suka wuce ita kuma tana baya dan cewa tayi bazata jera dasu ba...ganinshi tsaye a wurin ta sake dinke fuskanta tsaf tana cigaba da tafiya kaman batasan suna wajen ba...kafin ta wuce Nur ya kira sunanta"Lamido"...a hankali ta juya tana kallonshi with a little smile kan face dinta tace"Sir good afternoon"..yace"afternoon ya gajia"...murmushi kawai tayi batace komai ba...Miemie da a kallon farko taji ta burgeta sbd kyanta itama ta gaisheta..Aysha ta amsa ta murmushi tana mamkin inda provost ya samo yarinyar me kyau haka...so tayi ta wuce batareda ta gaishe da Bobby ba amma sai taga bai dace ba kuma yana iya hadata da daddy dan haka ta dan juya tana kallonshi a kaikaice fuskan nan ba fus tace"ina yini"...ko kallon inda take baiyi ba balle ya amsa mata...ita kuma jin yayi shiru ta daga ido sai taga wayanshi ma yake dannawa aikuwa ta daddage ta murguda masa baki sai kuma karaf a idanunshi...idanunta na sauka cikin nashi tayi kasa da nata da sauri...kallonta yayi for like 2 minutes snn ya dauke kai...ita kuma juyawa tayi zata tafi Ilham da har yanxu ke rikeda hannunshi tace"Ehihie Oma"...juyawa Bobby yayi yana kallonta da mamaki jin tayi mata igbo..kafin yayi mgn Aysha data juyo itama tana kallonta with smile tace"hey I don’t understand igbo...how are u"..ilham ta saki murmushi tace"am fine"...Aysha ta gyada kai dan yarinyar sosai ta burgeta sai ta ganta kaman Yusra don itama akwai surutu...tace"ya sunanki?.."da sauri ilham tace"sunana Nadia amma ilham ake cemin..mamana kuma sunanta Sumayya muna cemata aunty...wancan kuma sunan..."bata karasa ba Bobby ya toshe mata baki yana hararanta yace"and who asked u all these?.."turo baki tayi tace"Uncle Bobby let me finishi plss"...bai bari ta sake mgn ba ya kama hannunta suka bar wajen...Aysha ta bisu da kallo tana hararan bayanshi kaman idanun zasu fado...tsaki taja tacigaba da tafia itama...tana shiga inda hall din yake kafin ta karasa Bobby dake tsaye yana jiran shigowanta yace"come here"...juyawa tayi a tsorace tana kallonshi don batasan da mutum ba a wurin...ya wani hade rai yace"bazaki zoba?.."turo baki tayi ta wuce inda yake...tana karasawa ta rungume hanu tana ciccin magani and hakan bai dameshi ba ya nuna gashinta dake a waje fuska babu alamun wasa yace"maida wnn gashin da kika fito dashi"...dagowa tayi ta kalleshi hawaye har sun ciko idonta sbd haushi...har yanxu idan ta tuna batada daman yin rawa a wurin nan sai taji kaman ta shakeshi ya mutu...ganin yana mata wnn kallon da bata so takai hannu ta tura gashin nata ciki...ya bita da wani irin kallon kafin yace"now leave"...ba misu ta juya ta tafi daga wurin hawayen dake cikin idonta na gangarowa kasa...shima ya kama hannun ilham zasu shiga saiga Miemie da Nur sun shigo...Nur ya kalleshi da mamaki yace"wai dama baka shiga ba?..meka tsaya yi a nan toh?.."banza yayi dashi yaja ilham suka shiga ciki...shima shiga cikin sukayi yana mamakin abunda ya tsaidashi a waje bayan tun daxu ya shigo. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 23 Suna nan zaune daya daga cikin mawaqan da sukazo ya fara performance dinshi...hajia Aysha na zaune tana kallo kaman tayi kuka...yana kammalawa favorite din nata ya shigo tareda ganguna da ‘yan rawarshi aikuwa gaba daya hall din ya rude da sowa da tafi...kaman yasan halinda take ciki saida ya samo favorite dinta a cikin waqoqinshi nashi ma snn akayi playing ya fara miming...nan take hall din ya sake rudewa da muryan mata duk suna bin waqar wasu kuma suna zuwa suna mishi liki...itadai tana daga gaba gaba tana kallonsu tanajin ciwon da bata isa ko dan liki taje tayi ba...tana kallon su Billy sukaje sukayi liki snn suka dan taka rawa suka fito...hawaye taji suna ciko mata ido kawai saita rufe fuska da hannayenta tana kokarin mayar da hawayen...Bobby da tun daxun hankalinshi ke kanta daga inda yake yana ganin yanda ta rufe fuska fuska ya wani ta6e baki cikin ranshi yace"ko kukan jini zakiyi bazakiyi rawa a wurin nan ba wlh"...ita kuwa bata ma san yanayi ba saida ta gama goge tears din snn ta bude fuska...daga karshe ma mikewa tayi ta fita a wurin don bataga amfanin zamanta ba...duk akan idon Bobby da kona one second bai dauke idonshi kanta ba sbd yasan tsaf zata iya fakar idonshi ta shige cikin ‘yan rawa idan taga baya kallonta...can waje ta fita ta samu wuri tayi zamanta tana jera masa Allah ya isa a cikin ranta kmr daga sama taji sallaman mutum a kanta..idonta ta lumshe tasan yanxu zuwa zaiyi ya kara mata kan abunda take ciki dan ko ba’a ba tasan shine...muryan kadai taji ta gane Sir Abdool ne...kallon yanda ta kulle idanu yake kafin a hankali yace"may i?.."kai ta gyada mishi ba tareda ta bude idon ba...zama yayi nan kusada ita yana sake kafa mata eyes dinshi yace"Lamido wai bakida tausayi dama?..ace duk tsahon lokacin nan inata faman baki hakuri amma kinki hakura"...bude idon tayi tana dan turo lips dinta tace"Sir nifa ba fushi nakeyi dakai ba"...tana rufe baki yace"idan ba fushi kikeyi dani ba meye wnn toh?..meyasa har yanxun bakya picking calls dina?.."dan juyawa tayi tana kallonshi tadan marairaice tace"da gaske ba fushi nakeyi ba"...yace"then fadamin idan sona ne bakyayi I won’t force you"...sake narkewa tayi tana dubanshi tace"inada wanda zan aura ne"...hannu yakai ya dafe chest dinshi tared runste ido yace"that hurts"...a hankali tace"am sorry"...bude idon yayi yana kakalo murmushi yace mata"as i have said I won’t force u to love me and congratulations to the lucky guy"...dan murmushi kawai tayi batace komai ba..she’s happy yayi understanding dinta...muryanshi taji yana cewa"but akwai alfarma da zan nema wurinki"...tana gyada kanta tace mishi"inaji"..yace"if I can’t be ur lover at least i will be glad to be ur friend"...bright smile ta saki tana dubanshi tace"then we’re friends"...murmushin shima ya saki yace"yes we’re friends..thanks for accepting my offer"...daria kawai takeyi tana kallonshi..taji dadin yanda ya fahimce ta har hakan yaso yawa ta manta baqin ciki hanata rawa da akayi...shima darian yakeyi yana kallonta deep down yanajin ciwon rashin samun soyayyanta amma ya ya ita tunda bata sonshi?..kaman ance ta daga ido sukayi ido hudu da Bobby daya wani hade rai yana binta da tsinannen kallon nan bata qauna...darian da takeyi ya tsaya cak itama ta hade rai tareda dauke idonta daga gareshi...shi kuma wucewa yayi zuwa office dinshi yanajin haushin yanda heart dinshi ke neman deceiving dinshi yana sashi jin abunda sam bai kamata ace yajishi akan jinin Fulani ba. A takaice ranar haka aka tashi taron nan batayi rawa ba sbd tsoron kar ya fadawa daddy...haka suka koma hostel itada Billy tanata ciccin magani Billy batabi ta kanta ba ta shiga sabagar gabanta...sai dare da babynta yazo snn ta dan samu nutsuwa dan bai bar hostel dinba saida ya tabbata yayi flushing away wnn damuwan da take ciki. The next day around 10 suka fita sbd da wuri ake fara lecture din...dress code dinsu na ranan white ne dan basuyi anko ba saidai ance everybody should wear white cloth...itada Billy black straight skirt suka saka da farar shirt sai farin kimono da suka dora akan kayan itama white da digi digon black a jiki suka yafa black veil...ita Billy tasa turban snn tayi veiling da mayafin while hajia indo batasa komai ba sai dan mayafin data yafa akanta...daidai sa bags da suka rike iri daya ne suma duk farare...suna shigowa cikin school kiran Husna ya shigo wayan Billy nan ta dubi Aysha da sauri tace"Lamido ina tunanin su Hamma fasun karaso kinga Husna na kirana"...Aysha tace"to mu karasa parking space muga ko suna can"..daga haka suka wuce zuwa parking lots din...tun daga nesa suka hango motanshi dan haka suka nufi inda take...Hamman nasu ya shiga binsu da kallo yana murmushi yace"lallai ashe gayunku kawai kukeyi a makarantan bamu saniba"..Aysha tace"kai Hamma meya wani gayu a nan"..yana kallon Billy yace"gayu ne mana..dan bakiga yanda kukayi kyau bane"...kafin Aysha tayi mgn Husna tace"Hamma mudai dan Allah mu karasa ciki kar a fara abun arzikin bamu shiga ba..nasan anjima nayi zaka fara cewa azo a tafi daddy yace kar ayi dare"...murmushi kawai yayi gamida girgiza kai snn suka dunguma zuwa hall din...da yake yau kusan kowa yana inviting family ko friends dinshi sai hall din ya cika yayi taf fiyeda sauran ranakun...wuri suka samu suka zazzauna daga gaba gaba yanda za’ayi komai akan idonsu snn suka cigaba da kwasan hira kaman sun shekara basu hadu ba...suna nan zaune gab da za’a fara Sa’eed shima ya shigo tareda lubna aikam suna ganinta suka mike zuwa inda take sukayi hugging dinta..shi kuma Sa’eed ya karas shna gaisawa da Hamma dasu Husna...bayan sun gama rungume rungumensu suka karasa suma suka zauna Lubna nata jadda musu sai sunzo kd bikinta nanda few weeks sukace zasuje inshaAllah...saida kowa ya gama shiga snn Proprietor,Provost da kuma manya manyan doctors da zasu gabatar da lecture suka fara shigowa...duk yawan jama’an dake wurin baisan meyasa idanunshi suka hango mishi ita zaune a tsakiyar wasu maza ba...ranshi yaji ya 6aci sosai yanxun duk space dake cikin hall din nan ta rasa inda zata zauna sai ta shiga cikin maza?..wai wace irin yarinyace ne wnn?..wane irin shegen rashin hankali gareta?..har suka isa high table da aka tanada dominsu suka zauna bai denajin ciwo ba...sai a lokacin Aunty Sumy dasu Miemie suka karaso...Nur ne ya amsa mike daga hannun mc yayi welcoming guests dinsu snn ya gabatar da sunan disease da za’ayi lecture a kanshi Sickle Cell Anaemia wanda akafi sani da Sickler...tafi wurin ya dauka kowa yana ganin dacewar gabatar da lecture akan Sickler sbd yanda masu ciwo irinshi suke facing challenges a rayuwarsu na yau da kullum...bayan hall din ya danyi tsit ya dora da fadin"and before i hand over the mike to our qualified doctor Olusola Bulus...i will like to invite Aisha Ahmad Lamido for a brief introduction of Sickle Cell Anaemia"...fuska daure Bobby ke kallon abokin nashi ko meye ma’anar hakan da yayi oho?..meye amfanin wani kiranta tayi bayani tunda ga doctor zaiyi lecture a barshi ya gabatar da abunshi mana...Aysha da taji sunanta unexpected kasa mikewa tayi daga inda take zaune...Hammanta ne ya sunkuya yayi mata mgn a kunnenta kan idon Bobby da idanunshi ke wurin...a hankali ta mike daga inda ta fito zuwa kan stage...tana isa ya ba ta mike dake hannunshi ta amsa ta fara da gaishe da manyan baqi da colleagues dinta dake wurin snn ta shiga yi musu brief introduction ko ince explanation na Sickle Cell Anaemi kaman yanda aka bukaceta...ta burge mutane da dama a wurin domin tun daga kan yanda take mgn with courage and confidence zaka san ba karamar mai kwanya bace...uwa uba kuma dressing dinta daya sake fito da ainihin kyawunta hatta yanda take mgn ma abun kallo ne...hall din yayi wani irin tsit ko tari babu sai sweek voice dinta dake tashi ta cikin speakers...bata shiga deep ba ta tsaya iya introduction kmr yanda akace tayi snn ta sake miqawa Nur mike din ta sauka daga wurin..tafi sosai aka shiga yi mata hatta doctors dake wurin saida suka jinjina mata dan tayi kokari sosai ba kadan ba...tana karasawa inda take Hammanta ya mika mata hannu suka tafa and again kan idanun Dr.Bobby da yabita da wani hadadden harara data sauka daga stage...kawai haushi yakeji and ya rasa dalili...gaba daya mutanen wurin ma haushinsu yaji yanaji for clapping mata da sukayi ballantana kuma Nur dashine wanda ya haddasa komai...aunty sumy dake zaune daga dan gaba itama kallonshi kawai take tana mamakin abunda aka mashi yake wnn cin kunu haka...ta lura ko noticing zuwansu ma baiyi ba hankalinshi na can wurinda batasan me yake kallo ba...text tayi typing a wayanta"what’s wrong?..why are u frowning ur face?.."ta tura mashi...wayan na aljihunshi yanajin shigowan text bai duba ba..ta sake tura mashi"Bobbyyyy"...zaro wayan yayi cikeda haushin damunshi da akeyi zaisa a flight mode idonshi ya sauka kan sunanshi data kira...sender ya duba yaga itace sai ya bude message din da sauri shi sam ya mance sunyi mgn daxu tace mishi suna hanya...yana gama karantawa ya daga kai yana duban wurin wai ko zai hangota amma bai ganta ba...text ne ya sake shigowa wayan ya duba sai yaga tace"ba ganinmu zakayi ba kawai ka bar frowning face dinka haka kar guest dinka suyi tunanin wani abu"...ajiyar zuciya ya sauke yana sake wurga idonshi still bai gansu ba dan haka yayi typing"ohk na dena"shima ya tura mata...yana gama tafiya ya maida wayan aljihu yana kokarin daidaita face dinshi kmr yanda tace kar guest dinshi suyi tunanin wani abu...doctor Olusola ne ya fara bayani kan yanda Sickler yake..yanda yara ke samu ta hanyar iyayensu and hanyoyin daya kamata abi don ganin sun zauna cikin koshin lafia...saida ya dauki more than one hour yana abu daya kafin ya gama...bayanshi wani doctor Solomon shima yayi bayani stigmatization da suke fuskanta a society da kuma hanyoyin daya kamata abi don kiyaye wnn stigmatization din and lastly doctor Nuruddeen wato Provost yayi bayani kan hanyoyin da za’abi wajen preventing haihuwan yara masu sickler snn idan an haifesun hanyoyin da za’ayi taking proper care of them tun daga neonatal stage zuwa child har zuwa adolescent...daga nan kuma ya sake mika godia wa duk wanda suka halarci taron a matsayinshi na Provost na FCNM tareda fatan komawa gida lafia...daga nan kuma sai aka hau raba drinks da snacks each table aka ajiye musu nasu snn aka faraci...bayan sun gama Provost ya sake amsan mike yace yanaso su zama ready for the Fun Walk don in the next 10 minutes zasu fita...haka kuwa akayi duk mutane suka fara mikewa suna fita daga hall din...Bobby ma ya taso daga inda yake zuwa inda ya hango su aunty sumy zaune...tun kafin ya karasa Ilham ta mike tana rungumoshi..shi kuma yajata suka karasa wurin yana kokarin dora smile kan face dinshi yace"wai yaushe kukazo?..kinsan banga shigownku ba?.."aunty sumy tace"dama ya zaayi kaga shigowanmu hankalinka na wani wajen..wai mema kake kallo ne kam?..and meya 6ata maka rai da kaketa cin magani haka?.."dan shafa kanshi yayi yace"bafa wanda ya 6atamin rai kawai zaman wajen ne ya isheni..kuma zakuyi walk din ne ko bazakuyi ba"..mikewa aunty sumy tayi hannunta rikeda bag dinta tace"rufamin asiri da wnn tafiyar Bobby..komawa gida zamuyi dama lecture mukazo ji kuma an gama so we are going back home"...gyada kanshi yayi cikin jin dadin tafiyar da zasuyi yace"gara ku koma ai dan wnn walk din wahalar banza ne kawai"..aunty sumy ta wuce suka fara tafia tace"wnn karon ma bazakaje ba knn?.."yace"haba!.Allah ya kiyaye ai bazan iya wnn wahalar ba"..murmushi kawai ta sakeyi batace komai ba...saida ya rakasu har mota yaga sun shiga sun fita daga makarantan snn ya juya zuwa office din Nur don yasan da yawa daga guest din da basu tafi ba suna can...snacks ya samu sunaci da drinks dinsu sunata kwasan hira kaman basu ba...daidai lokacin da ya shiga yaji Gabriel na fadin"ni wlh yarinyar nan cema ta burgeni gaba daya tunda na ganta naji na gagara sukuni...yaya ma sunanta kace?.."yayi referring tambayar to Nur dake sauraronshi yana daria yace"kai wnn yarinyar tafi karfink wlh..Lamido matar manya ce ba yara irinku ba"..daria suka saka Gabriel din na cewa kodai shima Nur sonta yake Nuru yace ai babu mamaki ma idan yana son nata...Bobby dake tsaye jikin kofa yana sauraran conversation din nasu kasa karasawa ciki yayi..haka nan yaji wani irin faduwar gaba dajin abunda Nur ya fada..shi sam mgnr Gabriel bai daukeshi da wani abu kaman na Nur ba..da dadewa dama yana zargin Nur sonta yake and now ya tabbatar da zarginsa..dukda ba fitowa fili yayi ya furta yana sonta ba a iya mgnr daya fada ya fahimci da gaske son nata yakeyi...juyawa yayi ya bar office din yana sakin tsaki a fili ya furta"ko uban me Nur zaiyi da wnn yarinyar oho?.."shidai wlh wnn yarinyar yana ganin ko daura masa ita akayi a kafarsa zai kwance ya wurgar don baiga amfanin auren mace mai shegen rawar kai da kula samari ba..jiya ma ya ganta da Abdool and a yanayin da yaga suna mgn yasan da kyar idan shima ba saurayinta bane..daxun ma ya ganta zaune tsakiyar maza su dinma kuma ba abun mamaki bane idan ance samarinta ne shi kam me zaiyi da mace kaman wnn da take daukan maza kaman ‘yan uwanta mata?..a fili ya sake furta"God forbid"..harda tsartar da saliva.😹 Bayan few minutes gaba daya wanda zasuyi walk din suka fita masu police band nata kida haka masu dj sunyi playing music sauran kuma ana tafe ana rawa kowa rikeda banner da akayi rubutu a jiki...dukda tafiyan akwai nisa ba karamin enjoying dinshi sukayi ba don suna tafe suna takawa hadda Aysha data gama dubanta tsaf bataga proprietor a wurin ba...duk inda suka wuce anata kallonsu sbd yawansu haka duk titin da suka hau suke rufeshi gaba daya saidai masu wucewa su nemi wani hanyan...suna tafe sunata daukan pics da videos abundai sai wanda ya gani...haka suka gama zagayensu suka dawo college din a kafa. Suna shigowa college din can bayan classes dinsu dake nan kmr garden suka wuce kai tsaye suka shimfida manyan carpets a wurin snn suka fiddo abincin da sukazo dashi daga gida suka zazzauna nan sunaci sunata kwasan labari...idan kaga yanda suke hira zakayi zaton duk ‘yan uwan juna ne irin wanda suka shaqu da juna sosai...Lubna da Aysha da Billy sunacin nasu tare..Hamma da Sa’eed suma sunacin nasu sai Husna da Yusra...Billy ce kadai ba ‘yan uwanta kasancewar ita kadai ce mace a gidansu duk sauran siblings dinta maza ne...bayan sun gama ciye ciyen sai suka fara daukan pictures da videos Aysha nata ma Hammanta da bayason daukan hoto daria...a takaice basu suka bar FCNM ba sai after five...suka rakasu har mota suka tafi snn suka dawo ciki ya rage daga Aysha da Billy sai Sa’eed da Lubna...daga nan ya kwashesu zuwa hostel don Lubna cewa tayi ita sai dare zata koma gidan Hajia..hakan kuwa akayi don bai dawo ya dauketa ba sai around 9 na dare..haka suka rabu sunata zullumi kaman bazasu sake haduwa ba bayan ko gobe tace zata dawo kallon sports da zasuyi. Washegari Friday basu fito daga hostel ba sai wajen 11...lokacin already wanda zasuyi sports suna can field sun fara abunsh...karasawa suma sukayi inda babban sports field din nasu yake...waje suka samu suka zauna suna kallon football da maza keyi...Bobby kam zamanshi yayi a gida sam baiyi niyyar fitaba amma yana tuna zata iya zuwa ta aikata wani abunda ba shikenan ba idan baya nan sai ya mike da sauri sairi ya gama shiryawa ya fita...office din Nur ya tsaya suka tafi field din tare...suna karasawa ciki as usual ya hangota zaune tareda Lubna da Billy sai kallon ball suke suna ihu..muryanta mayafi na kowa tashi a wurin sbd bestynta yana kokari...yana daukan ball zakaji ta fara fadin"yes..yauwa besty na go on..yauwaaa"..Lubna sai daria take mata yayinda Billy tace"ai wlh zaki gaji kuwa indai Lamido ce..haka nan take kallon ball dinta tana ihu idan suna abun arziki knn..idan kuma abun tsiya sukeyi tsit zakijita kaman ba itaba"...Lubna dai dukda haka ta kasa dena daria...Bobby da suka zaune opposite dinsu yana kallonta tana ihu sai kace namiji..ranshi ya 6aci sosai ya rasa wace irin yarinya ce ita...yana kallo da aka tafi half time wnn saurayin da sukayi drama tare yazo inda suke ita kuma ta mike da sauri ta mika mishi dan towel ya goge jikinshi snn ta bashi ruwa yasha sai doka masa murmushi take tanajin kaman ta goyashi sbd farin cikin yana performing...yana gamawa ya maida mata towel da goran ruwan snn ya sake komawa ciki...zuwa yanxu Bobby a kule yake tsaf ji yake kaman ya mika hannu ya kwada mata mari..sbd kazanta har amsan towel daya gama goge guminshi takeyi?..wnn wane irin kazanta ne?..duk kokarinshi na yaga ya manta da abun kasawa yayi dan haka ya mike bayan yacewa Nur yana zuwa ya fita daga wajen...kai tsaye office dinshi ya nufa snn ya zaro wayanshi yayi dialing number dinta da ranar yayi saving as Lamid...wayan na cikin jaka yanata ringing bata gani ba shi kuma bai fasa kiraba sai a karo na uku tayi picking...murya a cushe yace mata"come to my office"...zatayi mgn yace mata"now.."da sauri ta matsar da wayar daga kunnenta sbd ihun da yayi...su Billy ta kalla rai a 6ace tace musu zataje proprietor na nemanta daga haka ta fita daga wurin da sauri tana zullumin ko wani abun ta sakeyi...tana shiga office din ya bita da wnn kallon as always..saida ta karasa gaban table dinshi ta tsaya kafin tayi mgn yace"waye wnn da kike mikawa ruwa daxu?.."da sauri ta dago tana kallonshi sai kuma tayi kasa da ido tace"besty na ne"...da mamaki sosai yake kallonta yace"bestie?.."gyada kai tayi tace"eh.."ranshi ya sake 6aci wato har bude baki ma takeyi tana ce mishi bestynta ne?..a fusace yace"ke yanxu ko kunya bakiji kike kiran wani qato da besty?..are u madd?.."turo baki tayi tana marairaice mishi tace"Allah Sir besty na n..."bata karasaba ya daka mata tsawanda yasata shiga taitayinta sbd firgici...yana huci yacigaba da fadin"wato ke gaba daya bakida aikinda ya wuce kule kulen maza koh?..jiyama na ganki da Abdool shi kuma meye tsakaninki dashi?.."kai tsaye tace"sona yakeyi"..wani irin dumm Bobby yaji gabanshi ya fadi..baisan meyasa duk yaji kalmar wani na sonta sai yaji wnn faduwar gaban ba...bazai manta ba jiya ma haka yaji da Gabriel yace yana sonta..amma why yake jin irin haka?..ganin baida amsan tambayan ya sake daure fuska yana kallonta yace"wato sonki yakeyi?..sbd bakida hankali ke kowanne namiji yace yana sonki saiki biye mashi kuna shashanci koh?..are u even alright?.."turo baki ta sakeyi cike da gajiya da wnn masifan nashi tace"nifa ba sonshi nakeyi ba..kuma ni bana kulashi ko jiyan ma daka ganmu hakuri yake bani ai"..yace"hakuri yake baki shine naga kuna daria?..ni zaki maida mahaukaci?.."kaman zatasa kuka tace"Allah hakuri yake bani kuma na ce mishi inada wanda nakes..."bai bari ta karasaba ya katseda fadin"just stop it okay?..stop it"..tsorata tayi sbd ganin yanda yanayinshi ya sake sauyawa lokaci guda..shi kuma ya dakatar da ita ne ba don komai ba sai don bayason jin wnn faduwar gaban da yakeyi idan yaji ana sonta...yanxun da take kokarin ce mishi tana son wani yasan zai iyajin fiyeda na baya...idanunshi a kanta yana kallon yanda take turo baki kawai sai ya runtse nashi idon don a yanda yakejin zuciyarshi yana iya gaura mata mari sbd zafin da yakeji...kofa kawai ya iya nuna mata ba tareda ya bude idon nashi yace"fita.."kaman jira takeyi ta mike zata fita har takai kofa yace"kuma idan baki maida gashin nan da kika fito dashi waje ba you will see the other side of me"..turo baki tayi ta zake juyawa zata fita yace"ba mgn nayi maki bane?.."dakatawa tayi da tafiyar ta janyo mayafin kanta zuwa inda gashin goshinta ya fito...bai tareda ya sake kallonta ba yace"now leave"..da sauri ta bude kofar ta fita tana fadin"mutum sai shegen baqin hali..ko ina yaji hausa haka maoho?..he speaks kaman hausawa ne suka haifeshi". Bayan sati hudu... A cikin four weeks din nan sau biyu suna zuwa gida weekend...karatunsu kuma yanxu ya dauki zafi as suna dab da gama 2nd semester year 2 daga nan kuma sai final year...Sa’eed kuwa shirye shirye sukeyi sosai na Council Exam dinsu daya gabato..Hospital Final Exam zasu fara daga nan kuma wanda yayi passing ya wuce School final inda daga nan kuma za’a turasu asibiti waiting results...har basu son tuna Council din nan sbd hakan yana nufin sun kusa rabuwa da besty...hatta Billy da ba wani shiri sukeyi sosai ba tana tunanin rabuwar nan sbd Sa’eed is one of the best things that have ever happened to them in Kano..sam basu san ya rayuwa zai kasance bayan babushi ba..wnn dalilin yasa Aysha har kuka takeyi idan ta tunada haka...kawai she is going to miss him like crazy...a 6angaren Bobby kuwa fita harkanta yayi completely sbd kwata kwata baison jin abubuwan da yakeji gameda ita...so yake ya dawo da tsanar da yayi ma Fulani ya dora mata amma sam zuciyarshi taki bashi hadin kai and baisan meyasa ba...sai suyi sati ma basu hadu ba sai idan da wani dalili idan sun hadun ma kuma dinke fuskanshi yakeyi tsaf wai kar ta rainashi...tsakaninshi da daddy kuwa zumunchi suke sosai don every Friday yana mishi sending friday text message snn yana kiranshi yana gaishesheshi once in a while haka..sosai yakejin mutumin na sake kwanta mishi a rai sbd mu’amala da yake dashi me kyau da mutane...har yanxun kuma bai dena mamakin how he end up giving birth to Lamido da tunda yake bai ta6a ganin fitinanniyar yarinya irinta ba. Yau Saturday tun safe Aysha ta tashi ta ciwon baya da kafa as a result of period dinta da yaz..tun safen kuma take kwance kan gadon Billy tanata faman murkususu tana rikeda bayan nata tana hawaye...Billy dake zaune kusada ita ajiyar zuciya ta sauke tun daxu take fama da ita ko dan pcm tasha taki sha kuma uk tabi ta isheta da kuka sai kace small girl...daga karshe mikewa tayi tana cewa"bari in dauki waya in kira Ammi in fada mata ni bazan iya wnn wulakancin naki ba..or better still in kira Proprietor in fada masa kawai yazo komai kukanda zakiyi ya danqara maki allura kowa ma ya huta"...tana rufe baki Aysha dake kuka wiei tace"dan muhammadu manzon Allah kada ki kirshi Billy..sai kace bakisan halinshi da mugunta?.."Billy tace"yo ya kikeso in miki kin sani a gaba tun dadu kinamin kuka...kiranshi zanje inyi wlh ni bazan iya da ta6ararki ba"...da sauri Aysha ta sake fadin"dan Allah don’t call him..kawai ki kira baby yazo ya kaini asibiti tunda nasan besty yanxu suna karatu"...disgusting look Billy ta watsa mata tace"seriously?..ke yanxu ko kunyan yasan kina period bakiji?.."daure fuska tayi dukda hawaye da takeyi tace"kawai dan nace ya kaini asibiti sai akace miki zuwa zanyi nace ga abunda ke damuna?..nidai ki dauki wayata ki kirashi kar in mutu"...Billy bata sake mgn ba ta dauki wayan nata ta fita..cikin ranta tace"zakiga karyar iskanci ba babyn da zan kira wlh"...searching contact din Bobby da tayi storing as Mr.Wicked tayi yana fitowa kuwa ta danna masa kira. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 24 Yana zaune bedroom dinshi yana aiki da MacBook kiran ya shigo...mamaki sosai ya kamashi ganin ita ke kira..tunda yake da ita bata ta6a kiranshi ba shima kuma bai kiranta sai idan tayi wani abun ya kirata tazo office dinshi ya kare mata tatas snn ta juya ta tafi...to yau kuma meyasa ta kirashi?..wata zuciyar tace mishi"kilan batada lafia"..da sauri ya dauki wayan daya tunada hakan...har zaiyi picking sai kuma kaman wanda ya tunada wani abu yaki dauka yana kallo har ya gama ringing dinshi wani kiran ya sake shigowa sai a snn ya daga baice komai ba...a daya 6angaren Billy tayi kokarin tattara jarumtarta tace"good afternoon Sir..Sunana Bilkisu"...shiru yayi na wani lokaci kafin yace"umhum what is it?.."saida ta sake nutsuwa snn tace"Sir Lamido ce dama tun safe batada lafia kuma nayi nayi da ita ko pcm tasha taki sha..shine nac..."bata karasa ba yace"kun kaita Clinic?.."da sauri tace"taqi yadda wlh..ba yanda banyi da itaba wai ita bazata jeba sbd kar ayi mata allura"...shiru ya sakeyi a cikin ranshi yace"wato har yanxu bata dena kukan allura ba koh?.."a zahiri kuma yace mata"tell her that nace tazo Clinic yanxu..idan ta bari na rigata zuwa kuma zataga abunda zai faru"...yana gama fadan haka ya kashe wayarshi tareda mikewa daga inda yake ya shiga Closet dinshi ya sanyo kaya snn ya fito ya dauki waya da keys dinshi ya fita..sam baida intension din zuwa ko ina yau din nan..niyyarshi kawai sai around 4 ya shiga Hospital daga nan kum ya dawo gida abunshi amma yanxu wancan ta sanyashi doleya fita ba don yanaso ba...sallama yayi dasu Mummy snn ya bar gidan...yau da kanshi ma ya tuka motarshi sbd ya riga ya sallami driver dinshi cewar sai da yamma zai fita...da yake cikin sauri yake driving din nan da nan sai gashi a makarantan...yana gama parking ya bude motar ya fita kai tsaye ya wuce clinic don ganin sun karaso ko basu zoba...tun kafin ya karasa dakinda suke yajiyo sautin kukanta tana cewa"nidai dan Allah bana son injection plss..wlh zai dena da kanshi ko bansha magani ba"...Nurse din dake kokarin bata paracetamol tasha tace"ki daure dai kisha zaki dan samu sauki ko yayane..daure kinji"...ta bude baki zata kwaso wani magiyan idonta ya sauka a kanshi aiko ba shiri ta tsuke bakin nata hawaye na sake gangarowa face dinta...fuska a murtuke ya karaso ciki bayan sun gaisa da Nurse din yace"bring the injection tray"..ba musu Nurse din ta wuce ta hada masa komai dazai buqata kan tray din snn ta dora kan trolley ta kawo mishi...hannu Aysha ta fara yarfawa ganin da gaske alluran zaiyi mata hawaye nata ‘yar tsere akan face dinta...daukan hand glove yayi ya fara sakawa yana dubanta sternly yace mata"get up"...hawaye sosai takeyi wani kan wani har yanxu kuma bata dena yarfa hannu ba...ya sake daure fuskanshi yace"bazaki saukoba?.."dirowa tayi daga gadon da sauri saura kadan ta fadi kasa sbd yanda legs dinta suka rike...Billy dai juyawa tayi ta fice daga dakin sum sum sbd kar masifan ya biyo ta kanta...itama Nurse data tabbatar ta kawo duk wani abu da zaiyi amfani dashi gabanshi saita juya slim alim ta fita daga wurin ya rage dagashi sai ita a cikin dakin...yana gama sa safarshi ya dauki alluran yayi withdrawing ya cire air bubbles snn yayi recapping syringe din yana kallonta yace"juya.."kuka ta saki sosai tana cigaba da yarfa hannu tace"Sir dan Allah dan Annabi kayi hakuri"...fuska a daure yace mata"ina wasa dake?.."girgiza mishi kai tayi da sauri yace"then kindly turn your back before i loose my temper"...juya bayan nata tayi tana cigaba da kuka tana yarfa hannu...baice mata komai ba ya dauki swab dake ajiye sai kuma ya kalli dogon rigan dake jikinta yace"daukeshi sama"...hawaye takeyi sosai gashi da kyar take iya tsaiwa sbd legs din a rike suke...ya sake fadin"i said ki dauke riganki sama..wane irin abune ma zaisa kisa dogon riga keda za’ama allura?..knn haka kike zuwa kina bude jikinki gaban ko wane kato koh?.."hawayenta ta goge tana turo baki ganin a wnn situation dinma saiya mata masifa tace"nifa ba haka nake zuwa ba..kuma ai inada wando a ciki"...tsaki yaja tareda fadin"naji..now dauke rigan in samu in maki i have something important to do"..sake turo bakin tayi tana hawaye takai hannu ta dage rigan nata daga can kasa..idanunshi ya sauka kan pure white legs dinta da suka bayyana..dauke ido yayi da sauri gabanshi har wani faduwa yayi kaman bai ta6a ganin farar fata ba sai a kanta...saida takai rigan iya waist dinta snn ta rikeshi a gun tana sake rushewa da kuka..tsaki ya kara saki yanajin kukan nata na damunshi ya risina ya danyi clearing injection site din da swab kafin yakai alluran ta saki rigan tana sakin wani shegen kara tace"wayyo Allah Sir i beg u in the name of Almighty kayi hakuri..plssss"..tsaki ya saki tareda kai hannunshi ya dago rigan nata cikin tsawa yace mata"rikeshi..and kika sake sakinshi wlh sai nayi doubling injection din"...tun kafin ya rufe baki ta kama rigan gam ta rike tana runtse idonta jikinta har shivering yake...kallon yanda ta matse jikinta yayi yasan idan bata saki jikin ba kuma ana iya samun matsala sai kawai ya girgiza kai ya sake risinawa daidai bombom dinta dake sanyeda pink leggings iya guiwa...lumshe idonshi yayi tareda kai hannu ya sauke mata leggings din kasa kadan snn ya bude idon yayi sauri ya zura needle din kafin ta kara sakin rigan..tanajin shigan needle din jikinta ta saki wani azababben kara lokaci daya kuma sai tayi dif ta tafi luu zata fadi yayi saurin kamota jikinshi Allah ya taimaka ya zare alluran daga jikinta...rungumeta yayi sosai ganin kmr ko numfashi batayi...gabanshi ya bada sautin dammmm kardai ace yarinyar nan suma tayi?...yana rikeda ita da hannu daya ya durkusa ya zura syringe din a safety box snn ya juyo da ita tana facing dinshi ya shiga girgizata yana fadin"Hey.."ganin ko motsi batayi yakai hannayenshi ya rike cheeks dinta dasu yana kallonta sai kawai yaji tayi kasa zata fadi sai ya dagata cak ya dora a kan gado...kallon very cute face dinta dake tsaya mishi a rai yayi...bakinta na nan a tsuke kaman ba suma tayi ba sai kuma kananun gashin goshinta da sajenta da suka kwance luf luf kaman na jariria...lumshe idonshi ya sakeyi ya bude a kan dogon gashinta dake nan a barbaje dan dan veil data yafa tuni ya zame ya fadi kasa..Bobby kasa controlling kanshi yayi..duk yanda yakai da son ya dauke idonshi akan gashin kasawa yayi and he couldn’t help it saida yakai hannu a hankali ya dora a gashin kaman wanda zai dora a wuta...lumshe ido ya sakeyi dayaji gashin nata da dan karen laushi..dunia ba abunda yakeso a jikin mace kaman gashi..yanason yaga gashin kan mace da tsayi da laushi and wnn da yake ta6awa is even more softer and longer than he thinks...kawai shafawa yake that har ya mance wacece kwance nan kusa dashi ya kuma mance Clinic suke and mutum na iya shigowa at any moment...a hankali ya gangaro da hannunshi kan sajenta nanma ya lumshe ido..ya dade yana ayyana yanda sajen nan nata yake domin duk yanda zata janyo hijab dinta saidai gashin goshinta su rufe amma ba sajenta ba...lokaci daya kuma ya dauke hannun nashi da sauri tareda wani irin mikewa a rikice kaman wanda ya tunada wani abun...zaro idanunshi yakeyi ya shiga girgiza kai yana tafia da baya da baya kaman wanda yaga abun tsoro cikin zuciyarshi yake fadin"Noo..not me plss..what have i done..what just happened?..innalillahi wainna ilaihi rajiun..Ya Allah forgive me..Astagfhirullah ya Rahman forgive me"..daga haka ya juya da sauri ya fita daga dakin...yayi kokarin daidaita kanshi snn ya karasa inda Billy ke zaune ba tareda ya kalleta ba yace"ki watsa mata ruwa idan bata farfado ba ki kirani"..yana gama fadan haka ya wuce Billy kuma ta koma dakin da sauri tana mamakin wai Lamido har suma tayi sbd injection?...tana shiga ta sameta kwance a kan gado kaman gawa dan haka tayi dispensing ruwa ta watsa mata a fuska...lokaci daya ta saki wani numfashi mai karfi tareda mikewa zaune da sauri tana kalle kallen dakin...Billy ta karasa kusada ita ta zauna tareda kamo hannunta tace"sannu ya jikin naki?.."kwace hannunta tayi a fusace ta wani daure fuska ta sauka daga gadon...taku daya tayi ana biyun taji kafanta ya sake rikewa dan haka dole ta nemi wuri ta zauna tana cigaba da hawaye..a hankali takai left hand dinta can inda akayi alluran ta dan dora a wurin tana murzawa a hankali da sunan ana mulmula alluran kuma har yanxu bata bar hawaye ba...Billy da taga haka sai tayi zaune abunta tana binta da kallo kmr sabuwar halitta...after like 12 mins Sa’eed yazo daukansu..saida ya shigo har dakinda suke snn ya samu ya lalla6a bestyn nashi ta mike suka fita dan kememe kin kula Billy tayi ita a dole tanajin haushin kira mata Proprietor da tayi...idan kaga yanda take tafia zakayi zaton karyewa tayi a kafan ko kuma wani babban matsala dai kafan ya samu har yayi affecting tafiyanta...suna isa inda motarshi ya bude maya front seat ta shiga Billy ta shiga back seat shima ya shiga driver seat snn ya tayar da ita suka wuce. Cikin ikon Allah washegari haka ta tashi garau kaman ba ita ke kukan ciwo ba jiya...kuma abunda mamakin shine yanda ko injection site din baya mata ciwo unlike before da duk akayi mata injection sai wajen ya kusa shekara yana damunta amma shi nashi yana gamawa ta dena jin ciwon wurin...she remember last time daya mata alluran ma hakan ya faru don a ranar ta warke garau babu ciwon kafa ko ciwon bayan snn kuma babu ciwo da dan swelling din da wajen allura keyi mata...tunda take bai ta6ayin wani abu ya burgeta ba amma this time around ta jinjina mashi kwarai don tunda aka haifeta ba’a ta6a mata allura wurin baiyi ciwo ba sai a kanshi...hakan ya nuna mata he isn’t only a qualified doctor he has magic handa too...tana zaune daki ta tasa pringles da babynta ya kawo kawo cikin shopping da yayi mata daxun saici takeyi kaman ba gobe...Billy suka shigo dakin tareda wata ta karasa ta dauki iron dinsu dake ajiye ta bata snn ta juya ta fita ita kuma ta karasa kusada Lamido ta zauna tana murmushi tace"wai Lamido har yanxu fushin ne?.."murguda baki Aysha tayi batace komai ba...Billy ta kara sakin smile kafin tace"dama Ammi ne tace idan baki kulani ba in kirata in fada mata"..tun bata karasa ba Aysha ta juyo tana kallonta da mamaki sosai tace"yanxu zuwa kikayi kika hadani da Ammi Billy?..sai kace bakisan halin fadanta ba?.."daria Billy ta saka tana mikewa daga inda take tace"dama mgn nakeso kiyi kuma kinyi..ba wata Ammi dana fadawa"...pillow dake kusada ita Aysha ta dauka ta wurga mata shi kaman zatasa kuka tace"amma kin shiga haqqina wlh..kinsan irin tsoron da naji kuwa?.."daria kawai Billy keyi ta fara rage kayan jikinta ta shiga bathroom. Zaune yake a parlonshi waya rike a hannunshi sai jujjuyashi yake kaman wanda yake tunani...tun daxun yake zaune nan wurin yanaso ya kira yaji ya jikinta yake amma wani zuciyan na hanashi wai idan ya kira zata iya misunderstanding dinshi...yayi kokarin kira kusan sau goma yana fasawa sbd zuciyarshi dake raya mishi cewa kar ya kira...tsaki ya saki yayi wurgi da wayan snn ya kwanta nan kan sofa da yake zaune yana wani daure fuska kaman Lamidon tana gabanshi yanxu haka...sam bayason yanda zuciyarshi ke saqa mishi abubuwa a kanta...ya rasa dalilinda yasa tun jiya ya kasa macewa da halin daya barta a ciki kiri kiri yana son kira kuma ya hana kanshi...har yanxun bai dena jin uban laushin gashinta a hannunshi ba kaman yanda bai ta6a mance cute face dinta dake tsaya mishi a rai ba...lumshe ido ya sakeyi cikin ranshi yana ayyana ko mutuwa zatayi bazai kirata ba..to meye ma ruwanshi da rashin lafiyarta da har zai bi ya damu kanshi?...juyi ya sakeyi yana dafe head dinshi duk a kokarinshi na ganin ya hana kanshi kiran nata saidai abunda bai saniba shine duk taurin kanshi heart dinshi bazai dauka ba sbd yafishi taurin kai don haka dole ne yayi mata abunda takeso idan har yana son zaman lafia...kasa daurewa yayi daga karshe ya sake mikewa zaune ya dauko wayan nashi...yayi dialing number dinta yana wani hade rai kaman tana ganinshi...tana kwance daki suna waya baby kiran nashi ya shigo sbd tsabar dadin hira ko noticing kiran nashi ma batayi ba...Bobby da yaji an buga masa wani abu kaman guduma a cikin heart dinshi sakamakon busy da yaji alaman tana waya...haka har ya gama ringing dinshi bata dauka ba hakan kuma ya mugun 6ata masa rai dan yasan da kyar idan bada namiji take wayan ba...sake kira yayi still bata dauka ba sai a na uku ne akayi sa’a taga shigowan call din dan haka tacema baby ya bata two minutes zata kirashi...picking call din tayi da sauri bayan tayi hanging wancan tana wani turo baki kaman tasan yanda ya hade ranshi shima...tana kokarin gaisheshi taji yace"dawa kike waya?.."murguda baki tayi cikin ranta tace"ina ruwanka?.."a fili kuma tace"Hamma na ne"..shiru yayi ba mgn as gaba daya ma mgnr baisan sanda ta fito ba..shi kanshi saida yaji wani iri daya tambayeta amma ba yanda zaiyi ne shiyasa ya tambaya...baisan meyasa abubuwa irin haka suke son su dinga faruwa dashi ba yanxu..shi da sam ba haka yake ba wlh...jin bai sake cewa komai ba tace"hello"...wani mgnr ne ya sake su6ucewa daga bakinshi ba tareda ya shirya ba yace"ya jikinki?.."ita kanta saida tayi mamaki jin tambayar amma bata nuna ba tace"naji sauki"..bai sake cewa komai ba ya kashe wayarshi yana dafe kanshi da yaji kaman zai rabu biyu sbd ciwo...da yasan abunda zai faru knn da bai kirata ba wlh...kawai yana zaman zamanshi ya janyoma kanshi 6acin rai..ko waye Hamman data fada ma oho..a iya saninshi dai idan ance Hamma ana nufin yaya namiji saida i baisan meyasa jikinshi ya kasa amincewa da yayanta take waya ba...sam yasan ba haka bane ta fada ne kawai don ta gujema fadanshi amma zaiyi wahala idan bada daya daga cikin boy friends dinta take wayar ba...wnn tunanin kadai ya sake dagula mishi lissafi. Kwanakin da suka biyo baya shirye shirye sukeyi sosai na End of Year Presentation da suka saba gabatarwa duk end of session. Bobby kuwa tun daga wnn ranan bai sake kiran Lamido a waya ba..ko a hanya suka hadu ko kallonta baiyi dan ko gaisheshi tayi bai amsawa wai duk a kokarinshi na ganin yayi yaki da abunda yake ganin bai kamata ace yanaji ba kuma a kanta...yau friday tun safe ya shigo college din sbd meeting da yake dashi da entire staff karfe 10...bayan sun fito Nur ya biyoshi har office dinshi yana mishi bayanin Presentation da za’ayi next week...ya gama sauraranshi tsaf snn ya bar office din shi kuma sai a lokacin wani tunani ya fado masa...yasan zaiyi wahala wnn abun ace ba’ayi selecting Lamido ba dukda dai kowane department voting sukeyi a tsakaninsu ko wanne class tun daga year 1,2 da 3 zasu bada mutum daya da suka yadda da brain dinshi sai a hadasu su ukun ayi masu test kowa akan gaba daya courses dinshi na shekarar duk wanda yayi winning a cikinsu shine zaiyi representing gaba daya department...baisan meyasa haka nan jikinshi ke bashi ita zatayi winning ba..kawai shidai baya sonta da wnn abubuwan ba don komai ba sai sbd shegen rawar kan daya lura tana dashi snn abune wanda a gaban mutane za’ayi shi hadda wanda ba daga makarantan suke ba..shi kuma yanxu baisan meyasa yaki jinin yaga tana wnn abubuwan ba..sam bai son yaga tanata wnn rawar kan nata a gaban mutane suna kallonta hakanba karamin 6ata mishi rai yake ba...sanin zaiyi wahala idan batayi din ba ya lalabo numberta ya danna mata kira don yayiwa tufkar hanci...shiganta class knn taga kiran nashi ta wani zare ido sosai tana sake kallon screen din to make sure ba idonta ke mata gizo ba...to me yake nema a wurinta yanxu kuma?..ta samu ta huta da masifarshi a yan kwanakin nn shine yanxu zai wani kama ya kirata salon ya wargaza mata jin dadi...ganin ya kusa tsinkewa ta daga tareda kai wayan kunne tana turo baki..kai tsaye yace"meet me now"...bai jira cewarta ba ya kashe wayar..ita kuma ta mike tana kwaikwayonshi”wani wai meet now...as if i am his child..inyamurin banza dan rainin hankali kawai"...mikewa tayi tanata sababi ta fita zuwa office din nashi...secretary dinshi na ganinta ta dauke kai bata kulata ba itama batabi ta kanta ba ta tura kofa ta shiga da sallama...yana zaune kan seat dinshi yana dan juyawa a hankali idanunshi kan kofa...kai a kasa ta karaso gabanshi ta tsaya snn ta gaisheshi still ba tareda ta dago idonta..shima bai damu da ta dago din ba ya nuna mata seat dake bayanta a nutse yace"seat.."dagowa tayi ta kalleshi da mamakin abunda ya fada dan bata ta6a zuwa office dinshi yayi mata tayin seat ba sai yau...janyo kujerar tayi a hankali ta zauna still idanunta a kasa tana wasa da fingers dinta...ba yabo ba fallasa yace"akwai end of year presentation da za’ayi next week nasan kin samu labari koh?.."gyada mishi kai tayi alaman ta sani...yace"then so nake koda anyi selecting dinki a cikin participants kice you won’t do it"...sake dagowa tayi tana kallonshi da mamaki tace"but why sir?..already an riga anyi choosing dina and I can’t say no because I don’t want my department to loose"...kallonta kawai yakeyi yanda take wani explaining mishi bata san kome zata ce ba ganewa zaiyi ba...ya wani hade rai yace"i said you are not going to do it and that’s final"...sake dagowa tayi tana kallonshi da mamaki shima kallon nata yakeyi wai ko zata fahimci abunda yakeji ta cikin idanunshi amma sai yaga ta kauda kanta tareda daure fuskanta itama tace"nidai I can’t say no"...tun kafin ta rufe baki yace"haka kikace?.."shiru tayi tana kallonshi ya sake fadin"haka kikace kou?..fine..we shall see"..dan marairaicewa tayi tana mishi puppy eyes tace"yanxu sir fisabilillahi kawai sai inje ince musu bazanyi ba bayan an riga anyi selecting dina?.."cikin fushi yace"na fada maki baza kiyi ba and if u like go and do it kiga what will happened..just try me and see"...kallonshi kawai takeyi yanda yake mgn ita kam kome zaiyi saidai yayi wlh amma bazata fasa yin abunda tayi niyya ba..besides ko daddy zai fadama tasan bazai hanata ba tunda ba wani abun rashin kyau bane and sai tayi abunta wlh...ganin kallon da yake mata sai tayi kasa da idonta a hankali tace"shikenan zan fada musu su samu wani"...ajiyar zuciya ya sauke a 6oye dan wani irin relieve yaji ya samu jin abunda ta fada ita kuma ta sake dubanshi cikin nutsuwa tace"ina iya tafiya?.."baice komai ba sai kofa daya nuna mata alaman she can...mikewa tayi a hankali ta fita saga office din cikin ranta tace"in your widest dream ba..ai wlh sai nayi abuna saidai kawai ka ganni kan stage..shknn sai ince na fasa kilan aje a dauko wanda bata iyaba ta kayar da department dinmu..to bada A’i za’ayi wnn wautan ba..dan rainin hankali kawai". Ranan Monday tana shigowa school ta wuce office din Nur da safe...yana zaune yana signing wasu papers ta karasa ciki ta zauna bayan sun gama gaisawa tace"Sir dama alfarma nazo nema wurinka"...Nur ya ajiye pen dake hannunshi yana kallonta sosai yace"ohk ina jinki"...tayi kasa da kai tana wasa da fingers dinta tace"Sir so nake dan Allah ko mgn zai hadaku da Proprietor kada ka nuna mishi ni zanyi representing midwifery a presentation din nan"...kallonta Nur yake da mamaki karara a face dinshi yace"amma why?.."tana turo baki tace"cewa yayi wai ko anyi choosing dina ince banyi and ni kuma inaso inyi shiyasa banaso ya sani saidai kawai ya ganni kan stage"...gyada kai Nur ya shigayi alaman gamsuwa before yace"no problem ur secret is safe with me..he won’t know inshaAllah"..murmushi ta saki tareda mikewa tace"thank u sir"..yana mata murmushi yace"u are welcom"..daga haka tayi mishi sallama ta bar office din...Nur ya bita da kallo cikeda mamakin abunda ta fada...shi bai gane kan wani dalili Bobby zai hanata participating ba..dama these days ya lura kaman abu na damunshi and bai ta6a fada mashi ba..."ko dai son Lamido yake?.."ya fada a fili trying to figure it out amma ya kasa...daga karshe sharewa yayi kawai cikin ranshi yace"kilan idan tayi wari ni zan faraji"..da haka ya kaida tunanin daga zuciyarshi. Bobby kam hankalinshi kwance yake sosai data ce mishi bazatayi ba...har wani nutsuwa yaji ya samu na musamman wnn dalilin yasa bai sake yunkurin nemanta sbd ya sake jaddada mata ba...ranan Thursday ya kama zaayi presentation din and tun safe Lamido suka shigo school sbd shirye shirye da ake...auditorium dinsu na nan a cike maqil da mutane participants kawai ake jira domin hatta malamai duk suna nan ciki...as usual Bobby da Nur tare suka shigo kowa ya samu wurinshi ya zauna...Nur ne ya danyi briefing jama’a yanda tsarin abun yake...kowane participant za’a rubuta sunan topics kaman guda uku cikin courses da sukayi a shekarar snnayi folding dinsu ya za6a and duk wanda ya dauka akanshi zaiyi presentation din...bayan dogon jawabi ya sake daidaita mike zuwa zaitin bakinshi yanda mgnrshi zai fito radau snn yace"and our two participants are Sa’eed Mukhtar Makarfi from Nursing department and Aysha Ahmad Lamido from Midifery department”...wani irin dammm Bobby yaji kaman saukan aradu a cikin heart dinshi...gaba daya saiya shiga rudani jin Nur ya ambaci Aysha Lamido and idan ba wai mancewa yayi ba da bakinshi ya ta6a fada mashi kta kadai take bearing da Lamido a college din...shi kuma yasan sunyi mgn da ita tace mishi bazatyi ba amma why zaizo ya kira sunanta kuma?..kodai watace mai suna irin nata bai saniba?...kafin ya samu amsan tambayanshi ya hangota ta taso daga inda take zaune zuwa seat da aka tanadar musu...sanye take cikin uniform dinta fari qal sai shinning yake sbd iron...dan hijab dinta daidai chest dinta sai gashin goshi da sajenta da suke nan waje as always...wani irin sanyi yaji yana lullu6eshi kaman fever zai kamashi...ya lumshe ido ya bude yana sake jin ciwon karyar da tayi mashi har cikin ranshi. Rano✨ Wnn litafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a turo evidence of payment via 07063800556. 25 A hankali take takawa wanda Bobby kejin each taku kaman a kana zuciyarshi take yinshi...wani irin nauyi yaji zuciyar tayi mashi kaman wanda keda heart problems...sake juyawa yayi ya kalleta nan take kuma yaji wani abu ja sake tokare makoshinshi...ko baa fada ba yasan gaba daya mazan wurin nan kallonta suke...hakan kuma yasa yaji kaman ya harbi kanshi ya huta...finally ta karasa seat da aka tanada dominsu ta zauna kusada Sa’eed daya rigata karasawa...sake runtse ido Bobby yayi yanajin ciwon zama kusa dashi a tayi...ya ganeshi sarai shine yaronda tayi acting as his wife ranan da sukayi drama and shine the same yaron da ta bama ruwa ranar da akayi sports...yanxun nan din ma a rasa da wanda za’a hadata sai dashi?..kodai wani hu ke tsakaninsu dashi ne wai?...bayan sun zauna daya daga cikin malamansu mata ta taso da wani box a hannunta mai kyau ta kawo wurinsu tace Sa’eed ya dauki daya tunda shine first presenter...ba mus ya zura hannu cikin box din ya dauko paper daya cikin guda uku da suke ciki snn ya bude...sunan topic din ya gani a rubuce dan haka ya mike daga inda yake yana nuna mata ita kuma ta amsa daga hannunshi ta nunawa malamai then back to students snn ta koma wurinta ta zauna...dan matsawa yayi jikin white board dake ajiye nan wurin ya rubuta sunan topic din nashi snn ya fara presentation dinshi a tsanake...gaba daya hall din yayi tsit voice dinshi kawai akeji...Bobby dai na zaune kaman gunki sbd tsabar abubuwa da suka taru suka mashi yawa...yasan yanxu ko bindiga za’a zare ace ya fadi abunda yaron ke fada bazai iyaba as hankalinshi baya wurin gaba daya...kawai yanajin ciwon deceiving dinshi da tayi tace mishi bazatayi ba...ruwa dake ajiye gabanshi ya dauka yayi sipping ya ajiye tun yanxun yanajin haka idan ta fara nata kuma kilan zaucewa zaiyi...baisan meyasa Allah zai dora mashi wnn masifan a kanta ba...Sa’eed saida ya cinye 40 minutes da aka deba mishi snn yayi handing over mike din ya koma ya zauna anatayi mas tafi dan yayi kokari sosai ba kadan ba...bayan Nur ya gama praising dinshi snn ya sake kiran Aysha Ahmad Lamido data karaso tayi nata itama...kaman dazu wnn matarta mika mata box itama tayi picking one a cikin papers uku dake cikin box din snn ta mike a hankali zuwa inda board yake...kallonta kawai Bobby yake kaman bai ta6a ganinta ba sai yau...glasses data sa a idonta ya zauna daram shi sai yaga kaman ma bai ta6a ganin kyan da glass din yake mata ba sai yau...ya sake daga eyes dinshi zuwa goshinta da kusan rabin gashinta ke waje sbd ita ba gwanar sa dankwali ba hula bane..sam bata sonsu sbd suna takura mata shiyasa hijab kadai take zurawa ta tafi abunta...ciwo yakeji sosai yasan yau kaf wurin kowa saiya gama ganin gashinta..kowa kuma sai yaji voice dinta to his satisfaction...tunanin hakan yasa wani hadadde zafi ya kunno kai cikin sanyin da already ya faraji...lumshe ido kawai yayi ysna karanta duk addu’a da yazo bakinshi for he don’t want to loose it kamar yanda yayi ranan festival...sam bayason a fara zargin ko da wani dalili yake aikata haka while baya da wani dalili kawai dai yarinya ce Allah ya jarabceshi da ita da ko kusa bata son ya zauna lafia...idanun nashi a rufe yaji ta fara presetation din cikin sweetes voice dinta...sake runste idon yayi yanaji kaman yaje ya toshe kunnen kowa dake wajen yanda ba wanda keda daman jin muryan nata sai shi kadai...kwata kwata baya fahimtan abunda take fada shidai kawai yasan mgn take in a sweet tone amma ko za’a kasheshi bai iya fadin ga abunda take cewa...tsoron bude idonshi yake sbd gudun abunda hakan zai haifar amma daga karshe kaman idon nashi sunfi karfinshi ne dan ji yayi sun bude kansu da kansu basu fada ko inaba kuma sai a kanta...nan kuma ya tsayar dasu a kanta yana kallon yanda take mgn tana demonstration da hands dinta...gashi sai dan matsawa take from one place to another hakan kuma yasa jikinta ke dan shaking as if she’s doing it intensionally ga kuma gashinta koshi yana iya ganoshi daga inda yake...baisan lokacin daya rike kanshi da yayi mishi wani azababben sarawa ba...har wani jiri yaji yana daukanshi all of a sudden...addu’a kawai ya shiga jerowa dan samun sassauci amma abun kaman gaba ma yakeyi...ita kuwa Aysha presentation dinta take hankali kwance as ba wani sabon abu bane a wurinta...gaba daya tama manta da wani Bobby and his masifa abunda yake gabanta kawai takeyi...bayan ta cinye 40 mins dinta itama ta koma ta zauna anata aikin yi mata tafi wanda hakan ke kara ta’azzara yanayin da Bobby ke ciki...daya daga cikin malamansu ne ya amshi mike yayi ‘yan jawabe jawabensa kafin a sake mika musu box kowa ya sake daukan paper daya this time around 20 mins zasuyi instead of 40...kaman daxu Sa’eed ne ya fara yin nashi yana gamawa itama ta mike ta fara...zuwa yanxu abunda Bobby keji ya ninka wanda yakeji daxu kusan sau uku...har wani gumi ke tsatsafo mishi sbd azaba don zazza6i sosai ya rufeshi kaman wanda yayi kwana da kwanaki yanayi...bai sake gigin bude idonshi ba har ta gama snn yaji hall din ya kaure da tafi...kafin ayi announcing wanda yayi winning a cikinsu wani babban mutumi daya saba halartan taron duk shekara yace a fadawa Lamido ya bata kyautan sabon MacBook hade da 50k a matsayin tukuici na burgeshi da tayi...aikuwa ana fada hall din ya sake kaurewa da ihu da tafi...masu jin dadi nayi masu rashin jin dadi ma duk sunayi...Bobby da yaji abunda mutumin ga fada kaman saukan aradu baisan time daya bude idonshi ba...daidai lokcin kuma Sa’eed ya dan kai bakinshi kusada kunnenta yace"congratulations besty..seems baby ya samu new rival"...da juyawa tayi tana kallonshi ta dan saki murmushi kafin itama ta matsar da nata bakin dab da kunnenshi tace"ai mai iya takara da baby saiya shirya besty..i am his and his alone"...ta karasa mgn tana blushing as ta tuna da habibie noorul qalbinta...wani azababben tari Bobby yaji ya sarkeshi babu gaira babu dalili...numfashinshi har yi yake kaman zai dauke sbd azaba...ya rasa da wanne ma zaiji...da wancan tsohon banzan daya bata kyauta ko kuma da wancan karamin kwaron dake mata rada a kunne itama tanayi mishi...kuma don iskanchi hadda yi mashi murmushi kaman qanin ubanta...ita kuwa bata ma san yanayi ba wai kunu a wani gida...bayan hayaniya ya dan ragu Nur ya amsa mike yayi godia wa wnn mutumi snn ya fadi scores dinsu inda Lamid ta dara bestyn nata da maki biyu...tun kafin a gama fada midwives suka hau ihu suna tafi sbd sunyi winning...sake juyawa Aysha tayi tana kallon Sa’eed sake zaune gefenta tayi mishi gwalo...daria kawai ya saki yana daga shoulders dinshi...daga nan dai aka sallamesu suka fara fita yayinda wnn mutumi yace a tsayar masa da Aysha yanason mgn da ita...Bobby na zaune yana jinsu amma uffan baice ba as shima ta kanshi yakeyi yanxu...ba musu Nur yayi mata mgn ta tsaya shi kuma mutumin ya taso zuwa inda take yanata smilling yace"yammata sannu da qoqari"..dan murmushi ta saki batace komai ba..yace"saqonki yana nan zuwa gareki gobe inshaAllah..zan iya samun phone numberki?.."shiru tayi tana tunani kanta kasa sai kuma ta dago kan tana bude baki zatayi mgn idanunta suka fada cikin nashi da sukayi wani irin jaa yana kallonta dasu kaman zasu fadi kasa...sauke idonta tayi da sauri sbd jin wnn abun da bata qaunar ji duk suka hada ido dashi...turo bakinta tayi dan ko baa fada ba tasan har yanxun idanunshi na kanta...shi kuma mutumin jin batace komai ba sai ya zaro card dinshi ya bata yana cewa"make sure kin kirani dan Allah...I want to discuss something with u"...gyada mishi kai tayi tana murmushi tace"zan kira inshaAllah"...daga haka ya juya yana murmushi ya koma inda yake...itama juyawa tayi zata fita Bobby ya tashi da sauri kaman ana tunkudashi yabi bayanta a kan idon Nur dake monitoring dinshi tun daxu...sbd saurin da yakeyi kafin ta fita hall din ya cimmata sai ya danyi slowing down ba tareda ya kalli gefenda take ba yace"meet me now"...daga haka ya sake daga kafa yayi wucewarshi...ita kuma ta bishi da harara kaman idon zasu koma jikinshi...cikin immitating dinshi tace"wai meet me now..sai kace durkusawa yayi ya haifeni masifaffen banza inyamuri kawai"...kai tsaye office dinshi ta wuce daga nan tana rikeda wayarta a hannu...tana shiga Bobby daketa sintiri cikin office din ya juyo yana kallonta voice dinshi na fita da kyar sbd zazza6i da 6acin ran da yakeji yace mata"are u satisfied?..kinje kinyi presentation kuma kin samu abunda kikeso hope u are now satisfied?.."dan turo baki tayi tana kauda kanta tace"aini ba sbd kowa nayi ba sbd department dina ne"...tun kafin ta rufe baki a fusace yace"if u dare say another word saina kwada maki mari a wurin..am i ur mate?.."shiru ta sakeyi tana cigaba da turo bakinta..ita fa kome zaiyi yanxu bazai daga mata hankali ba tunda ta riga tayi abunda takeso kuma sunyi winning...shi kuma ganin yanda taketa faman hade rai tana turo baki cikeda wani haushin yace"dama it’s what you’ve always wanted to get Men’s attention and now sai ki zuba ruwa kasa kisha tunda kin samu abunda kikeso...you think duk biye biyen maza da kikeyi banida labari kou?..well i am aware of every single thing da kikeyi kawai zuba maki ido nayi inga iya gudun ruwanki kuma na gani...sbd haka bear it at the back of your mind today babu abunda zai hanani sanar da Dad dinki duk iskancin da kikeyi?..so get ready for it"...ya karasa mgn har yanxu yana huci kaman angry lion...Aysha kuwa tunda ya ambaci kalmar biye biyen maza taji gaba daya ranta ya 6aci...wato ma kallon da yake mata knn?..idan akace biye biyen maza fa ana nufin karuwanci knn?..so this is what he thinks of her shiyasa komai sai yace zai hadata da daddy?..lokaci daya wasu hawaye suka ciko idonta dan sosai taji ciwon mgnr daya fada...ta dago idanun ta zuba masa su cikin nashi hakan kuma ya bawa tawagar hawaye da suka cika idanun nata damar saukowa fuskanta...bata damu da goge su ba tana kallon tsakar idanunshi yau ko wnn tsoron da idanun ke bata bataji ba sbd tsabar 6acin rai...shima kallon nata cikin idon yake yanaso ta gane 6acin ran data haddasa masa sbd abunda tayi..shine shi data cuta baiyi kuka ba sai ita da baiyi wa laifin komai ba?...cikin tsananin 6acin rai da bai ta6a ganinta ciki ba tace"so this is what u think of me?..karuwa mai biye biyen maza right?.."kallonda take mishi ne yaji ya kasa jurewa abunda bai ta6a faruwa dashi ba all his life kawai sai ya dauke kan daga gareta yana sake jin sabon kunchi na rufeshi zuciyarshi kaman zaiyi bindiga sbd kumburan da yake...juyawa kawai tayi zata fita daga office din a fusace yace mata"come back here?.."ai ko sauraronshi batayi ba ta bude kofa ta fita da gudu bayan ta bugo mishi kofan da mugun karfi har saida ya runste ido sbd karan da yayi...zuciyarshi na sake tafarfasa ya dunkule hannunshi ya kaiwa table dinshi duka yana fadin"damn it"...wani jiri yaji ya fara daukanshi dan haka ya karasa kam sofa ya zauna da sauri yana dafe head dinshi da yaji ke barazanar rabewa gida biyu...bude kofa akayi secretary dinshi ta shigo tana cewa"Sir pro..."bai bari ta karasa ba ya daga mata hannu har yanxun yana dafe da head dinshi yace mata"get out"...sake bude baki tayi zatayi mgn a fusace yace"i said get the hell out of my office..are u maddd?.."juyawa tayi da sauri ta fita daga office din jikinta har ya dauki rawa sbd tsawar da yayi mata...after like 5 mins Nur ya shigo office yana fadin"wai Bobby what’s wrong with u ne these days?..what is the matter with you?.."a fusace shima ya dago yana kallonshi da eyes dinshi da suka koma kaman garwashi sbd ja ya nuna mishi kofa yace"malam get the hell out of my office..leave me alone"...daure fuska shima Nur yayi yace"ni kake kora office dinka Bobby?.."a fusace ya sake dagowa yace"to hell with u an koreka din me zakayi?..kaga malam leave my office before I loose my temper with you"..ya karasa mgn yanaji kaman ya kwada masa mari..kawai haushinshi yakeji that har ya wani dakatar da ita sbd tayi mgn da wani qaton sbd shi baisan ciwon kanshi ba...Nur da ranshi ya gama 6aci shima yace"well tunda haka kace am not going anywhere until u loose it with me..fight with me if that’s what u want"...dafe goshi Bobby yayi yana dan murzashi abhankali feeling extra hot inside...kawai bayason ya biyema haushin da yakeji yanxu dan ba karamin tashin hankali zasuyi ba idan ya biyema hakan...mikewa yayi a fusace zai bar mashi office din Nur ya wani irin jawoshi ya dawo dashi baya yana cewa"where are u going"...fizge hannunshi Bobby yayi yana nunashi da finger dinshi yace"Fuck you"...daga haka ya juya ba fita daga office a mugun fusace...kai tsaye inda driver yayi parking motarshi ya nufa saidai bai ha driver din ba..sake dafe kanshi yayi ya jingina jikin motan yana sauke numfashi a jere sbd tashin hankali...can ya hango drivern ya taho dan haka yana zuwa bai bari ya fara masa dogon jawabi ba yace"open the damn car"...da sauri yasa key ya bude motar Bobby ya bude back seat ya shiga shi kuma driver ya rufe mashi kofa snn shima ya shiga side dinshi ya tasheta suka tafi...saida suka hau kan titi yace"Sir where are we going to.."a takaice yace dashi"home"...driver bai sake mgn ba ya kama hanyan airport road...suna isa gida ya bude mota ya fita still yana dafe da kanshi ko wayoyinshi daya ajiye nan kusa dashi bai dauka ba...Mr Obi ya kwashi wayoyin da suit dinshi yabi bayanshi dasu...yana shiga kai tsaye ya kama hanyan part dinshi bai ko lura da Mummy dake zaune parlor ba...ganin yanda yake tafiya yana hada hanya kuka ga head dinshi dake rike har yanxun Mummy ta kira sunanshi"Bobby"...juyawa yayi yana kallonta still yana rike da head dinshi yace"Mummy"...nuna masa kusa da ita tayi tace"zo nan"..ba musu ya juya zuwa cikin parlon...ya zauna nan inda ta nuna mashi snn ya sauke hannunshi daga kanshi yana kokarin daidaita kanshi wai kar su fahimci yana cikin wani hali...Mummy da duk kokarinshi saida ta fahimci halinda yake ciki da igbo tace"what is wrong with u?.."kakalo murmushi yayi kafin yayi mgn tace"karka fara cemin you are fine nasan you are not..why kake rikeda head dinka haka?.."lumshe idonshi yayi tareda dora head dinshi kan shoulder dinta yana sauke numfashi...hannu takai tana shafa head din nashi tace"fadamin meya sameka Bobby?.."dago kan nashi yayi a hankali yana kallonta kawai sai yaji hawaye sun ciko mashi ido...baidai bari sun zubo ba amma idanun sai shinning sukeyi sbd hawayen dake cikinsu..ganinshi a gabanta sai yaji damuwan na sake mishi yawa zuciyarshi yayi wani irin rauni da sam baiyi irinshi ba daxu...hankalin Mummy ya tashi da ganin kwalla a idanunshi a rikice ta sake bude baki zatayi mgn ya kuma maida kanshi shoulder dinta murya can kasa yace" i just want to be alone Mummy..please!"batayi yunkurin hanashi ba ta dago kan nashi tana gyada kai tace"it’s ohk u can go..we’ll talk later"...bai sake cewa komai ba ya mike yana sake dafe head dinshi ya wuce flat dinshi yana takawa da kyar sbd nauyi da legs dinshi sukayi mashi...da kyar ya iya kai kanshi parlor ya fada kan three seater yana sauke numfashi...har yanxu wani irin ciwo heart dinshi yake mishi..wani irin zafi yakeji a cikinta kaman ana hura huta a ciki...shidai yasan da kyar idan Lamido batayi ajalinshi ba...baisan meyasa Allah zaiyi masa irin wnn jarrabawa a kanta ba...shi har yanxu ko kusa zuciyarshi bai ta6a bashi cewa there is a reason behind abunda yakeji ba kawai gani yake sbd amanarta da daddy ya bashi ne...da kyar ya iya mikewa ya kai kanshi ciki tareda fadawa bathroom ya sakar ma kanshi ruwa batareda ko kayan jikinshi ya cire ba...saida ya gama jikewa tsaf snn ya rage kayan yayi wanka ya fito daure da towel a waist dinshi...jallabiya kadai ya iya zurawa a jikinshi ya maida towel din bathroom snn ya dawo ya kwanta kan sofa yana sake jin yanda ciwon kanshi ke karuwa...baifi minti shidda da kwanciya ba bacci yayi gaba dashi...dama shi haka yake indai 6acin rai yakai 6acin rai kanshi zaiyita ciwo sai ya samu yayi baccin nan yake samun saukin ciwon. Lamido na fita daga office din nashi kai tsaye inda classes dinsu yake ta nufa tanata faman kuka kaman wanda akama duka dan bazata iya komawa can wajen ba...a hanya suka hadu da Sa’eed da Billy da suka fito nemanta...tana hada ido dasu ta sake rushewa da kuka...yana mata ciwo that ya kirata da mai biye biyen maza a takaice dai yana nufin ita karuwa ce...tunda take ba’a taba fada mata mgn daya tsaya mata a rai kamn wnn ba...wato dama duk kallon da yake mata knn amma ya cuceta...tambayan dunia sunyi mata amma taki tsaida kukan ballantana ta fadi abunda ke damunta...saida kyar aka samu ta dakatar da kukan tareda yi musu bayanin abunda ya faru...gaba daya sukayi shiru Billy ta juya ta kalli Sa’eed shima ya kalleta suna hada ido kowa ya shiga kunshe daria...dagowa tayi tana kallon Bily ganin yanda daria ke neman kufce mata ta sake juyawa ga Sa’eed shima taga the same thing kawai saita kifa face dinta akan hannayenta ta sske rushewa da kuka...mikewa Sa’eed yayi da sauri ya karasa inda take yace"besty nidai ba ruwana wlh..Billy ce naga tana daria"...tun kafin ya rufe baki itama Billy ta matso inda suke tace"nima ba ruwana wlh..aishi kika ga yana daria"...dagowa tayi tana goge hawayenta bata cewa kowa komai ba kawai ta mike a fusace ta fice daga wurin sukabi bayanta da sauri ita kuma da taga haka kawai ta kwasa a guje ta haura sama...har kusan durkushewa suka kusa yi sbd daria...yanda ta fita a gujen ne ya basu daria sosai ba kadan ba...saida sukayi mai isarsu snn suka haura saman suma...kai class dinsu suka shiga basu sameta a ciki ba...ita kuwa dama tana haurawa can kusada class din karshe taje ta tsaya tana cigaba da hawaye...tana ganin shigarsu class dinsu tabi ta dayan staircase dake nan kusada inda take ta sauka qasa...kai tsaye gate ta nuf ta fita daga makarantan daga ita sai uniform dinta a jiki da wayanta a hannu...tana fita tayi dialing number baby...yana kan hanya shida driver dinshi yaga kiranta...yana dauka kafin yace wani abu yaji sheshshekar kukanta..muryanta na fita da kyar tace"Babyyy..."hankalinshi ne ya sake tashi sosai yace"baby meya faru?..why are u crying?.."da kyar ta sake cewa"baby kazo makarantan mu..ina bakin gate"...tun kafin ta rufe baki yace"gani nan zuwa yanxun nan..just stop crying okay?.."daga mishi kai kawai tayi tana kashe wayan...ganin zasu iya hangota daga nan inda take tsaye sai ta dan matsa gaba kadan ta samu inda ta tabbatar bazasu iya ganota daga cikin school din ba ta zauna...after like 20 mins Prof ya karaso makarantan...tun kafin ya kirata ya hangota nan inda take dan haka yace ma driver dinshi yayi parking mota shi kuma ya bude ya fita ya tsallaka titi zuwa inda take...tana ganinshi ta mike tana sakin wani kukan kaman wanda uwa da ubanta suka mutu...hankalinshi ya sake tashi sosai yana isa kusada ita yayi kasa da voice dinshi yace"baby girl a bar kukan haka mana indai baso kike ki karasar min da dan ragowar nutsuwata ba"...hannu takai ta share hawayen nan yaga idanunta sunyi suntum face dinta yayi jajir sbd kuka...da kyar ya samu ta dakatar da kukan suka tsallaka titi zuwa inda motarshi yake...da kanshi ya bude mata back seat ta shiga shima ya shiga driver already dama yana ciki dan haka ya tada motar suka wuce...bayan sun dau hanya ya tambayi inda zai kaisu Prof yace"ka kaimu valentino"...ba musu ya kama hanyan Valentino dasu...har suka isa baice mata komai ba banda kallonta da yakeyi yanajin kukanda ta kasa dakatarwa ba ta6a masa zuciya...suna isa ya bude mota ya fita itama ya bude mata ta fito...ya debo kudi masu yawa daga pocket dinshi ya bama driver yace"ga wnn ka samu ka koma gida malam Lukman idan mun tashi tafia zan tuka da kain"..ba musu malam Lukman ya amsa kudi tareda godia snn ya juya ya tafi...shi kuma ya nuna mata hanya alaman ta wuce ba gardama itama tayi gaba yabi bayanta...Vip section yayi musu reserving ba tareda yayi ordern komai ba don duk hankalinshi tashe yake sbd kukan nan da yaga tanayi...bayan sun zauna yayi facing dinta cikeda damuwa yace"baby idan baso kike ki fasamin zuciya ba ki bar kukan"...ba musu tayi kokarin tsayar dashi tacigaba da goge hawayenta...ya zaro handky daga aljihunshi ya shiga goge mata tears din dashi...batace komai ba sai lumshe ido da tayi har ya gama snn yace"now tell me abunda ya faru"...bata 6oye komai ba ta fada masa duk abunda ya faru tun daga ranan da yace bazatayi participating ba har zuwa daxu da maganganun daya fada mata...tunda ta fara mgn Prof yayi shiru yana kallonta har takai aya bai iya cewa komai ba...kallonta kawai yakeyi while gaba daya hankali da tunaninshi suna wani wajen...tsoro yakeji kada ace proprietor din nasu sonta yakeyi don a wnn labarin data bashi yasan definitely akwai lauje cikin nadi..bai yiwuwa ya dinga kishinta kawai sbd mahaifinta ya bashi amanarta...hankalinshi yaji ya tashi sosai sbd baison wani yazo ya kwaceta daga gareshi...ganin yanda yayi zurfi cikin tunani Aysha ta kira sunanshi..ya dago yana dubanta tareda sauke ajiyar zuciya still ya rasa abun cewa...turo baki tayi kaman zataci gaba da kuka tace"yanxu baby bazaka ce komai ba?.."wani ajiyan zuciyan ya kara saukewa kafin a hankali yace"inso inyi mgn da daddynki plss..when zaki hadani dashi?.."shiru tayi tana kallnshi cikeda mamaki tace"is that all u could say?.."kamo hannunta yayi for the very first time a rayuwarshi yace"baby duk wnn abun da kikaga yanayi its all out of love..kishinki yakeyi sbd yana sonki ni kuma banaso wani ya kwaceki daga gareni shiyasa nakeso ki bani dama inje Gombe muyi mgn da daddy"...kallonshi kawai takeyi full of suprise..like how on earth ma zai fara wnn tunanin..how could all that masifa da bala’in da yake mata turned out tobe love...how could this happened?..ina wnn zance akwai gayara cikinshi..sam bazai ta6a yiwuwa ba hakan bazai ta6a faruwa ba...ganin yanda tashin hankali da tsoron rasata ke tubuce kan face dinshi sai tayi kasa da murya tana binshi da kallon daya kusan zautar dashi tace"baby calm down plss...calm down wnn abunda ka fada sam ba haka bane...there is no way da za’ace wnn mutumin yana sona..bazai ma ta6a faruwa bane so relax..babu wanda zai kwaceni daga gareka am only yours"...girgiza kai ya shigayi still hankalinshi ba kwance ba yace"baby you won’t understand..na tabbata ko rantsuwa nayi yaron nan sonki yake bazanyi kaffara ba..idan ba haka ba why zaisa maki ido haka?..why zai hanaki participating kan abunda yasan ba laifi bane"...dafe goshi Aysha tayi tanajin yanda duk ya fadi kalmar son nan takejin wani irin radadi a zuciyarta..ita tanada yakinin ba sonta yakeba kawai yanayi ne sbd daddy ne ya bashi daman hakan amma ita tasan babu wani abu makamancin love a tsakaninsu...ganin yanda tayi shiru ta dafe kanta yace"so yanxun ma bazaki barni inje wurinshi ba kou?..baby anya kuwa kina sona?.."da mamaki ta dago tana kallonta ta wani kwabe fuska kaman zatasa kuka tace"haba baby how could you say this.."tana rufe baki yace"to baby idan bance haka ba me kikeso ince?..idan da gaske kina sona why kike gudun haduwana da mahaifinki?..why bakison inje sbd mgnr auren..."tun kafin ya karasa ta rufe mashi bakin da hannunta tana kallon tsakiyar idonshi da nata idon da har yanxu bai dawo normal ba tace"dan Allah baby stop saying this?..how could you say bana sonka?..wlh ina sonka..i love u sosai"...ta karasa mgnr hawaye na ske ciko idanunta...zuwa tayi gareshi sbd tasan zai share mata hawaye kuma yasa ta manta da damuwan da take ciki amma shima sai gashi yana neman kara mata akan wanda take ciki...hankalinshi ya sake tashi ganin zata fara mishi kuka yace"Noo..karki bari su zubo dan Allah"...ai kamar cewa yayi ma su zubo nan suka shiga sintiri kan fuskanta...sake matsawa yayi jikinta sosai ya lumshe ido kawai sai ya janyota jikinshi yana sauke numfashi...soyayyarta yakeji na sake ratsa ko ina na jikinshi...yana sonta fiyeda tunani amma gashi kiri kiri yana nema ya rasata sbd tsoron ta hadashi da mahaifinta...kuka takeyi sosai a jikinshi tayi wani luff kaman jariria..baiyi yunkurin hanata kukan ba sai shafa bayanta da yakeyi a hankali...saida suka dauki lokaci mai tsaho a haka kafin ya samu ta tsayar da kukan snn ya dagota daga jikinshi ya shiga goge mata hawaye...idanunta lumshe har ya gama snn ya sake yin kasa da murya yana kallon bakinta da take pouting yace"Aysha please!..ki bani dama inje in ganshi kada wani yazo daga baya ya shiga tsakanina dake"...sake kwa6e fuska tayi zatasa wani kukan da sauri yace"dan Allah Noo..why kikeson tayar min da hankali ne.."baki a tunzure tace"ni ka dena mgnr za’a kwaceni daga gareka banaso..mgnr zuwa wurin daddy kuma ka bani lkci in fara mgn da Hammana duk yanda mukayi dashi zakaji"...kallonta yake kafin yace"U sure?.."ta wani langabe kai tana kallonshi tace"yes sure"...murmushi ya saki mai kyau tareda fadi"na yadda dake my baby..yanxu me kikeso a kawo maki kici.."murguda baki tayi tana makale shoulder dinta tace"ooh bazanci komai ba tunda har yanxun baka yadda ina sonka ba"..another smile ya kara saki kafin yace"sam ba haka bane baby kawai dai inajin tsoro ne..kinsan duk lokacinda kake son mace mai kyau hankalinka bazai ta6a kwanciya ba idan ba daura maku aure akayi ba"...dan murmushi itama ta saki murya can kasa tace"to ka kwantar da hankalinka in Allah ya yadda Aysha Ahmad Lamido batada mijinda ya wuce Professor Ahmad Kurawa"...sake fadada smile dake fuskanshi yayi yace"to Allah ya nuna mana ranan da Aysha Ahmad Lamido zata zama property din Prof Ahmad Abdu Kurawa"...murmushi itama ta saki shima yanayi kaman ba sune ke 6acin rai a while ago ba...nima kaina da nake dauko maku rahoto bansan lokacin da na furta"soyayya ruwan zuma"..akace idan kasha kaba masoyi...i hope dai gaba dayanku kunya ba masoyanku?🤪...lol A can makaranta kuwa Billy da Sa’eed hankali tashe suke nemanta sun kuma rasa inda ta shiga...duk inda suke tunanin zasu ganta sun duba basu ganta ba...wasa wasa har yamma yayi likis basu dena nemanta ba kuma basu ganta...hankalinshi idan yakai dubu duk a tashe suke gashi mutane har sun fara raguwa cikin makarantan ba Lamido babu dalilinta...Billy kaman zata sa kuka take dubanshi tace"nidai wlh ba ruwana kaine ka farayi mata daria bani ba..kan wane dalili ma zaka fara mata daria bayan kasan bataso?.."da mamaki sosai yake kallonta yace"Seriously?..gaba daya laifin zaki dora a kaina sbd ga sarkin laifi koh?.."cikin tsiwa tace"laifinka ne mana tunda ka fara mata daria..yanxu idan bamu ganta ba ya zanyi ni Bilkisu?..dan Allah ina kake tunanin zataje?.."shiru Sa’eed yayi yana tunanin inda zata iya zuwa can yace"bakida number babyn nan nata?.."girgiza kai Billy tayi tace"bani dashi"..shiru ya sakeyi yana tunani Billy tace"ko Proprietor din zamu kira ko yasan inda take?.."girgiza kai yakeyi yace"i don’t think zaisan inda take gaskia..besides ke kanki kinsan besty ba fada mai zatayi ba"...cikin hankalin dake karuwa Billy tace"nasan bazata fada mashi ba amma at least zai iya taimakawa wajen gano inda take..dole muna buqatan taimakon wani babba and sanin kanka ne bazan iya kiran gida in fada ba amma shi idan na fada mishi na tabbata zaiyi wani abu akai tunda daddy ya bashi amanarta kuma shine yayi sanadin komai dake faruwa"...gyada kai yakeyi cikeda gamsuwa yace"yea kinada point..amma a ina zamu number dinshi?.."tace"bamu dashi amma sai mu tambayi provost ya bamu"...zaro waya Sa’eed yayi daga pocket dinshi yace"let me call Dr Aslam nasan bazai rasa numbershi ba"..daga haka yayi dialing number da yayi saving as Dr Aslam a wayarshi...yana fara ringing doc Aslam ya daga nan Sa’eed yace mishi number Dr Bobby yake nema babu 6ata lokaci kuwa ya turo mashi...message din na shigowa ya dubi Billy da har yanxu hankali ke tashe yace"yauwa gashi ya turo..dauko wayanki ki kirashi"...ba musu Billy ta dauko wayanta ta kwashi numbers din da aka turo snn tayi dialing...har ya gama ringing bai dauka ba sai ta sake kira...a takaice saida ta jera missed calls kusan 7 bai dauka ba hakan kuma ya sake tada hankalin hajia Bilkisu...bata hakura ba haka tayita jera masa kira har saida taji ya daga...tana jin ya dauka tayi saurin cewa"Sir sunana Bilkisu Muqaddas nice muke tareda Aysha Lamido..sir wlh tun daxun muke nemanta school din nan bamu ganta ba gashi har dare ya fara shine nace we should call ko akwai taimakon da zaka iyayi mana"...tunda ta fara mgn Bobby da har yanxun yake kwance baice mata qala ba..sauraronta kawai yakeyi yanajin yanda maganganunta ke shiga direct to his heart suna sake lalata mishi ita...ciwon kan daya fara mishi sauki nan take ya sake dawowa...da kyar ya iya bude bakinshi yace"where are u now?.."da sauri tace"school.."yace"will be coming right away"...da sauri tace"mun gode sir..Allah ya saka da alkhairi"..shidai bai sake cewa komai ha ya kashe wayarshi. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 220891344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 26 Mikewa ya samu yayi daga kwancen da kyar yanajin yanda ciwon kan daya samu ya fara raguwa na sake dawowa sabo...shikam baisan dalilinda yasa Allah ya hadashi da Lamido ba amma for sure ya fara tunanin ba alkhairi bane haduwan nashi da ita..gaba daya nema take ta zame mishi tauraruwa mai wutsiya da tunda ta shigo rayuwarshi take kokarin canxa mishi ita...yana mikewa wani jiri ya sake daukanshi don saura kiris ya fadi a kasa yayi saurin dafa wall da yake tsaye kusa dashi...da kyar ya karasa first aid box dinshi ya dauki maganinda yasan zaiyi saurin saukar mashi da headache da dizziness din yayi dispensing ruwa yasha snn ya koma kan sofa ya sake kwantawa for like 10 mins kafin ya dan ji dizziness din ya ragu dan haka ya mike ya dauki car keys dinshi ya fita...Mummy da har yanxun ke zaune parlor tana ganinshi ya fito da keys a hannu ga kuma yanda yake tafiya shows har yanxu akwai sauran matsala tattare dashi tace"ina zakaje kuma?.."kallon inda take yayi kafin yace"Hospital zanje Mummy...ba dadewa zanyi ba"...cikeda concern tace"amma bazaka iya driving a haka ba Bobby..kaga yanda kake tafia kuwa?.."dan murmushi ya saki ba karfin hali yace"Mummy don’t worry ba abunda zai faru..ya zama dole ne fitan shiyasa zanje"..bata sake cewa komai ba sai kai kawai data gyada mishi...shi kuma ya juya ya bar parlon walking slowly sbd kar taga yanda jirin da yakeji ke neman affecting tafiyan nashi...yana fita ya fada mota yayi mata key ya fita daga gidan...a hankali yake tafia sbd gudun problem don yasan idan yace zaiyi gudu a halinda yake ciki tsaf za’a iya samun matsala...cikin 35 mins ya iso makarantan bai shiga ciki ba yayi parking nan bakin gate snn ya kira number da Billy ta kirashi dashi daxu...tana dauka yace"am at the gate"..snn ya kashe wayan...Billy ta mike da sauri tana duban Sa’eed tace"kaji proprietor har yazo..yana bakin gate"...Sa’eed baice komai ba ya mike suka fita bakin gate din...suna tsallako titi suka nufi inda suka hangi motarshi...kanshi na hade da starring motan ko noticing dinsu baiyi ba saida Billy tayi mgn...da kyar ya iya dago kan nashi yana kallonta da eyes dinshi da sukayi jaa sbd headache da kuma damuwa yace mata"so kince kun duba ko ina baku ganta ba?.."da sauri tace"eh wlh tun dazu muke nemanta bamu ganta ba"...da kyar ya sake fadin"kuma baku tunanin she might have gone to someone a nan cikin gari like a friend or family?.."gaba daya shiru sukayi can Sa’eed yace"ina tunanin zata iya zuwa wurin baby"...juyawa Bobby yayi yana kallonshi da kyau yace"who was that?.."kai tsaye Sa’eed yace"saurayinta ne..sunanshi Professor Ahmad"...kallonshi kawai Bobby keyi yana kankance idanu tsabar bala’i...yanxu rashin hankalinta har yakai ta dauki kafa takai kanta wajen saurayi?..innalillahi wainna ilaihi rajiun?..wnn wace irin yarinyace?..lokaci daya ciwon kan daya samu saukinshi ya sake dawo mishi kaman zai rabe biyu...shima dizziness din kaman jira yake a fadi wnn mgnr sai ya ninku akan wanda yakeji a baya...6acin ranshi ya fito karara wanda hakan ya basu mamaki sosai...maida kallonshi yayi ga Billy dake gefe murya a cushe yace"have u tried calling her?.."da sauri Billy tace"tun daxu naketa kira bata picking".."ki sake kira"...ya fada mata feeling extra hot inside...ba musu Billy ta dauko waya ta sake dialing numberta..tana kokarin kaiwa kunne yace"put on speaker"..still batayi mashi musu ba tayi putting a speaker din nan sukaji kiran ya fara shiga amma har ya katse bata dauka ba...ta sake kira still no answer sai a karo na kusan takwas Prof da yaga anata jera mata kira tun daxu yace"yanxu baby bazaki picking calls dinki ba?.."turo baki tayi tace"nidai bazan dauka ba nasan Billy ne ko besty ke kira kuma fushi nakeyi dasu ni"..girgiza kai kawai Prof yayi tareda kai hannunshi ya dauki wayan..daidai lokacin wani kiran ya sake shigowa dan haka ya dauka ganin Billy ce ke kira...a daya 6angaren sunajin an daga Billy tayi saurin cewa"Lamido ina kika tafi kika barmu cikin tunani haka?..and why aren’t u picking my calls?.."dan murmushi ya saki jin yanda take mgn da damuwa yace"Bilkisu relax kinji koh?..tana tare dani yanxu haka"...wani irin darammm Bobby yaji kaman saukan aradu a cikin ziciyarshi..knn da gaske wurin saurayin nata ta tafi?..Billy da taji abunda ya fada ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"shiknn Prof nagode..tell her idan ta bari raina ya 6aci saina hadata da Ammi ko daddy wlh"...Prof yace"No inshaAllah bazai kai ga haka ba...yanxu xan dawo muku da ita"..gyada kai kawai Billy tayi ta kashe wayarta Sa’eed kuma na daga gefe baice komai ba...juyawa sukayi ga Bobby daya jingina kanshi da kujera ya dora right hand dinshi kan chest dinshi daidai saitin heart dinshi da yaji kaman zai faso kirjin ya fito sbd irin bugawan da yakeyi...wani irin zafi yakeji that har zata kwashi jiki taje inda saurayinta..abun yanayi mishi ciwo sosai fiyeda tunanin mai karatu...har yanxun eyes dinshi are closed don ji yakeyi kaman duniyan na zagayawa dashi...kanshi kuma na wani irin sarawa kama ana doka guduma akai...duk wani abu da yake tunanin yanaji daxun wnn da yakeyi yanxu is far more than wancan...ashe daxu somin ta6i ne kawai akayi mashi dan bai farajin komai ba sai yanxu..yanxu ne yakejin real ciwon kai da zuciya suna neman su hallakashi...daga Billy har Sa’eed tsayawa kawai sukayi suna binshi da kallo..yanda yake jujjuya kanshi from side to side da kuma hand dinshi dake dafe da his heart shows ba karamin ciwo yakeji ba...kamar yasan tunaninda sukeyi ya samu ya dago kanshi da kyar ya bude idanunshi a kansu wanda ba shiri gaba daya sukayi kasa da nasu don idon babu kyawun gani sam..idanunshin that ko lafia lau ma suke firgita mutum inaga kuma sun sauya launi haka?..bai damu da dauke idon nasu ba ya maida glasses dinshi sama tareda kwantar da kanshi jikin starring su kuma ganin haka sai suka tsallaka titi suka koma makaranta abunsu...saida ya dauki lokaci mai tsaho yana fama da kanshi kafin ya dago yana kokarin kunna motan...kawai haushin kanshi yakeji na fitowa da yayi ma at the first place..yasan da baizo ba ba yanda za’ayi yaji labarin tana wurin saurayinta ma balle ya karama kanshi bala’i cikin masifan da yake ciki...tada motan yayi ya haura kan titi yana tafiya slowly sbd yanda yakejin jikinshi...tafiyan minti uku kadai yayi yaji motan na barazanar kwacewa daga hannunshi sbd dizziness da har yanxun bai sakeshi ba..dole haka ya gangara gefen titi yayi parking tareda kashe motan ya sake kwantar da kanshi da starring...tunanin wanda ya kamata ya kira yake tunda dai yasan ko yasha giyan wake bazai fara daukan hanya yana a wnn halin ba..shidai wnn yarinya Lamido take ko Gidado ta cuceshi wlh..sam ya rasa abunda tayi mashi da yakejin irin wnn abun a kanta...sunyi fada da Nur daxu so bazai ma fara kiranshi ba..driver dinshi kuma yasan yanxu yana gida tareda iyalinshi shi kuma sam bai son ya katse mishi jin dadi ga Sab yana school da sai ya kirashi..Mummy kuma koda wasa bazai fara kiranta ba sbd yasan tambayoyi ne zai shasu kaman yana court...daga karshe dai daukan wayanshi yayi ya kira aunty sumy ya fada mata inda yake yace tazo ta daukeshi that he can’t drive...hankali tashe kuwa ta fita daga gida ta dauki drop din napep har zuwa inda yake...tana sauka ta biya mai napep kudinshi snn ta nufi inda ta gano motan nashi..saida tayi knocking sau uku snn ya samu ya bude mata...tana shigowa ciki ta shiga binshi da kallo ganin yanda lokaci daya kamanninshi suka sauya cikin igbo tace"Bobby lafia kuwa?..meya sameka haka?.."da igbo din shima ya amsa mata da"it’s nothing serious..just headache"...girgiza kai ta shigayi tace"ban yadda da abunda ka fada ba gaskia..you seems disturbed..kodai you are hiding something?.."girgiza kai ya shigayi shima cikin karfin hali duk a kokarinshi na kar ta dauki abun da zafi yace"aunty sumayya i am fine believe me..headache ne kawai ke damuna and am sure it’s stress..da zaran na samu bacci zai dena"...kallonshi kawai aunty sumy keyi kaman bata yadda da abunda ya fada ba...shi kuma bude motan yayi ya fita daga driver seat ya zagaya inda take zaune itama ta fito ta nufi driver seat shi kuma ya bude nan inda ta fito ya shiga ya jingina kanshi da kujera yana lumshe ido..bayason jin another tambaya da zai fito daga bakinta dan baisan amsan da zai bata ba...right now ba abunda yake bukata kaman yajishi alone..so yake ya ke6e shi kadai koya samu yayi jinyar zuciya da gangar jikinshi da kyau dan ji yake kaman sun dena aiki na wucin gadi...shi kadai yasan what is taking place in his heart sai kuma Allah daya halicci zuciya ya kuma baiwa kanshi kadai daman ganin abunda ke cikin kowacce zuciya...itama lura da hakan da tayi yasa ta tayar da motar kawai ta harba kan titi...har suka isa gida ba wanda ya sake mgn cikinsu..bayan tayi parking kafin ta bude ta fita yace mata"aunty karfa ki gayawa Mummy wani abu please..kinsan yanda take yanxun kina ce mata kinzo kin daukeni duk tashin hankalinta zatayi"..girgiza kanta tayi tace"bazan fada mata ba amma da gaske ban yadda da abunda ka fada ba Bobby..sam ban yadda onlh headache ke damunka ba..kaga yanda ka koma kuwa?.."dafe head dinshi yayi yanajin yanda ciwon kan ke neman karuwa sbd wnn maganganun da yake..kwata kwata ko bude bakinshi bai sonyi sbd azaba..shi kadai yasan halinda yake ciki...aunty sumy ta bude mota ta fita shima ya fito suka nufi entrance din gidan...Mummy na zaune parlor itada su Miemie da Ilham su suna kallo ita kuma hankalinta gaba daya na wani wajen data kurama id tana tunani...tanajin sallamarsu ta dago tana kallonsu Bobby bai yadda ya hada ido da itaba ya wuce flat dinshi sbd bayada amsan tambayoyin da yasan matukar yaje inda take sai tayisu...idonta a kanshi har ya shige flat dinshi snn ta maida hankali kan aunty sumy dake karasowa parlon..tana zama ta dubi su Miemie da suka hada kai suna kallo tace"Miemie kuje parlona ku cigaba da kallon"...ba musu Miemie ta mike ta kama hannun ‘yar uwarta suka bar parlon...bayan sun fita Mummy ta dubi aunty sumy hankali tashe tace"ya fada maki abunda ke damunshi?.."girgiza kai kawai aunty sumy tayi tace"yaqi fada Mummy..wai headache ne kawai ke damunshi amma ni nasan karya yake there is more to it..Mummy ko zaki gwada tambayanshi ko zai fada maki?.."sauke ajiyar zuciya Mummy tayi tace"nima dazu dana tambayeshi bai fadamin komai ba amma i will try again zuwa safe ko zai fada"..cikeda gamsuwa aunty sumy tace"eh hakan ma yayi..and Allah sa ya fada"..Mummy tace"Ameen"..cikin raunin murya sosai..kwata kwata batason abunda zai ta6a mata yaranta ko kadan musamman shi daya kasance guardian dinsu..kuma bata ta6a ganinshi cikin yanayi irin wnn ba tun bayan rasuwan mahaifinsu..to menene wnn dayasa shi fita daga hayyacinshi haka?..me yake damun yaron nan ne?..(nidai nace da kyar idan ba love bane mummy).🤪 Washegari ganin har wajen 11 bai fito ba Mummy ta hada breakfast dinshi ta nufi flat din nashi...yana zaune kan gado ya jingina jikinshi da jikin gadon idanunshi a lumshe dagashi sai singlet da shorts a jikinshi...Mummy ta karasa ciki ta ajiye abincin data shigo dashi kan table snn ta karasa gefen gadon nashi ta zauna kuma har ta zauna din baisaniba sbd nisa da yayi cikin tunani...kallonshi Mummy ta tsaya yi for like 5 mins tanajin tsananin taysayinshi yana ratsata...dukda bata san ainihin abunda ke damunshi ba ta tabbata abune mai girma tunda har ya saka abun cikin ranshi haka...yanada sa abu a rai sosai shiyasa duk wani abu da zai zame mishi damuwa bata kaunar ya ra6eshi sam..hannu takai ta dora forehead dinshi tanaso taji ya temperature dinshi yake aikam taji shi zafi zau kaman ana hura huta...a hankali ya bude idonshi yana kallonta hankalin Mummy ya tashi sosai da ganin idanun nashi...tun yana yaro tasan idan har idanunshi suka sauya din nan to ciwon da yakeji yakai ciwo knn...nan take hawaye ya cika idonta tana kallonshi da kyau tace"Attahir..."da kyar ya iya bude idanunshi ya saukesu a kanta..tace"meyake damunka?.."idanunshi ne suka ciko da hawaye dan yana ganinta yaji wani irin rauni ya dirar mishi kawai sai ya matsa jikinta ya rungumeta yana runste ido...kwalo idanu Mummy tayi waje tanajin yanda ya matseta jikinshi kaman zai 6allata wnn ma is another reason da ya sake tabbatar mata da cewa yana cikin damuwa...hannu takai tana shafa kanshi a hankali tanajin yanda heart dinshi ke beating da karfi kaman zai fito waje...shiko Bobby bakin kokarinshi yake na ganin bai fito da hawayen daga idonshi ba sbd a ganinshi yin hakan ba karamin abun kunya bane a gareshi..wai duk fadin dunia ya rasa wanda zai zubda hawaye kanshi sai Lamido?..yarinyar da dama ya tsaneta from the beginning..jiya ko baccin kirki kasayi banda abubuwanda suka faru ba abunda yake tunawa..gaba daya komai yayi masa tsaye cak and abunda yafi bashi haushi knn sbd yana ganin kwata kwata bai cancanta yana jin wani abu makamancin haka a kanta ba..sam bai dace ba shiyasa shi kanshi yakejin haushin kanshi kuma dui kokarin na yaga yayi stopping abun kasawa yayi...saida suka dauki lokaci mai tsaho a haka kafin ya dago daga jikinta a hankali yana yin kasa da ido sbd kar ya hada idanu da ita..Mummy takai hannu ta dago idanun nashi tana dubanshi sosai tace"fadamin..what is the matter with u?.."hannunta ya kamo ya rike cikin nashi yana kallonta shima ya rasa abunda zai fada..kawai tunani yake me zaice mata yana damunshi dan dai da kunya yace mata kan yarinya karama yake wnn abun...shidai zuciyarshi batayi mashi adalci ba wlh...ganin kallon da ya zuba idanu yana mata ta sake kiran sunanshi...ya lumshe ido ya bude cikin ranshi yana addu’an Allah yasa ta bar zancen amma sam Mummy ta dage sai taji damuwanshi...ganin ba hakura zatayi ba ya tattaro duk wani karfin hali da dakiya irin nasu na maza kafin yace mata"dama..mummy..it’s about a girl"...tun bai rufe baki ba Mummy ta wara idanu tana kallonshi tace"u mean kana son wata yarinya?.."girgiza kai ya shigayi da sauri yana wani ta6e baki jin abunda ta fada yace"Mummy Noo..wata yarinya ce kawai mahaifinta ya bani amanarta shine ita kuma take kokarin tasamin ciwon zuciya"...kallonshi Mummy keyi full of suprise don har yanxu bata fahimci inda zancenshi ya dosa ba..shima ganin kallon da take mishi sai ya shiga bata labarin tun haduwar da sukayi da daddy a college zuwa yanda ya gane shi son din Col Attahir ne da irin maganganun daya fada kan mahaifin nashi har zuwa yanda yace ga amanarta ban ya bashi yanaso ya kula da ita sbd batajin mgn...Mummy tayi shiru tana sauraronshi har ya gama kallonshi kawai takeyi dan she smells something cikin maganr nan nashi...tasan wanene shi sarai dan haka tafi kowa fahimtan halinda yake ciki fiyeda kowa a dunia and cikin maganganun daya fada ta tabbata ko ba son yarinyar yakeyi ba tabbas yanada interest akanta har tunda yake kishinta haka?..ita kuwa inama zataga wnn yarinya ta samu tayi mgn da ita?..inama Allah zai kar6i addu’anta ya zarginda takeyi ya zama gaskia?..inama zat...bata kai ga karasawa ba taji hannunshi a jikinta yana dubanta yake fadin"Mummy tunanin me kikeyi ne wai?.."dan murmushi ta saki tareda kama nashi hannun itama still tana smiling tace mishi"yama sunan yarinyar kace?.."hade rai yayi yana kallonta yace"Mummy me zakiyi da sunanta kuma?..yarinyar da ina fada maki tana kokarin halakani shine kikeso kiji sunanta?.."murmushi ta kara saki tace"nidai fadamin sunanta plss..watarana ma so nake ka kawomin ita mu gaisa"...da mamaki sosai ya tsaya yana kallonta jin abunda tace...shi bai gane me take nufi ba sam ya ya kawo mgnr da ya kamata ta tayashi jaje amma sai behaving take kaman wani abun celebration ne ya faru...daddagewa yayi ya kwa6e fuskanshi kaman zaisa kuka yace"Mummy manaa..meye haka kikeyi plss?.."daria sosai ta saki kafin ta dakatar dashi tana sake dubanshi tace"to yanxu tell me meya kamata muyi?.."gyara zama yayi yana dubanta in a serious tone yace"shine abunda ban saniba Mummy..na rasa wace irin yarinyace ita..wlh jiya ko bacci banyi ba sbd haushin data kunsamin shiyasa har yanxu kaina bai dena ciwo ba..na rasa meyasa na kasa mantawa da komai har zuwa yanxu"..sake kamo hannunta yayi ya rikesu gam idonshi na sake canxa launi yace"Mummy ya zanyi in manta plss...inaso in manta"...ajiyar zuciya ta sauke tana kallon yanda duk yanayinshi ya sake sauyawa dan haka ta kwantar da murya tace"karka damu watarana zaka manta inshaAllah..ni wnn damuwan naka ne banaso kaga har yanxun jikinka akwai fever..inaso ka nutu ka kwantar da hankalinka sosai snn kayima kanka treatment kuma ka dena damuwa dan idan baka denaba ko kayi treatment dinma a banza zai tashi..ko kanaso wani ciwon ya kamaka ne?.."girgiza kanshi yayi da sauri yace"definitely not because of that stupid girl"...Mummy tace"then ka dena damuwa..yanxu ga breakfast na kawo maka ka shiga kayo brush zanyi serving dinka"...baiyi musu ba ya mike tsaye da kyar snn ya shiga takawa a hankali zuwa bathroom dinshi...mummy tabishi da kallo tana tausaya mashi..cikin ranta tana addu’an Allah yasa dai ba soyayya ne zai wahalar dashi ba don a yanda taga alamunshi soyayya zaiyi matukar bashi wahala sbd yanda yake da riko da kuma sanya damuwa cikin ranshi. Bayan sati daya... Tun daga wnn rana Lamido bata shiga sabgarshi ba..dan gaisuwan ma da take mishi idan sun hadu a hanya ta dena snn idan zai shekara kiran wayanta bazata dauka ba...yau tsahon kwanaki uku knn dayake kiranta bata dauka..tana ganin wayan zaiyita ringing amma ko kallonshi bazatayi da sunan dagawa ba...yanayi mata ciwo duk ta tuna da kalmar daya jefeta dashi ranan..wai tana biye biyen maza bi ma’ana dai tana karuwanci..lokaci daya duk wnn tsoron nashi taji ya ragu dan cikin kashi dari tasan yanxu da kyar za’a samu kashi hamsin a cikinshi...su Billy kuwa saida suka dauki lokaci kai tsah suna bata hakuri snn suna saku ta hakura suka cigaba da gudanar da rayuwarsu...shirye shirye sukeyi ma na zuwa Kd bikin Lubna fa za’yi next week suna dawowa kuma ba dadewa zasu fara exams daga nan sai Clinical posting sai kuma su shiga level 3...tsakaninta da babynta kuwa sai sambarka dan soyayya sai kara karfi yakeyi kullum. A hankali ya shigo parlon yana tafiya a hankali kaman mara lafia hannunshi rikeda briefcase dinshi sai dayan kuma rikeda suit dinshi...kallo daya zakayi mashi ka gane bashida lafia sbd dan karen raman da yayi kaman wanda yayi wata a kwance...ya kara wani irin haske da idan ba saninshi kayi ha u will think ko bleaching ya fara...Miemie da Sab ne kadai zaune a parlon suna labari kaman basune ke fada kaman suna ganin hanjin juna ba...he is so lost in thought that har ya kama hanyan Flat dinshi bai lira dasu a parlon ba...Sabeer da bai dade da dawowa ba ya dan daga muryanshi da igbo yace"uncle Bobby sannu da zuwa"..dakatawa yayi tareda juyawa a hankali yana kallonshi yace"yaushe ka dawo?.."Sab yace"ban dade da shigowa ba..ya aiki?.."a takaice yace dashi"fine"..snn ya juya yacigaba da tafiyarshi walking slowly..dagashi har Miemie dankallo suka bishi sbd yanda yake tafia da yanda sukaga damuwa karara kan face dinshi shows kodai wani ya 6ata mashi rai ko kuma yana cikin serious rashin lafia idan akayi laakari da raman da yayi...yana shiga Mummy ta fito daga parlonta tana dubansu tace"kaman muryan Bobby naji yanxu"...Sab ne yace"shine..amma Mummy kinganshi kuwa?..bashida lafia ne?.."Mummy bata iya cewa komaiba ta bishi zuwa part din nashi...yana zaune gefen gado yana kokarin cire takalman kafanshi ta shigo dakin...saida ta isa har ciki ta zauna nan kusada shi snn ta dubeshi da kyau kafin tace"yanxu Bobby bakaji duk fadan da nayi maka ba daxun koh?.."rausayar da kai yayi yana kallonta kaman zaisa mata kuka yace"Mummy to yanxu me nayi?.."tace"kaki ka kwantar da hankalinka ka dena sama kanka damuwa mana...yanxu kana tunanin wnn damuwar da kake zaiyi sorting things out ne?.."rai a 6ace yace"Mummy yarinyar ce ta rainamin hankali...har wace ita da zan dinga kira tana ignoring min call?..har rejecting calls dina fa ta farayi sbd taga ban hadata da babanta ba"...murmushi Mummy ta saki tana kallonshi tace"kenan dai idan na fahimceka ignoring calls dinka da take bai maka dadi ba..u want her to be answering ur calls koba haka ba?.."da sauri ya shiga girgiza kanshi yace"Mummy don’t misinterpret me plss..that’s not what i mean"...tace"then why all this damuwa idan abun bai dameka ba?..why ka kasa cire abun a ranka har yake saka rama haka?.."shiru kawai yayi baice komai ba as basan mezai fada mata ba..sam bashida abun fada..shi kanshi yana mamakin kanshi wai the whole him ne yake damuwa sbd wata can tana ignoring calls dinshi...abun ya dameshi sosai bai abunda bai ta6a tunanin faruwa dashi ba har abada...ganin yanda yayi kicin kicin da fuska Mummy ta kara sakin smile tana cewa"nidai i want u to take it easy on urself plss..i told u kana bata hakuri komai wucewa zaiyi amma baka yadda ba"...tun kafin Mummy ta rufe baki yayi spitting yana fadin"over my dead body"..murmushi har yanxu takeyi tana girgiza kai...wnn hakilon nashi karamin daria yake bata ba wlh..kiri kiri ga abu yana feeling amma dan banzan ego dinshi bazai bari yayi admitting ba...mikewa tayi ta fita daga dakin don kawo mishi abincinshi tunda da dadewa ya yayema kanshi cin abinci tare dasu. Ranan Tuesday karfe biyu ya bar Hospital zuwa College sbd yanason mgn da Nur...tunda incident din nan ya faru basu sake haduwa ba...yasan tunda yaji shiru Nur ko a waya bai nemeshi ba fushi yakeyi dashi...da kanshi ma yayi driving sbd driver dinshi baida lafia...yana shiga cikin premises din bayan yayi parking ya nufi Office din Nur yanata baza ido wai ko zai ganta a nan waje amma ko mai kamada ita bai ganiba. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 27 Yana shiga ya iske Nur zaune kan office chair dinshi yana aiki da laptop yana ganinshi ya wani hade rai yanacigaba da aikin gabanshi ko kallon inda yake baiyi ba...Bobby ya karasa ciki ya zauna yana kallon yanda yake wani ciccin magani kawai saiya saki murmushi yana girgiza kai yace"Man how far?.."banza Nur yayi dashi yacigaba da aikinshi...Bobby ya sake cewa"Man meye haka ne plss?..stop acting like a kid"..tun bai rufe baki ba Nur ya dago yana kallonshi rai a 6ace yace"oh really?..wato I should stop acting like a kid sai kace kai ka manta wulakancin da kayimin harda korana office dinka ba"...saida ya barshi ya gama snn a nutse yace"I wasn’t on my sense..I was furious kai kuma kazo kana so kayi adding to what i was going through shiyasa nayi reacting that way amma am sorry"...wani harara Nur ya dago ya watsa mashi snn yacigaba da aikinshi...Bobby ya dan dafe goshi yanajin kanshi na wani sarawa sbd wnn abunda Nur yake..baisan meya sameshi ba amma shi yanxu sam bayason hayaniya..sam baison matsala idan ba hakaba head dinshi yayita mishi ciwo knn kaman me hypertension...after like 3 mins ya sake dagowa yana dubanshi yace"yanxu bazaka hakura ba dai knn?.."ba tareda ya dago ya kalleshi ba yace"ba haka ake bada hakuri ba ai..kai kanka kasan abunda kayi is uncalled for amma ya zanyi dakai?.."dan murmushi Bobby ya saki yana shafa lallausan gashin kanshi yace"to nace am soryy shikenan?.."sai yanxu Nur ya dago yana dubanshi yace"to yanxu kam na hakura..amma on one condition"...kallonshi Bobby yayi sai kuma ya dauke kai alaman baison wani mgn again..yasan tambayan da zaiyi mishi shi kuma sam bashida amsan bashi...tunanin nashi bai dire ba Nur yace"tsakaninka da Allah meya 6ata maka rai ranan?.."shiru kawai Bobby yayi as bayason fada mishi abunda ya faru...shi kuma Nur dage shoulder dinshi yayi yacigaba da aikin gabanshi yace"idan tayi naji"..qala dai baice mishi ba ya mike hands dinshi a aljihu...Kallonshi Nur yayi yace"so wucewa zakayi?.."yace"yes dama abunda ya kawoni knn?.."Nur ya sake daga shoulder dinshi yace"alright sai Thursday..my regards to Mummy dasu pretty"...Bobby ya amsa da"zasuji"..snn ya fita a office din..Nur ya bishi da kallo yana murmushi yace"dan rainin hankali zama ka gama guje gujenka ka dawo kan hanya ne...waya fada maka Borno gabas take?.."yana gama fadan haka sai ya kwashe da daria hadda su buga table ya sake cewa"su Dr Bobby in love har na matsu naga karshen love story din nan..da yake novice ne shi har dan ramewa naga yayi sbd damuwa..kai amma Lamido ta hadu wlh..kin gama min komai tunda kika fara daidaita wnn dan iskan"..ya karasa yana ske rushewa da daria...shikam ko baa fada mishi ba yasan definitely son Lamido yake sbd abubuwan da yaga yanayi dama wanda ita kanta Lamidon ta fada mashi. Yana fitowa yaci karo da ita ta fito daa office din Sir Abdool aikam tana ganinshi ta wani hade rai tayi wucewarta abunta ko kallon inda yake batayi ba...saida takai bakin kofa sai kuma ta juyo idonta a kasa tana sake daure fuska murya a ciki ciki tace"ina yini"..kallonta kawai Bobby keyi without blinking...wasu irin ramuka da baisan dasuba a cikin heart dinshi yaji suna ciccikowa just by seeing her...haka nan yaji ganin nata gladen his heart sai a wani 6angaren kuma yaji ciwon zuwa office din Abdool da tayi...idan bai manta ba da bakinta ta ta6a furta mashi Abdool din sonta yake kuma shine zata biyoshi har office dinshi sbd batada hankali...ganin ta gaisheshi bai amsa ba ta juya zata wuce yayi saurin dawowa hayyacinshi snn ya dan daa murya ya kira sunanta"Aysher"...juyowa tayi tana dubanshi da mamaki...this is the very first time da taji sunanta a bakinshi..ko Lamido bata ta6ajin ya kirata dashi ba balle kuma Aysha da dama ba kowa ke kira a college din ba...takawa ya shigayi a hankali zuwa inda take..ya juya tabbatar ba kowa inda suke kafin ya sake juyowa yana kallonta ba yabo ba fallasa ya nuna mata hanyar office dinshi yace"muje"...turo baki tayi tana sake cin kunu tace"sir nifa class nakeso in koma"...bai sake ce mata komai ba kawai ya zuba mata idanunshi da yasan bata isa ta sake mishi gardama idan har ta kallesu...lokaci daya ta wani hade rai ganin yana kokarin yasata yin abunda batayi niyya ba bayan duk wulakancin da yayi mata hadda kiranta karuwa shine yau zai wani zo yace mata muje kaman shi ya haifeta...kallon da taga bazata iya jurewa ba ta wuce zuwa office din nashi yana binta a baya...da kanshi ya bude office din ya shiga snn itama ta shigo ya maida kofan ya rufe..ya karasa kan sofa ya zauna itama ya nuna mata wanda ke opposite dinshi yace"seat"..rungume hannunta tayi tana sake hade ranta tace"am comfortable here"..baice qala ba ya mike daga nan inda yake ya karasa ya tsaya dab da ita har suna jin kamshin perfumes din juna ya rungume hannu idonshi na kanta yace"fushi kikeyi dani?.."da mamaki sosai ta dago tana kallonshi don batayi excepting such mgn daga bakinshi ba..shima kanshi Bobbyn baisan lokacin da mgnr yayi escaping lips dinshi ba..it’s like mgnr ya fito direct from his heart bawai a baki kadai ya tsaya ba...ganin yanda suka hada ido kuma sai taji kunya ta sake yin kasa da kanta tana turo baki...shikam bai iya dauke idanunshi kanta ba ya sake cewa"say something mana..are u mad at me?.."sake kautar da kanta tayi tana cigaba da turo bakinta tace"cewa fa kayi ina karuwanchi"...wara idanu yayi cikeda mamaki yana kallonta yace"Nii?..when did i say that?.."wani irin bacin rai taji ya rufeta na ba gaira babu dalili kawai sai tayi kasa da idonta...Bobby da duk yaji hankalinshi na neman tashi cikin wani irin murya dashi kanshi baisan yana dashi ba yace mata"Aysher speak manaaa"...runste idanu Lamido tayi nan take taji hawaye na neman ciko idanunta...a take hankalin nashi kuwa ya karasa tashi cikin wani irin rauni da baisan daga ina yake fitowa ba yaji yana ce mata"dont cry plss..ki fadamin yaushe nace maki kina karuwanchi?.."hannu takai tana goge hawayen nata baki a tunzure tace"ba haka kace ina biye biyen maza ba..kuma ni ba biye biyen mazan da nakeyi ko Sir Abdool da ka ganni dashi shi yake sona bani nake sonshi ba"..baisan lokacinda bakinshi ya furta"shi kuma wnn dayan fa?.."dagowa tayi tana kallonshi dan bata gane wa yake nufi ba..ya wani hade ranshi kafin yace"that boy..wanda kikayi acting as his wife ranan da kukayi drama"...dan murmushi ta saki da wet face dinta jin wanda yake nufi tace"bestie na nefa"...kallonta kawai yake rai a 6ace ya rasa ma abunda zaice mata...ganin ta sake maida fuskanta ta dinkeshi tsaf kmr ba ita ta gama murmushi yanxu ba yace"is that why u are not picking my calls?.."tana turo bakinda ya zame mata sabo ta daga alaman eh..yace"then i am sorry...da nace kina biye biyen maza i never meant that kawai raina ne a 6ace..are we good now?.."shi kanshi yana mamakin kanshi yanda ya kwantar da murya yana mgn da ita...kai ta sake daga mishi alaman eh snn kuma tace"amma sir dan Allah ka denamin masif.."bata karasaba sai tayi saurin rufe bakinta tana kallonshi tace"sorry ina nufin fada..kuma ka dena kallona da idanunka yana bani tsoro"..murmushi kawai ya saki abunda ya mance yaushe rabonshi da yayi kawai ya koma kan sofa ya zauna yana cigaba da binta da ido..har wani ajiyan zuciya ya saki a 6oye sbd wani irin relieve da yaji just by patching things up with her..zuwa yanxu duk taurin kanshi yasan tabbas bazai iya daukan tana fushi dashi ba sbd ya fuskanci zuciyarshi bata san wnn karatun ba...ganin ya koma seat dinshi ya zauna itama ta dan kalleshi gamida kauda kai tace"sir zan tafi"...kallonta still yake yanajin kaman kar ya barta ta tafi...sam bai gaji da ganinta ba amma ko kusa yaki yin addmitting hakan..sbd ya karyata zuciyarshi da take ta mishi ihun cewa Lamido wani 6angare ce mai girma na cikinta kawai sai ya nuna mata kofa tareda fadin"u can leave"...yana rufe baki ta juya ta fita tana mamakin wai yau proprietor ne yayi mgn da ita haka ba wnn masifan nashi har yana bata hakuri..lallai kuwa za’ayi ruwa da qanqara...shi kuma Bobby sai yaji kaman an sauke mashi wani abu mai nauyi cikin zuciyarshi just by patching things up with her...baisan meyasa ba amma sai yajishi garau duk wnn damuwowi daya sanyama kanshi na kusan sati guda babu su...ranan har 'yan gidansu sun fahimci yana cikin nishadi don yanda yake murna da farin ciki says it all...Mummy dai sai binshi da kallo take cikin ranta tana"Allah dai ya tabbatar min da alkhairi"...nikuwa nace mata"Ameen Ameen Mummy". Tun daga ranan sai suka koma mutunchi sosai da Proprietor dan yana daukan lokaci mai tsaho baiyi mata bala’i ba amma yanajin zancen saurayi ko something like that bai iya daurewa sai ya dan zazzaga mata yakejin dadi...yanxun ya koya mata duk ta shigo college da safe taje ta gaisheshi idan yana cikin makarantan..haka kuwa take zuwa ba don ranta naso ba..wani lokaci idan yana nemanta ko ta kashe waya ko bata shigo cikin makaranta dashi ba saidai kawai ta ganshi a class dinsu yazo ya wani hade rai yace yana nemanta..haka zatayita ture turen bakinta tabishi tana zabga mai harara ta baya..wnn dalilin yasa da yawa daga ‘yan class dinsu ke zargin akwai wani abu tsakaninsu wasu kuma sunyi zaton dan uwanta ne kamar yanda idan aka tambayeta sai tace"dan uwan daddyna ne fa". Yau Thursday tun 3 Sa’eed ya daukesu zuwa gidan lalle sbd gobe zasu wuce kaduna bikin Lubna...amarya sai damunsu take da kira wai suyi sauri suje itafa ba wasu qawaye gareta ba...basu samu gamawa da gidan lallen ba sai after six dan haka Sa’eed na daukosu direct ya kama hanyan college dinsu..a hanya yaketa kallon lallen da Aysha ke nuna mashi tana fadin"besty lalle na yayi kyau koh?.."Sa’eed dake driving dinshi yace"sosai ma kuwa besty..aike din dama mai kyau ce so duk wani abu da zakiyi dole ma yayi suiting dinki"...Lamido ta saki murmushi tanata blushing tace"godia nake besty nah..shiyasa nake sonka wlh..besty bansan wane irin missing dinka zamuyi idan ka tafi ba"..ta karasa kmr zatasa kuka...shi kuma dan murmushi ya saki ba tareda yace komai ba don kuwa shi kanshi yasan dole yaji a jikinshi duk ranan da akace ya bar FCNM..yasan duk lokacinda yaso ganinsu bazaiyi mishi wahala ba ya dauko mota ya taho kano amma yasan bazai ta6a samun enough time dasu kaman yanda suke samu a yanxu ba...bayason zancen yayi tsayi sbd karyar mishi da zuciya suke dan haka ya kallo Billy ta mirror yana sakin smile yace"Billy banji kince komai ba"...harara mai kyau ya samu daga wurinta hakan kuma ya bashi daria sosai dama yasan abunda zatayi knn..shi tunda yake bai ta6a ganin wanda abun harara bai mata kadan kaman Hajia Bilkisu ba..ya tabbata zaiyi missing dinta fiyeda tunaninshi sbd wnn draman dake tsakaninsu...har suka karasa hostel ba wanda ya sake cewa komai a cikinsu..suna zuwa ya saukesu sukayi ciki shi kuma ya juya kan motarshi ya koma gida. Washegari suna room dinsu sunata faman hada kaya a akwati yau ko makarantan bazasu shiga ba sbd da wuri zasu wuce...Aysha nata kiciniyar kulle akwatin da suka cikashi 6am da kaya kaman wanda zasuyi shekara a kaduna yayinda Bilkisu ke zaune gefen bed dinta ta zuba uban tagumi tana tunani..kamar daga sama taji tace"Lamido nifa har yanxu tsoro nakeji wlh..ina tsoron wani abu ya samemu a hanya bayan ko gida basu san zamuje kaduna ba"..tsaki Lamido ta saki tana cigaba da sabgar gabanta tace"matsalana da Billy dawo da mgn wlh...tun jiyafa muka gama mgnr nan na fada maki wlh kika sake gida sukaji zancen tafiyar nan bazasu bari muje ba kuma dai kinga idan mukayi haka bamuma Lubna adalci ba tunda da kunnenki dai kikaji tace batada qawaye sai mu..and koba wnn ba ko don besty bai kamata muki zuwa bikin nan ba nasan in Allah ya yadda lafia zamuje mu dawo lafia kawai dan kinsama ranki abun ne amma inshaAllah lafia zamu dawo kuma ba tareda kowa ya sani ba"...gyada kai Billy tayi cikeda gamsuwa dan har wani ajiyar zuciya ta sauke kafin ta sake cewa"to Proprietor kuma fa?..did u tell him?.."da sauri Aysha ta shiga girgiza kai tace"waye ya aikeni in fada mishi salon yace babu inda zamuje knn..kema dai kinsanshi Billy wlh indai ya samu labari bazai bari ba"..Billy tace"amma kina ganin baza’a samu matsala ba?..ina nufin zai iya yuwa har muje mu dawo baiyi noticing ba?.."Aysha na gyada kai tace"of course mana..ai kinsan ba kullum yake zuwa makaranta ba gobe ne kawai mu kuma monday inshaAllah zamu dawo so he won’t know in Allah ya yadda"..gyada kai kawai Billy tayi saidai har yanxun cikin zuciyarta tanajin tsoro..har mamakin yanda ita Aysha bata damu ba take sai wani shiri takeyi tanajin dadi zataje garinda bata ta6a zuwa ba..tsakaninta da kaduna saidai ta wuceshi idan zasuje Abuja amma bata ta6a shigan garin ba. Karfe 10 da wani abu suka kama hanyan kd...ita da Billy ne sai wani cousin din Sa’eed suka tafi gaba daya a motar Sa’eed din...ko a hanya Billy hankalinta ba kwance yake ba dan koya taji sun shiga gargada zata hau sallallami tana zare idanu wai a tunaninta ko hatsari ne zai ritsa dasu.😂 Basu samu isa kaduna da wuri ba sbd holdups da sukayita cin karo dasu a hanya sai kuma shi kanshi hanyan da ba wani kyawu kwarai ne dashi ba...lokacin da suka shigo kd was after one sosai dan har wasu masallatai sun fara sallahn jumu’a...kai tsaye unguwansu ya wuce dasu bayan ya kira Lubna ta shaida mishi cewa tana gidan wani uncle dinsu dake nan kusada gidan nasu...saida ya isa har kofar gidan snn ya sake kiranta nan da nan kuwa sai gata ta fito tana ganinsu ta daka tsalle ta wani cacimesu sai kace ba amarya...bayan sun gama cacime cacimensu suka karasa cikin gidan Sa’eed yabisu da kayansu ciki snn ya fito zuwa gidansu don yaje ya shirya sharp sharp ya wuce masallaci don ana idar da sallahn jumu’a za’a daura aure. Suna shiga ciki Lubna ta kaisu suka gaisa da matar gidan snn ta jasu zuwa dakinda take ita kadai din da gaske ba wasu qawayen kirki gareta ba...mai make up na zaune tana jiranta tun daxu akaso farawa tace sai sunzo tukun za’a fara...zaunawa tayi aka fara mai aikin gidan kuma ta kawo masu abinci da drinks bayan sun gabatar da sallah suka zauna suka faraci...ko kafin a gama mata make up sun gama dan haka kowacce ta mike ta fara shiryawa don ‘yan daurin aure suna gab da dawowa. Tare suka shiga gidan gaba daya su ukun bayan an gama cancada ma amarya kwalliyarta...Sa’eed da kanshi ya kaisu suka gaisa da Mom dinshi dukda taron jama’a dake gidan...daga nan kuma angwaye sukazo aka shiga daukan hotuna...su Lamido sai iyayi akeyi to abun nema ya samu...sai bayan sallahn asr suka koma can gidan uncle din amarya tareda few daga cikin friends dinta...karfe takwas na dare aka fara tafiya dinner...sudai suna tareda amarya tace qafarta qafarsu shi kuma Sa’eed yace lallai saidai ya tafi dasu..haka sukaita fafatawa daga karshe dai dole Lubna tayi hakuri ya wuce dasu bayan sun gama shiryawa...suna sanye cikin lace dinsu sea green iri daya duk cikinsu ba wadda tayi make up amma fadan kyawun da sukayi is a waste of time...tun daga mota Aysha ta dauko wayanta ta fara musu snap kala kala wani suyi gaba daya su ukun wani itada Billy wani kuma itada besty...koda suka isa hall din dinner ma cigaba da gashi sukayi...basu bar nan wurinda suke ba saida amarya da ango suka karaso...bayan an gama tsara masu shiga dasu Billy taja baya zatayi musu video Lamido kuma as usual tana sahun farko na wanda zasuyi rawa...ana sakar musu kida suka fara takawa zuwa ciki..Billy dai na gaba tana tafiya da baya baya tanata daukan video a wayanta...har suka raka bride and groom mazauninsu bata dena dauka ba...Aysha kuma bayan amarya da ango sun zauna ta nufi table din da ta hangesu zaune..videos din Billy ta hau nuna mata suna daria..Sa’eed ya kalli yanda take rawa yace"besty knn..na rasa wane irin soyayya ke tsakaninki da rawa wlh"...murguda mishi baki tayi batace komai ba...a takaice kafin a bar wajen dinner Aysha tayi rawa har jikinta saida ya gaya mata...pictures da videos kuwa tasha su a wajen Billy har ma da wanda bai kamata ba...saida suka koma gida suka nutsu kowa yayi shirin kwanciya snn Aysha tayi selecting wasu daga pics da videos da sukayi tayi posting a status dinta bayan tayi blocking duk wani wanda tasan idan ya gani labarin zai iya isa ga parents dinta...tana gamawa da whatsapp ta shiga instagram nan ma tayi posting snn ta kira babynta a waya sukasha hira abunsu..suna gamawa kuma bacci yayi awon gaba da ita. Kano... Tun safe Bobby ya shigo College dukda cewa saturday ne koda ya shigo bai samu zama ba don meeting suka shiga da staff bayan sun fito shi da Nur suka sake zama da wasu masu fili da yakeso ya siya a kusada college din daga nan kuma suka shiga hostel so gaba daya bai samu zama ba saida suka dawo daga sallahn jumu’a...yana shiga office driver ya kawo lunch daga gida snn ya fita...baa jima ba kuma sai ga Nur ya shigo..tare sukaci abincin a nan bayan sun gama ya kira driver ya tafi da ragowan shi kuma ya zaro phone dinshi ya shiga whatsapp sbd tun safe bai duba messages dinshi ba...reply ya farayi duk wani message mai muhimmanci yayi replying har zai ajiye wayan sai kuma ya fasa ya fara duba status..he is not a fan of viewing or uploading status amma yau haka nan yaji he should just check yaga what people are posting...na aunty sumy ya fara dubawa yaga picture dinshi ne a farko sai na ilham sai kuma na Sab da Miemie a hade...daga nata ya duba na Nur yaga pictures da Public Relation Officer na college din yayi musu daxu during meeting da sukayi ne duk yayi posting..dan ta6e baki yayi snn ya sake yin gaba har zai bude na wani colleague dinshi Dr Michael sai kuma ya fasa sbd ganin sunanta da yayi cikin jerin wanda sukayi posting...ba tareda tunanin komai ba ya danna sunanta nan take kuma picture din farko ya bayyana..ita kadaice a pic din tayi daria both dimples dinta sun fito..wani irin abu mai nauyi yaji yazo ya tokareshi a throat..dannewa yayi ya wuce gaba sai yaga itada Billy suna kallon juna still suna daria har dimples dinta sun fito...wnn karon zafi ya faraji all over his body ganin again ko mayafi babu a jikinta and ta fito da gashinta waje as usual..the next one kuma su uku ne a jiki ta turo bak tana kokarin sanya glasses dinta Billy kuma nayi mata mgn Sa’eed yayi musu selfie..na gaba kuma video ne ita kadai tanata dirkan rawa Billy tayi mata...sbd tsabar 6acin rai baisan lokacin da ya buga table dake ganashi ya furta"what the hell"da mugun karfi ba...daga shi kuma sai another video data daukesu su uku sunata murmushi sun sanya Sa’eed a tsakiya sai wanda aka daukesu tareda amarya da ango...haka dai yayita binsu daya bayan daya yana gani har saida ya gama gani tsaf snn ya ajiye wayar kan table ya dafe kanshi da both hands dinshi...Nur da tunda yaji abunda ya fada dazu ya dago yana kallonshi amma sai yaga all attension dinshi yanaga wayanshi yace"lafia dai?.."banza Bobby yayi dashi yana dafe da kanshi...wani irin zafi yakeji tun daga cikin zuciya zuwa gangar jikinshi..shidai ya rasa wace irin fitinanniyar yarinyace ita?..baisan wane irin rashin ji gareta ba?..yanxu kuma fisabilillahi ina taje sukayi wann pictures haka?..sbd tsabar batada hankali har rawa taje tayi a bainar jama’a..yasan kusan duk wanda ke wurin ya gama ganinta kilan ma baza’a rasa wanda yace yana sonta ba...tunanin hakan yasa yaji wani irin abu mai nauyi yazo ya tsaya mishi a kahon zuci...numfashi ma da kyar yake yinsa sbd azaba..shidai yasan Lamido idan ba nutsuwa tayi ba tana iya haifar mashi da ciwon zuciya watarana sbd abubuwan nan da yakeji a kanta sun fara wuce tunaninshi...duk wani jarumta da karfin halinshi na yaga ya 6oye abunda yakeji sbd Nur dake zaune wurin kasawa yayi...wani irin tari ya farayi sosai yana dafe da chest dinshi..Nur ya mike daga inda yake da sauri ya dauko ruwa daga fridge ya mika mishi yana cewa"sannu..have this zakaji sauki"...baiyi masa musu ba ya amsa ruwan dan shi kanshi yasan yanada buqatan duk wani abu mai sanyi a halin yanxu sbd turirin dake fita daga cikin zuciyarshi...tunda ya kafa goran ruwan a baki bai sauke ba saida ya shanyeshi..Nur dai na tsaye yana kallonshi har yaga ya dan samu nutsuwa snn ya zauna nan kusa dashi yace"mene wai..meka gani ya tayar maka da hankali haka?.."girgiza kai kawai Bobby yayi don baijin zai iya bude baki yayi mgn a halin da yake ciki...hannu Nur yakai ya dauki wayan nashi sai yaga sunan Lamido a jerin status da yayi viewing...bai tsaya wata wata ba shima ya shiga ya fara gani..saida ya gama tsaf snn ya dago yana kallon Bobby da har yanxu idanunshi ke lumshe yana dafe da head dinshi yace"so kishi ne ya motsa knn?.."wani irin kallo ya watsa masa kafin ya sake maida idonshi ya rufe...Nur ya fashe da daria yana cewa"idan ba kishi ba me kakeyi Dr Bobby?..you better wake up wlh"..ya karasa yana sake kwashewa da daria...Bobby dai diff yayi yana sake jin 6acin ranshi na karuwa...a fusace ya nunashi da yatsa yace"how dare you zakazo ka sani a gaba kanamin daria?..are u madd?.."ya karasa mgn da wani irin ihuu da saida Nur ya dora hannu a kunnenshi...bayan ya gama dariyarshi yace"continue deceiving urself kaji?..just keep on denying the fact that u love her..idan bakayi wasa ba kana zaune zata auri wani and ba yanda ka iya"...tun bai karasa ba Bobby ya sake buga table dake gabashi cikin karajii yace"how dare u?..how dare u talk to me like this?..nina fada maka ina sonta?.."gigiza kai Nur ya sakeyi yana shafa gemu cikin shakiyanci yace"har yanxu baka wahala ba shiyasa kake wnn kumfan bakin..idan kaji wuya da kanka zakazo ka sameni kayi kasa da voice dinka kace Nur i don’t know what to do plss help me..bansan yaushe na fara son yarinyar nan Lamido take ko Gidado?..".Ya karasa mgnr yana wani ta6e baki exactly irin yanda Bobbyn keyi kafin ya sake fashewa da daria...qala Bobby bai iya cewa ba ya mike ya kwashi wayoyinshi ya fice daga office din..idan ya tsaya ya tabbata za’a iya taruwa azo kallonsu don yanda zuciyarshi ke a kusa yana iya kwada mashi mari wlh..kawai takaici yakeji na wnn pictures da tayi posting ?..is she mad or something?..kwata kwata bata san kishin kanta ba..wai ma ina sukaje har sukayi pictures din at the first place?..yana buqatan ya kirata amma a wnn lokacin idan ya kirata kilan zaginta kawai zaiyi sbd yanda yakeji...kai tsaye motanshi ya nufa driver ya bude mishi ya shiga snn shima ya shiga suka fice daga makarantan..dama duk abubuwan da suka kawoshi college din ya gama..rabon zaiga wnn bakin cikin nema kila ya zaunar dashi. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 28 Kai tsaye gida driver ya nufa dashi..suna isa ya bude mota ya fita zuwa ciki..yayi sa’a ba kowa central parlor dan haka ya wuce flat dinshi..yana shiga ya ajiye wayoyinshi gefen gado ya shiga rage kayan jikinshi sbd azabar zafi da yakeji cox ba zuciyanshi kadai ke mashi zafi harda ilahirin jikinshi...saida ya tabbata ya cire komai shorts kawai ya bari da singlet snn ya shiga bathroom ya sakar ma kanshi ruwan sanyi duk a kokarinshi na ganin ya dena feeling zafin da yakeji amma a banza...saida ya kwashe almost 30 mins bayi yana abu daya kafin ya fito daure da towel yana goge gashin kanshi...turare kadai ya isa fesawa ya shiga closet ya sako amrless da three quarter snn yazo ya dauki one of wayoyinshi dake zube nan kan bed din nashi ya ya zauna yana kokarin kiranta..if u see how he’s frowning his face zakayi tunanin bai ta6a yin daria ba..he looks more angry than ever...kiran na shiga amma har ya gama ringing bata dauka ba saida ya sake kira ta daga tana wani tattaro duk nutsuwarta tace"Sir good evening?.."bai amsa mata ba sai cewa yayi"where are u?.."shiru ta danyi tana tunanin dalilin tambayar sai kuma tace"Sir banji me kace ba"...yace"i said where are u now?.."Aysha ta hadiye wani yawu praying Allah yasa ba asirinta ne ya tonu ba tace"sir..ina..hostel..mana..bacci nake daka kira shiyasa ban dauka ba"...dukda halinda yake ciki saida ya saki murmushi ganin raina mashi hankali zatayi yace"oh really?..kina hostel right?.."cikin dakiya tace"ehh.."yace"then come outside gani nan zuwa hostel din naku yanxun nan"..zaro ido Aysha tayi tana dafe chest dinta tace"na shiga uku"..Bobby da yaji sarai abunda ta fada yace"ki fito waje yanxun nan am coming right away"..da sauri tace mishi"sir dan muhammadu rasulillahi kayi hakuri..tsakanina da Allah bana cikin hostel yanxu haka?.."kai tsaye ya sake fadin"then ina kikaje?.."wani yawu ta sake hadiya kafin tace"gidan biki"..Bobby yayi shiru yana sauraronta baisan mema zaice mata ba...so yake ya sauke mata kwando kwando na rashin hankalin da tayi amma yafiso ya ganta a gabanshi tukun...ita kuma jin yanda yayi shiru sai ta sakeyin kasa da murya tace"sir please!.."ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"kina dawowa ki sameni office tunda ke bakida hankali?..kuma kika bari na sake kiranki zakiga abunda zai faru?.."hawaye sosai suka ciko idanun Aysha tace"sir nifa gaba daya bana gari"..wnn karon shine ya zaro eyes dinshi tamkar tana gabanshi yace"ban gane bakya gari ba..explain urself"..murya can kasa yaji tace"muna kaduna"..ya bude baki zai kwaso masifa kawai yaji diff ta kashe wayarta...Bobby yabi wayarshi da kallo yana mamaki..sake dialing yayi yaji ta kashe wayan gaba daya nan take ya runtse ido yanajin zafin da yakeji yana sake karuwa...nan take zazza6i yace salamu alaikum..can saiga ciwon kai da jiri duk sun dirar masa at once..har wani irin sanyi yana kadashi ga temperature dinshi da yayi rising...da kyar ya iya daga legs dinshi ya dora kan gadon snn ya kwanta a hankali ya lullu6e da duvet..lokaci daya yaji kaman an kanainayeshi ya kasa koda daga finger dinshi..sake runtse ido yayi yana mamakin yanda duk ciwon suka saukan mishi at once..few minutes ago baijin komai ba in banda slight headache da 6acin rai amma yanxun ji yake ko mikewa tsaye bazai iya yi ba sbd ciwo...koda yake ba abun mamaki bane dan yanxu zakaga mutum lafia qalau anjima kadan ace maka ya mutu so wnn ba komai bane daga cikin qudurar ubangiji...jikinshi har shivering ya fara gashi ko kwakwaran motsi bai iya yi balle ya tashi ya kashe acn da yake zaton ita ke kara mashi sanyin da yakeji...su Mummy kam ba wanda yasan ya dawo a cikinsu don time din da ya shigo bai hadu da kowa ba dan haka yamma nayi suka shirya Sab ya fita kaisu unguwa a motan Mummyn...basu suka dawo gidan ba sai after magrib sai a nan ne Mummy ta fara mamakin rashin dawowarshi har yanxu sbd yace mata yau ko Hospital bazai shiga ba yanaso ya huta...ganin har anyi sallahn isha tara na neman wucewa sai ta dauki wayanta ta shiga kiranshi...yanata ringing bai dauka ba har tayi mishi 4 missed calls ba wanda yayi answering a ciki...nan kuma hankalinta ya fara tashi dan tasan lafia lau dai baza’a yima Bobby har 4 missed calls bai gani ba..sake kira tayi for the fifth time ganin still no answer saita dannawa Nur kira hoping ko basa tare yasan inda yake...Nur dake kan hanyan komawa gida yana ganin kiran nata yayi parking snn ya daga kafin yayi mgn Mummy tace"Nuru kuna tareda Bobby kuwa?.."girgiza kai Nur yayi kaman tana ganinshi yace"No mun rabu tun daxu Mummy..ai tun around 4 ya baro college saidai ko Hospital ya wuce"..Mummy tace"anya kuwa?..na kira wayanshi bai dauka ba and yau yacemin yana gama da college dawowa gida zaiyi ya huta bazaije ko inaba"..shiru Nur yayi yana tuna a halin da ya bar college din yasan zaiyi wuya yaje wani wurin idan ba gida dan haka yace"Mummy a duba flat dinshi dai..zai iya yiwuwa ya dawo yana ciki bai fito ba shiyasa baku san yana nan ba"..gyada kai Mummy keyi before tace"shknn let me check"..daga haka ta kashe wayar snn ta juya zuwa flat dinshi...tana tura kofan tajishi a bude tasan yana ciki knn dan haka direct ta wuce bedroom dinshi..a kwance can karshen gado ta hangoshi ya kudundune kanshi kanshi cikin duvet dukda haka kuma jikinshi bai bar rawa ba...karasawa tayi da hanzari ta yaye duvet din tana ganin yanda ya dunkule waje daya saida gabanta ya fadi dan Bobby ba mai yawan rashin lafia bane..yana dadewa baiyi ciwo ba amma duk ya tashi yi sai ya kusan mutuwa sbd wahalan da yakesha...zaunawa tayi nan kusa dashi hankalinta duk a tashe in igbo tace"Bobby meke damunka?..yaushe ma ka dawo gidan bamu sani ba?.."da kyar ya iya bude idanunshi ya zubasu a kanta sai kuma ya sake maida su ya lumshe sbd baison ganin tashin hankalin dake rubuce kan fuskata...hankali tashe ta sake fadin"ba mgn nakeyi ba?..meya sameka?.."daurewa ya mike zaune da kyar yanajin yanda sanyin dakin ke sake ratsa mashi jiki Mummy data lura da hakan tayi saurin mikewa ta kashe ac snn ta sake dawowa ta zauna tana dafa forehead dinshi tace"u look seriously sick Bobby..meke damunka?.."hannunta kawai ya iya kamawa yana zuba mata idonshi dake mata nuni da bayason ganin damuwar nan da takeyi shiyasa tun daxu yaso ya tashi yasha magani kafin ta shigo amma ko motsi kasawa yayi...ganin kaman bazai iya mgn ba ta dauki wayanta data shigo dashi kai tsaye ta sake dialing number din Nur tace"bari in kira Nuru yazo ya dubaka idan abun bai yiwu ba kawai mu wuce asibiti"..tun kafin ta rufe baki yaji wani new 6acin rai na diran mishi jin ta ambaci Nur sbd tunawa da iskancin da yayi mashi daxun yace"Mummy..dont..call him..plss"..Mummy tace"why zakace haka?..kaji yanda temperature dinka yayi rising kuwa?.."lumshe idonshi yayi dan baisan me zaice ba again...kafin Mummy ta kira Nur sai ga aunty sumy ta shigo dakin tan sanyeda dogon riga da hula itama duk a gigice tace"Mummy wai jikin nashi ne har yanxu?.."Mummy tace"wlh har yanxu sumayya..ungo wayan nan ki samu ki kira Nuru yazo ya dubashi wnn high temperature bana lafia bane"..da sauri aunty sumy ta amsa wayan da Mummy ke mika mata ta zauna tareda dialing number Bobby sbd takaici kawai ya zare hannunshi daga cikin na Mummy hade da komawa ya kwanta ya juya musu baya...hada ido sukayi kafin aunty sumy dake sake trying number Nur tace"ni ban ta6a ganin likita da baya qaunaf treatment ba irin Bobby..duk rashin lafia ya kamaka saika bamu wahala wajen zuwa asibiti ko kuma kiran doctor"..shidai baice mata komai ba sbd shi kadai yasan abunda yakeji...Nur na ganin kiran yayi picking tareda fadin"yauwa Mummy yana gidan kou?.."aunty sumy tace"yea yana nan amma fa bashida lafia..he’s seriously sick inaga u should come forward ka duba jikin nashi"...da sauri Nur yace"ok gani nan zuwa yanxun nan"..daga haka ya kashe waya tareda juya kan motarshi zuwa airport road...aunty sumy na gama wayan itama komawa tayi ta zauna kusa dashi suka wani sanyashi tsakiya itada Mummy sai kace wanda ke fama da cutar ajali.😂 Ko cikakken 30 minutes baayi ba Nur ya karaso gidan..yana shiga ciki kai tsaye ya wuce flat din Bobby don bai samu kowa central parlor ba...saura kiris daria ya kufce mishi sbd ganin yanda sukayi wani tsuru tsuru suna kallonshi sai kace wanda akace musu ya mutu...karasawa yayi ciki yana kallonsu with smile yace"ya jikin nashi?.."Mummy ce ta mike daga inda take tana nuna Bobbyn da har yanxun ya juya musu baya tace"gashi nan dai..ka fara dubashi muga"...baiyi musu ba ya isa inda sphygmomanometer da stethoscope din Bobby ke ajiye ya daukosu snn ya dawo gefe gadon ya zauna ya ajiye kayan snn yakai hannu zai ta6a forehead dinshi ya wani daddage ya kwade mishi hannun aiko Nur ya fashe da daria sosai..bashi ba hatta su Mummy ya basu daria ganin yanda yakejin jiki amma har yanada energy din rigima haka...yana sake kai hannu Bobby ya kuma make hannun nan kuma Mummy ta daure fuskanta tace idan bai tsaya an dubashi ba zataci mutuncinshi..ba yanda ya iya haka ya mike zaune yana cika yana batsewa fuskan nan ba sarari kaman wanda aka aikoma sakon mutuwa...Nur bai damu da hade ranshi ba ya bude sphyg din ya zaro curf din ciki snn ya zurashi hannun Bobby yana tieing dinshi a hankali...bayan ya gama ya makale stethoscope dinshi a kunne tareda kama hannun nashi snn ya fara pumping...yana gamawa ya zare abun daga kunnenshi snn ya shiga kwance curf daya daura mashi yana duban su Mummy yace"Blood pressure dinshi is normal amma idan bai dena sa damuwa ba yana iya hawa nan gaba kadan"..Mummy ta gyada kai alaman ta fahimta shi kuma Nur ya mike zuwa first aid box dinshi ya dakko wasu drugs snn ya koma inda yake..Mummy tasa aunty sumy zuwa ta hado tea shima ya wani sake hade rai yace bazaisha ba saida Mummyn ta zauna da kanta itama ta daure nata fuskan snn aka samu ya sanyeshi tas ta amsa drugs din suma ta bala mashi yasha snn tace ya kwanta...ba musu ya sake juya musu baya ya kwanta yanajin yanda zuciyarshi keta harbawa sbd kular dashi da sukayi...bayan few minutes bacci ya daukeshi dan hadda maganin bacci aka hada mishi sai a lokcin suma suka fita daga dakin...kafin Nur ya tafi Mummy ta zaunar dashi tana tambayan ko wani abu ya hadashi da Bobbyn...Nur da har yanxu attitude din abokin nashi bai dena bashi daria ba yace"wlh ba wani abu Mummy love ne kawai yake dawainiya dashi kuma yaki admitting "..kallonshi Mummy keyi nan take kuma jikinta ya bata akan Lamido ne dan haka tace"u mean akan wnn yarinyar ne?.."Nur yace"a kanta ne wlh..kinsan halinshi da kafiya na fada mashi sonta yake yana maidani dan iska and the most funniest part of al’amarin shine azabar kishinta da yake wai amma har yanxun yaki accepting the fact that yana sonta..pics dinta fa kawai tayi posting a status shine yake wnn zazza6in"..gyada kai Mummy ta shigayi cikin ranta tace"lallai biri yayi kama da mutum"..a fili kuma sai tace"yanxu ya kake ganin za’ayi?..ni bansan irin Bobby ba wlh"..su Nur hadda gyara zama yace"nidai ina ganin dena mishi mgnrta kawai zamuyi..kuma idan kunayi ku dena nima daga yau ban kara fada mishi yana sonta..mu zuba mishi ido kawai na tabbata idan abun yafi karfinshi da kanshi zaizo ya fada"...shiru Mummy tayi tana nazari kafin tace"amma kana ga baza’a samu matsala ba?.."Nur yace"inshaAllah ba matsalan da za’a samu..a yanda halinshi yake indai za’a cigaba dayi mishi zancen yana sonta to ita kanta yarinyar zaiyita sauke mata masifanshi ne sbd zaiga kaman ita take janyo ana fada mishi haka..amma idan mukayi biris da al’amarin watarana da kanshi zaiyi admitting yana sonta"...gyada kai Mummy tayi tace"shknn Allah ya zaba mana mafi alkhairi..ni da zaka taimaka ka kawomin yarinyar ma in ganta"...yace"Kaii Mummy kinaso Bobby ya dena kulani knn?..a yanda yakeda kishin nan idan yaga na daukota a motata ai inaga kisan mutuwa zaiyi"..ya karasa mgn yana daria...aunty sumy da batsan da zancen ba sai yanxu tace"lallai Nur kasan kan abokin nan naka da yawa"...yace"ai aunty qanin naki ne kinsan zuma ne saida wuta"..daria suka saka kafin Nur yayi musu sallama ya wuce suma kowa ta nufi dakinta kafin a jima su sake zuwa ganin jikinshi. Har gari ya waye Bobby bai denajin zafin da yakeji ba...ya samu dai headache da fevern sun sauka amma zuciyarshi dai tana nan a jagule yanda take tun jiya kuma duk kokarinshi na ganin yayi maganin hakan gagararshi yayi...ko yau da safe sau uku yana kiran numberta switch off hakan kuma ba karamin sake tunzurashi yayi ba..sbd batada hankali ta kwashi jiki ta tafi har kaduna biki sai kace bikin ‘yar uwarta?..kuma yanada tabbacin a gidansu ba’a sani ba dan haka jira kwai yake ta dawo ya sauke mata nauyin dake cikin zuciyarshi. A can kaduna kuwa Lamido tunda tasan yasan inda sukaje hankalinta bai sake kwanciya ba dan ko bikin ma dena enjoying dinshi tayi..tsoronta Allah tsoronta kada ya kira daddy ya fada masa tasan yana fada itakam ta gama yawo..da farko kin fadawa Billy da shi kanshi Sa’eed din tayi sbd tasan zasu dora mata laifi musamman Billy amma daga baya dole suka gane akwai abunda ke damunta dan haka ta fada musu exactly yanda sukayi dashi...hankalin Billy ya tashi matuka dan ko ita Lamidon bazata gaya mata shiga tashin hankali ba dama yanda kasan farar kura haka take wajen tsoro...basuyi niyyan barin kd ranan sunday ba amma haka Sa’eed ya tattarosu suka wuce sbd yana guje musu matsalan da zasu iya fuskanta wajen proprietor dama kuma biki ya kare tunda ankai amarya...haka suka tafi ko sallama basuje sunma amaryan ba...karfe uku da wani abu suka dauki hanyan kano and basu suka shigo birnin dabo ba sai around six..suna ganin an dauki hanyan FCNM hankalinsu ya sake tashi musamman Aysha da cikinta har wani juyawa yake sbd tashin hankali...har tsoron kunna wayanta take sbd tasan tana kunnawa zai kira and hakan na nufin masifa da bala’i dan kuwa tasan idonta idon Dr Bobby saiya cinye mata mutunci tas tunda dama ba yanxu ya saba ba..kawai tsoronta kada ya hadata da babanta amma dan ta masifarshi mai sauki ne dan idan da sabo yaci ace ta saba dukda cewa yanxu sam bai cika mata ihu ba..wani lokaci ko abu ya kama na fadan ne da idan baiyiba bazaiji dadi ba sai yayi mata shi a nutse kaman ba fada yakeyi ba amma yau kam tasan idan akwai abunda ya wuce ihu ma zaiyi shi tunda ta gama kular dashi...har suka isa hostel babu mai kwarin guiwar yin mgn cikinsu shi kanshi Sa’eed din addu’a yakeyi Allah yasa bazasu samu matsala sbd shi ba tunda shine wanda ya daukesu zuwa kadunan and Allah ya sani da yasan basuyi informing parents dinsu ba ba dalilinda zaisa ya kwashesu har kd saidai rashin sani...kafin su rabu ya sake kwantar musu da hankali tareda assuring dinsu cewa inshaAllah komai zai tafi normal..sukam gaba dayansu jinshi kawai sukeyi amma gani suke dole fa sai wani abu ya faru either big or small. The next day sukayi shirin school kowa tasa uniform dinta suna jiran school bus saidai ba wanda takeda walwala a cikinsu...baa jimaba bus dinsu yazo ya kwashesu sukayi cikin makarantan...ana ajiyesu suka fice yau har rige rigen fita daga bus din suke a takaninsu sbd gudun haduwa dashi dukda ma sunsan monday ba ranan shigowarshi bane...daga nan direct class dinsu suka wuce basu sake fitowa ba har suka fara lectures. Karfe tara daidai yayima Bobby a college din dukda cewa Monday ne ga kuma jikinshi da bai gama sauki ba amma ko hospital ya kasa zuwa sbd yanaso ya ganta...kai tsaye sama ya haura zuwa class dinsu don yasan idan yace har saiya sameta a waya to bazai taba samunta ba dan ba kunna wayan zatayi ba...wani lecturer ya samu a class din yana musu lectures dan haka kai tsaye ya fada class din fuskan nan a tamke kamar baisan menene daria ba...hannu ya mikawa lecturer din suka gaisa snn ya maida hannun aljihu yana baza idanu yanaso ya hangosu amma ko daya daga cikinsu bai gani ba...hankalinshi ya maida kan ‘yan class din fuska ba fus yace"where is Lamido?.."da sauri suka nuna inda take can baya tana sunukuyar dakai..baice kala ba sai takawa da yayi har gaban seat din nata ya zuba mata idanunshi ko kadan bata sonsu snn a kausashe yace mata"mike.."ba musu ta mike tsaye kai a kasa..ya sake cewa"ina Bilkisu?.."da sauri itama ta nuna seat dinda Billy ke zaune itama kallon nata yayi tayi saurin dukar da nata kan snn ya juya still hands dinshi a aljihu yace musu"follow me"..sum sum suka bi bayanshi kaman marasa gaskia..yana gaba suna binshi dukda bai juyaba yanajin footsteps dinsu ta bayan nashi dan haka kai tsaye ya wuce office dinshi suna biye dashi..a hanya ya kusa cin karo da Nur ya wani wara ido yana kallonshi then su Lamido dake biye dashi sai kuma ya saki dan murmushi yana maida dubanshi gareshi yace"so ka warke knn?.."ko kallonshi Bobby baiyi ba ya wuce office dinshi...yana isa ya bude kofa da yake bai shigowa Monday so secretary dinshi bata zoba...shine ya fara shiga ciki snn sukabi bayanshi...a kan sofa ya zauna yana kallon yanda sukayi wani cirko cirko a gabanshi sai ya sauke idanunshi kan Billy da yake ganin kamar tafi hankali yace"Bilkisu hadda ke?.."da sauri Billy da kanta ke kasa tace"wlh sir ba laifina bane ba yanda banyi da ita akan mu fada a gida ba tace wai baza’a fada ba"..yace"then meya hanaki kirani ki fadamin?.."Billy da har ta fara hawaye tace"shima cewa tayi bazan fada ba wai sbd hanawa zakayi?..sir dan Allah kayi hakuri wlh bazai sake faruwa ba"..gyada kai yayi dan ya yadda da ita yace"next time kina ganin zatayi anything stupid just give me a call ai kinada number na"..gyada kai Billy tayi tace"inshaAllah sir"..yace"shknn u can leave"..Billy tayi godia snn ta juya zata fita Aysha tabi bayanta da sauri wai tunaninta ya sallamesu gaba daya amma sai taji cikin cunkushashen voice dinshi yace"who ask u to leave?.."juyowa tayi a hankali tana dubanshi kaman zatasa kuka tace"sir dan girman Allah in tafi"...ya sake hade rai yace"C’mon comeback here before i loose it with u"..juyawa tayi a hankali ta daw ciki idonta na cikowa da hawaye...kallon hawayen dake silalowa daga idon nata yayi nan take ya lumshe ido yanajin yanda hawayen ke sauka har cikin zuciyarshi...baisan meyasa these days ko tayi laifi tana fara kuka jikinshi ke mutuwa ba..so yake yayi mata masifa son ranshi amma yana ganin hawayen nan yaji zuciyrshi yayi waji weak...kujera ya nuna mata idanunshi a kanta yace"seat"...batayi musu ba ta zauna inda ya nuna mata tana hawaye na sake ambaliya akan face dinta...dafe goshi Bobby yayi hade da lumshe ido yanajin yanda takeso ta sake haddasa mishi ciwon kai da wnn kukan nata yace"For Gods sake me akayi makai na kuka ne wai?..nayi maki wani abun ne?.."girgiza mashi kai tayi still tana hawaye yace"then why are u crying?..nida kika haddasa ma rashin lafia banyi kuka ba saike zaki sani a gaba kinamin kuka?..kinama da hankali kuwa?.."turo baki tayi jin abunda ya fada wai ta haddasa masa rashin lafia..ta sake tale baki tana dan kallonshi ta gefen idonta tace"nidai dan Allah karka fadawa daddy plss"...kallonta yakeyi yace"naji I won’t tell him amma inaso ki dena kukan nan muyi mgn dake"..ba musu takai hannunta ta goge hawayen duk yana kallonta snn tace"na goge"..gyara zama yayi still idonshi kanta yace"tambaya nakeso inyi maki and i want u to be fair to yourself..idan da a Gombe kike gaban parents dinki would u do what u where doing now?.."girgiza mishi kai tayi a hankali alaman bazatayi ba...yace"then why kikeyi a nan sbd ba gabansu kike ba?..tsakaninki da Allah da ace wani abu ya sameki a hanya what do u want me to tell ur dad daya bani amanarki?..ko sbd kina ganin baki ta6a yin wani abu na sanar dashi ba?.."girgiza kai ta shigayi da sauri tace"sir wlh ba haka bane..gani nayi Lubna friend dinmu ce sosai and ko sbd besty bai kamata muki zuw..."bata karasa ba ya katseta cikin karaji yace"in your entire life karki sake mentioning min besty idan muna mgn..ina ruwana da wani besty ni ke na sani bashi ba and idan bakiji abunda na fada ba kuma you will see the other side of me"..ya karasa mgn har wani huci yake kaman tsohon zaki...Lamido dai kallonshi kawai take tana mamakin yanda yake changing forms within minutes..yanxun nan fa yake mata mgn a nutse kmr bashi ba within a second kuma ya dawo mata asalin proprietor data sani...kauda kanta tayi tana turo baki ita gara ma ya dingayi mata masifan kmr yanda ya saba ba yasata a gaba yanayi mata mgnr dake sa jikinta yana mutuwa ba...ganin yanda itama ta hade rai tana turo mishi baki ya danyi kasa da voice dinshi yace"wai meyasa bakijin mgn ne ke kam?..meyasa fitinanki yayi yawa?.."sake turo baki tayi tana gunguni kuma akan idonshi kawai sai ya rufe idanu tareda jingina jikin kujera yana karanta innalillahi a cikin ranshi...kamar yanda ya fada ne idan baiyi wasa ba yarinyar nan saita haifar mishi da ciwon zucia sbd abunda yakeji kanta is beyond his control...kawai yana ganin Allah ne ke jarabtarshi da ‘yar Gombe sbd tsananin kiyayyan da yakema ‘yan Gomben. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 29 Kallonshi Aysha keyi ganin yanda ya dafe goshi ya lumshe ido aikuwa ta daddage ta maka masa wani harara sai gashi karaf ya bude idon nashi...ta wani zaro ido hadda dora hannu a bakinta tace"sir i swear bada kai nakeba"..bai iya cewa komai ba sai kallonta da yakeyi nan kuma tayi kasa da idanunta tanajin idanun nashi har cikin brain dinta...ta rasa meyasa har yanxun ta kasa sabawa da idanun mutumin nan..sam bata kaunar ya zuba mata su sbd sawa suke tanajin wani iri wlh..sai su saka nutsuwar da baka shirya masa ba...shiko Bobby kallon nata yakeyi yana tattaro duk wani abu da yasan yanaji akanta yana dorasu cikin idon nashi wai ko Allah zaisa taga illar da take nemanyi mishi ta zubar da makamanta...sun dauki lokaci mai tsaho a haka har zaman wurin ya fara isanta kafin kuma taji yace"bani wayarki?.."juyawa tayi ta kalleshi sai kuma ta kwar da idon da sauri ta zaro wayan da aljihunta ta mika mashi..ya amsa ya duba sai yaga babu key a jiki dan haka kai tsaye whatsApp dinta ya shiga yayi deleting gaba daya status dinta daga nan ya shiga gallery nan ma yayi marking all pictures dinsu na kaduna yayi deleting snn ya shiga bin duk wani picture da sukayi itada besty yana deleting dinsu...a garin haka yaci karo da wani da sukayi itada Prof ya zuba mata ido yana kallonta da murmushi itama tana murmushin aka dauki picture din...wani abu mai daci yaji yazo ya tokareshi a makoshi..sai yayi zuru yana kallon pic din yana sakejin zuciyashi ma tafarfasa amma bai nuna mata ba yayi deleting pic din ya muma cigaba da abunda yake...bayan ya gama da wnn foldern ya fito ya shiga wani sai yaci karo da pictures din ‘yan Manchester rututu musamman Pogba dan nashi sunfi na kowa yawa a matsayinshi na best player dinta...tsayawa kawai yayi yana kallon pics din kaman gunki..yana yin minimizing ya sake cin karo da hoton pogba akan screen din wayan nata datayi making as wallpaper ai baisan lokacin da yayi wurgi da wayan nata ya fadi kasa ba...Lamido ta wara ido tana kallonshi idonta kmr zasu fado don mamaki kawai sai taga ya mike ya fada bathroom ya wani buga kofan da mugun karfinda saida ya tsorata ta...jiki na rawa ta mike ta fita daga office din ko takan wayanta da yayi rugu rugu a kasa batabi ba...shiko yana shiga samun wuri yayi ya zauna yana dafe head dinshi wani azababben kunchi na sake rufar mishi...ya tabbata da yaci gaba da zama a wurin nan ita kanta yana iya yin ball da ita sbd kuncin da yakeji...ashe rashin hankalin nata har yakai ta ringa tsayawa tana hoto da ko wane banza and to top it all har tara hotunan ‘yan kwallo takeyi a wayarta kaman ta hada wani abu dasu?..hadda wani sanya picture din namiji a wall paper dinta wai meke damun yarinyar nan ne kam?..waye wani Pogba da take mugun sonshi haka?..me akai akayishi ma gaba daya..anya kuwa yarinyar nan bata samu ta6in kwakwalwa ba?..idan ba haka ba why zatana abubuwanda ba kowace mace ce keyi ba..meya hada mace da kallon ball idan ba tsabar rashin hankali ba...saida ya dauki lokaci mai tsaho nan cikin bathroom kafin ya fito..bai sameta a office din ba amma wayanta na nan inda yayi wurgi dashi sai yanxu kuma yaga bai kamata ya fasa mata waya ba..kaman yayi overreacting amma shi kanshi ba laifinshi bane baisan meyasa yake kasa controlling abuna yakeji akanta ba...gaba daya ma sai yaji dana sanin zuwa college din yake at the first place kawai sai ya juya ya fita daga office ba tareda yabi takan wayan daya farfasa mata ba. Karfe hudu da kusan rabi ya baro hospital kai tsaye yacema driver ya kaishi FCNM zai shiga hostel yayi wani abu...driver ya dauki hanyan college din shi kuma Bobby yayi relaxing a back seat idanunshi lumshe yana sake sake cikin ranshi...tun daxu yasa aka kawo mashi sabon waya irin nata sak shine yakeso yakai mata tun kafin taje ta fara yamadidi dashi cewar ya fasa mata waya...bakin kokarinshi kawai yake na ganin abunda yakeji bai kwantar dashi ba amma ko Allah yasan ba karamin mawuyacin hali yake ciki ba...suna isa cikin hostel din yasa akayi mishi mgn da daya daga cikin matrons dinsu ya bata wayan bayan yace mata ta bada a kaiwa Lamido...daga haka gida ya koma dan ko ganinta bai sonyi ballantana ta sakeyin wani abun zuciyarshi tazo tana bugawa...koda ya koma gida yaki kwanciya kokari yakeyi sosai ya yaki abunda yakeji gameda ita yasan yana bari ya kwanta shknn ciwo zai samu galaba a kanshi. Haka kwanaki sukaita tafiya suna zama weeks..weeks kuma suna zama watanni har suka fara second semester exams...zuwa yanxu Bobby ya tabbata ko ba sonta yakeba to definitely he’s attracted to her and tunanin hakan kadai yana iya samai zazza6i sbd tsabar takaici...zuciyarshi kwata kwata bata mai adalci ba amma alqawari ne ya daukan ma kanshi bazai bari koma me yakeji a kanta yayi tasiri a zuciyarshi ba...da wnn alkawari ya samu yake yaqar abunda yakeji dukda cewa ba karamin wahala bane yake bawa kanshi...har suka gama exam suka tafi hutu bai sata a idanunshi ba hakan kuma ba karamin tada hankalinshi yayi ba abun har mamaki ya bashi...da farko gani yake kaman rashin ganin nata shine mafi a’ala amma zuwa yanxu ya tabbatar idan ba ganin nata yayi ba yana iya samun gagarumin problem...haka a daddafe suka cinye two weeks dinsu na holidays zasu dawo school Sunday..Monday kuma kowa ta fara zuwa Clinical Area...baisan hospital da za’ayi posting nata ba dan haka yau Saturday yana barin Hospital ya kira Nur yace yanaso su hadu a College that yanada mgnr da yakeso suyi dashi..Nur baiyi masa musu ba yace su hadu a college din...karfe biyar saura ya shiga cikin makarantan a lokacin ma ko Nur din bai karaso ba dan haka ya jirashi nan cikin mota ya karaso snn suka wuce office din Nur din gaba daya...bayan sun zauna Nur yace"to Dr Bobby ina sauraronka"...ajiyar zucia Bobby ya sauke yana tunanin ta inda ya kamata ya fara dan bayason iskancin Nur ko kadan dan haka ya dinke fuskanshi tsaf yana wani babbasarwa snn kai tsaye yace mishi"wane Hospital akayi posting Lamido?.."Nur yayi kuri da ido yana kallonshi yana daria cikin zuciyarshi yana tausayi abokin nashi amma bai nuna mishi komai ba a fili yace"well ina tunanin bazai wuce General Hospital ba..kasan rural posting ne"...da sauri Bobby yace"inaso a dawo da ita Freedom"...kallonshi dai Nur yacigaba dayi yana tuno ranan da tazo tace a canxa mata posting amma yace baza’a canxa ba yanxu kuma gashi da kanshi yakeso a canxa mata posting din..kamar zai tsokaneshi sai ya tuna yanda sukayi dasu Mummy dan haka ya basar tareda fadin"shknn zanyi mgn da isaac zaa canxa mata inshaAllah"...wani ajiyar zucia Bobby ya saki sai yaji kaman an sauke mashi wani nauyi...yanada reasons da yasa yace a kawota Freedom sbd yasan ba hankali ta cika ba kilan zuwa zatayi taita kule kulen maza tana abunda bai kamata ba shiyasa yake sonta a kusa dashi yanda zaisa mata ido...Nur dai nata kallonshi yana kunshe daria a haka sukayi sallama kowa ya shiga motarshi ya wuce. Washegari misalin 12 suka iso makaranta tareda Hamma daya dawo dasu as usual...kowa taje ta duba posting dinta suna murna zasuje rural posting amma sai sukaga an sake posting dinsu Freedom again...aikuwa gaba daya murnan da suke ciki sai ya koma ciki musamman Lamido da ko kadan last posting da tayi a Freedom din bataji dadinshi ba infact that was the most difficult and boring posting data ta6ayi a rayuwarta..lokaci daya duk wnn farin cikin na tafi rural ya koma ciki...kallon Billy tayi tana wani misti misti da ido sbd 6acin rai tace"zo muje mu samu provost mu fada mashi wlh..kan me za’a wani sake kaimu Freedom bayan ko last time can mukaje"...girgiza kai Billy tayi tace"nidai babu inda zanje and ina bakin shawaran kema ki hakura kawai..if u could remember last time ma kinje a canxa maki posting din hakan bai yiwu ba so yanxun ma ba canxa maki zasuyi ba"..sake hade rai Aysha tayi tace"amma nidai an cuceni wlh..dukma wanda ya bada shawaran a barmu a Freedom Allah ya isa tsakanina dashi wlh"...dan murmushi Bily ta saki kafin tace"nasan bazai wuce proprietor ba"..Aysha dai batace komai ba haka suka karasa cikin hostel kowa rai a 6ace. Ranan Monday tun seven Bobby ya bar gida zuwa Hospital ko breakfast bai iya tsayawa yayi ba duk yanda Mummy taso yayi hakan kuwa...so kawai yake ya sanyata idonshi ko zai samu ya cike wasu gurabe da yakejinsu so empty a cikin zuciyarshi...su kuma basu karaso Hospital ba sai after eight...bus dinsu na gama parking duk suka firfito zuwa cikin asibitin kowa sanyefa uniform dinshi...daga bakin office dinshi ya hangosu suna tafia and duk yawan nan nasu idanunshi basu sauka kan kowa ba sai ita..nan take kuma yaji wani irin sanyi mai hade da zafi yana mamaye zuciyarshi..shi sanyin dai na ganinta da yayi ne after a long period of time while shi kuma zafin na jin ciwon yanda tazo asibitin ne daga ita sai dan hijab dinsu na uniform da ko chest dinsu bai gama rufewa ba...wasu sukan dora hijab ko mayafi akai idan anzo makaranta ko asibiti sai a cire amma Lamido koda wasa bai ta6a ganin tayi irin wnn ba...haka take yawonta a college da hospital tana tallata surar jikinta kowanne jick and jerk yana kallo...gashi ya kasa dauke idanun a kanta tunda yake bai ta6a jin ciwon kananun hijabs din nan nasu ba sai yau..gaba daya jikinta a waje yake sararin Allah...har sukazo suka wuceshi bai dena kallonta ba saida suka shiga office din da za’a yi musu posting...already yayi mgn da CNO yace ayi posting dinta theatre yanda zai dinga samun ganinta sosai..idan basuda aiki kuma ta tafi Office dinshi dan yasan tsaf zai iya zuwa ya samu tana hira da doc Gabriel ko doc Vivian...kaman yanda ya tsara din kuwa haka akayi..tanaji anyi posting dinta theatre hankalinta yakai kololuwar tashi dan har yanxu bata mance suman da tayi last time da suka shiga theater ba..sbd tsabar wulakanci duk fadin asibitin nan a rasa inda za’ayi posting dinta sai theater?..aiko billahillazhi bazata zauna a theater ba saidai duk abunda za’ayi ayi...suna barin office din kowa ya nufi various post dinshi including Billy dake maternity...ita kuma sai ta nufi office dinshi da nufin ta hadashi Allah annabi yasa a canxa mata posting...da sallama ta shiga ciki kanta a kasa ta gaisheshi...ya shiga binta da kallo sama da kasa yana wani 6ata rai kaman baiji dadin ganinya ba ya nuna hijab din jikinta yace"shi wnn mezai hana ki cireshi sai ki dinga yawonki a haka kawai"..kallonshi takeyi kallo irin na mamaki jin mgnr daya fada kafin tace"sir in cire hijab dina fa kake nufi"..a fusace yace"to meye amfaninshi tunda dama jikin naki kikeso a gani ai saiki cireshi kawai yanda zaa samu daman kallon jikin naki da kyau"...daure fuska tayi tana turo jin inda zancen nashi ya dosa tace"nidai bazan iya yawo babu hijab ba"...yace"if u are referring wnn abun dake jikinki to a hijab then you are deceiving yourself..ke ko irin asa babban hijab akan uniform baki iyaba..u always come out like this kamar dai tallan jikin naki kike"...sake daure fuska tayi jin maganganun da yake fada..indirectly fa zaginta yakeyi knn?..ita batasan ma tsautsayin daya kawota office dinshi ba tunda tasan halinshi and bazai ta6a canxawa ba...juyawa tayi zata fita a fusace yace"come back here"..ba yanda ta iya haka ta juyo ta dawo tana tutturo baki...mikewa yayi ya shiga wani kofa dake office din can sai gashi ya dawo da coffee hijab mai girma a hannunshi yana zuwa ya mika mata...batayi musu ba ta kar6a saidai fuskan nan har yanxu ba fus...komawa seat dinshi yayi ya zauna ita kuma ta sake juyawa zata fita yace"dawo kisa hijab din nan"...kaman zatayi kuka ta dawo ta zura hijabin..shi kuma yana zaune yana kallonta har wani dan murmushi ya saki ganin hijab din yayi covering dinta yanda yakeso yace"perfect...now seat saiki fadi meke tafe dake?.."zaunawa tayi tana sake marairaicewa tace"Sir dan Allah so nake kayi mgn CNO a daukeni daga theatre..tsoro nakeji wlh"...murmushi sosai ya saki wanda har ya bata mamaki dan zaiyi wahala kaga murmushinshi shiyasa idan yayi ma sai ta ganshi wani daban kmr ba proprietor data sani ba...saida ya gama smiling dinshi snn ya sake relaxing kan seat dinshi yana kallonta kamar ba gobe yace"yanxu me kikeso inyi Lamido?.."da sauri ta sake dagowa tana kallonshi dan ita wlh bata ta6aji ya kirata da Lamido ba..ko sunanta ma ita baya kira saidai yace ke ko wani abu amma yau shine da kiranta Lamido?..duk yau sai taga kaman bashi ba..kaman canxashi akayi sbd yanda yake behaving is so unlike him...ganin yanda tayi wani zuru tana kallonshi sai yadan hade rai yace"meye?.."da sauri tace"sir cewa fa kayi Lamido"...ya sake hade ran yace"eh ba hakane sunanki ba?..ko kinfi so kiji nace Aysher?.."wani mamakin ya sake kamata da alama yau dai Dr Bobby na cikin farin ciki...saita dan saki smile itama kafin tace"sir you are in a good mood today"..yana cigaba da smiling dinshi yace"of course..rabona da jin farin ciki kaman na yau har na mance"..dan wara idanu tayi irin abun mamakin nan sai kuma tacigaba da smile dinta tana gyada kanta tace"to sir albarkacin farin cikin da kake ciki kayi mgn a canxa min posting dan Allah"...girgiza mata kanshi yayi in a serious tone yace"no..kawai kiyi hakuri kije tunda can aka kaiki"...kaman zatasa kuka tace"sir suma fa nakeyi idan naga ana yayyanka mutum"...murmushi ya kara saki before yace"zaki dena inshaAllah..kuma I promise idan naga kin maida hankali kin nutsu sosai da kaina zanyi posting naki inda kikeso?.."nan da nan face dinta ya washe da fara’a tace"dan Allah da gaske?.."yace"yea i mean it..kawai so nake inga kin nutsu"...yana rufe baki kuwa ta hau gyada kanta tana fadin"nama nutsu tun yanxu wlh..i will be behaving gently"...yace"ni kuma zanyi posting naki inda kikeso"...sake gyada mashi kai tayi tana murmushi sai kallon yanda shima ya kasa dena murmushin take...mamaki take ashe haka murmushi ke bala’in mishi kyau amma baya yi?..kam ai da itace ta gane murmushi nayi mata irin kyan da yake mishi da kullum cikin murmushi zata kasance wlh koda cikin bacci ne kuwa...shi kuma kallonta kawai yake yanajin yanda yau ta ware dashi ba tsoro ba fargaba ko 6acin rai a tattare da ita...shi kanshi so yake ya gina kyakyawan alaqa tsakaninshi da ita yanda ko sun koma college bazata na gudunshi ba snn bazata na daure mashi fuska ba...yayi na’am da wnn shawara na zuciyarshi dan haka ya daura damarar gina shakuwa tsakaninshi da ita. Cikin lokaci qanqani sai shakuwa ya shiga tsakaninsu kamar dai yanda Bobby ya daura damara a farko...sam yanxu basu fiya fada ba dan tanabin kusan duk abunda yace tayi sbd ya canza mata posting...ranan da farko da aka sake shiga theater da ita saida tayi wnn suman saura kadan ta fadi Bobby yayi saurin tareta ta fada jikinshi...gaba daya hankalinshi dama yana gareta sbd yasan something like this might happen...dole sai fita sukayi da ita suka kira wata tayi replacing dinta amma daga baya a hankali sai ta fara sabawa...gaba daya tsoron sai ta dena jinshi tunda gashi za’a shiga theatre da ita har ayi a gama bata ji jiri kota suma ba saidai dan wanda baza’a rasa ba...a zaman kuma ta koyi abubuwa da dama dan sai yanxu take gane ashe zama a theater din yanada amfani...a haka ta cinyeshi two weeks dinta a theatre. Yana zaune office dinshi yana duba patients wayanshi ya fara ringing bai daga ba saida ya sallami matar ta fita..ya saki dan murmushi ganin wanda yake kira snn yayi picking ya gaidashi with respect...a daya 6angaren daddy yace"Attahir kana lafia?.."yace"ina lafia sir..ya aiki?.."daddy yace"Alhamdulillah..kana gida ko asibiti?.."yace"ina asibiti"...daddy yace"alright send me the address na shigo kano sai inzo mu gaisa"..da sauri yace"right away sir..itama tana asibitin yanxu haka"..murmushi daddy yayi kafin yace"ni kai zanzo gani ba itaba"..murmushin shima yayi kafin suyi sallama ya tura mishi address din...cikin mintina qalilan daddy ya karaso hospital din..Bobby da kanshi ya fita ya shigo dashi yanata yaba kyau da tsaruwar asibitin har suka dangana a office dinshi...zaunawa yayi shi kuma Bobby ya bude fridge ya kawo mashi ruwa da lemo snn shima ya zauna suka sake gaisawa...daddy yayita janshi da hira yana yaba asibitin nashi shidai tun yana jin kunya har ya sake ya shigayi mishi bayanin yanda suke gudanar a aiki a asibitin..har Schools da Colleges da yake dasu a sauran states saida ya fada mashi...ya kuma sanar dashi cewa yanxu haka yana preparation na bude Freedom University a Lagos...daddy ya jinjina ma kokarin yaron sosai ya kuma jinjinama kwazonshi da yake iya hada aiyuka da dama haka shi kadai..dukda cewa yana assistant a ko ina shima ba karamin kokari yake ba..nan take yaji ya sake burgeshi matuka..soyayyarshi ta ninku a cikin zuciyarshi fiyeda na baya..saidai ko kusa baiyi mamaki ba sbd yasan jinin Col Attahir zai iya aikata fiyeda haka ma a doron kasa matukar ya gaji mahaifinshi...suna zaune suna wnn hira Aysha ta shigo office din tana kokarin zaro wayanta daya dameta da kara sakamakon kira da akeyi tace"ko uban waye wnn yake damuna da kira oho?.."a tare suka juya suna kallonta jin abunda ta fada...daddy yace"sannu shugaban masu hankali"..batasan lokacinda ta saki waya da jakan nata ya fadi kasa ba sbd muryan wanda taji..sam batayi tunanin ganinshi ba wlh...lokaci daya kuma ta saki murmushi bayan ta dauki bag da wayanta ta karasa cikin office din tace"daddy sannu da zuwa"..girgiza kai kawai daddy yayi yana kallonta..can kuma ya juya yana duban Bobby da kanshi ke kasa yace"nasan kana nan kana fama da ita kou?.."dan dagowa yayi ya kalleta sai kuma ya saki murmushi yana girgiza kai yace"ai tayi hankali yanxu"..daddy yace"kana dai kareta amma ni nasan akwai abubuwanda dole saita yisu zataji dadi"..murmushi kawai Bobby yayi baice komai ba..ita kuma ta wani turo baki a cikin ranta tace"wato da kallon mara hankali sukemin knn da za’a wani ce nayi hankali yanxu"...muryan daddy ya dawo da ita daga tunaninda take nan ta gaisheshi snn yace taje ta kira Bilkisu..bayan few minutes suka dawo tareda Billy itama ta gaida daddy yana tambayarsu ya posting sukace Alhamdulillah...bayan sun gama yace suje kafin ya wuce zai nemesu zaiyi mgn da proprietor dinsu ba musu suka bar office din..shi kuma daddy ya shiga tambayan Bobby if da akwai abunda takeyi wanda ya kamata ya sani Bobby yace sam tayi hankali yanxu ta dena rashin ji..daddy yaji dadi sosai ya kuma ce still dai yanaso yacigaba da monitoring dinta har zuwa lokacinda zata bar makarantan domin koshi a yanxu yaga canji tattareda ita hakan kuma alamane na Bobby ya rike amanar daya bashi knn...Bobby ya amsa mashi da zai kula da ita sosai can cikin zuciyarshi kuma wani abu yaji yazo ya tokare mashi wuya...tunda daddy ya ambaci har zuwa lokacinda zata bar makarantan yaji wani irin sanyi ya kamashi...ashefa watarana gama karatun zatayi ta koma garinsu koh?..shi wlh sam baya kawo hakan a cikin ranshi...baisan ko sbd yanxu yana son kasancewa tarea ita ba amma sam tunanin haka bai taba zuwa mashi ba..yanxu kuma da daddy ya fada saiya tuna mashi cewa watarana da gaske zata bar college dinshi dama kano gaba daya kuma hakan na nufin bazai sake ganinta ba har abada...tunanin hakan saida yasa gabanshi yayi mummunan faduwa..to meyasa bayason rabuwa da ita?..meyasa a kullum yakejin sabbin al’amura gameda ita?..meyasa kuma idan ya ganta da wani yakejin kaman ya rataye kanshi sbd kunci?..for sure zuwa yanxu yasan kishinta yake saidai ko kusa bayaso yayi admitting yana sonta sbd hakan na nufin wargajewar abubuwa da dama a tare dashi..yayi nisa cikin tunani har baiji lokacinda daddy ya mike yana mishi mgn ba...saida ya dafa shoulder dinshi snn firgigit ya dawo hayyacinshi...daddy ya zuba mashi ido sosai yana kallon yanda duk yanayinshi ya sauya lokaci guda...bai tambayeshi dalilin hakan ba sbd a ganinshi ba huruminshi bane dan haka yayi mishi sallama yace zasu wuce Gombe...Bobby yayi mashi rakiya har inda motocinshi suke bayan ya sallami su Aysha ya shiga motar suka fita daga asibitin...Aysha kuma kai tsaye ta bishi office dinshi sbd mgnr changing posting da yace zaiyi mata. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba... masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 30 Kallonta kawai yakeyi tunda ta shigo office din zuwa yanxu...duk yanda yaso ya dauke idonshi a kanta kasawa yayi...baisan meyasa yakejin wani new feeling tattare dashi ba...baisan meyasa mgnr daddy ya tsaya mashi a rai ba..abu daya daya sani shine ko kusa bayason rabuwa da ita..baiki ta dawwama tana karatu a FCNM ba sbd ya dinga samun ganinta kullum amma saidai sam hakan ba mai yiwuwa bane...sanin kanshi ne hakan bazai ta6a yiwuwa ba koda a garin ga6a ga6a suke kuwa...watanni kadan da ya tabbata basu kai shekara ba suka rage mata ta gama karatunta and this means watanni kadan ya rage masa a tareda ita..watanni kadan ya rage masa kafin ya dena ganinta har abada tunda shidai yasan nor matter the situation bazai ta6a kai kanshi Gombe ba balle watarana yace zai nemeta su gaisa tunda ya shiga garinsu...gaba daya wadan nan tunanin sun cika mashi zuciya sun kuma hanashi sukuni...Aysha da taga idanunshi ne kadai a kanta amma mind dinshi is elsewhere ta dan buga table dake gabanshi tace"Sir am talking"..da sauri ya lumshe idanunshi kafin kuma ya budesu a kanta yanayi mata kallonda zata iya rantsuwa da Allah tunda suke bai ta6ayi mata irinshi ba...voice dinshi can kasa yace"what happened?.."narkewa tayi tana wani kallonshi kasa kasa tace"sir kace fa idan nayi two weeks zaka canxamin posting"...dan wara idonshi yayi a kanta kafin yace"then ki dawo office dina"..ta wani turo baki tace"nidai no dan Allah..cewa fa kayi duk inda nakeso zaka kaini?.."gyara zama yayi still yana kallonta yace"to ina kikeso?.."da sauri tace"eclamptic ward nakeso naje nayi two weeks..the remaining two weeks kuma sai inyisu a Ante Natal Clinic"...gyada kai yayi alaman ya gamsu kafin yace"zakije inda kikeso but on one condition"...da sauri tace"meye condition din?.."yace"bazaki shiga harkan kowane doctor ba a wurin..infact bama doctors kadai ba kowane staff indai namiji ne i want u to stay far away from him"..da sauri ta shiga gyada kai tana murmushi tace"bazan shiga harkan kowaba wlh..aini bana da interest kan doctors ko health workers sbd son matan su yayi yawa..besides inama da wanda zan aura"..fuska a tamke yace"to waya tambayeki?..nace maki inason ji ne?.."dan turo baki tayi tace"to kayi hakuri nidai"..yace"tashi ki barmin office"..ta marairaice tace"sir posting dinfa?.."yana nuna mata kofa yace"i said out"...maimakon ta fita saita fara bubbuga legs dinta a qasa zata fara mishi kuka tace"toba kai kace zaka canxamin idan ma nutsu ba?..alqawari fa ka dauka"...kallon yanda take tale baki yayi kawai sai ya saki murmushi hade da girgiza kai...wnn yarinya shidai bai ta6a ganin irinta ba wlh...ita kuwa kuka ta fara na karya kafin ya dakatar da dariyan da yakeyi yace"da nace saikin nutsu ai ba nutsuwan kikayi ba..yanxun fa kika gama min rashin kunya a nan"...ta wani zaro ido tana cewa"rashin kunyan me nayi?.."fuska a dan daure yace"kikace baki son doctors da health workers..sbd tsabar rashin kunya hadda cewa kinada wanda zaki aura"..if u see yanda ya karasa mgn face dinshi daddaure zakayi tunanin bashi ne ya gama daria a while ago ba..abun yayi mashi ciwo da har ta iya bude baki ta wani ce mishi tanada wanda zata aura?..sai kace cewa yayi shi zai aureta?...ganin yanda ya sake dinke fuska sai tayi kasa da murya tace"to am sorry"..a takaice yace"naji..tashi ki tafi"..kaman zata tashi sama haka ta dauki jakanta ta fita daga office din nashi rai a 6ace tanata faman bambami ita kadai...shi kuwa tana fita ya kifa kai da table din gabanshi ya shiga sauke numfashi. Washegari haka tazo office din nashi fuskan nan cunkus dashi kaman bata taba daria ba...sbd presence na Dr Aslam yasa bai nemi jin dalilin fushin nata ba yayi mata posting dinta kawai ta tafi...ranan har ya bar hospital din bai sake sanyata idonshi ba...washegari ma same thing happens kuma har ward din da take yaje bai sameta ba..duk jinshi yake wani iri da bai samu ganinta ba...a haka suka cinye satin nan tas bai sake ganin Lamido ba...damuwan da ya shiga a dalilin haka har mamaki yake bashi...yaudai yayi alqawarin dukma ina take zuwa ta 6oye idan ta ganshi sai ya nemota tunda ya tabbata zai iya samun matsala wajen bacci matukar bai sanyata a idonshi ba...cikin toilet dinsu aka ganota wai ashe tana hangoshi ya taho sai tayi wuf ta fada bandaki kuma bazata fito ba har sai ya fita..yaudai asirinta ya tonu dan har office dinshi yajata snn yace ta zauna suyi mgn..idanunshi a kanta kaman yau ya fara ganinta yace"why are u doing this?.."dan turo baki tayi tace"ba kaine ba"..yace"me nayi?.."ta sake turo bakin batace komai ba..shi kuma ajiyar zuciya ya sauke mai karfi kafin yayi lowering voice dinshi sosai yace"to kiyi hakuri"...dagowa tayi ya kalleshi da mamaki...ya sake cewa"kinji?.."murmushi ne ya kwace mata ganin yanda ya maida face dinshi abun tausayi...murmushin shima ya saki mai kyau yana kallon dimples dinta da yakejin kaman ya saka finger dinshi a wurin...ya sake yin kasa da murya yace"kin hakura?.."tace"eh mana..amma zaka denamin masifa koh?.."kallonta ya tsaya yi for some minutes kafin ya sauke numfashi yace"idan kin nutsu kin dena aikata abunda zanyi maki masifan ba?.."murmushin dai ta kara saki tareda fadin"na dena". Bayan sati hudu... Tuni sun gama posting dinsu sun koma makaranta...’yan year 3 su besty kenan tuni suma sun rubuta Hospital Final exam dinsu wanda sukayi passing sune suka fara rubuta council exam cikin satin nan...gaba daya Aysha ta zama wata iri daga ita har Billy ba karamin missing Sa’eed suka fara ba tun ma kafin ya tafi...kuka kuwa yana shanshi dan kullum ne idan suka hadu sai anyi mishi kukan nan hadda Billy data kasance abokiyar rigimarshi...shi kanshi shima ji yake kaman yayi kukan amma bazaiyi ba sbd namiji da dauriya aka sanshi amma only Allah knows yanda yakejin zafin rabuwa da zaiyi dasu...ranan Thursday bayan ya fito daga exams yaje hostel ya kwashesu suka fita wai yanaso su ragema juna radadin rabuwa da sukeji...duk inda yasan suna so saida ya kaisu including market da Lamido bata da burin da ya wuce ta shiga kasuwa a kano idan ta koma Gombe tayita bada labarin taje kwari taje sabon gari taje singa taje wambai taje bakin asibiti saidai wnn karon yawon sam baya masu armashi as kowa yanada damuwa cikin ranshi...a takaice sun shafe almost 3 hours suna abu daya kafin daga bisani ya saukesu gidan Hajia itama kuwa hadda dan kwallarta wai ta kusa dena ganinsu tunda Sa’eed zai tafi...kuka sosai sukasha a gidan nata kafin ya sake daukansu sai hostel dinsu..a bakin hostel din ma sun kwashi lokaci mai tsayi yanata aikin rarrashi da basu baki amma har suka rabu baiga alaman zasu dena kuka ba...the next day which is friday ranan sukayi final exam ma’ana sun gama da council saura waiting results kuma...ranan ma haka suka hada kai sunata faman kuka a cikin makaranta har mutane na kallonsu...saida akayi da gaske snn aka samu suka daina kukan yayi musu rakiya da kanshi har cikin hostel dinsu. Washegari Saturday tun safe Bobby ke kiran wayarta sbd saqo da babanta ya aiko mata dashi amma bata dauki waya ba...saida ya kiraya kusan sau shida snn yayi sa’a ta dauka...kafin yayi mgn Billy tace"sir nice..batada lafia ne bazata iya daukan waya ba"...zaro idanu yayi sosai hankalinshi a tashe sosai yace"meya sameta?.."a takaice Billy tace"fever.."yace"kun kaita clinic?.."tace"sir kasan halinta ai..taki yadda"...da sauri yace"kice mata nace ku sameni a clinic yanxun nan"..Billy ta amsa da"toh.."snn ta ajiye wayar tana duban Aysha da tun daxu ta kudundune cikin bargo ko oxygen na kirki bata shaka...as usual sai da kyar da sidin goshi ta samu ta mike suka tafi clinici din...tun kafin su shiga Bobby dake zaune cikin motanshi ya hangosu..gabanshi yaji ya fadi da yaga situation da take ciki dan ko tafiya ma da kyar take yinshi ga wani irin haske da yaga ta kara tun daga nan inda yake...bude motan yayi kawai ya fita kafin su karasa ya iskosu hankalinshi a kanta yace"kin tabbata only fever ke damunta?.."Billy tace"maybe baza’a rasa headache ba tunda kuka taita yi har yasa mata zazza6i"..kallonta kawai yayi kamar zai tambayi dalilin kukan sai kuma ya fasa...Billy ta sake cewa"sir ciki zamu shiga?.."girgiza kai yayi hankalinshi gaba daya na ga Aysha data samu wuri ta zauna tana sauke numfashi yace"i think saidai muje hospital sbd inaso ayi mata test shi kuma lab din nan ciki sun tashi..ki sata a mota kawai"...ba musu Billy ta sake kamata zuwa inda motarshi yake ta sakata a back seat snn ta rufe kofar...karasowa yayi shima ya shiga yana dubanta yace"ke bazaki jeba?.."girgiza kai Billy tayi tana murmushi tace"no sir..inaso inyi mata girki kafin ku dawo"..gyada kai kawai yayi ya rufe glass dinshi snn ya tada motar suka tafi Billy ta bisu da kallo tana fadin"love birds".🤪 Kai tsaye Freedom ya nufa da ita...yana shiga ciki ko parking daidai bai tsaya yi ba ya bude motar da sauri ya fita zuwa cikin asibitin...few minutes later ya dawo tareda wasu nurses mata guda biyu suna tura trolley bed...bude motan yayi matan suka taimaka mata ta fito suka dorata kan trolleyn snn suka shiga ciki...direct office dinshi suka kaita suka dorata kan bed da yake scanning da other examinations akai snn suka fita...maida kofa yayi ya rufe bayan sun fita ya shiga takawa a hankali zuwa inda take...idanunta yaga a kulle amma still hawaye basu dena fitowa daga cikinsu ba...hannu yakai forehead dinta yaji akwai zafi sosai dan haka ya koma seat dinshi yayi using landline ya kira lab yace a kawo mashi sample bottle...babu wasting of time aka kawo mashi..ya bude wani drawer nan cikin office din nashi ya dauko 5cc syringe da tourniquet kana ya koma inda take...hannunta ya kama a hankali ya daura tourniquet din a jiki aikuwa da sauri ta bude idanu tana kallonshi..ya wani hade rai tareda rike hannun nata da kyau dan yasan tsaf zata iya sawa yaji mata ciwo snn ya soka needle din cikin vein dinta...wani irin kara data saki saira kiris ya ya zare needle din daga jikinta sbd shiganshi da karan nata yayi...haka tana buge buge tana kuka ya dauki sample din nata ya zuba cikin sample bottle da aka kawo snn ya bada yace mp/widal yakeso ayi mashi yanxun nan...bayan fitar mutumin yayi checking vital signs dinta yaga all normal snn ya koma seat dinshi ya zauna waiting for the results...ana kawo mishi ya duba yaga da akwai malaria kadan babu typhoid dan haka ya rubuta drugs da injection da zaiyi mata ya bada aka amso mashi a pharmacy...saida ya gama withdrawing alluran da zaiyi mata snn ya karasa inda take yana tunanin ta yanda zaiyi alluran nan ba tareda ta tara mishi jama’a ba..kallonta kawai yakeyi yanda bacci ya fara daukanta yasan yanxu yana tashinta tayi ido hudu da allura ba karamin rikicewa zatayi ba...hannu yakai forehead dinta ta bude idon a hankali...tana ganin injection a hannunshi ta mike zaune da sauri idonta na cikowa da hawaye tace"Allura zakaimin?.."shiru yayi yana kallonta duk sai yaji ta bashi tausayi yanda tayi tambayar...zaunawa yayi kusada ita yana kallonta a hankali yace"bakya so?."da sauri ta hau gyada kai tana goge hawayenta...yace"amma Aysha alluran ne kadai zai saukar da wnn temperaturen naki da wuri?..bakiji yanda jikinki yayi zafi ba?.."ta shiga yarfa hannayenta hawaye na ambaliya fuskanta tace"nidai banson allura"...kallonta yacigaba dayi not knowing what to do or say...harga Allah yafison ya mata allura sbd fevern zaifi sauka da wuri amma kuma tausayi take bashi da wnn kukan da takeyi...lalla6ata ya shigayi da bata baki amma sai botsarewa take wai ita baza’a mata allura ba...nan kuma yayi abunda bayaso wato forcing dinta dan matseta yayi yayi mata alluran tanata rizgar kuka tana ihu bai saurara ba saida ya gama...sai kuma ya hadata da jikinshi ganin yanda legs dinta ke trembling murya can kasa yace"am so sorry"..kuka kawai take har breathe dinta yana kamar zai dauke...zaunar da ita yayi kan gadon shima ya zana gefe tareda cupping fuskanta yana kallon cute face dinta yace"stop crying mana..yanxu fevern zai sauka kinji?..am sorry"...kasa ce mishi komai tayi sai hawaye da sukaki tsayawa...Bobby ya lumshe ido ya bude shima kaman zaisa mata kukan yace"nace fa am sorry Aysher..kukan ya isa haka mana"..hannu takai tana goge tears din nata baisan lokacinda ya daga hannunshi ba kawai sai ganinsu yayi akan fuskanta yana goge mata tears din...saida ya gama snn ya sake kasa da murya yace"zakici abinci?.."girgiza mishi kai tayi tana turo baki shi kuma ya saki murmushi kafin yace"toki kwanta abinki..idan fevern ya sauka sai in maidaki hostel"...batayi masa musu ba ta juya masa baya ta kwanta shi kuma ya sake lumshe ido yanajin wani abun mai kamada magnet na kokarin janshi gareta...ganin ta cure legs dinta wuri daya ya janyo kujera ya zauna bayan ya gyara mata kafan sai ya tallabi cheeks dinshi yana kallonta...ta dauki almost an hour tana bacci shi kuma yana nan zaune inda yake yana kallonta..he just can’t take his eyes off her baisan meyasa ba...he drives pleasure staring at her..har wani smile yake saka akai akai ba tareda saninshi ba...a hankali yaga ta fara mosti kaman zata bude ido saita fasa ta wani turo baki inda kasan idonta biyu...daria sosai ya saki ganin yanda ta turo bakin..ya lumshe ido tareda kai hannunshi a hankali ya aza kan lips din nata sai kuma ya janye da sauri yana yarfa hannun idanunshi a kanta sbd wani abu da yaji kaman electric shock...sake juyawa tayi nan hulan dake kanta ya zame tareda faduwa kasa black silky hair dinta da bata cika yima kitso ba ya bayyana...saida breathe dinshi ya dauke na wucin gadi ganin gashin nata...da dadewa yasan tanada gashi tunda ya ta6a ganin kan nata amma sai yaga kaman daga wancan lokacin zuwa yanxu an kara mishi tsayi da baqi dan har wani daukan idonshi yakeyi...sake lumshe idonshi yayi a karo na ba adadi kawai sai ya mike daga wurin ya koma kan sofa ya zauna because abubuwan nan da yakeji bana lafia bane ya sani...tsaf zai iya mancewa ya aikata abunda daga baya zaizo yana regretting so it’s better he leaves kafin azo a samu matsala...haka yayaita zaune yana duban agogo saida tayi baccin 3 hours cur snn ta tashi tana wani yatsine fuska kaman wanda taga poopoo...mikewa yayi daga inda yake zaune ya karasa kusada ita yana dubanta with concern yace"how are u feeling now?.."a hankali tace"da sauki..inajin yunwa"..murmushi ya saki tareda sunkuyawa ya dauko hulanta dake kasa ya mika mata yana cewa"ki shiga bathroom ki farayin brush kafin a kawo abincin"...batayi mishi musu ba ta sauko daga gadon zuwa bathroom dinshi...da mouth wash tayi amfani da wanke bakinta snn ta dauro alwala ta fito rikeda hulan nata a hannu...kallon gashinta daya sauka shoulders dinta yayi yace"ya kika cire hulan kuma?.."turo baki tayi ta mayar da hulan batace komai ba...carpet ya shimfida mata da kanshi snn ya dakko jilbab dinta daya cire mata daxu shima ya mika mata..amsa tayi ta zura ta tayar da sallah shi kuma ya koma ya zauna waiting for abincin da yayi mata order yazo...tana idar da sallah ta sake dubanshi tana kwabe fuska tace"yunwa fa nakeji"...murmushi ya kara saki yace"Aysher ki kara hakuri mana..nayi ordern abincin ne and nasan suna hanya inshaAllah"...gyarawa tayi zata kwanta nan kan carpet din yayi sauri tasowa daga inda yake yace"karki kwanta kasa"..ba musu ta mike ta koma gado...bayan few minutes akayi delivering abincin nata dan haka ya mika mata gaba daya snn ya zauna yana kallonta...ita kuwa cik abincinta take hankali kwance sai kallon dimples dinta dake lotsawa idan tana tauna abincin yake...ba kanta ya fara ganin dimples ba amma nata kullum shi yake tempting dinshi yaji kaman yaje yasa finger dinshi a wurin...tana gama cin abincin tasha drink din kadan snn ya bata drugs suma tasha badon tanaso ba...saida yaga ta nustu ta dawo hayyacinta snn yace"can we talk now?.."kallonshi tayi batace komai ba...shi kuma yana kallon eyes dinta da sukayi luhu luhu sbd kukan da taci yace mata"what happened to ur eyes?.."raurau tayi da ido zatasa mishi kuka yace"I didn’t ask u to cry...cewa nayi meya samu idonki?.."tana kwabe fuska tace"kuka nayi"..."kuka?.."ya maimaita abunda ta fada kafin yace"me aka maki kikai kuka da har ya sanya maki zazza6i haka?.."lumshe ido tayi nan hawayen dake ciki suka silalo kan fuskanta tace"Bestie ne zai tafi"...cak yaji komai nashi ya tsaya including breathe dinshi...nan take face dinshi ya sauka murya a dakile yace"sbd shi kike kuka knn?.."cigaba da kukanta take tace"tafiya fa zaiyi ya barmu...ba sun gama council ba"..a kufule ya mike zuwa inda ya ajiye wayoyinshi yace"sai ki bishi ai"...harara ta watsawa bayanshi tana turo baki...ya dauki wayoyinshi daya ajiye nan wurin snn ya kama hanya zai fita yace mata"fito mu tafi"...da kallo kawai ta bishi tana mamakinshi..har yanxu bata bar mamakin yanda he can change forms in a blink of an eye ba..he can be nice for a second and become annoying the other second...shiyasa kwata kwata bata gane mashi...mikewa tayi ta zura jilbab dinta snn ta fita daga office din..a bakin kofa ta sameshi yana ganin ta fito yayi locking office dinshi snn ya wuce parking space...motanshi ya bude ya shiga itama tana karasowa ta shiga sai turo baki take...bayan sun dauki hanya ta dan saci kallonshi ganin yana driving..tunda suke bata ta6a ganin ya tuka kanshi ba saidai yayi d’urum a baya mota ana driving dinshi yau kuma wane salon ne yasa shi driving din oho?...motan yayi tsit ba abunda kakeji sai sanyin ac dake tashi...wayanshi dake ajiye kan dashboard ne ya fara ringing...yayi connecting Bluetooth snn ya daga..daga daya 6angaren da igbo Mummy tace"Bobby where are u?.."shima da igbo din yace mata"ina kan hanya Mummy..what happened?.."tace"jikin yarinyar nan ne naga kaman gaba yakeyi wlh..ko asibitin zamu kawota?.."yace"aah Mummy gani nan zuwa gidan yanxu"..Mummy tace"to kayi sauri dan Allah"..yace"toh.."snn ta kashe kiran...Lamido data kasa kunne tana jinsu bata fahimci komai a zancen nasu ba tace"kilan mamarshi ce"...yaji abunda ta fada sarai kulata ne kawai baiyi don a yanda ta kular dashi tsaf zai iya kwada mata mari wlh...haka ta ringa baza ido tana kalle kalle har suka iso kafar gidansu...maimakon ya shiga da motar ciki sai yayi parking a nan waje ya bude motar ya fita ya wani sake hade ranshi yace"saura kuma ki fito daga ciki kiga me zanyi maki"...tabe baki tayi ta kauda kai shi kuma ya juya ya nufi gate..kwankwasawa yayi mai gadi na lekowa yaga shine ya bude mishi da sauri ya shige cikin gidan...Lamido na ganin ya shiga ta bude motar ta fito tana karema gidan nasu kallo tace"ai wlh saina fito na bawa idona abinci"..sake juyawa tayi tana kallon zabgegen mansion din tana girgiza kai tace"gaskia mutumin nan me kudi ne..ji gida kaman ba’a Naija ba ni Aisha"..karasawa tayi jikin gate din ta shiga lekawa ta wata ‘yar karamar kofa kamar daga sama taji an danne mata horn ta bayanta...a rikice ta matsa daga wurin tana kallon motar dake kokarin shiga gidan sai tayi saurin komawa inda motarshi yake kafin ta shiga taji ance"yammata"..juyawa tayi tana kallon matar duk sai taji kunya ya kamata tana leka musu gida..ta shiga washe baki tace"ina..ina yini"..aunty sumy ta bude mota ta fito zuwa inda take tana kallonta da fara’a tace"lafia lau yammata..zaki shiga ciki ne?.."da sauri tace"aah tareda proprietor muke shine nake jiranshi"..ta karasa mgnr duka daburce kaman matsoraciya...aunty sumy ta saki smile jik tareda Bobby suke tace"to mu shiga daga ciki mana saiki jirashi a can"..tun kafin ta rufe baki Aysha tace"aa ba saina shiga ba wlh..yace kar in shiga"..dafa shoulder dinta aunty sumy tayi tace"karki damu bazaiyi maki komai bafa..aini nace ki shiga sbd haka muje plss"...narkewa tayi tana kallonta kafin tayi mgn aunty sumy ta sake fadin"please!.."haka nan ta bita suka cikin gidan ba don tanaso ba...mai gadi taba key ya shigo mata da motar snn suka wuce...matar ce tayi mata kwarjini wlh amma ita sam bata son shiga yazo yana wulakantata...suna shiga compound ta ware idonta tana kallon lafcecen compound din dake zube da uban motoci kaman na siyarwa..cikin ranta tace"babban burin inyamuri a dunia kenan..a danqara gida snn a hau motoci"..ganin bata daga kafa aunty sumy ta kama hannunta suka nufi entrance...basu samu kowa central parlor ba dan haka direct ta nufi parlon Mummy da ita...Mummy na zaune da Ilham akan cinyarta shi kuma yana rikeda hannun ilham din yanayi mata alluran jijiya..yarinyar tayi luf jikin Mummy sai sauke numfashi take...saida suka isa ciki aunty sumy ta saki hannunta tana doka wani uban murmushi tace"Mummy ga bakuwa na kawo maki"...dagowa Mummy tayi tana kallon yarinyar da kanta ke kasa kafin tace"to bismillah zauna kinji bakuwa"..karasawa tayi ta zauna a hankali har yanxun kanta yana kasa...Bobby da sai yanxun ya gama mata alluran yana dago kanshi yayi ido biyu da ita tana zaune kusada aunty sumy sai wani sussunne kai take...cikeda mamaki sosai yake kallonta yace"ke bakida hankali ne?..waya baki izinin shigowa gidan nan?.."juyawa Mummy tayi tana dubanshi tace"ka santa ne?.."dauke kai yayi yana huci ya kasa cewa komai...tambayoyin nan ne bai shirya amsawa ba shiyasa yace tayi zamanta cikin mota amma sbd tsabar rashin ji irin nata saida ta fito...yanxu shknn yasan ya shiga uku da tambayoyi a wurin su Mummy...ganin bazaice komai ba aunty sumy tace"ganinta nayi fa a cikin motarshi shine na tambayeta tace tare dashi suke amma yace ta zauna nan cikin mota karta fito"..juyawa Mummy ta sakeyi ta kalleshi sai taga ya sake hade rai yana muzurai sai ta maida dubanta ga Aysha da har yanxun kanta ke a kasa lokaci daya ta saki wani murmushi dan tasan zaiyi wuya idan ba itace Lamido ba dan haka tace"yammata meye sunanki?.."a hankali tace"Aysha"..Mummy ta shiga gyada kai tace"MashaAllah Aysha me babban suna ce ashe?.."daga kai kawai Lamido tayi tanajin kamar ta saki fitsari a wando sbd yanda takejin idanun Bobby nata kaiwa da kawowa a kanta..ko baa fada ba tasan kallonta yake...Miemie ce ta shigo parlon rikeda tea data hadoma Ilham..tana karasowa ta mikawa Mummy snn ta zauna tana kallon Aysha dake zaune tace"Mummy bakuwa mukayi?.."Mummy da har yanxu bata bar smiling ba tace"wlh bakuwa mukayi Miemie”..Miemie ta matsa kusada ita tace"sannu da zuwa ina yini?.."dan dagowa Aysha tayi ta kalleta kafin tace"lafia lau"..wara ido Miemie tayi da taga face dinta tace"laa Mummy ai na ta6a ganinta a FCNM wall..."bata samu karasawa ba sbd wani kallo da Bobby ya watsa mata ba shiri taja bakinta yai tsit..aunty sumy da tun daxu take kallonshi ganin yanda duk yabi ya takura kanshi kawai ta saki murmushi..ita bata ta6a ganin mai hali irin na Bobby ba wlh..kiri kiri ga abu kana sonshi amma wai kake kaiwa kasuwa?...mikewa Mummy tayi ta ba aunty sumy tea din Ilham tace"ki bata tasha"..snn ta karasa inda Malama A’ee take zaune ta kama hannunta ta mike tsaye snn ta jata zuwa dakinta tace"tashi muje mu gaisa ‘yata"...daga haka suka shige bedroom din Mummy..Bobby yabisu da kallo kaman idanunshi zasu koma jikin kofar dakin...hankalinshi yaji ya tashi kardai Mummy taje ta fadama yarinyar nan abunda zaisa ta rainashi fa..gabanshi har wani faduwa yakeyi wlh...kaman wanda aka tsikara yabi bayansu zuwa dakin da sauri kamar zai tashi sama... Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 31 Yana shiga ya marairaicewa Mummy yace"Mummy dan girman Allah mu tafi..bama ta da lafia shine na kaita asibiti"...murmushi Mummy tayi kafin tace"to ka jiramu a waje yanxun nan zata fito"..da sauri ya canxa yare yace"Mummy me zaki fada mata?.."da yaren itama tace"akwai abunda kake 6oyewa wanda bakaso ta sani ne?.."girgiza kai yayi da sauri duk yabi uzzurawa kanshi babu gaira babu dalili...kofa Mummy ta nuna mishi alaman ya fita haka ya juya ya bar dakin yana sake sake...bayan fitarshi Mummy ta dawo da dubanta ga Aysha tace"zauna mana Aysha"..maimakon ta zauna saita risina har kasa tana kallon kasan tace"Ina yini"..Mummy ta amsa da"lafia lau..ya karatu?.."tace"Alhamdulillah"..Mummy tace"to dawo nan ki zauna tunda mun gama gaisawa"..ba musu ta mike ta zauna inda ta nuna mata...kallonta kawai Mummy keyi taji ta shiga ranta sosai...irin wnn kyau da take dashi ai ba Bobby ba kowane namiji ma yana iya samun matsala idan aka jarabceshi da qaunarta...tana cigaba da dubanta tace"da gaske bakida lafia?.."kai kawai ta iya dagawa...Mummy tace"to Allah ya baki lafia..yanxu bari a kawo maki abinci kici"..da sauri tace"wlh mama na koshi banajin yunwa"...Mummy ba girgiza kai tace"aah dole kici wani abu"..daga haka ta kwaloma Miemie kira...tana shiga Mummy tace"jeki kawo mata abinci"...kafin ta fita Aysha tace"wlh ban dade da cin abinci ba banajin yunwa"..Mummy tace"to shknn dukda haka dai ko tafiya sai kinyi dashi...Miemie ki samu abu ki zubo mata pepper chicken sai ki hada mata da lemo"..ba musu Miemie ta fita don yin yanda aka sata...suna nan zaune ta dawo da wani bag mai kyau datasa pepper chicken din a ciki...Mummy tace"to ki rike mata saiki rakata waje dashi"..a hankali tace"toh.."snn ta juya ta fita...mikewa Mummy tayi zuwa wadrobe dinta ta dauko wasu turaruka masu kyau guda biyu ta zuba mata su cikin dan karamin jaka mai kyau snn ta bude drawernta ta dauko two sets na sarkoki suma masu azabar kyau duk ta zubasu cikin jakan...hajia indo dai tana zaune kai a kasa kamar munafuka..hannunta Mummy ta kama suka fita daga dakin...Bobby daketa safa da marwa ya juya yana kallonsu kamar idonshi zasu fadi kasa..saida daria ya subucewa Mummy sbd ganin yanda duk yabi ya addabi kanshi ba gaira ba dalili..shi kuma ya wani kwabe fuska da igbo yace"Mummy me kike ce mata dan Allah?.."bayan ta staida dariyarta tace"gata nan ka maidata kuma wlh ban yadda kayi mata fada ba Bobby..idan kayi kuma zai dawo kunnena"..daure fuska kawai yayi baice komai ba...aunty sumy ma ta fito daga dakinta rikeda wani dan box mai kyau tana karasowa ta mikama Aysha tana murmushi tace"to ga wnn Aysha..i hope zaki sake kawo mana ziyara?.."murmushi kawai tayi bata iya amsawa ba duk sun sata jin wani iri wlh..sunada kirki sosai unlike Proprietor da sukayi hannun riga da kirki...ta amsa abun tayi godia..Mummy tace"ai zai sake kawota mu gaisa"..aunty sumy tace"kwarai kuwa..idan ma bai kawota Mummy da kaina zanje har hostel dinsu in dauko mana ita"..shidai yana fsaye fuskan nan a tamke baice musu kala ba...after long surutunsu finally ya samu aka bashi ita suka fita..Miemie ta rakata har mota da kayanta ta zuba mata su back seat snn ta zaga inda take da nufin tayi mata sallama Bobby dake cika yana batsewa ya wani 6alla mata harara tareda fadin"bar nan"..ba shiri ta koma ciki tana turo baki...tada motar yayi da wani irin gudu suka bar layin nasu..Ita dai a tsorace take sai rarraba idanu take...suna hanya wayanta ya fara ringing ganin wanda ke kira sai tayi silencing wayar taki dauka sbd gudun masifanshi...sake kira akayi ta kuma sawa a silent shi kuma ganin batada niyyar dagawa yakai dubanshi kan wayar dake cinyanta sai yaga baby boo kan screen aikuwa ya sake dinke fuskanshi tsaf yana sake figan motan a guje kmr zai tashi sama...gani take kaman tsoron dunian nan a kanta ya sauka wnn uban gudun da yake idan yaje ya watsar dasu fa?..bata dai ce masa komai ba har suka isa gate din hostel...ya cire mata lock ba tarefa ya kalleta ba yace"fita"..da sauri ta kama kofar zata bude sai kuma taji yace"bana hanaki kiramin wani besty idan muna mgn ba?..ke wato bakyajin mgn koh?.."da sauri tace"kayi hakuri"..yace"sbd kinga banaso shiyasa kike fada wato koma me zanyi inyi koh?.."ta dan lankwasa wuya tace"sir nace fa kayi hakuri"...dauke kanshi yayi daga gareta yace"fitamin daga mota"..ta sake langabewa tana kwabe fuskanta tace"sir i said am sorry mana..kayi hakuri bazan kara ba"...juyo da kanshi yayi yana kallonta yace"idan kika kara inyi maki me?.."hannu takai tana shafa cheeks dinta kafin a hankali tace"ka mareni"..murmushi kawai ya saki tareda jinginar da kanshi jikin kujera..dama yasan fushin ma ba wani iyawa zaiyi da ita ba..itama murmushin ta saki tace"sir kacigaba da smiling dan Allah..yana maka kyau"..bude idonshi yayi ya zubasu a kanta..wasu sabbin al’amura yakeji suna zagayawa cikin jini da tsokarshi...mikewa yayi daga inda ya jingina still yana dubanta ina serious note yace"da gaske banason jin wani besty ko waye a bakinki..banaso idan kuma kika sake kiramin shi muna mgn marinki zanyi kaman yanda kika fada"..murmushi take tace"bazan ma kara ba inshaAllah"..yace"shknn u can go..and make sure kinsha drugs dinshi akan lokaci kuma banda skipping idan ba haka ba kuma alluran da bakiso shi za’a kuma yi maki"...bude motar tayi ta fita still tana murmushi tace"aah banason allura zansha maganin..saida safe"..kanshi kawai ya iya daga mata snn ta juya ta tafi bayan ta kwashi kayanta dake baya...saida yaga shiganta ciki snn yaja motarshi ya kara gaba. Tun daga wnn ranan suka sake dinkewa abunsu...tanajin magananshi sosai and hakan ba karamin farantawa Bobby yake ba..zuwa yanxu ya gama admitting ya kamu da soyayya..soyayya kuma na bafulatana data fito daga jihar Gombe..what a miracle..tunda yake bai ta6a tunanin zaiso wata mace ba ballantana ‘yar Gombe amma ita sai yaga kaman turota akayi dan tazo ta wargaza duk wani tanadi da alqawura da yayima kanshi...shida yake shiga college only Thursdays da Fridays amma yanxu kusan kullum sai ya shiga sbd kawai ya samu ya ganta domin ganin nata shine kadai samun nustuwarshi...yanayi mata sonda shi kanshi bai tunanin yana yiwa kanshi amma har yanxu ya kasa nuna mata dukda yasan wani lokacin actions dinshi suna nunawa sbd kasa controlling kanshi da yake amma ita kota fahimta bata ta6a nuna mishi ba...abu biyu dake damunshi sune na farko amanarta da mahaifinta ya bashi yana gudun kada mgnr sonda yake mata ya fita shi kuma mahaifinta yaga kamar bai rike mashi amana ba tunda har shi da kanshi zaice yana sonta..sai na biyun kuma shine Gombe..bayan kasancewarta ‘yar Gombe muma tazo a bafulatana..har yanxu bai mance yanda ‘yan uwan dad dinsu fulani sukayi treating Mummy ba..shima yana tsoron kada yaje neman aurenta ace dan inyamura ne shi baza’a bashi ba..ga kuma su kansu ‘yan uwan daddyn da matukar zaiyi aure dole saiya nemi inda suke sbd su shige mishi gaba kan mgnr saidai sam baiji zai iya zuwa ya samesu ba..har yanxu yana nan akan bakanshi na babushi babusu amma kuma tayaya zai samu auren Lamido ba tareda sa hannunsu ba?..gaba daya ya zama wani iri yanxu ko abincin kirki baici..aiyukan nashi ka neman tsaywa suke cak sbd damuwar da yake ciki..har dan ramewa yayi sbd tunani..Mummy tayi tayi dashi ya sanar mata abunda ke damunshi amma kullum mgnrshi daya shine babu komai...ganin yana neman rasa nutsuwarshi yau dai ya yanke shawaran zaije ya samu Nur suyi mgn ko yanada solution da zai bashi...gashi itama yarinyar wahalar dashi takeyi these days baisan laifin da yayi ba duk ya kirata a waya bata dauka...hankalinshi ba karamin tashi yayi ba yau kusan 5 days knn baiji muryanta ba kuma bai ganta ba dan haka yake jin kanshi kaman mara lafia..baisan meyasa take mishi irin wnn ba..haka nan babu laifin zaune babu na tsaye saita dauke mishi wuta sai yayita binta yana lallashi snn zai samu kanta amma this time around yace bazai ske nemanta ba inyaso sonta yayi ajalinshi shima sai ya samu ya huta. Yana shigowa College zuwa office din Nur da yace mashi yana jiranshi a ciki...da sallama ya shiga yana takawa da kyar sbd matsaloli da suka taru suka cika mashi brain...Nur na ganinshi ya mike ya koma kan sofa shima karasawa yayi ya zauna nan kusa dashi tareda jingina da jikin kujeran yana lumshe ido...Nur yace"kace zamuyi mgn i hope dai lafia?.."girgiza kai Bobby ya shigayi tareda bude idanunshi yace"ba lafia ba Nur..ina cikin damuwa"..gyara zama Nur yayi yace"to inajinka"..ajiyar zuciya Bobby ya sauke yana shakar iska da kyar yace"it’s about Lamido..i think..i think i’ve fallen for her"...dukda Nur ya dade da sanin yana sonta yayi mamaki sosai jin a yanayin daya fada mashi...kamo hannunshi Bobby yayi yana kallonshi da idanunshi da suka sauya kala muryanshi cikin raunin da Nur zai iya rantswa bai ta6ajinshi a ciki ba yace"i am in a serious mess Nur..na rasa nustuwata gaba daya..komai bayamun dadi..komai banajin dadinshi abu daya da yake keeping dina company shine tunaninta..zuciyata ta cuceni duk iya kokarina na ganin na kaucewa abunda nakeji abun yafi karfina Nur..bansan meya kamata inyi ba nasan yarinyar nan bazata ta6a sona ba"..yana rufe baki Nur da yaji asalin tausayinshi na ratsashi ya dafa shoulder dinshi yace"Man take it easy plss..idan kana wnn damuwan kana iya samun problem ka sani..nayi maka alqawarin i’ll help you in anyway possible dan inga ka samu soyayyarta..wnn matsalan nake guje maka shiyasa tun farko naso ayima tufkar hanci baka bani dama ba"..sake damke hannunshi yayi yace"yanxu na baka do your best plss..ka taimakeni before i loose my sanity..inajin zafi sosai duk lokacinda na ganta da wani..yanxu haka da nake mka mgn ko wayana bata dauka kuma bansan laifinda nayi mata..nasan kilan Allah yanaso yayi punishing dina ne kan abubuwanda nayi mata a baya amma wlh bada son raina bane..bansan meyasa ina ganinta raina yake 6aci har yasa nayi mata abubuwanda nayi ba"..rungumeshi Nur yayi cikeda tausayinshi sosai yace"it was all the love Bobby ganewa ne bakayi ba..tun daga ranan da tacemin kace baza tayi presentation ba nasan da akwai wani abu a ranka gameda ita..Lamido is a good girl..tanada hankali sosai and am sure ko bata soka yanxu ba watarana zata soka"...dagowa yayi daga jikinshi yana kallonshi with a wide smile jin abunda ya fada yace"nagode sosai Nur..thank u..kasan a da nayi tunanin sonta kake sai kuma daga baya naga ba haka bane"...Nur yace"well a gaskia bazan boye maka ba i once had a crush on her amma tunda ja fahimci kana sonta saina hakura sbd nasan sonda kake mata yafi wanda zan mata..kuma dakai tafi dacewa bada ni ba and inshaAllah i will do my possible best inga na hada wnn soyayyan..ba karamin matching couple zaayi ba kai da Lamido"...murmushi sosai Bobby yake wanda ya manta when last yajishi so lively haka...maganganun da Nur ya fada sai yajisu tamkar diamond da gold sbd tsananin dadinsu da yaji...cikin murmushin da yaki bajewa fuskanshi yace"thank u so much friend..u are really a friend indeed"...shafa kai Nur ya fara yana wani murmushin shakiyanci yace"gaskia ya kamata ayi saluting Lamido data canxaka haka?..yau Dr Bobby ne da godia haka ba kakkautawa?.."murmushin shima ya kara saki shi kanshi ya dade yana mamakin kanshi..ya dade yana mamakin yanda ya canxa ta 6angarori da dama duk kuma a dalilin Lamido...Nur dake kallon yanda yake blushing yace"amma wait..laifin me kayi ta dena daukan wayanka?.."da sauri Bobby yace"nima i dont know..haka nan ta daukemin wuta rabon dana samu peaceful sleep tun ranar dana ganta last..ina cikin damuwa sosai Nur ka taimakamin dan Allah..I really want to see her..na dade ban ganta ba"...wani murmushin Nur ya saki kafin yace"karka damu yanxun kuwa zaka ganta..let me call her"..yana fadan haka ya dauki wayanshi dake kan table ajiye snn ya nemo numberta yayi dialing..da sauri Bobby ya matso kusa dashi yana kallon wayan kamar zai ganta ne a ciki..Nur yasa a speaker nan kuma sukaji kiran ya shiga..tana dauka tace"Sir ina yini"..Bobby ya wani lumshe ido yanajin yanda muryan nata ke zagayawa cikin dukkanin systems dinshi..he missed her like crazy..jin muryanta kuma sai ya sake kwadaita mishi son ganinta..yasan yau idan bai ganta ba matsala zai samu gaba daya..he don’t think zai iya daukan rashin ganin nata anymore..he just can’t..he need to see her...idon Nur na kallonshi yana kallon yanda ya fada duniar shauki sbd jin muryanta yace"hajia Lamido manyan mata..ya studies?.."tace"Alhamdulillah sir dama inaso inzo wurinka akan mgnr malam Mukhtar"..yace"then kizo office yanxu dama nima nemanki nake"..tace"ohk gani nan"..daga haka Nur ya kashe wayar yana duban Bobby yace"she’s coming"..kai kawai Bobby ya iya daga mashi yana tunanin yanda zasu kwashe da ita...mikewa Nur yayi ya koma seat dinshi yana zama sai gata ta shigo office din sanyeda uniform dinta as usual da glasses dinta a ido...tana gama kulle kofa ta juyo zata nufi inda yake zaune kawai idanunta duka hango mata shi a zaune ya waniyi crossing hands dinshi yana kallonta kaman wani soko...dan daure fuskanta tayi ta dauke kai snn ta karasa gaban table din Nur tace"Sir i think zanje sai in dawo some other time"..da sauri Nur yace"amma why?.."bata amsa mashi ba ta juya da sauri zata fita Bobby ya mike da saurin shima yasha gabanta...ta dago tana kallonshi fuskan nan a kwabe tace"nifa wucewa zanyi"..mai mata bazan sai aikin kallonta da yake kaman ba gobe...matsawa tayi zatabi gefenshi ta wuce nan ma ya sake tare mata hanya kawai saita dago tana kallonshi kaman zatasa kuka...Nur da yaga wasan nasu ya fara daukan zafi sai ya mike daga inda yake ya ra6a ta gefen Bobby zai fita daga office din ya dan rankwafa saitin kunnenshi yace"Man karka raga mata wlh..make her fall for u"..yana gama fadan haka ya fice daga office din Lamido tabishi da kallo kamar zatasa kuka...sake matsawa tayi zata wuce shima ya sake tare mata hanyar...tayi kasa da kanta kawai tana turo baki kawai sai jin mutum tayi dab da ita dan har numfashinshi a jikinta ke sauka..ta matsa baya tana sake turo baki shima ya sake matsawa inda ta matsa din..ta sake taking two step backward shima yayi haka kawai saita shiga yarfa hannunta tace"sir ni me nayi?.."baice mata komai ba sai binta da yacigaba dayi har ta fada kan sofa..maimakon ya zauna kan sofa sai ya janyo table dake wurin ya zauna a kai yanda zaina kallonta da kyau..muryanshi kasa kasa yace"why are u ignoring my calls?..no why are u ignoring me?.."sake turo baki tayi tace"sir ni banyi ignoring dinka ba"..yace"shi kuma kin daukan wayana na meye?.."tace"ba komai"..kallonta ya tsayayi for like five minutes kafin ya sauie ajiyar zuciya ya sake yin kasa da muryanshi yace"nayi maki wani abun ne?.."ta girgiza kai...yace"then why all these?..why are u doing these?..if saboda na kwace maki rings dinki ne zan maido maki kayanki amma ki dena wahalar dani haka plss"...kallonshi tayi jin abunda ya fada kafin tace"nifa bakayi min komai ba..kawai naga mutane sun fara tunanin soyayya mukeyi shiyasa na dena kulaka"..diff yayi yana kallonta jin kalamanta...yace"yanxu sbd ana tunanin muna soyayya shine zaki dena daukan wayana?.."tace"to sir muda ba soyayya muke ba meyasa zamu ba mutane kofar da zasuyi tunanin soyayya muke?.."tana rufe baki yace"nina fada maki haka?..ko kinsan mind dina ne?.."dagowa tayi ta kalleshi da mamaki sai kuma ta kawar da kanta tana wani daure fuska tace"wlh ba soyayya muke ba"..cikin 6acin ran da yaji ya fara diran mishi yace"wai yaushe kika rainani ne haka?..kinsan zuciyata ne?..well idan baki saniba to let me tell you now..i love you..i love you with my whole heart kuma i want to marry u"..a rikice ta sake dagowa tana kallonshi taga yanda ya tsareta da ido kawai saita rufe fuska da hannayenta ta rushe da matsnancin kuka...hankalinshi yaji ya tashi sosai ga wani irin rauni da yakeji kawai saiya dafe goshi yana sauke numfashi..wai dama haka soyayyan yake ko kuwa nashi ne yake zuwa mishi da wann problems haka?..yana kokarin solving matsala sai kuma ga wani ya kawo kai sun taru suna neman fasa mashi zucia..ganin da gaske kuka takeyi yayi kasa da murya yace"yi hakuri i was kidding..bana sonki..amma seriously idan baki dena ignoring dinaba zaki sani cikin matsala wlh..koma meye ya faru I apologize and idan laifi nayi maki you are free to punish me amma ki dena bani wnn attitude din i beg of u plss"..dakatar da kukan tayi tana kallonshi hawaye sha6e sha6e a fuskanta tace"kace da wasa kake?.."da sauri yace"yea wasa nake..i never loved u"..ajiyar zucia ta sauke tana goge hawayen idonta tace"thank you"...kallonta kawai Bobby keyi yanajin wani irin daci a bakinshi sbd 6acin rai..yanxu tsanar da tayi mishi har yakai tasa mishi kuka sbd yace yana sonta?..anya kuwa zai samu soyayyar yarinyar nan?..anya kuwa zai iya jure wnn matsalolin?..ganin ya tafi wani dunian daban ta mike tsaye tana dubanshi tace"sir ni zan tafi"..dagowa yayi ya kalleta from head to toe before saying"ina hijab dinki?.."kallonshi tayi tace"wane hijab?.."rai a dan 6ace yace"ba nace ki dinga sa hijab idan zakizo makaranta ba?..wato mantawa kikayi koh..?"da sauri tace"nazo dashi fa yana class"..nuna mata inda ta tashi yayi yace"to zauna bamu gama mgn ba"..ba musu ta koma ta zauna tana wani ta6e baki tace"amma dan Allah kayi sauri ana jirana ne"...kallonta kawai yake dan baisan amsan da zai bata ba..wai shi yarinyar nana take gayawa mgn haka...idan ba ruwa daya daki babban zakara ba ita ta isa ta zauna gabanshi tana fada mashi mgn haka bai gaura mata mari ba..amma yanxun wai shine nan zaune tana zuba mishi iskanci iri iri kuma bai iya ta6uka komai ba sbd soyayya..amma soyayya baima Dr Bobby adalci ba wlh...saida ya bari ta gama ta6e ta6en bakinta snn yace"kinaji?.."tace"ehh.."yace"dan Allah inaso daga yanxu duk nayi maki laifi ki fadamin ba kije kiyita fushi kinakin daukan wayana ba..banajin dadi..snn kullum kika shigo school ki dinga zuwa office ina ganinki kinji?.."kallonshi tayi kaman zatasa kuka tace"sir kullum kuma?..ai ba kullum kake shigowa ba..kumani banaso inzo kayita min fada fa"da sauri yace"ina shigowa kullum mana..every morning zan shigo idan muka gama gaisawa sai in wuce hospital...kawai nidai ki dinga picking calls dina and ki dinga zuwa ina ganinki?..fada kuma indai ba ganinki nayi da wani ba ba abunda zaisa na miki..duk abunda kikaga na maki rashin jinki ne ke janyowa"mamaki sosai ya bata jin abunda yake fada...ba tareda ta kawo komai a ranta ba tace”zanzo..kuma ni ai bana kula kowa..besty ma da ya taf..."bata karasa ba yace"enough..zaki fara kou?.."da sauri ta dora hannu kan bakinta tace"yi hakuri toh..na dena"..kofa ya nuna mata yace"jeki"..da sauri ta mike ta fita shi kuma ya lumshe ido tareda jingina da kujera...shidai zaiga ranara da za’ayi mgn na minti goma da ita ba tareda tayi mentioning wnn bestyn ba...duk yanda yakai da son ganinta da kuma son kasancewa da ita gara ta tafi akan dai ta zauna tana mishi hiran wani wai besty..shi tunda yake bai ta6ajin ya tsani wani kaman yanda ya tsaneta da bestyn nan ba...ya samu ganinta kuma yayi mgn da ita maimakon ya samu farin ciki sai yajishi akasin haka..sam abunda yakeji is not close to farin ciki...wai shi soyayya dai haka yake cikeda rudu da matsaloli dama?..meya jefa kanshi a ciki ne?..innalillahi wainna ilaihi rajiun..yaketa maimaitawa a cikin ranshi...Nur na ganin fitarta daga office din ya dawo ciki yana kallon Bobby yace"Man how far?..ka samu ka shawo kanta?.."ba tareda ya bude idanunshi ba yace"for where?..yarinyar nan tanada rigima wlh..maimakon in samu sauki fa karamin tayi akan damuwan da nake ciki"...zaunawa Nur yayi kusa dashi yana murmushi yace"ai dama da ganin Lamido nasan mijinta sai yaci ubanshi wlh..at times sai inyita tunanin da wnn shagwa6an nata ya takeyi da boyfriend dinta ne kam?..i never tought it’ll turn out to be you sai yanxun"...kallonshi kawai Bobby daya bude idanunshi yakeyi..yasan abunda yake fada gaskia ne..shi kanshi ko a da din ya kanyi tunanin ya mijinda ya aure ta zaiyi coping da wnn halayyan nata sai gashi ya tsinci kanshi cikin tafkin sonta tsundum kuma baya fatan fitowa har abada...fatanshi ya samu ya shawo kanta idan tayi accepting love dinshi to duk abunda zai biyo baya mai sauki ne. Ita kuwa tana fita ta kama hanyan class dinsu tana fadin"kam lallaima mutumin nan wani wai yana sona?..to ni ko rasa miji nayi me zanyi da inyamuri Allah na tuba...Allah ya kiyaye na auri dan yaro ma kamanshi wlh..aini matar manya ce ba matar irinsu kananun yara ba..dan rainin wayo kawai". Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 32 Da misalin 9 na dare yana zaune dinning yasa abincinshi a gaba amma ko loma daya ya kasa kaiwa bakinshi...goshi ya dafe da both hannayenshi yanatunanin abubuwanda suka faru...kawai gani yake dalilin kauracewa yan uwan daddy da yayi Allah yakeson ya hukuntashi da ita...shi gani yake wnn abun da yakeji gameda ita yayi yawa...tunda yayi mgn da ita zuwa yanxu bai samu peace of mind ba sbd yanda tayi reacting da yace yana sonta..kawai tasa mishi kuka sbd da gaske ta tsaneshi ne ko kuwa sbd tsabagen ta6ara da yake dawainiya da ita...yayi zurfi cikin tunani har baisan sanda Mummy tazo ta zauna kusadashi ba sai hannunta da yaji ta dafa shoulder dinshi..da sauri ya dawo hayyacinshi tareda daukan spoon dake nan cikin abincin nashi da sauri ya shiga cin abincin kamar mayunwaci..bayason ta gane halinda yake ciki baisan kuma ta riga ta gano ba...batace mishi komai ba sai kallon yanda yake tunkuda abincin take tana jira ya gama suyi mgn dan yau ko yaki ko yaso saiya sanar da ita damuwarshi...tausayi yake bata yanda yake kokarin 6oye suffering dinshi bayan bayyanawa kadai ne maslaha...bata katse mishi cin abinci ba saida ya gama ya kora da drink snn ta kira sunanshi...kasa amsawa yayi sai juyawa da yayi yana kallonta...kallonshi takeyi itama sosai tace"Bobby wai meye matsalarka?..why kake kokarin 6oye abunda ba kai ka dorama kanka ba kuma 6oyewan bazai haifar maka da komai ba..kanaso ciwon zucia ya kamaka sbd wnn damuwan daka dorama kanka ne?..baka tunanin halinda ni da ‘yan uwanka zamu shiga idan wani abu ya faru dakai?..duk bakayi wnn tunanin ba kake kokarin cutar da kanka koh?.."shiru kawai yayi yana kallonta yasan duk mgnr data fada gaskia ne..da gaske abunda yakeji bashi ya dorama kanshi ba..kuma kokarin 6oye hakan ba abunda zai haifar mashi sai dana sani amma ya zaiyi?..soyayya ne Allah ya jarabceshi dashi na yarinyar nan kwata kwata bai ganin zata soshi..shi kuma so yake ya yakiceta daga zuciyarshi amma zuciyar taki bashi hadin kai dama tun ba yanxu ba yasan zuciyarshi tafi shi kanshi taurin kai sbd yanda yayita kokarin dakatar da abun tun yana dan karami abun bai yiwu ba har yanxu aka kawo wnn matakin...yasan yanxu tana gama makaranta kilan a hadata da wani ta aura ko kuma ta fitoda wanda takeso tunda tasha fada mishi ita tanada wanda zata aura...tunanin hakan yasa yaji wani irin nauyi a cikin zuciyarshi...idonshi suka kada sukayi jaa har wani shinning suke sbd dan kwalla daya cikosu...da sauri ya kifa kanshi jikin Mummy ya sauke wani ajiyar zuciya irin na wanda yaci kuka ya koshi...numfashinshi ma da kyar yake shaqa sbd kokarin 6oye hawayenshi da yake...baison Mummy ta gani shiyasa yayi haka amma yasan da kyar ma idan bata gani ba...saida ya dauki almost 3 minutes a haka kafin ya dago daga jikin nata yana sauke kanshi kasa...wnn raunin da yake zuwa mishi duk yayi mgn da itane bayaso shiyasa bai cika son yin mgnr da itaba..da akwai wani irin rauni da karyewar zuciya dake zuwa ma mutum duk yake gaban mahaifiyarshi idan ya tsinci kanshi cikin wani yanayi mara dadi...baisan ko kowa haka yakeji ba amma shidai haka yake tun yana dan karaminshi...hannu Mummy takai ta dago fuskanshi tana kallon idanunshi da har yanxun suke shinning sbd hawaye da suka kuma taruwa a ciki tace"let them out son..zakaji sauki"..da sauri ya sauke kanshi yana sake kokarin mayar dasu amma wnn karon sai yaji kamar turosu akeyi da gayya dan haka ya sake maida kanshi jikinta da sauri daidai lokacin kuma hawayen suka silalo kan fuskanshi...bayanshi Mummy ta shiga shafawa a hankali itama nata muryan a raunane tace"cry as much as u want zaka samu sauki"..shidai bai iya cewa komai ba sai hawaye da har yanxu basu dena zubowa fuskanshi ba...mamaki da haushin kanshi suka dirar mishi lokaci guda...shi kanshi he can’t remember when last ya zubar da hawaye da idonshi amma wai yanxu shine ke kuka sbd karamar yarinya..wnn wace irin jarabawa ce?..some months back idan kace mishi zai kamu da soyayya kuma har yayi kuka sbd wata mace kallon you are not normal zaiyi maka amma yanxun gashi dumu dumu cikin soyayya snn kuma gashi yanata kwararar da hawaye abunda zai iya cewa rabonshi dayi tun bayan rasuwar mahaifinshi...Allah ma yasoshi ba kowa a wurin da kunya zaiji wlh...Mummy ce tasa hannu ta dagoshi tana goge mishi hawayen da yayi saura fuskanshi kafin tace"fadamin..what exactly happened?.."hannunta ya kama duka biyun yana dubanta cikin voice dinshi daya fara disashewa yace"she doesn’t love me Mummy..she despise me..da bakinta tacemin tanada wanda zata au.."kasa karasawa yayi sbd wani abu dayazo ya tokare mishi wuya..sake dora kanshi yayi shoulder dinta yana jujjuaya kan nashi from side to side yace"mutuwa zanyi Mummy...wlh duk ranan da ta auri wani i won’t survive zuciyata bugawa zatayi in mutu Mummy ki taimakamin please!.."rungumeshi Mummy tayi itama nan take hawaye suka ciko idanunta tace"u won’t die inshaAllah..Bi’iznillah batada mijin aure sai kai sbd haka ka kwantar da hankalinka"...girgiza kai yacigaba dayi yace"Mummy wlh i can’t..dan bakisan yanda mukayi da ita bane..she even cried da nace ina sonta kuma nasan halinta Mummy da gaske bata kaunata shiyasa takemin haka...bansan meyasa Allah zai..."bai karasa ba Mummy tayi saurin rufe mishi baki tana cewa"karkayi sa6o Bobby..kayi hakuri mubi komai a sannu inshaAllah komai zai wuce..komai zai zama tarihi"...wani numfashi ya sauke mai karfi tareda fadin"Allahumma Ameen Mummy..Allah sa ya zama history kaman yanda kikace"..tace"Ameen InshaAllah..yanxu tunda ka gama cin abincin ka samu kaje ka kwanta naji jikinka da zafi anya ma zaka iya bacci a haka kuwa?..kodai muje asibiti?.."girgiza mata kanshi yayi kafin a hankali yace"don’t bother haka yakeyi dama"..da mamaki tace"u mean haka kake kwana da fever kullum kuma bakayi kokarin kayi wani abu ba?.."dagowa yayi ya kamo hannunta yace"Mummy ai bai dade da farawa ba..for the past few weeks ne kawai and inashan magani"..girgiza kai Mummy keyi tace"ban yadda ba..nasan ba maganinda kakesha"..yace"da gaske inasha Mummy..kinsan bazanyi wasa da lafiyana ba"...tace"ya kamata dai kar kayi wasa dashi din idan kuma baso kake Lamido tace batason mai yawan rashin lafia ba"..da murmushi ta karasa mgnr aikam shima saiga wani hadadden murmushi kwance akan fuskanshi...Lamido kawai da aka kira yaji kaman anyi mishi gagarumin kyauta wnn baisan yanda zaiji duk akace ta zama matarshi ba...ganin yanda Mummy ta tsareshi da ido sai ya mike yayi mata sallama ya kama hanyar Flat dinshi...da kallo Mummy ta bishi tausayinshi na sake kamata..ta tabbata authentic so yakema yarinyar nan har tunda taga yayi abunda ita kanta ta manta yaushe rabonda yayi shine hawaye...addu’anta bai wuce Allah ya karkato da hankalin yarinyar kanshi ba snn yasa ayi komai da komai cikin sauki da kwanciyar hankali. Shiko Bobby yana shiga Flat dinshi kulle kofanshi yayi ya wuce direct zuwa bedroom dinshi...bayan yayi wanka yasa pyjamas dinshi snn ya kwanta ya dora wayanshi kan kirji wani sashe na zuciyarshi sai azalzalanshi yake ya kirata ko muryanta yaji yasan zai danji sauki yayinda daya sashen kuma yake cewa idan har ya kirata bayan duk wulakancin da tayi mishi daxu to ya tabbata a kirashi da mara zuciya...shiru yayi gamida runtse ido yanajin shawarwarin da ko wane sashe na zuciyar ke bashi...shi kanshi yayi na’am da kin kiran nata dan haka ya sake kulle ido ya lullu6e da duvet shi a lallai bacci yakeso ya daukeshi sbd kwata kwata bayason yawan tunanin nan da yake amma kememe bacci yace baiga daman daukanshi ba..haka ya karaci juyi yana rungume pillow daga karshe dai dole kasa daurewa yayi saida ya danna mata kira...har ya gama ringing bata dauka ba dan haka ya sake kira..yana gab da katsewa ta daga cikin magagin bacci tace"baby ka bari in tashi daga bacci sai muyi waya kaji?.."wani irin abu yaji yazo ya tokareshi a wuya har numfashinshi na barazanar daukewa...bai iya ce mata komai ba ya kashe wayarshi gaba daya...ita kuma jin baice komai ba ta dago wayan tana kallon screen sai taga proprietor a jiki nan take baccin dake idonta ya wartsake ta wani zare ido tareda fadin"na shiga uku"...sam bata duba wanda ya kira ba tayi zaton shine tunda daxun yace mata idan ya isa gida zai kirata..hankalinta taji ya tashi tasan yanxu da kyar idan basuyi rigima dashi ba..sake kiran wayanshi tayi amma har ya gama ringing bai dauka ba..data sake kira kuma sai taji wayan gaba dayanta ma swicth off...haka nan ta hakura ta kwanta tana tunanin yanda zasu kwashe dashi gobe...shi kuma Bobby tsabar 6acin rai ne ya hanashi mgn...sbd wulakanci shine zai kirata ta wani kirashi da sunan saurayinta sbd bata da hankali..haushin kanshi ka yaji ya kamashi ga zafi da zuciyarshi ke mishi..shidai ya hakura da yarinyar nan kawai inyaso idanma mutuwa zaiyi sbd ya mutu amma bi’iznillah bazai sake nuna yanada wani feeling gameda itaba tunda ita batasan mutuncin hakan ba...wnn daren ma kamar sauran saida dare ya tsala sosai snn ya samu bacci. Washegari Thursday ranan shiga college dinshi ne amma yana sane yace bazaije ba sbd bama yaso ya ganta ballantana ya karya alkawarin daya daukan ma kanshi...ko a gida bai zauna ba ya shirya ya tafi hospital sbd yasan idan Mummy ta ganshi a gida zata tashi hankalinta ne and shima kanshi yana bukatar ya fita ko dan wani wurin ne yaje at least zai shaki fresh air. Lamido na shigowa makaranta ta nufi office dinshi kaman yanda yace kullum taje ta gaidashi da safe and ita kanta tanada bukatar yin mgn dashi akn abunda ya faru jiya..ga mamakinta bata sameshi office dinba haka ta koma class tana sake trying numbershi yana shiga amma bai dauka ba...suna fitowa break ta sake komawa office din nashi still baya nan kuma tanata kiran wayanshi har ta gaji bai dauka ba...hankalinta ya tashi sosai tasan yanxu kilan yace zai hadata da daddy...tasan dan abu karami ke 6ata mishi rai amma ita ai bada niyua tayi ba...ranar har suka bar school bata ganshi ba kuma bai dauki wayanta ba...hankalinta ya tashi fiyeda yanda take zato duk sai taji wani iri dan tunda suke bai ta6ayi mata haka ba...a ‘yan kwanakin nan da yake mata mutunchi ta fara fahimtan waye shi...sure tasan yanada fada amma kuma yanada kirki and yasan darajan mace...gaba daua jinta take wani iri addu’anta bai wuce Allah yasa kada ya hada da daddy ba. Washegari friday same thing happens shima har suka tashi Lamido na nemanshi bata ganshi ba wayanshi kuma tun yana kin dauka har ya fara rejecting call din...hankalinta yayi mugun tashi har hakan yaso bata mamaki dan bata taba tunanin zata damu haka ba...da dadewa tasan ta saba dashi amma batasan sabon yakai hakaba sai yanxu...koda yake bataso ya hadata da daddy ne shiyasa hankalinta yaki kwanciya...a takaice saida ta kwashi three days tana nemanshi bata samu ganinshi ba...ranan Sunday tana zaune dakinsu itca kadai saida ta bari Billy ta fita snn ta kira Nur a waya sbd tasan idan sukayi mgn a gabanta zatacigaba da cewa soyayya ne tsakaninta dashi ita kuma bata son haka..yana dauka tace"sir dama ina neman proprietor ne"..Nur yace"baki sameshi a waya ba?.."a hankali tace"baya dauka"..da mamaki Nur yace"ban gane baya dauka ba?.."tace"sir inata kira bai dauka..rejecting call dinma yakeyi"..Nur ya danyi shiru for some minutes before yayi adding"kinyi mishi laifi knn?.."a hankali tace"sir kawaifa kirana yayi bansan shi bane na zata baby ne shknn fa yaketa fushi dani har yanxu..kuma sir ni ina tsoron kar ya hadani da daddyna"..shiru Nur yayi yana saurarnta yana murmushi...addu’a yake Allah yasa itama ta damu dashi koda baikai rabin damuwar da yayi da itaba..saida ya gama smiling dinshi before yace"bani two minustes inyi mgn dashi"..a hankali tace"toh"snn ta kashe wayar...suna gama mgn Nur ya dannawa Bobby kira..ringing biyu ana uku ya daga da sallama...Nur yace"maza ina ka shigane kwana biyu?.."Bobby yace"wlh banjin dadi ne shiyasa kajini shiru..ya aiki".."Alhamdulillah kana gida ne?.."Nur ya tambayeshi kai tsaye shi kuma ya amsa da fadin"no ina hospital"...da sauri yace"ohk gani nan zuwa asibitin yanxu..bakada lafia ne naji muryanka somehow?.."ajiyar zuciya Bobby ya saki before saying"sai kazo din dai kawai"..Nur ya amsa da"ohk"..daga haka kowa ya ajiye waya..sake kiran Lamido Nur yayi tana dauka yace"munyi mgn dashi yace yana hospital yanxu haka..ko zaki shirya in kaiki?.."shiru tayi tana nazari for a while sai kuma a hankali tace"toh.."yace"ki shirya yanxu gani nan zuwa"..ta sake amsawa da"toh.."snn ta kashe wayar..mikewa tayi ta dora dogon hijab akan jessy da straight skirt dake jikinta..tazo fita daga dakin saiga Billy ta shigo ciki..kallonta takeyi from sama zuwa kasa tana ta6e baki tace"ina kuma aka nufa hakia indo?..fushin ya kare knn?.."wani irin harara Aysha ta watsa mata snn ta bangajeta ta fice daga dakin Billy ta bita da kallo baki bude tana cewa"anya kuwa Lamido batada aljanu?.." A hankali take tafiya har ta iso first gate na hostel din dan haka Nur na karasowa bai karasa ciki ba yayi picking dinta a nan suka wuce...suna hanya da yaga yanda tayi shiru ta zubama spot daya ido yace"duk Dr Bobby ya sanyaki a damuwa koh?.."da sauri ta daga kai tana cewa"eh mana..kumafa ni banga abun jin haushi a mgnr dana fada ba"..murmushi Nur yayi yana girgiza kai cikin ranshi yace"ai bazaki ganiba dama"..daga haka ba wanda ya sake mgn cikinsu har suka iso Freedom...yana gama parking duk suka bude mota suka fita zuwa cikin asibitin...saida sukazo daidai office dinshi taji wani irin faduwar gaba ya risketa..ko wane kalan masifa zai sauke mata oho?...Nur ne ya fara tura kofar ya shiga kafin itama tabi bayanshi...Bobby dake kwance kan sofa ya bude idanu a hankali ya saukesu kan Nur then back to Lamido dake tsaye bayanshi sai faman sunkuyar dakai take...da sauri ya mike zaune yana kallonta da kyau duk idanun nan a waje kaman yaga abun tsoro..yakai hannu yana murza idanuwan nashi wai ya tabbatar ba mafarki yake ba ba kuma gizo take mishi kmr yanda ta saba ba..ganin da gaske itam ce nan tsaye a gabanshi baisan sanda ya wani daure fuska yana kallonta ba...a hankali tayi kasa da idonta tanajin yanda tsatstareta da wnn idanun...kafin tayi mgn ya nuna mata kofa yace"out of my office"..da sauri ta dago tana kallonshi wnn karon shi ya kawar da nashi idon kafin ya sake fadin"i said ki fitarmin daga office"...kafin tayi mgn Nur yace"Haba Bobby"..k kallonshi baiyi ba ya sake nuna mata kofa ita kuma tayi tsaye taki tafia kawai sai ya dafe head dinshi da hannu bibbiyu yana sauke numfashi...ganin haka Nur ya dan matsa kusada ita murya can kasa yace"karki yadda kibar office din nan ba tareda kun daidaita dashi ba..idan yacigaba dayi maki masifa kawai kuka zakisa shknn kinyi maganinshi"..yana gama fadan haka ya juya ya bar office din..jin karar kofa ya sashi bude ido sbd yana tunanin itace ta fita amma sai yaga Nur ne...sake dawo da kallonshi yayi gareta murya can kasa yace"ba cewa nayi kibar min office ba?.."da sauri tace"sir dan Allah kayi hakuri"..girgiza mata kanshi yayi yace"kimin laifi ne kike bani hakuri?.."kwabe fuska tayi zatasa kuka tace"nifa bansan kaine ba Allah"..kallonta kawai yake ganin zata fara mishi kuka bayan ba abunda yayi mata..shi baisan dalilinda yasa ma Nur ya daukota ya kawo mashi ita har nan ba..ajiyar zuciya ya sauke gamida dauke kanshi daga gareta ya sake komawa ya kwanta kan sofa...ita kuma ganin yanda yaba banza ajiyarta sai ta daddage ta rushe da kuka kmr yanda Nur yace tayi..da dadewa tasan bayason kuka tasan kuma shine kadai abunda zatayi ya saurareta...sake runtse ido yayi jin yanda take mishi kuka ya dauki throw pillow ya danne face dinshi dashi wai ko zai denajin kukan nata amma a banza..da dane ya tabbata ko zata shekara tana kuka a gabanshi bazai dameshi ba amma yanxu wani irin rauni kukan nata ke haifar mashi..sai yaga kaman yayi mata wani abun alhalin kuma ba uwar da yayi mata..har cikin zuciyarshi yakejin kukan..kasa daurewa yayi ya mike zaune yana kallonta da idonshi da sukayi red yace mata"wani abun nayi maki da zaki sani a gaba kina kuka?.."cikin kuka tace"sir kaine fa kaki hakura"..yace"cewa nayi ban hakura ba?..ni bakiyimin laifin komai ba kawai kije I don’t want to see u"..haushi sosai mgnrshi ya bata dan haka ta juya a fusace zata bar office din garin sauri ta take hijab dinta dake jan kasa aikuwa ta tafi luu saura kiris ta fadi Bobby yayi hanzarin mikewa ya tareta a jikinshi...ta runste ido tana sauke numfashi dan yanda ta gama tsorata ta gama sadakarwa zata jita a kasa sai kuma taji ba haka ba...shi kam kallonta kawai yakeyi kaman an aikoshi...the more ya kalleta the more yake sake ganin asalin beauty dinta wanda da bai cika gani ba sam...zuciyarshi yaji tayi wani tattarewa ta dunkule waje daya sai wani irin harbawa take da mugun karfi...ya lumshe ido ya bude still yana kallon yanda har yanxu ta kasa bude idanunta baisan ya akayi ba kawai shidai yaji ya hadata da jikinshi..rungumeta yayi da kyau yana sauke numfashi a jere kaman wanda yayi race tareda lumshe ido yanajin wani irin mixed feeling tattare dashi...Lamido kuwa mutuwar tsaye tayi jin yanda ya cacimeta sbd tsabar tsorata kasa ko motsi tayi balle tayi kokarin kwatan kanta..Bobby kuwa is far gone sam bai ankara da abunda ya aikata ba saida yaji ta fara mutsu mutsu a jikinshi..sakinta yayi da sauri yakai hannu ya dafe head dinshi tareda fadawa kan sofa...sai sauke ajiyar zuciya yake kmr wanda yayi tsere..he just can’t believe what happened..he can’t believe he hugged her after all alqawuran daya daukan ma kanshi...runtse ido yayi yana salati dama abunda yske gudu knn shiyasa tun farko yace ta tafi amma taki tafiya...yasan idan yacigaba da ganinta abubuwanda yake 6oyewa suna iya kokarin tona mashi asiri and now see what happened..ya kasa controlling kanshi har yayi hugging nata wanda yakeda tabbacin mutuncinshi ja iya zubewa a idonta...Aysha kuwa shiru tayi ta kurawa spot daya ido kawai tana mamakin abunda yayi mata...gani take kodai aljanu sun shafeshi ko kuma yana fama da serious rashin lafia tunda ga alama nan ta gani yanda yake dafe da kanshi..kuma tasan yana cikin hankalinshi bazai aikata abunda ya aikata ba for she trust him..tasan yanda suke rigima dashi ko wani ya gani tareda ita so ta tabbata bazaiyi hugging dinta for his selfish interest ba..kilan yayi haka ne don ya taimaketa ko kuma sbd wani abu dake dawainiya sam bata kawo wai da gaske sonta yake ba...ganin har yanxu bai motsa ba ta karasa a hankali ta zauna kan one of kujerun office din tana dubanshi murya a hankali tace"sir ai ka hakura koh?.."a hankali ya bude ido yana kallonta..ta wani sake langabewa tace"nace fa bansan kaine ba"..gyada kai kawai yayi kafin ya safe maida eyes dinshi ya rufe..tace"kuma bazaka fadama daddy ba?.."nan ma kan ya daga mata without saying anything..shiru sukayi a office din shi yanajin kaman ya fallasa mata asirin zuciyarshi ita kuma tana tunanin wane irin ciwo ke damunshi da duk yabi ya canxashi haka?..mikewa tayi tana murmushi tace"sir zan tafi"...kai kawai ya sake daga mata ta juya ta fita shi kuma ya sake dafe kanshi yana cije lips dinshi...baisan garin ya yayi loosing control dinshi ba wlh..Allah dai yasa yarinyar nan batayi masa muguwar fahimta ba. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 33 Tana fita taga ba motan Nur a parking space dan haka ta kirashi a waya..yana dauka yace mata"Lamido kiyi hakuri wani abu ne ya tosomin yanxu nan aka kirani shiyasa na tafi..kiyi mgn da Dr Bobby nasan zai maidaki"..bata iya cewa komai ba har ya gama bayaninshi ya kashe wayar...kuyawa tayi a hankali ta koma office din nashi...ta tura kofar ta shiga kai a kasa..yana zaune yanda ta barshi ya dago idonshi da kyar yana dubanta yace"what?.."tace"provost ne yace mu tafi tare waishi ya tafi wani wuri"..bai iya cewa komai ba ya mike zuwa wani drawer ya dauki drugs dinshi ya 6alla snn yayi dispensing ruwa yasha maganin dashi...duk wnn abun da yake bai sake kallon inda take ba sbd baison ya sake aikata wani abun..yana gama sha ya dauki waya da keys dinshi yace mata"muje.."ba musu ta juya suka fita daga office din...yasa key ya rufe snn suka wuce parking lot...dirver na hangoshi yazo ya bude mishi kofa as usual yana karasowa ya shiga ita kuma Aysha ta bude front seat zata shiga da sauri yace mata"are u mad?..C’mon come back here"..batace kala ba ta maida kofan ta rufe snn ta bude nan kusa dashi ta shiga..shima driver ya shiga tareda tayar da motar suka fita asibitin...ko a hanya Bobby bai kallon inda take..haka nan yajishi duk a takure sbd kusancinda sukayi da juna..gaba daya bai yadda da kanshi bane a yanda yakeji din nan yasan tsaf zai iya sake aikata wani abun kwatankwacin na dazu shiyasa duk yaki ya saki jikinshi ya wani takure can karshe kaman ba motarshi ba...Aysha kuwa bata ma lura da abunda yakeba don duk a zatonta bashida lafia...shiru motar babu mai cewa komai banda sanyin ac ba abunda ke tashi sai Lamido dake dan motsawa time to time...har suka isa FCNM Hostel ba wanda yace qala..driver na gama parking ya bude motar ya fita ya rage su biyu kadai a ciki...a hankali ta kama handle zata bude kofar sai kuma ta juya tana kallonshi nan kuma taci karo da idonshi a kanta kusan a tare kowa ya janye nashi idon...dan murmushi ta saki tana dubanshi tace"sir nagode..sai anjima"..kafin ta bude motar taji shima a hankali yace"am sorry"..sake juyowa tayi tana kallonshi still da murmushi sai kuma ta girgiza kai tana cewa"bakayi laifin komai ba sir..nasan u are a good person and bakayi kama da irin wnn mutanen ba..so u don’t have to apologize"..wani ajiyar zuciya da bai shirya ba ya sauke har dan wani smile yayi sbd samun relieve najin abunda tace...at least dai yasan batayi mashi kallon mutumin banza ba..shi sai yaga yau tayi wani irin nustuwa na musamman kaman dai ba Lamido da kullum suke rigima da ita kan rashinji ba...baisan ko sbd ya fara sonta ne kuma ya fara ganin nutsuwarta ba amma dai yau ta burgeshi fiyeda tunaninshi...bude motar tayi ta fita kafin ta rufe ta sake sunkuyowa tana dubanshi har yanxu da wnn murmushin kan fuskanta tace"thank u so much sir..sai anjima"..kai kawai ya iya dagawa yana kallon yanda murmushin keyi mata kyau kaman wani soko..rufe mishi kofar tayi snn ta juya ta tafi shi kuma hadda su sauke glass yana sake binta a kallo yanajin wani abu kaman maganadisu nason janshi gareta dan haka ya sauke glass din tareda maida kanshi yayi relaxing akan kujera yana cigaba da tunaninta...gaba daya ta mamaye jini da tsokarshi ta yanda bai iya cikakken mintuna 10 ba tareda yayi tunaninta ba...ta 6ata mishi rai jiya amma yau ta faranta mishi matuka..kawai sai yaji dadin yanda yaga ta nutsu da kuka yanda batayi misunderstanding dinshi ba..sai kuma yanda ta damu har saida ta nemo inda yake ta bashi hakuri..she really is amazing and ya tabbata if abubuwa zasu cigaba da kasamcewa haka watarana yana iya samun soyayyarta..tunanin hakan kadai ya sake saukar mashi da wani farin ciki...duk wnn kunci da 6acin ran da yake ciki sai yaji sunyi disappearing..a haka driver ya shigo ya sake tayar da motar suka dauki hanyan gida. Da fara’a ya shigo cikin gidan saidai mutanen daya gani parlon zaune tareda su Mummy yasa yaji new 6acin rai na neman taso mishi...suna jin shigowarshi suma gaba daya suka maida hankali kanshi kaman dai jiran zuwanshi suke...dauke kanshi yayi ba tareda yace qala ba ya kama hanyan flat dinshi Mummy da aunty sumy suka hada ido kafin Mummy ta mike ta dubi mahaifiyar Isma’il grandma din su Miemie knn tace mata"ina zuwa bari inyi mgn dashi yanxun nan"..daga mata kai matar tayi duk jikinta yayi sanyi..ita gani take kaman shi zai hana su samu yafiyar da sukazo nema wurinsu..dukda already sun riga sun gama mgn har Mummy tace itakam bata rikesu ba dama ta yafe musu itama aunty sumy jin Mummy tace haka itama sai bataja zancen da nisa ba tace ta yafe..su Miemie kuwa ya rage nasu su yafe ko karsu yafe amma sunsan komai dadewa watarana zasu yafe musu tunda duk tsiya dai ahalinsu ne...Mummy na shiga dakin ta sameshi zaune gefen gado ya hada uban tagumi kai kace uwa da ubanshi ne suka mutu..yana ganinta kaman jiran shigowan nata yake yace"Mummy why dan Allah?..why?.."kallonshi kawai Mummy keyi dama tasan za’ayi haka..tun kafin suzo dama tasan rana irin wnn zaizo and gashi yayi reacting exactly yanda take tunanin zaiyi...tasan yanxu ko auren sumayya za’a maida daga wurinshi za’a fara samun matsala sbd wnn dan banzan rikon nashi da bai iya mance abu komai tsahon lokacin daya dauka...karasawa tayi kusa dashi ta zauna tana dan murmushi tace"yau an hadu da Lamido knn?.."tana rufe baki yace"Mummy ba mgnr Lamido ake ba meya kawo mutanen can cikin gidan nan dan Allah?..me sukazoyi mana?.."ajiyar zuciya Mummy ta sauke tareda kamo hannunshi still murya kasa kasa tace"yafiya sukazo nema Bobby..sunaso mu yafe musu dukkan laifukansu na baya kuma nidai na yafe musu..itama Sumayyan ta yafe sbd haka dan Allah kar kace zakayi kokarin causing scene a wurin nan dan Allah"..kallonta kawai yake yanaji yanda 6acin ranshi ke ninkuwa ninkin ba ninkin...kamar zaisa kuka yace"yanxu sbd Allah Mummy duk abubuwanda suka aikata har kun manta knn?..kin manta wulakancin da sukayi mata kawai sbd ba ita sukaso ya aura ba shine yanxu sbd sunaso ya maida ita zasu wani kwaso legs dinsu suzo mana gida..Mummy yanxu ko don sbd su Miemie bazaku duba wnn al’amarin ba..sukayi abandoning dinsu for almost seven years shine yanxu zasu wanizi suce ku yafe musu ku kuma ku yadda dasu?.."yana rufe baki Mummy tace"kaine ya kamata ka hakura kodon sbd su Miemie din..duk yanda muka kai da rashin sonsu fa bamu isa mu rabasu da yaran nan tunda jininsu..snn kuma kowa ya kallesu yasan sunyi regretting abunda sukayi so don me bazamu yafe musu ba?..meyasa bazamu yafe musu ba tunda sukazo har gida neman a yafe musun..kada ka manta ubangiji da kanshi yana son masu yafiya..idan ka kasance mai yafiya sai Allah kaima ya yafe maka..baka tunanin ko don wnn ya kamata a yafe musu?.."shiru kawai Bobby yayi yana sauraronta amma shidai harga Allah baiga dalilinda zaisa kawai daga zuwansu su wani ce sun yafe musu ba..juyawa gareta sai yaga ta daure fuskanta tsaf dan haka yayi kokari ya sassauta nashi tareda yin kasa da nashi muryan kafin yace"Allah ya baki hakuri Mummy..ba haka nake nufi ba"..sassauta nata muryan itama tayi before tace"kuma anjima inason mgn dakai"..a hankali ya amsa mata da"toh"..snn Mummy ta mike ta bar masa dakin shi kuma ya rage kayan jikinshi ya fada bathroom yana sake tunawa da Lamido da duk abubuwanda suka shiga tsakaninsu yau..ya lumshe ido yana sakin wani murmushi daya tuna yanda yayi hugging dinta..he felt kaman ya rike ‘yar jaririya sbd taushin jikinta..ga wani qamshi da shidai bai ta6ajin irinshi ba sai daxu a jikinta..baisan lokacinda daria ya su6uce mishi ba daya tuna yanda ta gwalo idonta a lokacin..yasan she was shocked amma da yake tanada positive mind sai batayi thinking negative a kanshi ba sai ma yabonshi da tayi..shi tunda yake bai ta6a sanin haka mutum kejin dadi idan an yabeshi ba sai yau din nan kuma a kanta..lokacin data yabeshi sai yaji kaman duk dunia ko kowa bazai yabeshi ba nata kadai ya isheshi...nata kadai ya isa yasashi farin ciki...har ya gama wanka ya fito bai dena tunaninta yana sakin murmushi time to time ba...koda ya gama shiryawa sai yayi kwanciyarshi nan cikin dakin yaki fita sbd yasan kilan wadan nan mutanen suna nan basu tafi ba shi kuma baison haduwa dasu dan haka gwara yayi kwanciyarshi a daki...wayanshi ya dauki ya shiga gallery dinshi hoping inama zaiga pictures dinta amma babu..bayada pictures dinta ko daya amma yanada bukatar ya samu ko guda daya ne sbd irin wnn lokacin..kunna data dinshi yayi ya shiga whatsApp wai ko zai ganta online amma she’s offline...ya duba status dinta nan ma batayi updating komai ba sai wani short video na wasan PSG da Manchester..dan ta6e baki yayi cikin ranshi yana ayyana dole ma ya rabata da kallon ball din nan wlh..shi bazai dauki ta wani dinga son ‘yan ball tana supporting dinsu ba..hakan 6ata mishi rai yakeyi sosai...kashe data dinshi yayi ya ajiye wayar ganin har lokaci bata online...yana ajiyewa kuma kiran Nur ya shigo wayan dan haka yayi picking yasa a speaker yana sakin wani murmushi yace"Dr Nuruddeen Ugo"..daga daya 6angaren Nur ya wara idanu yana fadin"ah lallai abu ya tafi yanda ya kamata i don’t even have to ask"...Bobby yace"of course..ka kayuta sosai daka kawomin ita thank u"..da sauri Nur yace"always welcomed angon Lamido..yanxu a bani labari in detail inji abunda ya faru"..murmushi Bobby ya kara saki yana shafa beard dinshi hadda su lumshe ido yace"ka bari kawai Nur..sai yanxu na fara yadda da mgnrka..tanada hankali sosai"..Nur ya fashe da dariya before yace"bana fada maka ba?..tanada hankali wlh kawai idan ba zama kayi da itaba bazaka fahimci hakan ba"..Bobby na gyada kai zai sake wani mgn Ilham ta shigo dakin tace mishi Mummy na nemanshi..sallama yayi da Nur snn ya janyota yana kallon yanda har yanxu bata gama maida jikinta sbd rashin lafiyan da tayi ba yace"mutanen nan sun tafi ko suna nan?.."ilham tace sun tafi dan haka ya mike rikeda hannunta suka fita parlor...Mummy kadai ya samu a parlon ya karasa ya zauna yana kokarin zaunar da Ilham kan laps dinshi Mummy tace"kyaleta taje wurin su Miemie mgn zamuyi ai"..ba musu ya saketa fa nufi parlon aunty...Mummy ta maida hankalinta gaba daya gareshi fuskanta ba yabo ba fallasa tace"ya mgnr zuwa duba Waziri?.."wani irin damm yaji gabanshi ya fadi amma bai bari ta lura ba yace"za..zamu..je mana Mummy..ba kince yana india ba?.."yana rufe baki tace"an dawo dashi jiya..yana nan a Abuja kuma wnn satin nakeso kuje ku duboshi"..Bobby ya hadiye wani irin yawu kafin ya tattaro abunda zai fada mata yace"kenan..Gombe zamuje..mu dubashi?.."kallonshi Mummy tayi rai a dan 6ace tace"bakaji nace yana Abuja bane?.."da sauri yace"yi hakuri Mummy banji ba..amma why not a bari next week sai muje"..tun kafin ya rufe baki Mummy tace"ban yadda ba wnn satin nakeso kuje ku dubashi..idan kuma kanaso ka nunama dunia ban isa dakai bane Bismillah"..kallonta kawai Bobby yake yana mamakin sudden change din nan nata..Mummy ba mace ce mai fada ba sam..zaiyi wahala kaga tana fada musamman ma shi amma yanxu gashi ta daure fuskanta tana mishi fadan akan mutanenda bai daukesu a bakin komai ba..mutanen da basu ta6a kaunarsu tsakani da Allah ba tun mahaifinsu ma yanada rai...yasan duk wnn abun tanayi ne sbd kar yayi mata gaddama kaman yanda ya sabayi a baya amma shidai har yanxu baiji zai iya zuwa wani duba waziri ba..Wazirin da shi kanshi ba kaunarsu yake ba...ganin yanda yayi shiru ya wani kafeta da ido tace"bazaka jeba knn?."da sauri yace"aah ba haka bane Mummy..zanje..amma in..."bata bari ya karasa ba ta dakatar dashi da fadin"kaje ka fara shiru this coming weekend zakuje gaba dayanku ku duboshi"..kallonta yake yace"gaba dayanmu kuma?..wai kina nufin hadda su Miemie?.."kai tsaye tace"ko su ba jininshi bane da baza suje dubashi ba?.."a hankali yace"amma Mummy su meye hadinsu da Waziri da zasuje duboshi"..kallonshi Mummy keyi cikeda takaici tace"kaidai idan bakayi wasa ba sai Allah ya kamaka da laifin yanke zumunta..su Miemien zakace meye hadinsu dashi sbd bakada hankali?.."shiru kawai yayi yana kawar da kai shidai harga Allah wnn abun da Mummy keson tursasa su suyi bai gamsheshi ba..kilan ma suna zuwa Wazirin yasa koresu yace bayaso ya sake ganinsu har abada...ita kuwa Mummy ganin idan tacigaba da zama tana mgn dashi 6ata mata rai kawai zaiyi sai ta mike bayan ta gama mgnrta ta wuce zuwa 6angarenta...sbd iskanci zai wani ce a bari ba yanxu ba sai azumi ya shigo knn yakeso suje dubiyan nashi ko sai bayan sallah?..ta rasa wane irin taurin kaine da Bobby da ko ita data haifeshi watarana bya tankwaruwa ta dadi a wajenta?...yana ganin ta shige ciki shima ya mike zuwa flat din aunty sumy..he need to talk to her about this ko zata iya lalla6a musu Mummy ta bari sai bayan sallah tunda yanxu dab ake da fara azumi...yana shiga kai tsaye bedroom dinta yaje ya kwankwasa kofa ta bashi izini snn ya bude kofar ya shiga...a zaune ya sameta tsakiyar gado tana aiki da system dinta..ya isa ciki ya zauna kusada ita yana dubanta a hankali yace"mgn nakesonyi daks aunty sumy"..ba tareda ta dago ba tace"to ina sauraronka Uncle Bobby"..dan 6ata rai yayi yana kallon kaman zaisa kuka yace"aunty plss be serious mana..please!.."ajiye system din tayi tana dubanshi da murmushi tace"to yi hakuri..ina jinka"..gyara zama yayi kafin yace"Mummy ce take mgnr zuwa dubiyan Waziri"..ajiyan zuciya ta saki kafin tace"kaima ta fada maka knn?.."yace"ta fadamin..yanxu ya kike ganin zamuyi?..nidai bana son zuwa inda suke kwata kwata..bana son ganinsu"..kallonshi aunty sumy keyi kafin ta sake sauke wani ajiyan zuciya tana cewa"na fuskanci wnn karon Mummy da gaske take kan mgnr nan..idan mukace zamuyi kokarin kaucewa umarninta muna iya samun matsala da ita"..shiru Bobby yayi yana nazari shi kanshi yaga alaman hakan zai faru amma ya zasuyi?..yace"yanxu knn kina nufin bamuda wani option dole sai munje?.."gyada kai tana cewa"gaskia dai kamar bamuda wani option din..kasan yanda Mummy take da damuwa Bobby idan bamuyi abunda takeso ba muna iya sawa ta samu wani matsalan kuma kasan yanda bp dinta yake..baason tana shiga damuwa da yawa"...shiru ya sakeyi yana nazari..tabbas mgnr data fada gaskia ne...yasan yanda ta kwallafa rai kan sai sunje din nan idan sukace zasuki zuwa tsaf zata iya sama kanta damuwa har jinin nata yazo yana hawa shi kuma abunda baiso knn har abada...ajiyar zuciya ya sauke tareda runtse ido yasan wnn karon kam bashida wani hanyan tsira..duk wani kauce kauce bazaiyi tasiri akan Mummy ba wnn karon tunda har tasama ranta sai sunje dole...haka nan zai hakura yaje domin mahaifiyarshi amma wlh ba donshi wazirin ko don wani daga cikin ‘ya’yanshi ba...aunty sumy ta dafa hannunshi cikin sigan lallashi tace"haka nan zamu hakura muje wnn karon..koba komai zamu samu ladan da su bazasu ta6a samuba sbd kin nemanmu da sukayi na tsahon shekaru"..gyada kai kawai ya iyayi tareda mikewa ya fita daga dakin...tabbas zasuje amma ba don wani daga cikinsu ba sai domin Mummy..sbd gudun 6acin ranta daka iya haifar mata da matsala amma ba sbd su ba. Bayan kwana biyar... Da sallama ya shigo parlon Mummy ya sameta zaune tana answering call...karasawa ciki yayi ya zauna nan kusada ita saida ta gama wayan ya wani kwa6e fuska yana dubanta yace"Mummy am back..Mummy yunwa nakeji wlh ni yanxu duk kin deddena sona"...dan murmushi ta saki tana kallonshi..cikin ‘yan kwanakin nan ta fahimci yana cikin farin ciki..batasan ko sun daidata da yarinyar ba amma she’s happy seeing him like this...sake kwa6e fuska yayi yace"kuma Mummy ko ki tambayeni yanda mukayi da Lamido"..murmushi ta saki tana kama hannunshi tace"ai nasan tunda na ganka cikin farin ciki these days kilan kun gama daidaitawa da ita"..tana rufe baki yace"a ina?..we are still patching things up dai..kawai inaso tasoni koda baikai wanda nake mata ba"...sake damke hannunshi Mummy tayi tace"zata soka inshaAllah..just continue being a good guy"...murmushi ya saki mai kyau yana shafa lallausan gashin kanshi yace"Allahumma Ameen Mummy..I can’t wait to see that"...dan rankwashi Mummy ta kai mashi a kai tana cewa"rashin kunya kou?.."dafe kan yayi yana dan saki kara yace"ouchh..Mummy da zafi fa"..dungure mishi kai tayi tana hararanshi tace"Comot for this place"..murmushi ya kara saki ya wani makale mata kafada...kallonshi kawai tacigaba dayi full of excitement..seeing him like this really gladdens her heart and she prays Allah yasa ya dore har karshen rayuwarshi...Allah ya mallaka mashi yarinyar nan idan har ta kasance alkhairi a gareshi...ganin yanda taketa kallonshi sai ya dan 6ata fuska yace"Mummy wnn kallon fa?.."murmushinta ta fadada tana fadin"am just suprised and impressed..My Bobby is in love i can’t believe this"..murmushi shima ga kara saki yana cigaba da shafa gashin kanshi kaman zaisa kuka yace"Mummy manaaaaa..am shy plss"..daria ta saki sosai kafin tace"ba wani u are shy bayan har rowarta kake mana..tun yaushe nace maka ka sake kawo mana ita mu gaisa amma baka kawota ba"...yana cigaba da smiling yace"zan kawota Mummy inshaAllah..amma dan Allah idan tazo kar kice mata wani abun plss"..murmushi take tace"bakaso ta sani?.."gyada mata kai yayi tareda cewa"not now"..Mummy tace"dont worry she won’t know anything..yanxun dai take these"..ta zaro wasu papers dake bayanta ta mika mashi...amsa yayi yana dubanta yace"Mummy meye su?.."a takaice tace"ur flight tickets"..kallonta yayi da sauri cikin mamakin abunda tace..kafin ma ya tambayi na meye ta sake cewa"to Abuja"..kallonta kawai yake full of surprise..a hankali yace"Mummy badai ke da kanki kikaje airport siyo mana tickets ba?.."harara ta watsa mishi tace"it’s non of ur business..nasan ba son zuwa kuke ba ai shiyasa nayi maku haka..sai kuje ku fara shiri flight dinku is tomorrow by 4"..kallonta kawai yake kafin ya koma kallon tickets din...na gaba dayansu ne including Miemie da Ilham...sbd tsabar mamaki kasa ce mata komai yayi..shi wlh da yaji shiru ta dena mgnr ma yayi tunanin mantawa tayi ashe tana sane ido kawai ta zuba musu...numfashi ya sauke yana cigaba da duban tickets din shidai Allah ya sani ba son zuwa Abujan nan yake ba..sam baison tafiyan shi baima san ta ina zasu fara ba idan sukayi ido da ido da Wazirin shin gaisuwa za’a fara ko kuwa kallon kallo zasuyi a tsakaninsu...itadai Mummy mikewa tayi ta shiga bedroom dinta shima yaja jiki a hankali ya fita daga parlon nata..knn dai gobe i yanxu suna can Abuja tareda Waziri..what the heck shi baisan ma da wane ido zasu kallesu ba wlh..sam baisan ya haduwan nasu zai kasance ba. Washegari ko fita baiyi ba dan Mummy hanawa tayi..haka ta tsaresu gaba daya kowa ya dauki kayanshi set daya tunda gobe zasu dawo...Bobby na fitowa daga Flat dinshi ta kalleshi from head to toe kafin ta mike zuwa insa yake tana cewa"koma kasa manyan kaya"...kwabe fuska yayi yace"manyan kaya kuma Mummy?.."tace"yes haka nace..hanga dalilinda zaisa ka tafi wajen grandpa dinka haka ba"...kallonta Bobby yake kaman zaisa kuka yace"Haba Mummy kaman wanda zaije wajen surkai?.."kama hannunshi tayi suka koma Flat din nashi tana fadin"komai abunka bazaka tafi a hakaba wlh..kuma idan ma kayan daka dauka na gobe irin wnn ne then ka sake wasu"...kasa cewa komai yayi suna shiga bedroom kawai ya shiga closet dinshi ya sako wani coffee yadi mai taushi ba tareda yasa hula ba ya fito yace"Mummy amma dan girman Allah ba saina sa hula ba koh?.."kallonshi tayi taga yanda yayi kyau saita saki smile kafin tace"da kasan yanda manyan kaya ke maka kyau da ka dena saka wnn suits din wlh..now wuce muje time na kurewa"..ba yanda ya iya haka ya wuce gaba Mummy tabiyoshi a baya...a central parlor suka tadda sauran suma gaba daya sun fito kowa ya gama shiryawa...haka ta hada kansu suka fita zatayi musu rakiya airport..aunty sumy da Mummy da kuma Miemie suna motan Mummy da driver ke tukawa..shi kuma Bobby yana tareda Ilham da Sab shima cikin nashi motan...duk ranshi a 6ace yake sbd tafiyar nan nunawa ne kawai baiyi sbd Mummy...bayan sun isa airport duk dukayi sallama da ita har zasu wuce Bobby ya sake dawowa inda take yana dubanta kaman wanda zaisa kuka yace"yanxu Mummy ke kadaifa zamu tafi mu bari a gidan..dan Allah ni in dawo su su tafi sbd kar a barki ke kadai"..girgiza kai Mummy tayi tana jan cheeks dinshi tace"nafa fada maka ba abunda zai faru ai akwai masu aiki a gidan"...turo baki yayi yace"nidai dukda haka u take care of yourself"..wnn karon rungumeshi tayi gamida manna mishi kiss a forehead dinshi tace"zan kula inshaAllah..Allah ya kaimin ku lafia ya dawo daku lafia"..a hankali ya amsa da Ameen..da sauri Sab ya matso kusa dasu yana cewa"Mummy nima bakiyi hugging dina ba"..bude mishi hannu Mummy tayi yace"come here dan autana"..da gudunshi kuwa ya fada jikinta kafin ta maida hannu ta rungumeshi snn ta dagoshi shima ta manna mishi kiss a goshinshi...daga nan kuma sai Miemie da Ilham suma duk suka dawo tayi musu aunty sumy dai ba tsaye tana kallonsu...Ilham ce ta kalli mamanta snn ta kalli Mummy tace"Mummy to saura aunty"..dungure mata kai Mummy tayi tace"wa yake ta wani aunty...auntyn da ta girma"..daria gaba daya suka saka nan kuma aka fara announcing passengers su zama ready jirgi ya kusa tashi..a gurguje suka sake sallama snn suka wuce itama Mummy ta shiga motanta driver yaja suka koma gida. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 34 Karfe biyar da wani abu jirginsu ya sauka Nanmdi Azikiwe International Airport Abuja...wani Friend dinshi mai suna Dr Fariq ne yazo ya daukesu daga airport din zuwa Freedom Medical College inda ya ware ma kanshi apartment guda sbd irin wnn lokacin...apartment din na dauke da babban parlor guda daya sai three bedrooms inda shi ya dauki daya Sab ya dauki daya su aunty sumy ma suka dauki daya...gaba dayansu ba wani mai cikakken walwala cikinsu kowa yake kawai yakeyi amma ta ciki na ciki...tunani da kuma zullumin yanda haduwarsu da ‘yan uwan mahaifinsu zai kasance bayan kusan shekaru shidda suke...aunty sumy dai addu’a take Allah yasa karshen komai ke yazo while shi kuma Bobby jikinshi ke bashi ko sunje dinma Waziri ba accepting nasu zaiyi ba har yanxu..kawai ya riga ya sawa kanshi tunda baiyi kokarin sawa a nemosu har tsahon wnn lokacin kilan ba baya sonsu ne..ko kuma bai shirya kar6ansu a matsayin jikokinshi ba...Dr Fariq ne yayo musu takeaway na abinci ya kawo musu dukda basa tareda yunwa...Mummy dake can gida hankalinta gaba daya yana kansu ta kira Bobby tana tambayan ya suka sauka...yace sun sauka lafia sai sunyi sallahn magrib zasuje can asibitin da wazirin yake..dadi taji sosai tareda sa musu albarka..har tausayi yaji ta bashi sbd yanda take mgn..ya tabbata ita kanta tana cikin zullum ko waziri basan amince dasu ba...saida sukayi sallahn magrib kaman yanda yace snn gaba daya suka fito suka nufi asibitinda waziri yake cikin motan Dr Fariq da Bobby ya tuka da kanshi...koda suka shigo cikin asibitin saida gaban kowa ya fadi including Bobby da baisan dalilin faduwar gaban ba...bayan sun fito daga mota suka nufi cikin asibitin da yake nan kaman ba dare ba sbd hasken dake ta ko ina...daida suka tambayi wani sub staff room 105 yayi directing dinsu har zuwa can...a kofar dakin suka tsaya suna kallon kallo an rasa wanda zai fara karfin halin shiga a cikinsu..aunty sumy ce tayi murmushin yake tareda tura kofar a hankali ta shiga da sallama suma duk sai sukabi bayanta...yana kwance kan gado idanunshi a rufe da alama bacci yakeyi..sai wani dan matashi dake zaune kan kujera daga dam gefenshi...kallon kallo aka shigayi tsakaninsu da matashin shi yana musu kallon kamar ya sansu amma ya kasa tuna a ina suma suna mishi kallon saidai ya kasance jika a wajen waziri domin kaf yayanshi sun sansu amd bashida karamin yaro kamarshi...wuri ya nuna musu suka zauna yana kokarin dora murmushi kan fuskanshi yace"sannunku da zuwa"..aunty sumy ta amsa da"yauwa sannu..ya mai jiki?.."yace"Alhamdulillah ya samu sauki"..gyada kai kawai tayi kafin tace"Allah ya kara sauki"..daga nan kuma sai dakin yayi shiru ba wanda ya sake mgn cikinsu...a hankali Bobby ya daga ido yana kallon tsohon da a kallon farko za’a gane jininshi ne sbd kamanninshi daya dauko..mahaifinsu na kama da waziri sosai shima kuma Bobbyn sai ya dauko mahaifinshi...kallonshi kawai yake yana tuna duk abubuwanda suka faru a baya sai yaji ranshi na 6aci..da sauri ya dauke kanshi tareda mikewa tsaye da hannayenshi a aljihu yace"i think we should leave tunda bacci yakeyi da safe sai mu dawo"..babu wanda yayi masa musu cikinsu duk suka mike da nufin su fita sai kawai sukaji am turo kafar dakin wata mata ta shigo sanyeda katon hijab da glass a idanunta...tana dora idanu a kansu ta saki ledan dake hannunta tana zare idanu sosai a kansu bakinta yana motsi alaman she wants to say something...da sauri ta karasa inda suke ta shiga nunasu da finger dinta daya bayan daya har yanxu bakinta bai bar motswa ba amma ko kalma daya yaki fita daga bakin...ta tsayar da idanunta kan Bobby da shima yayi kasake yana kallonta kawai saita rungumeshi hawaye na saukowa fuskanta tace"Bobby is this realy you?..anya ba mafarki nake ba?.."hannunshi yakai shima ya zagayeta dasu snn a hankali yace mata"you are not dreaming"..dagowa tayi tana kallonshi har yanxu bata bar hawaye ba..takai hannayenta tayi cupping fuskanshi dasu tana cewa"my son..where have u been?..ina kuka shiga kuka 6oye nayita wahalar nemanku ban sameku ba?.."kafin yace wani abu ta sakeshi tareda matsawa inda Sabeer shima tayi hugging nashi tightly tana cewa"Sabeer..Sab kaine ka girma haka?..kaine ka zama saurayi haka?..zaka iya tuna ni?.."duk a lokaci daya ta jero mai wadan nan tambayoyin sbd tsabar shock data shiga na ganinsu..bata ta6a tsammanin ganinsu a nan ba..tayi wahalar nemansu na tsahon shekaru amma da yake ita mace ce kuma ba mazauniyar kano ba sai ta kasa samunsu har daga baya ta hakura...shima ta dagoshi tana cupping fuskanshi still tana zubda hawaye tace"baka ganeni ba koh?.."a hankali Sab dake hawaye shima yace"na ganeki"..tace"then wacece ni?.."da sauri yace"Our only aunt...Aunty Munubiya"..yana karasawa ta sake rungumeshi tana fashewa da kuka...su aunty sumy ba gefe suma suna nasu kukan dan hatta Bobby dakeda taurin zuciya yau saida yaji kaman ya zubar da hawayen shima sbd maganganun da take...bayan ta saki Sab saita isa ga aunty sumy...kallon juna suka shigayi kowacce hawaye na tsere a fuskarta ko pump albarka...a tare suka wani rungume juna kowacce tana sakin wani irin kuka mai tsuma zuciya...saida suka dauki lokaci mai tsaho haka kafin su sake dagowa suna kallon juna..aunty Munubiya ta saki murmushi da wet face dinta tana dubansu Miemie tace"mu grand kids...haka kuka girma kuma?.."kallonta kawai suke ba wanda yace uffan...hannu ta bude musu tace"come to me kuni?.."ai tun bata rufe baki ba suka karaso da gudu suma suka fada jikinta...shidai wanda ke jinyar Waziri yayi kasake yana kallonsu kaman ya samu movie...hayaniyar da sukeyi ya tada Waziri kawai sai jin tarinshi sukayi..da sauri duk suka karasa inda yake..shi kuma idanunshi na kan Bobby ya shiga kokarin nunashi da hannunshi amma ya kasa...Aunty Munu ta karasa gareshi tana kama hannun nashi tace"Baffa sune..iyalan Attahir dinka ne suka dawo gareka"...har yanxu idanunshi na kan Bobby sai kokarin mgn yakeyi amma ya kasa..a hankali ya dawo da kallonshi ga aunty sumy da Sab kawai sai wani tari ya sake turnukeshi har numfashinshi nayi kaman zai dauke...Bobby da yaga haka baisan lokacinda ya karasa kusa dashi da sauri ta kama hannunshi ba...har yanxu kallonshi wazir yake ya kasa dena kokarin yin mgn dukda breathe dinshi da yake kaman zai dauke..da sauri aunty Munubiya ta fita sai gata ta daw tareda doctor...taimakon gaggawa ya shiga bashi har yanxun hannunshi na rikeda na Bobby daya kasa sakewa...doctor ya samu ya daidaita breathe dinshi snn ya mishi alluran bacci sbd yaga idan ba haka akayi masa ba bazai ta6a dena yunkurin mgn ba and yana bukatar hutu dan haka ya juya garesu yace"you all shoulf go outside plss..he needs to rest bansan ya akayi ma aka barku kukazo har kuka cika dakin ba haka"...ba wanda ya kulashi har ya juya ya fita..suma hada kansu sukayi gaba daya sukayi waje don ya samu enough rest kaman gabda doctor ya fada...suna fita aunty Munubiya tace"amma dai zaku jira har lokacin da zai tashi koh?.."Bobby yace"no zamu dawo safe..yanxu hutu yake bukata"..gyada kai tayi tana kokarin dakatar da hawayen idonta tace"ya kamata mu zauna muyi mgn sosai..a ina kuka sauka?.."aunty sumy tace"Gwagwalada"..zaro wayanta tayi ta mika mata tace"sakamin numberki da safe zanzo inda kuke muyi mgn"..ba musu aunty sumy ta amsa wayan ta saka mata digits dinta snn ta mika mata tayi saving..ta sake mikawa Bobby shima tace ya saka mata nata dan haka ya saka still ta karba tayi saving snn tayi musu rakiya har bakin motarsu tareda alqawin zatazo gidansu gobe da safe su tattauna kafin suzo asibitin...haka suka tafi jikin kowa a sanyaye...gaba daya wani irin feeling sukeji tattare dasu...Aunty Munubiya only sis din mahaifinsu ce..ita kadai ce sis dinshi da suke uwa daya uba daya sauran duk uba kadai suka hada...ko a da can sunsan Aunty Munu bata daya daga cikin wanda suka tsani Mummy dan ko itama Mummyn tana fada...sai yanxu Bobby yaji rashin dacewar abunda yayi at least ita ya kamata su nemeta tunda yasan mai kaunarsu ce kuma bai zama lallai ta iya binciko inda suke ba tunda ita mace ce dole sawa zatayi a bincika mata...for the very first time yaji kaman bai kyauta ba abunda yayi..yaji gaba daya bai kamata ita su kasa nemanta ba duba da kasancewarta qanwar babansu...sai yaji guilty conscience ya rufeshi..tabbas bai kyauta ba abunda yayi mata domin daga yanayin yanda tayita kuka daga ganinsu yasan ba karamin missing nasu tayi ba..kilan ma tayita faman neman inda suke bata gansu ba...har suka karasa gida bai bar tunane tunanen nan ba...suma gaba daya sauran kowa da tunaninda yake dan haka suna karasawa gida kowa dakinshi ya kama yana sake tuntuntuni. Washegari karfe bakwai ta kira Bobby tace mishi gata nan zuwa gidan nasu..da kanshi ya fita bakin gate ya shigo dasu mota guda itama tayo itada yaranta...a parlor suka zauna gaba dayansu kafin ta shiga kallonsu one by one idonta na cikowa da hawaye tace"why plss?..idan kun kauracewa kowa sbd laifinda akai maku ni me nayi?..meyasa bakuyi tunanin halinda zan shiga ba"..da sauri Bobby yace"Aunty kiyi hakuri dan Allah..it was all my faul..nine na yanke duk wani alaqa daku kuma na hana kowa ya nemeku sbd ciwon abubuwanda akayi mana..nasan bai kamata na hada dake ba amma ina neman yafiyarki on behalf of all of us kiyi hakuri please!.."ya karasa mgn yana hade hannayenshi wuri daya...dan murmushi ta saki da wet face dinta kafin ta yafitoshi da hannunta alaman yazo..ba musu ya taso daga inda yake ya dawo kusada ita..yana zama ta daddage ta rankwashi kanshi tana fadin"this is ur punishment"..dafe kan yayi da sauri yana murmushin jin dadi..at least yasan yanxu ta yafe mishi...aunty sumy ma murmushin takeyi da hawayenta...itama Auntyn Munu bata dena hawayen ba ta sake fadin"ina Mummy?.."Sab ne ya amsada"tana gida"..kallonshi take tanaso tace gida ina?..sai aunty sumy tace"Kano"..kuyawa tayi tana kallonta da mamaki tace"u mean all this while kano kuke zaune?.."aunty sumy ta gyada mata kai alaman yes...tace"ikon Allah..kinga Allah ne kawai baiyi zamu hadu daku ba sbd nima kusan watanmu 6 da komawa Kano da zama"..Bobby yace"yanxu knn kano kuke?.."tace"kano muke..bari inyi introducing dinku wa kids dinku"...da sauri Bobby yace"haba sai kace bamu sansu ba"..ya nuna babban cikinsu da bazai wuce mate din Sab ba yace"ga ma sunan Daddy"..aunty Munubiya tace"umhum.."ya nuna mai bi masa yace"shi kuma wnn Habeeb"..nanma kai ta sake gydawa tana kallonshi...ya nuna ‘yar macen da bazatafi sa’ar Miemie ba yace"ga Nusaiba..wnn kuma itace bansan sunanta ba"...daria sukayi gaba dayansu ganin da gaske bai manta su din ba...Aunty Munubiya tace"ita wnn dama bai zama lallai ku santa ba"..juyawa tayi tana duban yarinyar tace"baby yama sunanki?.."da sauri yarinyar tace"sunana Nadia Usman"...wara idanu sukayi gaba daya jin sunan Mummynsu nema da yarinyar...Bobby ya kalleta yanaso yace da gaske sunan Mummy ta saka ko kuma coincidence ne..kamar tasan me yake shirin tambaya tace"yes sunan Mom dinku nasa mata...inaso ta dauko kyakykyawan hali da hakuri irin na mahaifiyarku and Alhamdulillah ta dauka"..shiru kawai sukayi kowa cikeda Mamaki...ilham da taji yarinyar ta fadi sunanta amma ita baace ta fadi nata ba tace"nima Sunana Nadia Isma’il"..a take suka kwashe da daria jin mgnr nata...Aunty Munu ta janyota jikinta tana murmushi tace"da gaske kema Nadia ne sunanki?.."da sauri Ilham tace"yes amma ana cemin Ilham"..rungumeta Aunty Munubiya tayi tana cigaba da murmushi...daga nan kuma sai labari ya 6arke tskaninsu...kowa ya shiga bada labarin bayan saduwa..farin ciki suke sosai na sake haduwa da juna after six long years...a tare sukayi breakfast daga nan kuma suka nufi asibiti gaba dayansu. Waziri na zaune tun safe ko bacci ya kasa komawa sai tambaya yake wai da gaske ‘ya’yan Attahir dinshi ya gani ko kuwa dai mafarki ne kaman yanda ya sabayi?..mutum uku daga cikin yaranshi dake wurin dai babu wanda ya bashi gamsashshen amsa don basu san ko su dinne sukazo da gaske ko kuma a mafarkin dai ya gansu shine yake zargin a gaske ne...suna shigowa dakin gaba daya hankalinshi ya koma kansu..kallonsu yake yayinda hawaye ke zarya kan fuskanshi..gabi yake bai masu adalci ba daya kasa nemansu duk shekarun nan amma saidai ba laifinshi bane..babu wanda baisa ya nemosu cikin yaranshi ba amma kowa da labari daya yake dawo mishi cewa ba’a gansu ba..shi kuma ba lafia ne dashi dazaije neman nasu da kanshi ba...yanxu kuma da yake ganinsu gabanshi sai yaga kaman ba gaske ba...da hannu yayi musu alama da suka karasa inda yake...ba musu suka isa suka tsaya jikin gadon nashi...kallonsu yakeyi daya bayan daya yana sakejin kewar mahaifinsu na rufeshi..hannu yakai ya kamo hannun Bobby dake nan kusa dashi muryanshi ba rawa yace"Attahiru.."kawai sai ya rungumeshi yana cigaba da hawaye...ya janyo Sab da other hand dinshi duk ya rungumesu yana zubda hawaye..Sab ma hawayen yake likewise su Aunty Munubiya da Aunty Sumy dake tsaye gefe...Bobby kuwa wani irin different feeling yakeji tattare dashi..bai taba tunanin zasu samu tarba daga wajen waziri balle har yayi kuka sbd farin cikin ganinsu ba...ganin yanda yake kuka kawai ya isa ya gane ba karamar wahala yasha na rashinsu a tareda shi ba..nan take ya sakejin rashin kyautuwar abunda yayi..wani irin tausayi da kuma kaunar kakan nashi suka taru suka cika mashi zuciya..sun dade rungume da juna kafin ya sakesu yana duban Aunty Sumy dasu Miemie suma yace su karaso kusa dashi..suna karasawa haka ya dinga binsu yana runguma ko kalma daya ya kasa furtawa sbd farin ciki..sun dauki lokaci mai tsaho a haka kafin Waziri da har yanxun ya kasa barinsu subar kusa dashi ya shiga neman yafiyar su kan abubuwanda ya aikatawa mahaifiyarsu..ya kuma rokesu da susa mahaifiyarsu itama ta yafe mishi...a take duk sukace sub yafe hadda Bobby da yake sake jin tausayin kakan nasu...yanda yaga yanayi musu ba karamin tausyi ya bashi ba...ya rasa inda zai sanyasu sbd farin ciki duk wanda ya shigo kuwa saiya nuna mishi su a matsayin iyalan Attahir dinshi...uncles dinsu wajen mutum biyar sukazo asibitin and duk cikinsu ba wanda waziri bai nuna masa su yana cewa sun dawo gareshi ba..sbd tsabar farin ciki lokaci daya ciwon daya dade yana fama dashi ya samu saukinshi fiyeda zato dan har hakan yaba doctor dinshi mamaki...koda sukazo tafiya hanasu yayi yace bai gaji da ganinsu ba...haka sukacigaba da zama kowa yana bashi labarin bayan rabuwa...Aunty Sumy da Aunty Munubiya suka tafi gida zasuyi girki su kawo tareda yaran..Sab shima sai yabi Taheer da yayi driving nasu zuwa gidan...ya rage daga Bobby sai kakan nashi a dakin...tambayoyi sosai Waziri keyi mishi na duk abubda ya shafi rayuwarsu shi kuma yana bashi labari daki daki...sunyi nisa cikin labarinsu sosai aka turo kofar Lamido da daddy sai wani yayan daddyn suka shigo dakin a tare...da mamaki Bobby ya daga kai yana kallonsu sai kuma ya mike daga inda yake zaune yana musu murmushi yace"barkan ku da zuwa"..daddy ma kallonshi yayi da murmushi yace"Attahir kana nan knn?.."yace"ina nan daddy..Bismillah ku zauna"..karasawa ciki sukayi suka zauna Lamido da Waziri suka fara gaisawa..baya sun gama su daddy ma suka gaisa da Waziri tareda tambayarshi ya jiki yace jiki yayi sauki...daddy na duban mahaifinshi yace"Baffa wnn shine Proprietor din makarantar su Aysha ai..dan wajen Col Attahir ne"..da mamaki Lamido yace"ikon Allah..yanxu wnn karamin Attahir ne yayi girma haka?.."cikin farin ciki waziri yace"tareda yan uwanshi sukazo tun jiya..ashe duk tsahon lokacin nan suna kano bamuda labari"..gyada kai Lamido keyi yana cewa"ikon Allah knn..Allah ya jikan Attahiru"..gaba daya suka amsa da Ameen..dakin ya danyi shiru kafin Lamido dake duban Bobby yace"kace kasan amaryata knn?.."murmushi kawai Bobby yayi kai a kasa..Lamido ya sake cewa"batajin mgn koh?..nasan kilan kuna can kuna fama da ita"..wnn karon daria ya danyi jin abunda Lamidon da kanshi ya fada still dai baiyi mgn ba...wato ita dai ko yan uwanta ba wanda baisan fitinanniya bace...nan take kuma sai akalar tunaninshi ta koma kacokam kanta yaji duk wani iri yau throughout baiji muryanta ba..ya kamata kuma ya kirata ko don ya bata labarin yau yaga Lamido..hira sosai ya barke tsakaninsu shidai nashi murmushi ne kawai sai idan waiziri ya tambayeshi wani abu ya bada amsa...gaba daya hankali da tunanin nashi sun koma kanta kuma..so yake suyi suyi su tafi shima ya dan samu ya fita waje ya kirata amma basu suka bar asibitin ba sai dab da magrib..bayan ya rakasu yayi sallah masallaci snn ya koma ciki nan kuma ya samu su Aunty Munubiya sun dawo suna cikin dakin...lalla6awa yayi zai fita waziri daya ankara dashi ya dawo dashi wai bai yadda ko nan da can yaje ya barshi ba...haka yayita zaune suna labari duk hankalinshi yayi kanta...sai da kyar suka samu waiziri ya yadda su tafi don da farko cewa yayi saidai Bobby da Sab su zauna su kawan dashi amma sbd ganin wanda ke kwana dashi yazo and bazaiji dadi ba sai suka lalla6ashi tareda alqawarin zasu dawo gobe kafin su wuce kano...ko sanar dashi tafiyan nasu ma basuyi ba sbd basusan kalan rigiman da zaiyi musu ba don sun fahimci yana fama da ita in excess. Suna kowawa gida ya shige bedroom dinshi yayi wanka sharp sharp ya fito ya saka pyjamas snn ya dauki wayanshi ya kwanta kan gado yana dialing number dinta...kafin ya gama ringing ta dauka cikin muryanta da yake ganin bazai ta6a gajiya da sauraronta ba tace"hello"..lumshe ido yayi ya bude yana jin wani irin feeling tattare dashi a hankali yace"La..mi..do"..tace"sir ina yini"..yace"lafia lau..how are u"..tace"fine"..suka danyi shiru na wani lokaci Bobby baisan lokacin daya furta"i missed u"ba..ta wara idanu sosai kaman yana ganinta tace"sir banji me kace ba"..kai tsaye ya sake cewa"i said i missed u..i missed ur rashin jin mgn"..ta dan turo baki tace"nidai inajin mgn"..murmushi ya saki yana shafa beard dinshi ko ba’a fada ba yasan turo mishi baki takeyi yanxu haka..kawai sai yaji yanaso yaga bakin datake turowan amma babu hali..ita kanta so yake ya ganta ji yake kaman yayi tsuntsu kawai saidai ta ganshi a hostel dinsu amma still babu halin yin hakan...rage muryanshi yayi can kasa yanda bazata jiba yace"i love u..i wish i can tell u"..tace"sir me kace?.."yace"cewa nayi yau na hadu Lamido a Abuja"..ta wara ido kaman yana ganinta tace"Lamido dai namu?.."yace"yea tareda dad dinki sukazo"..tace"amma dai bakace musu nayi wani abun ba koh?.."cikin zuciyarshi yace"nace musu mana..na fada musu kin sacemin zucia"..a zahiri kuma murmushi yayi kafin yace"ke me kike tunanin zan fada musu?."tace"sir ban saniba..kawai dai banso kace nayi laifi sbd nasan Lamido ina komawa gida zai rufeni da fada..kilan ma yace in fito da miji amin aure"..ta karasa mgn tana turo baki...shiko Bobby shiru yayi wani tunanin na darsuwa a zuciyarshi...hakane fa Lamido shine zai bada aurenta tunda yana raye koh..sai yaji inama sun daidaita da ita kawai yacema Waziri yanaso a nema mishi aurenta...yasan kuma bazasu hana ba sbd a yanayin yanda yaga mu’amalarsu ya tabbata ba karamin zumunchi ke tsakanin Familynsu da Familyn Lamido ba...nan take yaji wani kwarin guiwa yazo mishi..zuciyarshi ke fada mishi inshaAllah kaman ya samu auren Lamido ne ya gama tunda yanxu baida wani problem da yake ganin yana iya sawa a hanashi aurenta..problem daya da yake fuskanta yanxu shine rashin sanin actual abunda ke mind dinta..shin tana sonshi ne ko kuwa bata sonshi?. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 35 Washegari gaba dayansu suka tafi airport bayan gwagwarmaya da akasha da waziri dan cewa yayi fafur bazasu tafi su barshi ba..da kyar da sidin goshi suka samu suka shawo kanshi tareda alqawarin dawowa nan bada dadewa ba...kafin su wuce saida aka zagaya dasu cikin Freedom Medical College suka gani sosai kowa sai santinta yake musamman su Aunty Munubiya da basu ta6a zuwa ba..daga nan airport suka wuce already dama sun siya tickets so suna zuwa duk suka shiga Plane dinsu da is about to flight sbd time din tashinsu yayi...karfe goma da wani abu suka sauka Malam Aminu Kano International Airport..Aunty Munubiya bata yadda ta wuce gida ba tace saita fara zuwa gidansu taga Mummy snn zata wuce..motoci uku ne sukazo daukansu daga airport ciki hadda Mummy data kasa hakuri har su karasa gida..suna haduwa da Aunty Munubiya nan ma suka rungume juna kowaccs tana hawayen tunawa da rayuwar baya..saida aka 6an6aresu daga jikin juna snn suka shishshiga mota suka wuce...ko a mota hiran yaushe gamo sukeyi kowa tana sake neman gafarar kowa dukda cewa ba wanda yayima wani laifi a cikinsu...bayan sun isa gida ma thesame thing ne yaci gaba da faruwa har saida yaran suka koma yi musu daria...Bobby dai samu yayi ya lalla6a zuwa Flat dinshi ya dau car keys dinshi ya fice zuwa FCNM ba tareda sun lura dashi ba..so yake kawai ya ganta ko bai samu yin mgn da itaba its ok amma he really needs to see her...kafin ya karasa College din ya kira Nur ya sanar dashi yanaso ya ganta..Nur yace bashida wani matsala kafin ya karaso ma zai kira mishi ita office dinshi...cikin sauri yake driving har ya karasa college din..yana gama parking ya fito zuwa office din Nur...zaune ya sameta office din suna duba wasu papers itada Nur..baisan time daya saki wani lallausan murmushi yana kallonta ba..seeing her really makes his day..addu’a kawai yake Allah ya karkato da hankalin yarinyar nan zuwa gareshi dan ya tabbata idan bata soshi ba matsala zai samu gagaruma ma kuwa...karasawa ciki yayi ya zauna seat dake opposite to her ita sai a lokacin ma ta ganshi..saita dan saki murmushi idonta a kasa tace"sir good morning"..kallonta kawai Bobby keyi ya kasa amsawa..ta dan dago a hankali ta kalleshi sai taga gaba daya attention dinshi na kanta tayi kasa da idon da sauri tana turo baki..itafa ba son wnn idanun nashi a kanta take ba ya sani amma shine zaiyita wani tsareta dasu salon yasa ta farajin wani iri..kallonta yakeyi sosai kamar yau ne ya fara ganinta..Nur da yaga haka sai ya lalla6a ya mike ya bar musu office din yana kunshe daria...kaman jiran fitan nashi yake ya matso da seat dinshi dab da nata har suna jin kamshin turaren juna..kallonta yakeyi har yanxu kuma baida alamar denawa dan haka Lamido ta runtse ido tanajin yanda gabanta har faduwa yake sbd kallon nan da yake mata..bakin nan kuwa ta gama turoshi tamkar zai tafi Gombe ya barta nan kano sbd tsabar tsinin da yayi...a hankaki yakai hannu yayi cupping fuskanta dasu tareda dora nashi fuskan ya hadeshi wuri daya da nata yana sauke wani numfashi da karfi kaman wanda yayi aikin karfi...sake runtse idanunta tayi and gabanta bai bar faduwa ba...shima nashi idanun a lumshe suke yanajin wani irin abu yana zagaya cikin jinin jikinshi har zuwa zuciyarshi...shi kanshi nashi gaban faduwa yake so yake kawai yajita a jikinshi ko dan yayane amma baisan tayaya ba...a yanda yakeji din nan yasan idan bai samu abunda yakeso ba yana iya zautuwa..wani irin karatu yakeji daga can cikin kwakwalwarshi ya kusa rasa hanyar da zaibi ya biya karatun...da kyar ya daga hannunshi da yayi masifar nauyi ya dorashi kan lips dinta da har yanxun suke a ture tayi wani irin zabura ta kwace face dinta daga hannunshi garin haka kujeran da take zaune a kai yayi baya saura kadan ta fadi yayi azamar janyota ya dawo da ita jikinshi...a tare suka sauke ajiyar zuciya kafin ta shiga kokarin kwace kanta amma ba rikon banza yayi mata ba..ji yake yau idan bai furta mata abunda ke cikin ranshi ba yana iya mutuwa...gaba daya zuciyarshi ta gama narkewa yana kuma da yakinin babu taimakon da zata iyayi mashi matukar bai furta mata what he’s feeling ba...a hankali ya bude baki cikin muryanshi daya canxa completely yace"i..i..l..ov"bai samu daman karasawa ba sakamakon kwace jikinta da tayi da wani mugun karfi har hakan yayi sanadiyyan faduwanta kasa tim kafanta ya bugu da wani table aiko ta kwalla wani mugun kara daya dawo dashi hayyacinshi..ya mike da sauri kafin ya isa gareta cikin kuka tace"don’t touch me"..tsayawa yayi cak yana kallonta da idanunshi da suka canxa launi kaman ba nashi ba...kallon yanda ta rike kafanta tayi tana sakin wani irin kuka yayi nan yake yaji kukan nata na damunshi..sake takawa yayi still bai karasa ba tace"i said stopp..don’t come near me idan ba haka ba zan buga kaina da wnn table din"..da sauri ya tsaya nan inda yake murya a dakushe yake fadin"No..don’t do that plss..am..sorry..i never meant to hurt u"..bata kulashi ba sai kokarin mikewa da take amma ta kasa dan da gaske kafan nata ba karamin buguwa yayi ba..Bobby da yakejin kaman tashin hankalin duniyan nan aka tattaro aka dora mishi ya dan sake matsawa da nufi ya taimaka mata amma wani hadadden kara data saki dole yasashi tsayawa daga nan inda yake gamida runtse idanunshi...ba tun yanxu ba dama yasan ta iya kara sosai yasan kuma idan yace zai cigaba da kokarin matsawa kusada ita tara mishi jama’a zatayi da wnn uban ihun nata...gashi kuma ta kasa mikewa da alama tana jin jiki sosai..hankalinshi yakai kololuwar tashi ya kuma rasa taimakon daya kamata ya bata...Nur ne ya shigo office din ganin abunda ke faruwa ya karasa ciki da sauri yana cewa"Subhanallah meya sameta haka?.."kallonshi Bobby yayi da jajayen idonshi da kyar ya bude bakinshi yace"i..i.."kasa karasawa yayi sbd wani irin sarawa da kanshi yayi kawai sai ya durkushe nan wurin yana sauke numfashi...Lamido dai kukanta takeyi bilhaqqi tana rike da leg dinta..ganin haka sai Nur ya karasa kusada ita shima ya risina nan gabanta yana fadin"Lamido meya sameki?..what happened?.."cikin sheshshekar kuka tace"kafana ne ya bugu..sir bazan iya tashi ba ka taimaka min"..a rikice Bobby ya dago yana kallonta jin abubda tace...yanxu knn ta gwammace Nur ya ta6ata akan shi?..wani irin kishi yaji ya lullu6eshi baisan lokacinda ya mike ya kama hannun Nur dake kokarin taimaka mata ta mike ba kawai sai yajashi sukayi waje...kallonshi Nur yake da mamaki ganin yanda ya wani hade rai yace"meye hakan?.."fuska daure yace"you will not touch her"...idanuwa Nur ya ware akanshi daria na son kufce mishi yace"seriously?..kai meya hana ka taimaka mata tunda kana gani ta kasa mikewa"..a hankali yace"she won’t let me..she is upset sbd na ta6ata and wlh Allah Nur ba laifina bane..kai kanka kasan wnn ba halina bane amma when it comes to her..i dont know what just got into my head..i.."kasa karasawa yayi sbd rauni da muryanshi yayi..idonshi ya sake kadawa yayi jajir ya kamo hannun Nur yace"dan girman Allah kada ka ta6ata Nur..kanayin haka matsala zan samu na sani"...kallonshi Nur keyi duk kuma sai yaji ya bashi tausayi...rike hannunshi yayi shima kafin yace"don’t worry bazan ta6ata ba amma bari inyi mgn da Meena da Billy friend dinta sai suzo su dauketa mu kaita clinic"..kai kawai ya gyada mishi tareda sauke numfashi...lokacin da suka koma office din kuka take wiwi kuma har yanxu bata bar rike kafan nata ba...wani irin sanyi da zafi yaji sun rufeshi all of a sudden..duk wnn abun daya faru laifinshi ne..laifinshi ne daya kasa controlling feelings dinshi har ya janyo mata wnn matsalan...tsoronshi Allah tsoronshi kada taje tayita langabewa har kafan yazo yana rurucewa sbd ya santa sarai da raki da kuma kin magani da allura...duk hankalinshi yayi 6agal 6agal ko mgn ma kasawa yayi...bayan mintuna kadan Billy ta shigo office din tareda Nurse Meena nan suka taimaka mata ta mike kafan nan a dangale ko takashi batayi ba sbd azabar raki...Bobby ya lumshe ido dama yasan za’ayi haka...yanxu Allah kadai yasan adadin tashin hankalin da zata haifar mashi dalilin wnn ciwon...yasan yayi bye bye da kwanciyan hankali idan har ba gani yayi ta koma normal ba...kai tsaye clinic suka nufa da ita Bobby da Nur na binsu a baya...suna kwantar da ita kan bed Nur ya dakko wani muscle pain killer ya mikama Billy yace"ku shafa mata"..ba musu suka amsa suka shiga shafa mata a kafan nata ita kuma sai gursheken kuka take tana cewa da zafi...kallon yanda suke shafa maganin a hankali Bobby yayi yasan indai ba murzashi sukayi yanda zai shiga ciki ba ba abunda zaiyi mata amma kuma shima murzawan yanxu aiki ne tunda ba yadda zatayi ba..ajiyar zuciya ya sauke yana cigaba da kallonsu har suka gama Aysha bata dena kuka ba kaman yanda zuciyarshi bata dena tsalle tana ce mishi bai kyautawa abar sonta ba...suna gamawa Nur ya dakko wani magani ya basu shima aka samu da kyar suka bata tasha snn ta kwanta tayi luf tana sauke ajiyar zuciya kafin a hankali kuma bacci ya sadado yayi gaba da ita...sai a lokacin Bobby ya sauke ajiyar zuciya mai karfi amma har yanxu hankalinshi bai kwanta da yanda yaga kafan har ya fara kumbura ba...ganin yanda duk yabi ya zama wani iri Nur ya kama hannunshi suka zauna ya shiga kwantar mishi da hankali..idonshi sun kada jajir yace"duk ni na janyo mata wnn suffering din Nur..da ban biyewa son zuciyata ba da duk wnn bai faru ba..ji nake kaman zan hadiye zuciya in mutu..ciwo nakeji sosai bazan ta6a yafema kaina idan wani abu ya sameta a dalilina ba"...ya karasa mgn cikeda wani irin rauni da tashin hankali...kama hannunshi Nur yayi yana kallonshi cikeda tausayi yace"ba laifinka bane..dama Allah ya rubuta hakan zai faru so ka kwantar da hankalinka"..girgiza kai yakeyi yace"hankalina bazai ta6a kwanciya idan ina ganinta cikin wnn halin ba"..daga hannun Nur din yayi ya dora saitin heart dinshi yace"ni kadai nasan me nakeji a ciki..ni kadai nasan tashin hankalin da nake ciki"..yana gama mgn ya mike da sauri ya fita daga dakin sbd hawaye da yaji sun cika mashi ido...barin clinic din yayi gaba daya ya bude office dinshi ya shiga tareda kullewa ta ciki..yanada bukatar ya kebe ya zubda hawayen nan ko zai samu saukin nauyin da yakeji acikin zuciyarshi...yana shiga ya wurga kanshi kan sofa kawai sai ya shiga dukan head dinshi da hannunshi yana fadin"why why why plss?..why me"...ya karasa mgnr yanajin wani zafi a cikin heart dinshi..hawayen da yake son su zuba ko zai samu sassauci ma sunki zuwa amma kallo daya zaka mashi ka gano tsantsar damuwa da rudanin da yake ciki...ciwo yake mishi daya kasance sbd shi ta shiga wnn halin..sbd son zuciyanshi..da bai aika abunda yayi ba yasan babu yanda za’ayi garin kwace kanta har taje tana faduwa haka?..ya tuna yanda mahaifinta yace ya yadda tarbiyyarshi shiyasa zai damka amanarta a hannunshi shine yanxu yici amanar tashi haka?.."oh Allah what a monster i have become?.."ya fada a sarari yana cigaba bubbuga kanshi..a takaice saida ya kwashi almost 30 mins yana abu daya kafin ya sarara...bathroom ya shiga ya wanko face dinshi dukda ba kukan yayi ba amma face dinshi ya canxa sosai..yana fitowa ya bude office din ya koma zuwa clinic...zaune ya sameta Billy da wata colleague dinsu na kokarin taimaka mata ta sauki daga gadon ita kuma sai hawaye take yi...wani irin daci yaji har cikin bakinshi yana karasawa ciki ta wani hade rai snn ta dauke kai tana turo baki...murmushin yake ya saki wnda akace yafi kuka ciwo yana kallonsu da kyar suka iya sauko da ita snn suka kama hanyan fita daga dakin...su Billy da basu lura dashi ba sai yanxu suka gaidashi snn suka fice kowacce rikeda hannunta guda suka barshi tsaye yana binsu da kallo...juyawa yayi shima ya fita ya tsaya daga bakin kofa ya rungume hannu yana kallon yanda ko daga kafan da kyar takeyi kilan sbd zafi ne ko kuma sbd tsabar raki ne irin nata...saida yaga sun 6ace ma ganinshi snn shima ya bar wurin ko office din Nur bai komaba ya shiga motarshi ya bar makarantan...a hankali ya tuka kanshi har ya isa gida..yana shiga yayi mamakin ganin har yanxu su Aunty Munubiya nan nan basu tafi ba shidai ya wuce flat dinshi sbd baison ma ya zauna nan cikinsu bare su fuskanci yana tareda damuwa...haka yayita zaune a daki yinin ranan har su Aunty Munubiya sukazo tafia ta aiko a kirashi suyi sallama amma yayi pretending yana bacci yaki fita...har dare bai fito daga Flat dinshi ba ko sallahn magrib da ishaa a nan cikin dakin nashi yayisu sbd fever da yaji ya rufeshi...hankalinshi gaba daya yana kanta so yake yaji halinda take ciki amma tsoron kiranta ma yakeyi sbd yasan ba dauka zatayi ba...yasan Nur ne kadai zai iya taimakonshi a halinda yake ciki dan haka ya danna masa kira..yana dauka ko salam dinshi bai amsa ba yace"Nur inaso inji halinda take ciki plss..kunyi mgn da ita?.."Nur yace"bamuyi ba..ka kirata a waya mana"..da sauri yace"ba dauka zatayi ba..nidai taimako na zakayi zako gida saika kiramin ita a wayanka..inaso inji ya jikinta"...ajiyar zuciya Nur ya sauke kafin yace"shknn gani nan zuwa"..da sauri Bobby yace"nagode sosai friend..nagode"..Nur ajiye waya yayi yana mamakin wnn so da Bobby kema Lamido haka?..duk yabi ya koma kaman wani soko sbd soyayya...shi kanshi daxu ba karamin tausayi ya bashi ba...yaji inama Lamido zata amince ta aureshi kawai a wuce wajen...keys din motanshi ya dauka ya fita daga gidan...su Mummy na zaune parlor lokacinda ya shigo tabishi da kallo kawai..tun daxu ta fuskanci akwai abunda damun Bobby zuba ido kawai tayi taga gudun ruwanshi and wnn zuwan na Nur ya sake tabbatar mata da lallai ba lafia ba...ko zama baiyi nan parlon ba kawai ya gaishesu ta wuce ciki Aunty Sumy da kanta saida tayi mamakin hakan...a kwance ya samu Bobby har yanxu eyes dinshi basu dawo normal ba..yana ganinshi ya mike zaune shima Nur din karasawa yayi kusa dashi ya zauna snn ya shiga kiranta yasa a speaker...har ya gama ringing baa dauka ba ya sake kira wnn karon yaji an daga amma maimakon ita sai yaji muryan Billy na fadin"bacci takeyi sir"..Nur yace"ya jikin nata?.."Billy ta juya ta dan kalli yanda kafan har ya fara swelling tace"sir kumbura kafan yakeyi..yanxu ta gama kuka sai da kyar muka samu bacci ya dauketa"..ba Bobby ba shi kanshi Nur din hankalinshi tashi yayi da sauri yace"i will get back to you"..daga haka ya kashe wayar yana kallon Bobby daya dafe head dinshi da hannu bibbiyu yana jujjuya kan cikeda tashin hankali yace"Nur na shiga uku..zuciyata bugawa zatayi wlh"..da sauri Nur ya kama hannayen nashi ya rike tareda fadin"ba abubda zai faru inshaAllah..ka kwantar da hankalinka yanxu zanje in nemi doc saratu muje can hostel din ta dubata"..mikewa yayi da sauri har wani juwa ke neman daukanshi yace"muje ka kaini in ganta plss..hankalina bazai kwanta ba idan banga halinda take ciki ba"..kamashi Nur yayi ya zaunar dashi yana dubanshi yace"relax dan Allah..kaga yanda jikinka ke rawa kuwa?..kaima kana bukatan medication sbd haka kasha magani ka kwanta ka huta ni zanje inyi duk abunda ya kamata ayi mata"..tun kafin ya rufe baki Bobby ke girgiza kai yace"u won’t understand..kona zauna hankalina ba kwanciya zaiyi ba..i need to see her"..shiru kawai Nur yayi yana kallon yanda yake mgn da kyar sbd tashin hankalin da yake ciki...basu san sanda Mummy ta shigo ba jin mgnrta sukayi kusa dasu...Bobby na daga ido daya ganta kawai sai ya mike tsaye da sauri ya fada jikinta murya a raunane yace"Mummy inaso inje in ganta plss..zuciyata bugawa zatayi"...da mamaki Mummy ke kallon Nur tace"Nuru meya sameshi haka?.."a nustu Nur ya bata labarin iya abunda ya sani itama nan take taji nata hankalin ya tashi..kada dai ace Bobby wani abu yaje yayiwa yarinyar mutane fa...dagoshi tayi daga jikinta tana kallonshi..tambaya take son mishi kan abunda ya haddasa faruwar haka amma sai ta kasa sbd tsantsar tashin hankali data karanto a fuskanshi da kuma yanda idanunshi suka juye lokaci guda tasan tsaf zuciyan nashi zai iya bugawa kaman yanda fada..batayi gaddama ba ta kalli Nur tace"kaje dashi ya ganta..snn duk halinda ake ciki ka kira ka sanar dani and make sure shima kayi mishi treatment sbd zazza6i ne sosai naji a jikinshi"...kallonta Nur yake kafin yace"amma Mummy shima yana bukatar hutu fa"..tace"idanma bakuje dashi hutun da muke so yayin ba samun yinshi zaiyi ba..banason zuciyar nashi ya samu matsala kaman yanda nace kuma nasan halinshi muddin baa kaishi ya gantan ba yana iya samun problem"..gyada kai kawai Nur yayi snn ya kama hannun Bobbyn suka fita...kwace hannunshi yayi daga na Nur yana cigaba da tafiya da kanshi gamida tattaro duk wani sauran jarumta da karfin halin da sukayi mashi ragowa ya dorasu bisa kanshi snn yacigaba da tafiya har zuwa inda Nur yayi parking..da kanshi ya bude front seat ya shiga shima Nur ya shima driver seat snn ya tada motar suka dauki hanyan FCNM..zuciyarshi sai bugawa takeyi sbd baisan me zai tarar a wurinta ba amma ya gwammaci duk wani wulakanci da zatayi mishi akan dai yayi zaune a gida batareda yazo yaga halinda take ciki ba..gani yake kaman Nur ba tafiya yakeyi ba don bai ta6a ganin nisan college din ba irin na yau...suna shiga makarantan direct suka wuce hostel nan ma Bobby yaga nisan hostel din kaman yau ya fara shigoshi...saida sukazo daidai gate na female hostel Nur yayi parking snn ya sake dialing number Lamido...Billy ce ta sake dagawa yace"gamu hostel din naku zaki iya fito da ita?.."juyawa Billy tayi ta kalli Aysha dake rikeda kafan tana sauke ajiyar zuciya cikin bacci itama kaman zatasa kuka tace"sir bazan iyaba..bacci takeyi tun daxu ni bansan yanda zanyi mata ba"...Nur kashe wayan yayi yana duban Bobby daya gama jin duk abubuwanda Billy ta fada...daya daga cikin matrons sukasa akayo musu mgn da ita...ta bada sanarwan zasu shigo hostel din snn ta dawo tayi musu jagora har cikin apartment din da yayi tsit sbd kowa ta shiga daki sbd sanarwar da akayi musu...kai tsaye dakinsu suka nufa Bobby najin each taku na kara masa adadin tashin hankalin akan wanda yake ciki already. Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 36 Matron da Billy ne suka fara shiga dakin snn Nur shi kuma Bobby ya shiga daka karshe...har lokacin bata dena sakin ajiyar zucia cikin baccin da take yi ba...a hankali ya karasa inda take hannayenshi zube a aljihu ya tsaya kusada gadon yana kallonta tun daga fuskanta da yayi jaa as a result of kukan da tayi har zuwa legs dinta da rigan jikinta ya danyi sama kadan sai fair skin dinta daketa glowing...kallonta kanta yayi shima ya ganshi a bude duk gashinta a waje kawai sai yaji ranshi ya baci..kan wane dalili zasu barta a haka tunda sunsan zasu iya shigowa har inda take..kawai sun bar jikinta da gashinta a bude gashi nan Nur yana ta kallo abunshi..kallon Billy yayi da face dinshi dayaji kaman shi yake daure kanshi da kanshi a takaice yace"batada hula ne?.."da sauri Billy tace"sir da kanta ta cire wlh..wai bazata iya bacci dashi ba"..yana sake dinke fuska yace"shi kuma jikinta da kuka bari a bude fa?.."kallon jikin nata tayi da sauri tanaso taga inda suka bari a buden sai taga rigan ta ya danyi sama..batace dashi komai ba ta karasa ta janyo mata rigar har kasa snn ta dauki hulanta data yar nan kasa shima ta shiga kokarin zurawa a kanta daidai lokacin kuma ta dan bude ido snn ta sake mai dashi ta rufe..Billy na gama sa mata hulan takai hannu zata cire murya a cushe Bobby yace"idan kika cire hulan nan sai ranki ya 6aci wlh"..bude ido tayi da sauri tareda mikewa zaune tana kallonshi...ta dauka a mafarki taji muryanshi amma sai taga da gaske shi din ne a gabanta..to me kuma ya kawoshi bayan abunda ya gamayi mata daxu..daure fuskanta tayi ta wani kauda kai gefe tana harare harare..shima ya daure nashi fuskan dan yasan idan ba haka yayi mata ba tsaf zata sake cire hulan ta bar gashi a bude tunda ba hankali ne ya isheta ba..Nur dai na tsaye gefe yana kallon ikon Allah..mamaki yake na ganin yanda Bobby ya wani hade rai yana mata fada kaman ba shine yake kokarin sa mishi kuka ba daxun sbd ita ba..wato har yanzu dai wnn ki fadin nashi yana nan baije ko inaba..idan ba haka ba why kaida ke dab da shiga matsala sbd son yarinya kuma still kanada kafin hali daure mata fuska haka...karasawa yayi ya durkusa nan kusa da ita yana kallon legs dinta dake nan kan gadon yanaso ya gane wadda take ciwon a ciki amma ya kasa..daga ido yayi ya dan kalleta sai kuma ya kawar da kan nashi jin wani bakon abu dake zagayawa cikin jikinshi..duban nashi ya maida ga Billy kafin yace"wanne kafan ne yake ciwo?"..a hankali tace mishi"na dama"..bai sake cewa komai ba ya juya yana kallon kafan damar nata..ganin bai ganin komai sai yakai hannunshi a hankali da nufin ya dago kafan Aysha ta saki wani irin kara tana fadin"Noo"..kallonta kawai yayi baice komai ba sai kuma ya mike still yana duban Billy yace"ki bata hijab tasa muje asibiti"..wara idanu Aysha tayi jin abunda ya fada idonta har ya cicciko da hawaye tace"nidai bazanje asibiti ba wlh..ni bazaa yi mun allura ba banaso"...kallon Nur Bobby yayi cikin sigar ka taimaka mun...Nur ya saki murmushi tareda karasawa inda take yace"Lamido ba allura za'a maki bafa..duba kafan kawai za'ayi ko da akwai matsala ta ciki"..yana rufe baki tace"nidai dan Allah banason zuwa sir..bazan iya takawa ba"..kallonta kawai yakeyi rungume da hannu ita kuma sai tayi kasa da ido tana goge tears dinta tace"to zanje..amma dan Allah banda allura wlh ciwo yakemun"..Nur yace"baza'ayi maki allura ba inshaAllah..yanzu matron da Billy zasu taimaka maki ki mike tunda bazai iya tafiya ba"..batace komai ba sai hawaye data cigaba dayi..tsoro takeji kar suje suyi mata allura ita dai..a muguntan Dr Bobby tasan wlh da kyar idan baiyi mata allura ba tunda baida imani...Billy ce ta dauko hijab ta saka mata snn suka kama hannunta itada matron din don fita da ita waje...taku daya ta iyayi ta saki wani kara da saida Bobby yaji shi har cikin zuciyarshi...nan da nan saiga hawaye a fuskanta ta shiga kokarin durkushewa nan kasa sbd azabar zafi da taji har cikin bones dinta...girgiza kai kawai take murya can kasa tace"bazan iyaba"..kallonta duk suka tsaya yi harda Bobby da yakejin kukan nata har can cikin ranshi..ji yake kamar yaje ya sungumeta yayi waje da ita amma ba halin yin haka...sai da kyar da taimakon Billy suka samu ta yadda ta mike suka riketa har zuwa inda sukaƙi parking...kafin su karasa Nur ya bude musu kofa dan haka suna zuwa suka Sanya ta ciki Billy ma ta shiga suma suka shiga snn Nur ya tada motar suka tafi...Bobby dake zaune front seat jingina kanshi jikin kujeran yayi tareda lumshe idanu..jin kukan nan nata yakeyi har cikin zuciyarshi yayinda wani irin zafi da kunchi suke sake rufe shi..Allah kadai yasan yanda yakeji nunawa ne kawai baiyi amma yana cikin matsala gagaruma ma kuwa...kasa cigaba da hakuri yayi ya juya yana kallon yanda take rikeda kafan tana kuka..murya can kasa yace"kukan ya isa haka dan girman Allah"..ko kulashi ba tayi ba ta cigaba da kukan ta...a takai ce har suka isa Freedom bata bar kuka ba...Bobby duk ya rikice ya tasa inda zai tsoma kanshi yaji dadi..Nur na gama parking duk suka bude mota suka fito banda ita da ko motsawa ba tayi ba...Billy ta zagayo ta bude mata kofa tareda kamo hannunta tace"ki daure mu karasa ciki"..rike hannun nata tayi snn ta sakko da kafan a hankali sai kuma ta gagara mikewa..Nur dai na tsaye yana kallonsu shi kuma Bobby ganin sake bata musu lokacin take kawai ya karasa wurin baiyi wata wata ba ya daga ta cak ya nufi cikin asibitin da ita..sai ihu taka tana ita ya sauketa amma ko tanka mata baiyi ba har ya karasa office dinshi su Billy na binsu a baya..Nur ya karasa ya bude office din suka shiga..kai tsaye ya direta kan gadon dake nan cikin office din fuskan nan a daure kamar bai taba dariya ba...yana ajiye ta ya bude wani drawer ya dakko wani muscle pain killer ya ajiye kan trolley snn ya shiga bathroom ya zuba ruwa cikin wani bowl mai zurfi ya hada da towel dan karami snn ya dawo dakin..daga Nur har Billy kallonshi kawai suke ba wanda yace kala..kujera ya janyo ya zauna nan kusada ita snn ya zaka towel din cikin lukewarm watare daya debo ya matseshi snn ya kama kafan nata ya rikeshi da kyau yanda bazata iya kwacewa ba ya shiga danna mata towel din a wurin..banda ihu da musu mutsu ba abunda take amma ta kasa kwace kafar daga hannunshi sbd rikon da yayi mata bana wasa bane..danna mata kawai yakeyi ba tareda ko kallonta yayi ba sbd gudun abunda hakan zai haifar mashi..yasan idan ba haka yayi mata ba ba bari zata yi ayi mata abunda ya dace ba and Allah ya sani bazai taba samun sukuni ba idan ba gani yayi kafan nata ya warke gaba daya ba..idan zai biye ta zuciyarshi nan ma bazai iya mata abunda ya dace ba kuma shidai akan ya bari wani ya tabata gwara shi yayi mata duk abun daya kama ta idan yaso daga baya sai yayi aikin rarrashi dan dai yasan rigima ne zai sashi kamar ba gobe..tunda ya fara bai saurara mata ba sai da ya tabbatar kafar ya gasu snn ya kyaleta..ya dauki towel da bowl din ya maida su bathroom ya dawo sai kuma ya dauki maganin da zai shafa mata a kafar yana kallonta..kuka take yi sosai har numfashinta na seizing kamar zai dauke..ga wani uban zufa data hada sharkaf kaman wanda aka gasata a oven..tausayinta yaji ya kama shi ganin yanda take kuka yasan dole zataji zafi amma ya zaiyi?..shima ba a son ranshi yayi mata haka ba babu yanda zaiyi ne kawai..janyo kujeran yayi a hankali ya zauna still yana kallonta duk sai yaji ya kasa aikata komai..juyawa yayi ya kalli Nur wai ko zai taimaka mashi amma sai yaga shi dariya ma yakeyi abun shi sai kuma ya juya ya fita daga office din...Billy ma ba tayi wata wata ba tabi bayanshi don Allah ya gani bazata iya zama nan ciki ba...juyawa yayi yana kallonta suna hada ido ya dauke nashi da sauri ya shiga matsa maganin a hannunshi..sam baison wnn raunin dake kokarin dakatar dashi ne...runtse ido yayi ya bude snn yayi watsi da raunin dake dake kunno mishi kai ya kamo kafan nata a hankali zai shafa maganin kawai sai yaji ta kanakameshi tana sakin wani marayan kuka..lumshe ido yayi yanajin wani irin yanayi a cikin jikinshi...wani irin weird feeling da bai taba tsintan kanshi ciki ba..cikin muryanta da bai fita sosai tace"sir dan Allah..dan Annabi kayi hakuri"...lumshe ido ya sakeyi yanajin zuciyarshi na wani irin tattarewa ya cunkushe can wuri daya yana bugawa da mugun karfi...a hankali yakai hannunshi ya zagaye bayanta dasu bakinshi saitin kunnenta yace"am..sorry..plss"gyada kai kawai takeyi tana cigaba da kuka tace"toh bazaka shafamin ba koh?.."dagota yayi daga jikinshi yayi cupping fuskanta yana kallon cikin idonta yace"hakan bazai yiwu ba Aysher..kiyi hakuri a shafa maki ko yayane zakiji sauki"..girgiza kai ta shiga yi tana cigaba da hawaye tace"dan girman Allah No..mutuwa za.."bata karasa ba ya rufe mata bakin yana girgiza kai duk ya gama goge maganin hannun nashi a jikinta...kamata yayi ya kwantar da ita kan gadon snn ya sake matsa maganin a hannu yayi saurin kama kafar ya shiga murzawa a hankali..banda kuka da ihu ba abunda Lamido take har wani shidewa take sbd azaba shi kuma bai saurara mata ba saida ya tabata maganin ya shiga ciki snn ya ajiye kafar..har yanzu kuka takeyi tana sauke ajiyar zuciya shi kuma ya kama hannunta a hankali ya sake cewa"am..so..sorry love"..ko sauraranshi ba tayi ba ta kwace hannunta tana cigaba da kuka shi kuma yayi tagumi kawai yana kallonta..Allah kadai yasan yanda kukan nan nata ke daga hankalinshi..ita kanta da tasan yanda yakeji idan tanayi da batayi ba ko dan sbd shi...haka yayita kallonta tana kuka da yayi yunkurin taimaka mata zatace bataso..duk tabi ta sake daga mishi hankali da kukan nata..saida bacci ya dauketa snn ya sauke ajiyar zuciya..mikewa yayi daga inda yake zaune ya leka ya tabbatar baccin tayi da gaske snn ya gyara mata kwanciya a hankali yanda bazata tashi ba..lumshe ido yayi yakai lips dinshi forehead dinta ya manna mata peck a hankali murya can kasa yace"get well soon love..i love you"..daga haka ya gyara mata kafar snn ya janyo kujeran dab da ita ya zauna tareda rike hannunta cikin nashi ya dora kanshi gefen gadon shima daga haka bacci ya sadado yayi awon gaba dashi. Nur na barin office din dama kai tsaye inda ya ajiye motarshi ya nufa ya bude ya shiga ciki sai ga Billy itama ta karaso ta dan langabe kai tace"sir nima ka ajiyeni hostel plss"..kallonta yayi kafin yace"why?..bazaki bari ku koma tareba?.."da sauri tace"nasan proprietor zai dawo da ita sir dan Allah ka mai dani"..bai sake cewa komai ba ya bude mata motar yace"to shigo"..ba musu ta shiga ciki Nur ya tayar da motar suka fita daga asibitin. Karfe sha daya da kusan rabi Lamido ta shiga bude idonta a hankali har ta waresu fes akan Bobby da har yanzun kanshi ke kife nan kusada ita yana nashi baccin..zare idanun tayi da kyau tana kallonshi da mamaki ganin ya wani kwakwume mata hannu ya rike cikin nashi..daddagewa tayi ta kwace hannun nata tana zabga masa harara kamar idonta zasu fadi kasa..daidai lokacin shima ya farka tareda dago kanshi a hankali sai yaci karo da nata idon tana hararanshi...baice komai ba ya mike da sauri ya fada bathroom..wanko face dinshi yayi ya fito sai yaga ta hade kai da gwuiwa kamar zatayi kuka...da sauri ya karasa inda take ya zauna nan gefen gadon yana dubanta a hankali yace"what again?.."dagowa tayi tana kallonshi fuska daure tace"ni ka mai dani hostel"..kallonta ya tsaya yi for some secs kafin ya hada hannayenshi waje daya in a pleading tone yace"nace fa am sorry..da gaske bazan kara ba kiyi hakuri plss"..batace komai ba sai juya mishi baya da tayi zata fara hawaye yace"idan Allah noo..please am sorry..ki yafemin"..goge hawayen tayi kafin ta juyo ba tareda ta kalleshi ba tace"to ka mai dani hostel nidai"..yace"zakiyi hakuri ki dena fushi?.."gyada mashi kai tayi..da sauri yace"thank u so much"..tana turo baki tace"kuma kada ka sake tabani nidai"..yace"ban karawa inshaAllah..ki tayani da addu'a"..da mamaki ta kalleshi tace"addu'an me?.."shiru kawai yayi yana kallonta dan baisan yaushe mgnr ya fito ba..a hankali yace"kafan yayi sauki?.."still kai ta daga mishi tana cigaba da turo baki shi kuma sai yayi kasake yana kallonta kaman wani soko..kallonta yakeyi full of love and affection..yarinyar na burgeshi fiyeda tunanin mai karatu..komai tayi burgeshi yake sai yaga tana kyau da duk wani abu da tayi shiyasa yake kishinta sosai...a yanda yake kishinta shi ko cewa za'ayi babu wanda zai na kallonta duk dunia sai shi kadai so zaiyi amma yasan hakan ba mai yiwuwa bane...agogon hannunshi ya duba yaga its almost 12 and Allah ya sani yana tunanin yanda zai maidata hostel cikin daren nan dan yasan Nur da kyar idan ba tafiya yayi ba..dagowa tayi ta kalleshi zata sake mgn wayanshi dake cikin aljihu ya fara ringing..ya zaroshi da sauri ganin Mummy ke kira yayi picking tareda kaiwa kunne..a daya bangaren Mummy tace"kana kina Bobby?..ya jikin nata?.."yace"da sauki Mummy"..tace"ka tabbata da sauki ba wani problem din?.."yace"yes Mummy"..sai kuma ya juya yare zuwa igbo yace mata"Mummy babu mota hannuna and inaso in maidata hostel yanzu..Nur ya wuce tun daxu"..Mummy tace"saidai in turo Sab ya kawo maka..amma why not ka bari ta kwana asibitin sbd a sake tabbatar da samun saukin nata..kuma ga dare yayi"..ajiyar zucia ya sauke yana kallon Aysha da tayi masa kuri da ido tana kallonshi jin ya wani canxa yare cikin ranta tace"dan kyar idan ba gulamana yakeba wlh..inyamurin banza"..ba tareda ya dauke idonshi daga kanta ba yace"bazata yadda ba Mummy..nima kaina ba son zuwa hostel din nasu nake da daren nan ba amma idan ban maidata ba daga min hankali zata yi nasani"..shiru yaji Mummy tayi kafin can tace"ko zaka kawota nan gida ta kwana zuwa safe ka maidata hostel din?.."shirun shima yayi kamar me nazari yace"anya kuwa zata yadda Mummy?..rigima zatai tayi wlh"..dan murmushi Mummy ta saki jin abunda ya fada kafin tace"ba rigiman da zatai inshaAllah..if tana kusa ka bata wayan muyi mgn"..bai sake cewa komai ba ya mika mata wayan yana dubanta a hankali yace"My Mom..wants to..talk to u"..batayi musu ba ta karba tana turo baki tasa wayan a kunne..Mummy tace"daughter ya jikin naji?.."da sauri tayi kasa da kai kmr Mummy na ganinta tace"Mama ina yini"..Mummy daketa faman smiling tace"lafia lau daughter..ya jiki?.."tace"Alhamdulillah"..Mummy tace"MashaaAllah..dama ce mishi nayi ya kawoki gida sbd dare yayi bai kamata yaje hostel dinku yanzu ba..snn ya sake duba kafan naki to make sure ba wani problem kuma..hope bazaki ce aah ba?.."Lamido tayi shiru tana tunanin amsar da zata bata..gani tayi gwara ta kwana gidan nasu akan dai ta kwana asibiti..afterall ba daki daya zasu kwana ba dan haka bazata damu kanta ba...saida Mummy ta sake mgn snn a hankali tace"toh Mama"..Mummy tace"nagode sosai daughter Allah miki albarka..yanxun zan turo Sab da mota yazo ya dauko ku"..Aysha tace"toh"..daga haka kuma Mummy ta kashe kiran..ajiye wayar tayi tana kallonshi kama zatasa kuka tace"shine zaka hadani da mamanka koh?.."murmushi ya saki kafin a hankali yace"am sorry"..turo baki kawai tayi ba tace komai ba..shi kuma sai ya cigaba da kallonta before saying"kinci abinci?.."banza tayi mashi kamar bataji ba..ya sake cewa"Aysher am talking"..nan ma shiru ba mgn dan haka ya dan daga murya yace"Lamidooo"..juyowa tayi a fusace tana kallonshi tace"ni banaso"..kmr wani abun tausayi yace mata"am sorry tou..zakici abinci?.."ta girgiza kai alamar no snn ta sake komawa ta kwanta..shima baice mata komai ba sai kallonta kawai da yakeyi kamar yau ya fara ganinta...after like 20 minutes Sab ya iso asibitin bai shigo ciki ba ya kirashi a waya ya fada mashi ya karaso dan haka ya mike ya isa inda take bayan ya tattaro mata takalmanta dake kasa yace"get dawn mu tafi..ya iso"..ba tace komai ba ta sauka daga gadon ta zura takalmanta snn ta shiga takawa a hankali sbd zafi da taji kafan na mata..daxun da yake kwance take sai bataji ciwon komai ba amma yanxu zafi takeji sosai saidai bai kai na daxun ba tunda tana dan iya takawa...ita ta wuce gaba Bobby na binta a baya har suka fita waje..ko yaya ta danyi kwakwaran mosti sai yaga kaman faduwa zatayi bai dai yi kokarin riketa ba har suka iso parking lot..Sab na hangosu ya fito ya bude musu motar..tana karasowa ya nuna mata front seat yana fadin"sannu"..wani harara Bobby ya sakar masa kafin ya bude back seat ya zurata ciki shi kuma ya shiga front seat din Sab dake murmushi ya shiga driver seat snn ya tayar da motar suka tafi...baya cikakken minti biyu bai juya ya kalleta ba..gaba daya hankali da zuciyarshi suna gareta..gani yake kmr wani abu zai faru da ita idan baya gani shiyasa yake juyawa akayi akayi..Sab dai driving dinshi yakeyi amma a karon farko yau yaga wani irin canji tattare da yayan nashi kuma dukda Mummy bata sanar dashi wacece Lamido a wurinshi ba shi ya gama tabbatarwa kanshi matsayinta sbd wnn special attension da Bobby yake bata bana wasa bane..ba ko wane ordinary mutum ake bama wnn attension din ba sai mutumin da ake mutuwa so da kauna shi kuma ya tabbata Uncle Bobby son yarinyar nan yake...haka har suka karasa gida ba wanda yace tak a cikinsu sai Bobby daketa faman juyawa yana ganin halinda take ciki sai kace wadda take labour...Sab na gama parking ya bude mota ya fita shima Bobby ya fita snn ya zagaye ya bude mata kofa yana dubanta a hankali yace"to sauko"..ba musu ta fito daga motar tana wani dangale kafa kmr mai karaya a jiki..taku daya biyu tayi sai ta koma da sauri ta zauna cikin motar da bai riga rufe kofar ba tana girgiza kai idonta har sun ciko da hawaye tace"bazan iyaba"..kallonta kawai Bobby keyi yana mamakin taki irin nata..durkusawa yayi nan inda kafan nata yake yana kallo shidai baiga wani alamun har yanzu yana ciwo ba tsabar langwai ne kawai irin nata..shi baisan yanda za'ayi duk ranar da akace ga Lamido a labour room ba..kilan saita daga hankalin kowa kafin ta haihu..tunanin haka ya sashi sakin murmushin da bai shirya masa ba kafin ya kama kafan a hankali ya shiga tofa mata addu'a akai ita kuma ta wani lumshe ido tana jin abunda yakeyi...saida ya dauki almost 5 mins yana mata addu'a a kafar kafin ya gama..ya ajiye kafar tareda mikewa yana dubanta yace"to yanxun ki gwada mu gani nasan zaki iya"..ba tace komai ba ta sake sauka daga motar ta shiga takawa a hankali kmr mara laka a jiki..shi kuwa murmushi kawai yakeyi yana bin bayanta cikin ranshi yana jinjina tsananin raki irin nata..yasan da baiyi mata yanda yayi daxun ba da wlh haka zatayi ta zama kafar yana sake rurucewa shi kuma tana daga mashi hankali amma da bai bari raunin da yake dashi yayi tasiri a kanshi ba yayi mata abunda ya kama ta ai gashi yanzu har ta mike tana taka kafar...har suka shiga parlor bai dena kallon yanda take tafia yana sakin murmushi ba..Mummy da Anty Sumy dake zaman jiransu a parlor suna ganinsu duk suka mike aunty Sumy tayi saurin kamota ta karaso cikin parlorn da ita tana cewa"sannu Aysha"..Mummy ma bayan sun zauna tace"sannu daughter"..murmushi kawai Aysha tayi tareda dan dukawa tace"Mama ina yini"..Mummy tayi saurin mikar da ita tana fadin"lafia lau..ya jikin maki?.."kai a kasa tace"naji sauki"..Mummy tace"toh Allah ya kara sauki"..tace"Ameen"..sai kuma ta juya tana gaishe da aunty Sumy..itama ta ansa da ta bayanta ya jiki tace da sauki..Bobby dai na zaune yana kallonsu feeling relieved sbd ganin da gaske jikin nata yayi sauki..shi kanshi yafi son ta kwana a nan din yanda ko wani matsalan zai tashi cikin dare bazai rasa abunda zaiyi ba unlike in tana hostel da bai zama lallai ma yasan halin da take ciki ba..Mummy ce ta dubeshi ganin yanda yake smiling tace"ya jikin naka kaina?.."murmushi kawai ya kara saki maimakon ya amsa mata sai cewa yayi"Mummy ba taci abinci ba"..yana rufe baki Lamido tace"banajin yunwa fa"..Mummy tace"ya kamata kici wani abu kafin ki kwanta..Sumayya shiga kitchen ki hada mata ko tea ne tasha bari na shiga da ita ciki tayi wanka"..Anty Sumy ta mike zuwa kitchen ita kuma Mummy ta kama hannun Aysha suka nufi flat dinta...other bedroom dinta da ba amfani takeyi dashi ba ta shiga da ita ta ajiyeta kan gado ita kuma ta shiga bathroom ta hada mata ruwa mai dan zafi ta fito mata dasu towel da komai da zatai amfani dashi snn ta fito tana dubana tace"toh shiga kiyi wanka zakiji dadin jikin ki"..ba tace komai ba ta mike zuwa bathroom din Mummy tabita da kallo tana murmushi..zuwa yanxu ta tabbatar ita din farin cikin Bobby ce shiyasa a kullum addu'anta bai wuce Allah ya karkato da hankalinta gareshi ba...tana kokarin fita daga sakin aunty Sumy ta shigo da tea da omalet ta ajiye sai kuma ga Bobbyn nan shima ya shigo hankalinshi kan Mummy yace"Mummy batada kayan sawa ko in fita in samu mata wani kayan yanxu?.."kama hannunshi Mummy tayi tana murmushi tace"ka kwantar da hankalinka bazata rasa kayan da zatasa ba a gidan nan"..murmushin shima yakeyi kafin yace"nagode sosai Mummy"..ta sake kama daya hannunshi tace"sai yanxun nake sake tabbatar da cewa my son is in love..Allah ya karkato da hankalinta gareka"..ya rungumeta yana cewa"Ameen Ameen Mummy na..wlh ina sonta sosai..ni kaina bansan irin son da nakeyi mata ba"..shafa kanshi kawai Mummy keyi tana murmushi...Anty Sumy da tun daxun take kallonsu tace"ina ganin wariyar launin fata a gidan nan"..harara Mummy ta wata mata ita kuma ta fita daga dakin tana dariya...Mummy ta dagoshi daga jikinta tace"oya kaje ka samu kayi wanka kaima sai kaci abinci"..baiyi mata musu ba ya juya ya fita daga dakin itama Mummy ta fita don samo mata kayan da zata saka. U people should include me in ur prayers plss..am seriously sick😣😢bana son nayi keeping naku waiting shiyasa nayi wnn amma if kun jini shiru gobe kuyimun uzuri plss...ina gama warwarewa zuwa jibi zaku jini..thanks and love u all❤️ Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 37 Yana shiga bedroom dinshi direct ya wuce bathroom bayan ya rage kayan jikinshi...wanka yayi sharp sharp ya fito zuwa closet ya saka pyjamas har zai kwanta sai kuma yaga he needs to see her ko don sbd ya tabbata taci abinci...fita yayi daga dakin zuwa flat din Mummy..ganin ba kowa a parlorn ya nufi dakinda take ciki..kan gado ya isketa zaune da zumbulelen hijab dinta tayi tagumi da hannunta...ya karasa ciki da sauri ya zauna kusada ita kafin yace"what again?.."kallonshi ta danyi sai kuma ta dauke kai tana turo baki...yakai hannu ya juyoda fuskan nata gareshi yana kallonta yace"Lamido plss..menene ya faru again?..nayi maki wani abun ne?.."girgiza kai ta shiga yi kmr zata fara hawaye tace"ni bacci zanyi"..ajiyar zuciya ya sauke mai karfi yana kallonta..har kullum yana mamakin yanda hawaye sam baiyi mata wahala..kan dan karamin abu zata fara kuka kuma saika rantse wani gagarumin laifin akayi mata...ganin ta juya tana neman kwanciya yayi saurin dakatar da ita da fadin"ki tsaya to kici abinci plss"..ture hannunshi tayi tana cigaba da turo mishi baki tace"ni na koshi"..daga haka ta juya mishi baya ta kwanta abunta shi kuma sai yayi zaune yana binta da ido..baisan ta inda ya kamata ya fara rokonta taci abinci ba..yasan ko a hostel din ma da kyar idan taci wani abun shi kuma baiso ta kwana da yunwa ko kadan..suna zaune haka Mummy ta shigo dakin rikeda sabon dogon riga na bacci a hannunta...tana ganinta a kwance taga tea kuma a ajiye tace"Aysha bakisha tea din ba?.."mikewa tayi da sauri tana sunkuyar da kai tace"yanxu zansha"..daga haka takai hannu ta dauki mug din tea din ta kai bakinta ta fara sha...Bobby sai kallonta yakeyi yanajin wani irin relieve sbd shan tean da take..wato sbd shine yayi mata mgn tace bazata sha ba amma da yake yanxu Mummy ne shine ta dauka tana sha..shi ko a hakan ma yaji dadi at least dai bazata kwana da yunwa ba...tunda ta kada mug din a baki bata ajiye ba saida ta shanye Mummy ta karasa tana mika mata rigar hannunta tace"to ga wnn ki sa zuwa safiya..naga bakici omalet din bama"..a hankali tace"na koshi"..Mummy tace"to amsa rigan kisa..idan kina bukatar wani abun karkiji komai kizo ki fadamin kinji?.."kai kawai ta gyada tareda amsan rigan..Mummy ta maida dubanta ga Bobby dake kallonta har yanzu tace"to tashi muje kaima ka samu ka kwanta"..baiyi mata musu ba ya mike suka fita daga dakin..suna zuwa parlor ya wani marairaice yace"Mummy kina ganin zata iya kwana ita kadai kuwa?.."kamo hannunshi Mummy tayi tana murmushi tace"bana son a takurata ne shi yasa na barta ita kadai..ka kwantar da hankalinka nothing will happen inshaAllah ba gani nan kusa da ita ba?.."gyada mata kanshi yayi kafin ya rungumeta yana cewa"nagode sosai Mummy"..tace"nima nagode..yanxu kaje ka kwanta saida safe"..dagowa yayi yana kallonta da murmushi yace"ka chi fo"..murmushin itama takeyi mishi tace"ka chi boo"..sake rungumeta yayi hadda yi mata peck kafin ya juya ya fita Mummy tabi shi da kallo tana cigaba da smiling..zata iya rantsewa rabon da ta ganshi cikin farin ciki irin wnn har ta manta..fatanta bai wuce Allah ya daidaita tsakaninshi da yarinyar ba..ta fuskanci so ne yakeyi mata matsananci. Washegari ringing din wayanshi ne ya tada shi daga baccin da ya koma bayan yayi wanka...ya mike zaune a hankali yana murza ido ya dakko wayan ya daga tareda karashi a kunne ba tareda ko sunan wanda ke kiran ya duba ba..muryan waziri yaji yana fadin"Attahiru"..da sauri ya wartsake daga baccin yana sake rike wayan da kyau yace"Baffa kaine?.."Waziri yace"nine Attahiru..ya kukaje gida?.."yace"mun sauka lafia Baffah..ya kafin jiki?.."yace"jiki yayi kyau sosai cikin satin nan nake sa ran komawa Gombe..ya mahaifiyar taku take?.."yace"tana lafia Baffa..na fada mata sakonka kuma tace ta yafe maka duk abunda ya faru"..waziri yace"nagode sosai amma dukda haka ka kai mata Waya inason mgn da ita"..da sauri ya diro daga gadon yana fadin"ohk bari in bata"..daga haka ya fita zuwa flat din Mummy...a bedroom dinta ya sameta ya mika mata wayan da sauri yana cewa"Mummy Waziri ne ke mgn"..a hankali ta karba wayan tareda komawa ta zauna kan sofa tana gaisheshi...ko gaisuwar nata bai amsa ba ya shiga bata hakuri da neman yafiyarta kan duk abubuwa daya aikata mata a baya...nan da nan Mummy data fara hawaye tace ta yafe mishi dunia da lahira dama ita bata taba rikeshi a rai ba...sun jima sosai suna mgn duk akan abubuwanda suka faru a baya..Mummy tace zataje Abuja da kanta ta dubashi itama yace ba sai tazo ba shima cikin satin nan zai koma Gombe and yanaso ya fara biyowa Kano yaga inda suke...Bobby dai na zaune yana kallon Mummy data kasa dena zubda hawaye har suka gama wayan...mika mashi wayan tayi tana share hawayen idonta tace"ka gani ko Bobby?..yanxu ka yadda da abunda nake fada?.."kama hannunta yayi kafin a hankali yace"na yadda Mummy..shiyasa hausawa suke cewa abunda babba ya gano yaro ko ya hau kan tsauni bazai iya ganoshi ba...ni kaina nayi mamakin irin tarbar da muka samu a wurinshi..ban taba zaton yana sonmu har haka ba sai yanxu Mummy..kuma duk laifina ne dana hana ku mu'amala dasu"..ya karasa mgn da wani irin rauni a muryanshi..kamo hannunshi itama tayi tana kallon cikin idonshi tace"ka bar damun kanka anything happpens for a reason..kilan hakan ya faru ne sbd ya zama darasi wa mutane irinka wanda basu yafe laifi komai qanqantarshi da kuma masu yanke zumunta..yanxun tunda komai ya wuce mu bar tunawa dashi sai muyi duba zuwa ga future kuma"..kissing hannunta dake rike da nashi yayi yana fadin"shiyasa nake sonki Mummy..Allah ya yafe mana baki daya"..tana murmushi ta amsa da Ameen sai kuma tace"kaga yanxu kuna daidatawa da Aysha sai ayi mgnr aure kawai..nasan waziri bazaiki nema maka aurenta ba"..da sauri yace"and Mummy kinsan me?..da Lamido da Waziri fa abokan juna ne?..na hadu dasu a Abuja sunzo dubashi tareda dad dinta"..Mummy tace"ai ba abota kadai ne a tsakaninsu ba..akwai alaqa mai karfi tsakanin ahalin Lamido dana Waziri tun zamanin yarinta..alaqa ne irin na gidan sarauta so inshaAllah bazasuki baka aurenta ba"..Bobby daya kasa dena smiling sbd farin ciki yace"Allahumma Ameen Mummy..Allah ya amsa bakinki"..dungure mishi kai tayi tana hararanshi tace"mara kunya kawai...ya jikin nata ma?.."yace"Mummy ai ke za'a tambaya ya jikinta tunda a flat dinki ta kwana"..Mummy tace"ai nayi tunanin wurinta ka fara zuwa kafin kazo nan"..da sauri ya shiga girgiza kai har yanzu bai dena smiling ba yace"haba Mummy..haka nan sai in fara shiga mata daki this early morning?.."mikewa Mummy tayi tace"ai gwara da bakaje ba sbd kada ka fada mata daki tana bacci..yanxun muje mu duba jikin nata"...baice komai ba ya mike suka fita dan Allah ya sani tun daxu dama yakeson zuwa ya ganta...zaune suka sameta gaban mirror tana shafa cream a jikinta Allah yaso da hijab dinta a jiki da shknn haka wnn mutumin zai gama ganin jikinta...ajiye cream din tayi tareda mikewa a hankali ta koma gefen gado tana kokarin durkusawa tace"Mama ina kwana"..Mummy ta mikar da ita tsaye tana cewa"ki dena wnn durkuson keda baki da lafia..ya kafan naki?.."a hankali tace"yayi sauki"..Mummy tace"kin tabbata yayi sauki?.."ta daga mata kai alama Eh..kamata Mummy tayi ta zauna gefen gadon snn ta isa ga wardrobe din dakin ta dakko wani sabon abaya data ajiye mata nan ciki tun jiya ta mika mata rigar tace"maza ki shiga bathroom kisa sai ki fito muje muyi breakfast koh?.."ba musu ta amsa rigan snn ta juya ta shiga bathroom...bayan mintina uku ta fito sanyeda rigar da yayi matukar amsarta...ta yafa mayafin a kanta sai kyawunta ya fito sosai kmr balarabiya...kallonta kawai Bobby keyi harta karaso ciki ta zauna kanta kasa..dukda ba kallonshi takeyi ba zata iya rantsuwa kallonta yake sbd yanda takejin eyes dinshi na zagayawa a jikinta..ba tareda ta kalli inda yakeba tace"ina kwana"..ko jin abunda ta fada ma baiyi ba hankalinshi gaba daya yayi nisa yana kallonta...saida Mummy ta tabashi snn yayi firgigit ya dawo hayyacinshi yana shafa kai...tace"bakaji ana gaisheka bane?.."shafa kan yacigaba dayi yana dan murmushi yace"am..la..lafia lau"..mikewa Mummy tayi tareda kama hannun Aysha tace"to taso muje muyi breakfast daughter"..ba musu ta mike ta shiga binta suka fita daga dakin Bobby ya sauke wani wawan ajiyar zucia yana cigaba da shafa kai..wai me yake damunshi ne haka?..meke faruwa dashi?..mikewa yayi daga kashe shima ya fita daga dakin...a dinning ya samesu gaba daya...Miemie na zaune kusada Aysha sai zuba mata dan banzan surutu take ita kuma tana murmushi sai ta ganta kmr Husna...karasawa Bobby yayi ya zauna yanata kallon dimples dinta dake fitowa sbd murmushin da take..sai yaji kaman an yaye mashi duk wani baqin ciki da yake tare dashi an musanya mashi da farin ciki..ganin murmushin nan nata kadai ya isa yasa ya mance da duk wani damuwa daya tsinci kanshi a ciki...Anty Sumy da Sab da Mummy sai satan kallonshi suke suna dariya..gaba dayansu zuwa yanxu ba wanda baisan irin son da yake mata ba...Miemie ce tayi serving dinsu kmr kullum snn kowa ya shiga cin abincinshi..Lamido dai a hankali takeci dan ko Allah yasan jinta takeyi a takure wlh..gashi ta baro wayanta a can hostel da ko baby saita kira ya rage mata damuwa..kafanta kuwa ya warke garau sai dan abunda baza'a rasa ba...ita ta riga kowa gamawa amma bata tashi ba saida Miemie ta gama suka mike tare..suna tashin kuma wayan Bobby daya ajiye kan table ya fara ringing..yana dubawa yaga daddy ne ke kira dan haka ya mike shima ya koma parlor ya zauna idanunshi a kanta yayi picking da sallamar..a daya bangaren daddy yace"Ameen wa'alaika salaam Attahir..ya aiki?.."cikeda respect yace"Alhamdulillah daddy..ya naka aikin?.."daddy yace"mun gode Allah..ya jikin Aysha?..daxun na kira wayanta ai Bilkisu ke sanar dani kuna asibiti"da sauri yace"eh tama ji sauki daddy..bayan na gama mata treatment sai na kawota nan gida wajen mahaifiyata ta kwana sbd dare yayi lokacin"...daddy yace"MashaAllah sannu da kokari kaji Attahir..Allah ya maka albarka"..Bobby ya amsa da"Ameen Ameen..bari na bata wayan kuyi mgn"...daddy baice komai ba shi kuma ya mike zuwa inda take ya mika mata wayar...kara tayi tareda kaiwa kunnenta a hankali tace"daddy goodmorning"..yace"morning..ya kafan naki?.."tace"ya warke..daddy ina su Yusra?.."daddy yace"gasu"..daga haka ya mika masu wayan Husna ce ta fara cewa"hello Addah"..Aysha ta saki wani murmushi kafin tace"sunanki Yusra dama?.."a fusace Husna tace"idan bakiyi haka ba ai ba kece Adda ba..ga Yusran nan ai sai kuje kuyita yi"..dariya ta saki wanda bata shirya ba..Husna badai saurin hawa ba wlh..sam bata iya wasa ba...kmr daga sama taji muryan Yusra na fadin"Addatah"..nan da nan ta sake sakin wani murmushi tana cewa"habibty na..ya kike ya school"..tace"lafia lau Addah ya ciwonki?..Adda Billy tace mana baki da lafia kin kwana asibiti"...tana cigaba da murmushi tace"hakane amma yanxu na warke habibty..ina Hamma na?.."tace"Daddy ya aikeshi Bauchi..Ammi ma tace idan zamu tafi Umrah zamu biy.."bata karasa ba taji tayi shiru and zata iya rantsewa dakatar da ita akayi..tana jin muryan Husna a background tana cewa"ke Yusra ba Ammi tace kada mu fada mata ba?.."daga haka kuma sai taji an kashe wayar..ta dagota da sauri tana dubanshi duk ta wani maraifaice ta mika mashi wayan tace"sake kiramin dan Allah"..amsa wayan yayi yana kallon yanda ta tsuke fuskanta yace"wnn kuma na menene?.."da sauri tace"cewa fa tayi wai zasu je Umrah su barni"..yace"kuma saiki yadda da mgnr ta..ba yarinya baice?.."girgiza kai takeyi tace"da gaske ne wlh..ai dama duk Ramadhan muna zuwa..nidai ka sake kiramin inji"..bai sake cewa komai ba yayi dialing number ya mika mata..a maimakon Yusra sai taji daddy ne ya dauka..tayi shiru tana tunanin me zata ce sai taji yace"bakida abun cewa ne?.."runtse idonta tayi tanajin kaman ta rushe da kuka tace"ba..komai"..yace"then sai anjima..Allah ya kara sauki"..daga haka daddy ya kashe wayar shi..itama ta mika mashi nashi tana sake daure fuska kai kace wani gagarumin laifi akayi mata...tasan wlh da kyar idan ba da gaske Umran zasuje ba..ai dama suna zuwa da azumi and idan ba mantawa tayi ba yau baifi saura one week a fara azumin ba...ta rufe fuska da hannayenta kmr zata fara kuka Bobby yayi saurin rike hannayen nata yana girgiza mata kanshi yace"dont cry plss..inshaAllah ba inda zasuje su barki"..bata iya cewa komai ba sai bude fuska da tayi nan kuma yaga ba kukan takeba...daidai nan su Mummy suka shigo parlorn ganin yanda taci kunu Mummy tace"Subhanallah meya faru haka?."a hankali yake duban Mummyn yace"wai 'yan gidansu zasuje umrah banda ita"..Mummy ta zauna nan kusada ita tana dubanta da kyau tace"haba stop frowning ur face mana daughter ba sai Azumi zaaje umran ba?.."Aysha ta gyada kai alamar Eh..Mummy tace"then don't cry inshaAllah baza suje su barki ba kinji?..kiyi hakuri"...su aunty Sumy dai na zaune suna kallon ikon Allah..cikin ranta fadi take"lallai Bobby zaiyi fama da shagwaba a wurin nan"..shi kuwa gogan kallonta kawai yakeyi yana mamakin yanda batayi kuka ba..shidai Allah ya kawo ranar da zaiga ta dena saurin kukan nata..ya rasa wace irin shagwabace da ita wlh...bayan ta dan saki fuskanta ya mike zuwa Flat dinshi ya sake shiryawa ya fito...har lokacin suna zaune parlorn sai janta da hira suke...yana duban iwacth dake hannunshi yace"Mummy bari in maida ta hostel in dawo"..Mummy tace"dan wuri haka?..baka bari sai zuwa yamma?.."yace"gwara in maida ta yanxu sbd kada tayi missing lectures dinta..ba dadewa zanyi ba ina ajiye ta zan dawo"...Mummy tace"to shknn Allah ya tsare..Aysha sai yaushe kuma?.."shiru tayi kanta a kasa..Mummy dake murmushi tace"idan inason ganinki zan cema Bobby ya kawoki mu gaisa..Allah ya kara sauki kinji?.."a hankali tace"Ameen..nagode Allah ya kara girma"...da murmushi Mummy tace"babu komai daughter"..juyawa tayi ga aunty Sumy itama tayi mata godia..duk suka bita da adduan samun sauki snn Miemie tayi mata rakia har compound bayan sun cikata da abubuwa iri iri...driver dake zaman jiranshi a compound yana ganin fitowarsu ya mike da sauri zuwa inda motar da zasu fita yake...Bobby na karasawa ya mika mashi hannu yace"bani kyes din kayi zamanka yanxu zanje in dawo"..da sauri ya mika mashi key din tareda komawa ya zauna..shi kuma ya bude motar ya shiga itama ta shiga bayan Miemie ta sa mata kayanta a booth yaja motar suka tafi...baisan meyasa sam bayason driver yayi driving dinshi idan yana tareda ita ba..gani yake kaman zaiyita kallonta ne ta mirror shi yasa yafi gane yayi driving da kanshi idan yana tareda ita...har suka iso hostel babu wanda yace komai a ciki su...ta bude motar zata fita bayan tayi mishi godia ya dauko ledan wani magani ya bata yana cewa"kici gaba da shafawa a kafan har zuwa lokacin da zai dena ciwon"..karba tayi tace mishi"nagode"..ba tareda kallonshi ba..shi kuma kallon nashi yakeso tayi amma sam taki yin Hakan kmr dai tasan yanda yake son ganin fuskanta da kyau...bai takura ta ba yace ta shiga ciki tasa uniform sai ta fito ya ajiyeta area classes..ba musu ta shiga ciki tasa uniform din snn ta fito ya sake maidata cikin school din...har wajen class dinsu yayi parking snn ta bude motar ta fita bayan ta sake mishi godia shi kuma yaja motar ya koma gida. Tun daga wnn lokacin ta fara bashi cold attitude..ba wai dena kulashi tayi ba saidai kwata kwata ta dena sakewa dashi...zataje har office ta gaisheshi kmr yanda ya bukata amma fa bai cika ganin dariyarta ba...haka zatayi duk wani abu daya sata amma dai bazai ga walwala da farin cikinta ba...ya rasa me yayi mata take bashi wnn traetment din don ko Allah yasan ba karamin damuwa ya sakashi a ciki ba...tun yana tambayan if yayi mata wani abun ta fada har ya hakura ya bar tambaya sbd amsa daya kullum take bashi shine ba komai...duk hakurinshi saida ta bashi haushin dan haka shima yayi alkawarin cigaba da treating dinta yanda takeso tunda ita batasan mutunchi ba...ita kuwa tanayi mishi haka ne ba don komai ba sai dan abubuwa biyu data fahimta tare dashi..cikin dayan biyu dole za'a samu daya..ko dai sonta ya farayi kmr yanda su Billy ke fadi ko kuma mutumin banza ne shi kmr yanda tasan yawanci inyamurai haka suke...wnn dalilin yasa ta daukan ma kanta alkawarin yin baya baya dashi sbd gudun koma mene a cikin zuciyarshi gameda ita don itadai tasan ko daura mata shi akayi a kafa zata kwance don ko kusa baya daga cikin jerin mazajen da takeso...kuma da taga shima ya fara sha mata kamshi sai abun yayi mata dadi dan dama so take ta yadda kwallon mangoro ta huta da kuda. Har aka fara azumi suna a wnn halin yayinda ita Lamido take harkokin gabanta hankali kwance don har mantawa takeyi dashi..shi kuma yana can zuciyarshi na neman bugawa sbd tarin matsalolin da sukayi mashi yawa...bai taba tunanin haka ya damu da yarinyar nan ba sai yanxu..ya damu da abubuwanda takeyi mishi fiyeda tunanin mai karatu...rayuwar kawai yakeyi a haka ba don yanajin dadinta ba..ya zamana baijin dadin duk wani abu sbd wnn attitude da take bashi...gani yake idan bai samu daidaitawa da itaba yana iya mutuwa amma taurin kai bazai barshi yayi abunda ya kamata ba...ya gwammace idan ma mutuwa zaiyi ya mutu akan dai ya cigaba da binta tana walakantashi haka. Ranar da aka kai azumi na goma ana gobe zasu fara exam din first semester daddy yace yana son idan ba damuwa Bobby ya kawo mishi ita airport suyi sallama sbd daga Kano zasu tashi...baiyi musu ba amsa mishi da zai kawota saidai cikin ranshi yana tunanin yanda tafiyan nasu zai kasance bayan ba wani jituwa sukeyi ba yanzu...ranar da safe ya danna mata kira abunda shi kanshi ya manta yaushe rabon daya kirata...tana dagawa ko sallamarta bai amsa ba yace"ki shirya zanzo daukanki by 1..ur dad wants to see u"...yana gama fadin haka ya kashe wayarshi ko tsayawa jin amsarta baiyi ba...yana yi mishi ciwo idan ya tuna yanda take treating dinshi kmr wani stranger...kilan dan taga ya fara damuwa da ita take mishi haka so Its better ya koma old self dinshi yanda zasufi daidaitawa da kyau. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 38 Karfe dayan nayi kuwa ya kama hanyan FCNM...tareda da driver dinshi suke amma haka nan ya sallameshi sbd baison ya tukashi if suna tareda ita...yana isa makarantan ko ciki bai shiga ba yayi parking daga nan waje snn ya kira yace ta fito ta sameshi bakin gate...duk yanayin haka ne sbd jin ciwon shariyar data tsiri yi mash...da tasan yanda ya damu da ita da batayi mishi haka ba wlh...ita kuwa shiryawa tayi cikin long doguwar rigarta na wani cotton material orange da qananun flowers lemon green a jiki...bata sa dankwali ba as usual tayi rolling dan karamin veil dinta daga kai zuwa shoulders dinta...bata dauki bag ba sai phone dinta a hannu snn ta saka flat shoe dinta ta fita tanata mitan ya sata tafiyan kafa..da bestie na nan ne tasan batada matsala duk inda tace ya kaita zai kaita amma now that he is not around dole ta zage ta koyi tafiya da kafafunta tunda dai tasan baby bazai yiwu ya dinga kaste aikinshi yana zuwa kaita ko ina da ina ba...kafin ta bar first gate dinsu taga wani mota yazo ya wuceta da gudu sai kuma taga yayi slowing down tareda yin reverse ya dawo inda take...dauke kanta tayi kmr bata gani ba sai taji wanda ke cikin motan yace"Hajia Lamido"..dan juyawa tayi tana kallonshi sai kuma ta saki murmushi ganin shine tace"Tajuddeen ashe kaine"..yace"yeah nine..ina zakije haka a kafa?.."tace"cikin college zan shiga wlh"..yace"amma why bazaki kira bus ya kaiki ba?.tafiyan akwai nisa fa"..dan murmushi kawai tayi batace komai ba...hannu yakai ya bude mata kofan kafin yace"to bari nayi dropping dinki"..girgiza kai tayi da sauri tana cewa"no nagode"..kallonta yake sosai yace"i insist..if kina tunanin wani abu ne ki dena don na dade da hakura ni kam..nasan ba sona kike ba amma for this once ki bari na taimaka maki"..bata sake mashi musu ba ta karasa ta shiga motar shi kuma yaja suka wuce...ganin bata ga motarshi a premises ba tace ya fita da ita waje kilan ta sameshi a can...suna fitowa kuwa ta hango motar nashi a tsallaken titi dan haka yayi dropping nata ta tsallako titin...tunda ta fito daga motar yake kallonta bacin ranshi na sake karuwa fiyeda wanda yake ciki already...wato da yace ta fito shine ta kira one of samarinta ya fito da ita sbd batada hankali...ta zauna gaban motarshi tanata washe mashi baki sbd batasan ciwon kanta ba ga wani shegen riga da tasa da bai gamsheshi ba sam..gaba daya rigan ya bayyana surar jikinta instead of tasa hijab shine ta dakko wnn dan veil din tayi rolling sbd rashin nustuwa...ranshi yaji yayi wani irin 6aci baisan lokacinda ya hada kan nashi da starring motar ba...yana rantsuwa da Allah idan har yarinyar nan zata cigaba da abubuwa haka mutuwa zaiyi...yasan for sure ko wulakancin da take mashi bai kasheshi ba to duk ranar da aka daura mata aure da wani nashi ya kare...a yanda yakejin zuciyarshi tamkar tana dab da fashewa ne sbd ciwon da yakeji cikinta ya fara mishi yawa...kiri kiri wai kana son mutum shi kuma baya sonka wani yakeso...duk ya tunada wnn abu sai yaji kmr yayi commiting suicide ya huta...har ta karaso inda yake bai iya dago kanshi ba..ganin tanata knocking ko dagowa baiyi ba kawai ta bude motar ta shiga fuska daure kmr wanda tayi ido hudu da makiyinta...duk abunda take yana jinta amma ko dagowa baiyi dan shi kadai yasan what is taking place in his heart...addu'o'i yayita karantawa iri iri har yaji ya dan samu relieve snn ya dago kan nashi ba tareda ya kalleta ba ya tada motar suka tafi...a hankali ta dan saci kallonshi taga fuskan nan a dinke kaman na saniya dan haka ta shafawa kanta salama tayi kasa da kanta tareda cewa"ina yini"..ko kallon inda take baiyi ba balle tayi tunanin samun amsa daga wurinshi...ta tabe baki tana gyara zamanta dama ba gaisheshi tayi dan ya amsa ba dan rainin hankali kawai...haka suka cigaba da tafiya in silence har suka isa Malam Aminu Kano International Airport...mamaki ya cikata ganin airport ya kawota ko me zasuyi a nan kuma oho?..bata dai tambayeshi ba tanaji bayan ya gama parking ya dauki wayanshi yayi dialing number daddy...bayan ya dauka Bobby yace"mun iso airport din sir"..daga daya bangaren daddy yace"muma gamu nan shigowa ciki yanxun nan"..daga haka ya kashe wayarshi snn ya bude motar ya fita...itama ta bude daya side din ta fita...suna fita kuma motan daddy yazo yayi parking a kusada nasu...ta wani zare ido tana kallon motar kmr bata taba ganinta sbd mamaki...kenan daddy ne yace ya kawota airport zasuyi tafiya ne ko kuma yaya abun yake?..daddy ne ya fara fitowa daga motar sai Ammi sai Husna da Yusra suma suka fito a tare...da sauri ya karasa inda suke yana kokarin durkusawa daddy yayi saurin kama hannunshi ya hada da nashi sukayi musabiha yana fadin"bana hanaka durkuson nan bane Attahir"..murmushi kawai Bobby ya saki kanshi kasa yace"barka da isowa"..daddy yace"barka dai..ya aiyuka?.."kai a kasa yace"Alhamdulillah sir"..sake kama hannunshi daddy yayi yana nunawa Ammi yace"to Maimunatu yau dai gaki ga Attahir"..ya juya yana duban Bobbyn shima yace mishi"itace Maman Aysha"..kokarin durkusawa ya sakeyi still daddy ya hanashi...ba yanda ya iya haka nan ya mike saidai ko kusa ya kasa dago kanshi ya kalleta a hankali yace"Ina yini"..Ammi dake kallonshi tana murmushi tace"lafia lau Attahir..ya aiki ya kuma akaji da fama da Aysha?.."murmushi kawai ya saki kanshi a kasa...daddy ya sake nuna mashi su Husna kafin yace"ga sisters dinta nan..wnn sunanta Asma'u karamar kuma Yusra"..kallonsu Bobby ya shiga yi yana murmushi..Husna ta fara gaisheshi snn Yusra duk ya amsa musu smilingly...yaji gaba daya ahalinta sun shiga ranshi don sunada karamci sosai...ita kuwa Aysha da tayi mutuwar tsaye tun daxun tana kallonsu sai yanxu ta samu sararin karasawa inda suke hankalinta duk ya tashi kar ace tafiya zasuyi ba tareda ita ba tac"daddy sannunku da zuwa"..daddy yace"yauwa..ya karatun?.."tace"fine daddy gobe zamu fara exams"..yace"Allah ya bada sa'a"..ta amsa da Ameen snn ta juya tana kallon Ammi jiki a sanyaye tace"Ammi ina yini"..itama ta amsa mata da"lafia lau..ya mkarantan?.."tace"fine..Ammi tafiya zamuyi?.."murmushi Ammi ta saki gamida girgiza kai tace"tafiya zamuyi dai..keda zaki fara exams waye zaiyi tafiya dake?.."nan ta marairaice tace"Ammi dan girman Allah zanje kinga ko last year ma da banje umrah ba..kuma ai Friday zamu gama exams din"..kafin Ammi tayi mgn daddy yace"yanxun ma ba cewa akayi bazaki jeba ai..zakije amma sai kin gama exams dinki zaku taho tareda Najeeb"..shiru tayi batace komai ba itadai Allah ya sani tafi son ta tafi tare dasu...Yusra ce ta matsa kusada ita kmr zatasa kuka tace"daddy nima zan zauna da Adda"..daddy yace"no itada take makaranta a ina zata ajiyeki"..da sauri ta sake cewa"daddy nidai zan..."bai bari ta karasa ba yace"stop it Yusra bazaki zauna nan ba"..ba musu tayi shiru tana turo baki Ammi dai kallonsu kawai take tana murmushi...hannun Bobby daddy ya kama yace"zo muyi mgn son"..ba musu ya bishi a baya...Aysha kmr jira takeyi su bar wurin ta matsa kusada Ammi kmr zatasa kuka tace"Ammi dan Allah ki cema daddy ku jira in gama exams plss"..harara mai kyau Ammi ta watsa mata kafin tace"sbd ke kika haifemu sai mu zauna zaman jiranki ki gama exams koh?..idan kika cigaba da damuna wlh gaba daya zan soke tafiyan naki saiki koma gida ki jiramu kafin mu dawo"..ta wani tale baki kmr zata sa kuka tace"kai Ammi dan Allah"..harara ta kuma watsa maka before tace"just dare me and see what will happen..keda har yanxu bazakiyi hankali kisan kin girma ba"...shiru tayi bata sake mgn ba sai turo baki da take...juyawa tayi taga yanda suke mgn cikin kwanciyar hankali har wani smiling taga sunayi duk su biyun cikin ranta tace"ai dole kayi daria tunda kana neman shiga tsakanin da mahaifina..mugu dakai kawai"...bayan kmr 5 mins suka dawo wurin...Bobby yayi sallama da Ammi dasu Husna snn ya bar wurin...itama Aysha sallamar tayi dasu idonta har ya ciko da hawaye ta juya zuwa inda yayi parking...tana bude motar ta shiga saita hada kai da guiwa ta shiga sauke numfashi...Bobby yayi shiru yana kallonta baidai ce komai ba...lumshe ido yayi ya jingina da kujera yana jin wani irin zafi na neman rufeshi...wai after duk wulaknci da ignoring dinshi da take still bayason ya ganta cikin damuwa...ya rasa wani irin al'amari ne wnn ace wai duk bata maka rai da mutun zaiyi even for once bazaka iya fita sabgarshi ba...ko kuka yaga tanayi sai yaji kaman da idanunshi takeyi...baya son jinshi ko kadan kuma yasan ko yayi mata mgn ma zaiyi wahala ta dena..baisan meyasa ta tsaneshi to this extent ba...bude idonshi yayi a hankali tareda tada motar suka bar cikin airport din...driving yakeyi a hankali yanajin yanda har yanxun kukanta bai bar taba zuciyarshi ba...ganin abun nata bana kare bane sai ya gangara gefen titi yayi parking shima ya hada kanshi da starring motar yana sauke numfashi...duk duniyar sai yaji tayi mashi wani irin kunchi da zafi da baisan daga ina hakan ke fitowa ba...saida ya dauki lokaci mai tsayi a haka kafin ya dago kan nashi da kyar yana kallonta...cikin muryanshi da yaji ya disashe all of a sudden ya kira sunanta"Aysher"...banza tayi dashi bata amsa ba kuma bata dago kanta ba..ya sake kiran sunan nata still bata amsa ba baisan lokacinda cikin karaji yace"idan baki denamin kuka a mota ba saukeki zanyi wlh..are u small kid da zakisa mutum a gaba da kuka sbd an tafi an barki.."..shiru tayi still bata dago kan nata ba..da karfi yakai hannunshi ya dago fuskan nata sai yaga ko digon hawaye babu..iskanci ne kawai yasa tayi hakan ashe ba kuka take ba..kallon cute face din nata ya tsaya yi without blinking...rabonshi daya kalli face dinta haka har ya manta..a hankali yaji wani irin nutsuwa na sauko mishi sbd ganin fuskan nata...ya lumshe ido yana sake budeshi kan face din nata da har dunia ta nade yasan bazai taba gajiya da kallonta ba...sai ya nemi duk wani haushinta da yakeji ya rasa..baisan ko magic take using a kanshi da baya taba iya dogon fushi da ita ba..duk yanda zata kai da bata mashi rai yana kallon face dinta sai yaji ya yafe mata komai sbd tsabar farin cikin da kallon fuskan nata ke sanyashi musamman idan tana cikin farin ciki...lokaci daya kuma ya dauke idonshi daga kanta ya wani sake dinke fuska snn ta tada motar suka cigaba da tafia...wani babban super market taga yayi parking yace ta jirashi nan ciki snn ya fita daga motar...bayan few minutes ya dawo da babban leda a hannunshi yasa back seat snn ya shiga ya tada mota suka cigaba da tafia....ko a hanya bai iya cikakken minti uku ba tareda ya juyo ya kalleta ba...haka nan sai yakejin ganin nata na tafiya da duk wani kunchi da damuwarshi...babu wanda yayi mgn har suka isa FCNM Hostel...daidai gate dinsu yayi parking kafin ta bude motar ta fita yayi saurin dauko ledan daya ajiye a baya ya mika mata cikin wani irin kaushin murya yace"ina iya neman wani alfarma wurinki?.."juyawa tana kallonshi wai alfarma zai nema shine fuskanshi cunkus haka..kai kawai ta daga mashi alamar eh...ledan ya sake mika mata kafin yace"hijabai ne nan ciki..inaso ko dan darajar amanarki da mahaifinki ya bani ki dinga sawa idan zaki fita..ko cikin college zaki shiga ki dora akan uniform dinki idan kinje class sai ki cire tunda na fuskanci ke har yanxu bakisan ciwon kani ba"...kallonshi kawai takeyi kmr mai tunanin wani abu sai kuma can ta numfasa tareda karban ledan da yake miko mata tace"nagode"..da sauri yace"banji kince zaki na sawa ba"..a takaice tace"zan sa"..ya saki wani murmushi yana binta da ido yace"nagode"..komai bata sake cewa ba ta bude motar ta fita shi kuma yayi relaxing nan ciki yana kallonta har saida ta shiga ciki snn yaja motar yayi reverse ya wuce. Ranan Thursday suna kwance hostel bayan sun fito daga exams kowa tana fama da azuminta musamman Lamido da sai juyi takeyi kan gado wai tanajin yunwa...sbd tsabar haushi Billy ko tanka maka tabayi ba har ta gama surutunta ta hakura...tana nan kwance har bacci ya fara daukanta taji wayanta na ringing...hannu ta mika ta dauko wayan daga kan study table dinta tareda dagawa takai kunne...muryan Sa'eed taji na fadin"my bestyyyyyy"...wani irin mikewa zaune tayi da sauri tana zare idanu tace"besty is this really you?.."full of excitement yace mata"its me besty...ur very own best friend"..tun kafin ya rufe baki ta wani turo baki tace"ba wani my very own best friend..yanzu tsakani da Allah haka ake rayuwa besty?..tunda ka tafi ba hello ba hy kaman dama ka gaji damu"...tana rufe baki shima yace"dadina da besty rigima wlh..to yanxu dai ku fito gani bakin gate ina jiranku".. sake zare idanuwanta tayi tamkar wanda tayi gamo da aljani tace"are u serious besty?."yace"come outside mana zaki gani ai"..daga haka ya kashe wayar ita kuma ta diro daga kan gadon ta rarumi hijab dinta ta zura snn ta karasa gadon Billy ta fara tashinta daga bacci...a fusace ta mike zaune tana cewa"Lamido wai meye baka plss?..meyasa bakyaso kiga nayi bacci a hostel din nan"..kama hannunta Aysha tayi ta mikar da ita tsaye ta dauko mata hijab ta mika mata snn tace"wai besty ne yazo yana bakin gate..kinji dan rainin hankali zaizo ko fada mana baiyi ba"...tabe baki Billy tayi tana kokarin momawa gadonta don sake kwanciya tace"kuma shine zaki tasheni daga bacci sai kace besty na ne yazo?.."sake kamata Aysha tayi ta shiga turata waje tana cewa"ai wlh baki isaba sai kinje"..daga haka ta ja hannunta suka fita daga dakin bayan Billy ta zura hijab dinta itama...suna fita suka hangoshi daidai inda ya saba tsayuwa idan yazo dan haka suka nufi wurin da sauri...har suka karaso inda yake kallonsu yakeyi yana murmushi...bai taba sanin da akwai friendship irin wanda yake tsakaninshi da su biyun nan ba...jinsu yake a jikinshi tamkar sun zama family...suna karasowa Lamido data wano hade girar sama dana kasa tace"nidai ba kulaka zanyi ba wlh"..murmushi ya saki kafin yace"idan besty taki kulani kuma ai sai in samu matsala..yanxun kiyi hakuri mu zauna sai in fada maku uzuri na nasan kema idan kikaji zaki hakura ki dena fushi"...ba musu gaba daya suka nufi inda suka saba zama nan cikin hostel din as usual...bayan sun zauna ya shiga musu bayanin tafiya sukayi zuwa Canada tareda Dad dinshi shine dalilinda yasa basu samunshi a waya...shima kuma bai samu yayi roaming ba and bai hau social media ba har suka dawo shiyasa sukajishi tsit kmr baya existing...kmr yanda ya fada kuwa nan da nan ta sauko daga fushin nata sai kuma aka hau labari na yaushe gamo..hatta Billy da ba wani dasawa sukeyi ba yau labari na musamman sukeyi dashi sbd missing juna da sukayi...bashi yabar hostel din ba sai around 4 yace su shirya kafin magrib zaizo ya daukesu su fita don akwai special iftar daya hada masu for the three of them...murna wajensu kmr ba gobe haka suka koma hostel kowa ta fara shirin fita tunda yace before magrib din zaizo yayi picking dinsu. 6 nayi kuma yazo yayi picking dinsu sai Cilantro...wurin har wani decoration yasa akayi mashi specially for them dama already yayi reserving so daga su sai su zasuyi iftar dinsu...tun kafin asha ruwa aka cika masu gabansu da kayan ciye ciye iri iri...sunata hiransu abunsu har aka kira sallah Sa'eed ruwa kadai yasha ya wuce masallacin dake nan ciki yayinda su kuma suka gabatar da sallahrsu a inda suke...yana dawowa suka shiga iftar dinsu hankali kwance kowa ka gani cikinsu is full of happiness and excitemet sbd kada cewa tareda junansu after a long period of time...Sa'eed sai snapping dinsu yakeyi wani su biyu kadai wani kuma yayi musu selfie gaba daya..a takaice sunyi having fun dinsu yanda ya kamata suna barin wurin kuma ya kaisu gidan Hajia nan ma taji dadin gani su sosai daga nan kuma yayi musu siyayyan kayan kwalam snn yayi dropping nasu a hostel as usual. A daren ranar Dr Bobby yana parlonshi yana karatun Qur'ani kiran daddy ya shigo wayanshi...ajiye alqur'anin yayi tareda dagan wayan da sallama..bayan sun gaisa daddy yace"wani nauyin dai zan sake dora maka son Allah yasa bazaka gaji dani ba"..da murmushi Bobby yace"not at all sir..ka fadi kome kakeso zaayi inshaAllah"..cikeda jin dadin amsan daya bashi daddy yace"nagode sosai Attahir...mgnr Aysha ne dama gobe zasu gama exams koh?."yace"yeah gobe zasu gama"...daddy yace"so nake if it's ok by you ka kaita wajen mahaifiyarka ta kwana biyu zuwa sunday wanda zasu tafi dashi ne har yanxun Passport dinshi bai zama ready ba amma yacemin zuwa sunday komai zai zama ready inshaAllah..banson ta koma Gombe ne snn ta sake dawowa Kano tunda dole ta kano flight dinsu zai tashi"...da sauri Bobby yace"no problem sir..zan kawota inshaAllah"..daddy yace"i hope dai ba wani matsala koh?.."yana gyada kanshi yace"babu wani matsala inshaAllah"..murmushi daddy ya kara saki kafin yace"to nagode sosai Attahir..zuwa sunday din komai inshaAllah zai zama ready ita dama passport da visa dinta duk basuda matsala so ticket kawai zaa sai mata"...gyada kai kawai yakeyi yama rasa abunda ya kamata yace...sallama sukayi snn daddy ya kashe waya..shima ya ajiye nashi yana sakin wani numfashi da karfi gamida dafe kanshi...farin ciki ya kamata yayi sbd zata dawo kusa dashi amma what he's feeling is not close to farin ciki at all...yasan zamanta a kusa dashi din ba abunda zai amfaneshi dashi saima karin damuwa da zai sanya mishi tunda yasan ba sonshi takeyi ba...duk sai yaji damuwan da ya fara raguwa a tare dashi yana neman dawowa sabo...dunia yanxu babu abunda ke bata ranshi kmr idan ya tuna yarinyar nan bata daukeshi a bakin komai ba bata kaunarshi...dukda har yanzun ba bai furta mata yana sonta ba yasan ko a can kasan zuciyarta babu wani abu makamancin sonshi shiyasa idan ya tuna haka yakejin kmr zai hadiye zucia ya mutu...ganin damuwan na nema yi mishi yawa sai ya dauki alqur'aninshi yacigaba da karatun da yakeyi...nan take kuma yaji ya samu saukin damuwar daya fara rufeshi. Washegari bayan ya gama shiryawa kafin ya fita ya nufi Flat din Mummy dan sanar da ita yanda sukayi da daddy jiya...tana zaune itama tana karatu ya shigo dakin..ya karasa kusada ita ya zauna har takai aya snn ta rufe Qur'an din tana dubashi tace"har ka fito?.."yace"na fito Mummy..dama wata mgn ce nazo muyi dake"..Mummy tace"to ina jinka"..saida ya lumshe ido ya bude kafin a hankali yace"baban Aysher ne dama yace in kawota tayi kwana biyu a nan wai wanda zasu wuce Saudi dashi passport dinshi bai gama zama ready ba"..full of excitement Mummy ta wara idanu tana cewa"da gaske?..to Allah ya kawota lfy yaushe zasu gama exam din?.."a takaice yace mata"yau"..sake wara idanu tayi tana murmushi tace"to Allah ya kawota lfy kace mishi babu wani matsala zatayi zamanta tare damu a nan"...kallonta kawai yakeyi ganin how happy she is kawai sbd zatazo gidan tayi kwana biyu...baisan meyasa ba shidai tun jiya da aka fadi mgnr nan yakejin jikinshi wani iri kmr dai ba nashi ba...Mummy ta kamo hannunshi tana dubanshi da kyau tace"wnn damuwan kuma na menene Bobby?.."dan matsala yayi ya dora kanshi kan shoulder dinta murya can kasan makoshinshi yace"bata sona Mummy..har yanxun bata kaunata dan Allah Mummy me zanyi mata ta soni..ko bai kai yanda nake sonta ba at least itama ta soni"...Mummy dake rikeda hannunshi tace"inaji a jikina zaka auri yarinyar nan kawai ka kwantar da hankalinka"..sake lafewa yayi a jikinta yace"na gaji ne Mummy..na gaji da chasing dinta tana nuna banida muhimmanci a wurinta..Allah kadai yasan halin da nake ciki these days ko bacci wahala yakemin..ji nake idan abubuwa suka cigaba da tafia a haka mutuwa zanyi"..girgiza kai Mummy ta shiga yi tace"nace maka ka dena fadin haka amma ba kaji..ajiye duk wani pride and ego dinka zakayi a gefe ka fada mata how feel..tell her that you love her and you can die for her amma ba kazo kana tambaya yanda zakayi ba"..lumshe ido kawai yayi yana sauke numfashi da kyar..baisan meyasa when it comes to love yakejin brain dinshi na toshewa ba..gaba daya sai yaji ya rasa me ya kamata yayi...abu daya daya sani shine ya dena chasing dinta infact yama dena nuna yana son nata tunda batasan yanayi ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ta fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 39 The next day which is Friday tunda suka fito daga exams Lamido keta trying number din Hamma amma bai shiga...duk ha kalinta yabi ya tashi kada dai ace shima wucewa yayi ba tareda ita ba...ta dubi Billy dake zaune kusada ita kmr zatayi kuka tace"Billy anya kuwa ba binku zanyi mu tafi ba?..kinga fa wayar Hamma har yanxun bai shiga ba"..Billy tace"tunda kika ga bai shiga ba kilan wani abun ne ya faru shiyasa nace ki kwantar da hankalinki kinsan Hamma bazai iya wucewa ya barki ba"..ta bude baki zata sake mgn wayarta ya shiga ringing ta duba da sauri don a tunaninta ko Hamman ne amma sai taga proprietor..dan bata rai tayi tana turo baki tayi picking call din ba tareda tace komai ba...shima sai yayi shiru na dan wani lokaci kafin yace"are u done with the exams?.."a hankali tace"eh.."yace"am coming right away to pick u up..if u like kije ki shiga motan saurayi kiga abunda zan maki"..yana gama mgn ya kashe wayarshi..itama ta ajiye nata tana 'yan mitocinta..Billy dake sauraronta tace"me yace wai?.."rai a bace tace"wani wai he's coming to pick me up ko gidan ubanwa zai kaini oho?..na fara gajia da halin mutumin nan wlh..mutum sai shegen zafin rai"...murmushi Billy ta saki kafin tace"ni salon love dinshi nema yake burgeni"..da sauri Aysha ta juya tana kallonta fuska a daure tace"what do u mean?.."girgiza kai Billy take tana cigaba da murmushi tace"aah ba abunda nake nufi nikam..kidai cigaba da rainama kanki hankali"...sake dinke fuska tayi ta cika tayi fam tace"kinga Billy bana son irin wnn abun da kikemin..na meye zaki dinga hadani da mutuminda kinfi kowa sanin yanda na tsaneshi"..har yanxu Hajia Billy bata bar smiling ba tace"shine nace kici gaba da rainama kanki hankali ai..kiri kiri kinsan mutumin nan sonki yake amma kina wani nuna baki saniba kina raina mana hankali kawai..continue deceiving yourself"..kallonta Aysha keyi fuskan nan ba sarari kmr zatasa kuka...dunia ba abunda ta tsana kmr wani ya bude baki yace proprietor sonta yake hakan ba karamin bata mata rai yakeyi ba...ita kuma Billy da gayya ma take mata haka sbd tasan yanda ta tsaneshi..idan ma ba wulakanci ba ta ya za'a kalli tsabar idonta ace wnn mutumin wai yana sonta..bayan duk wulakancin da yake mata shine mutane har suke da bakin cewa yana sonta?..ita bata taba ganin inda akayi soyayya haka ba..a iya saninta dai idan mutum na sonka baison bata ranka amma fa shi ko yanxu daya kirata a wani tsatstsaye ya fada mata mgn babu irin tausasa murya amma still sukeda bakin cewa yana sonta sbd basuda hankali...wnn dalilin ne yasa shi kanshi take dauke mashi wuta dan sai tayi sati bataje inda yakeba sbd kwata kwata bata son yanda mutane ke tunanin soyayya sukeyi...Billy kuwa kallonta kawai takeyi tana kunshe daria..al'amarin Lamido ba karamin daria yake bata ba wlh..ai ko makaho zuwa yanxun ya kamata ace yasan Dr Bobby sonta yakeyi amma ita kullum sai taita wani nuna batasan me yake faruwa ba...haka sukaita zaune a wurin babu mai cewa kowa komai ita Aysha na daure fuska yayinda Billy kuma ke daria kasa kasa...bayan wani dan lokaci akazo daukan Billy daga Bauchi nan kuma hankalin Lamido gaba daya ya tashi da taga da gaske Billy tafia zatayi ta barta..to ita ina zata zauna ne wai?..yaushe ne kuma zasu wuce Saudi don har yanxu bata samu mgn da Hamma ba...haka ta rakata har mota sukayi sallama snn suka wuce ita kuma ta koma ciki idonta na cikowa da hawaye...tana kokarin haurawa sama zuwa class dinsu wayanta ya sake daukan ringing...ta dakata da hawa stairs da takeyi snn ta dauka still batace mishi komai ba...a takaice taji yace"where are u?.."tace"Sir ina class"..a dan fusace yace"ni kike jira inzo in sauko dake knn?.."tayi shiru tana turo baki..yace"if u like ki fito nan premises ina jiranki and don't waste my time"..kmr zatasa kuka tace"wai ina zamuje?.."baice mata kala ba ya kashe wayarshi ita kuma ta sauka kasa zuwa premises din tanata banbami cikin ranta...can inda ta hango motarshi ta nufa kai tsaye ta bude front seat zata shiga taji ya daka mata wani tsawa yana cewa"ba nan akace ki shiga ba"..rufewa tayi snn ta bude na baya ta zauna nan kusa dashi driver ya tada motar suka tafi...shiru cikin motar babu wanda ke cewa wani abu a cikinsu...Bobby ya jingina kanshi da kujera tareda lumshe ido yana sauraran heart beat dinshi yayinda ita kuma ta rakube can karshen mota tana kallon window fuskan nan a tamke...kawai tunanin inda zai kaita takeyi..ita batasan meyasa ma Allah ya hadata dashi ba at the first place..kawai gashi nan yasa mutane na tunanin suna soyayya...maimakon gida sai taga hanyar Hospital dinshi ya dauka..ta tabe baki bata dai ce komai ba har suka isa Freedom Specialist Hospital...kafin driver ya bude mashi kofa ya bude ya fito da kanshi...itama ta fito suka shiga ciki..office dinshi ya bude suka shiga ya nuna mata seat yace ta zauna nan ta jirashi theater zai shiga..batace mishi komai ba har ya fita daga office din sai a snn ta bishi da harara tana fadin"da azumin ma mutum bazai dena bakin hali ba..wani wai zai shiga theatre sai kace dai a kanshi aka fara zama doctor bashida aikin daya wuce theatre"...haka tayita zaune nan office din tana jiranshi har kusan magrib bai dawoba duk ranta yabi ya gama 6aci..knn a asibiti yakeso tasha ruwa ko a ina?..kawai yazo ya wani ajiyeta office dinshi kmr wata gantalalliya...har ta cire ran dawowarshita gama sadakarwa yau a nan cikin asibitin zatayi iftar dinta sai kuma gashi ya dawo hajaram majaram dashi kmr wanda ya kwana yana theatre😂bai tsaya wasting anymore time ba yace ta tashi su wuce...su A'i ba musu ta mike tabi bayanshi...suna shiga mota driver ya tayar da ita suka tafi...har suka isa gida ba wanda yayi mgn cikinsu..driver na gama parking ya bude mota ya fita ya rage su biyu a cikin motan..har ya bude shima zai fita sai yaga hankalinta na wani wajen..kallonta ya tsaya yi for like 5 mins kafin ya dauke kanshi a hankali ya bude motar ya fita..ga mamakinshi har ya kama hanyar entrance bata fito daga motar ba..yayi kmr zai wuce ya kyaleta nan ciki sai kuma ya fasa tareda juyawa inda take...bude kofa yayi yana kallonta ba yabo ba fallasa yace"fito"..kallonshi tayi da sauri sai kuma ta shiga duban inda suke taga gidansu ne ya kawota..to me kuma zatayi a gidansu fisabilillahi...kallonta yakeyi har ta gama kalle kallenta snn yace"don't let me repeat myself"..saukowa tayi daga motar tana sake tura mishi baki kmr zai bar muhallinshi...hanya ya nuna mata ta wuce gaba yabita a baya har cikin gidan...a central parlor suka iske auntu sumy da Mummy tsaye suna mgn and bisaga dukkan alamu mgn ne suke mai muhimmanci dan har suka isa kusa dasu basuji shigowarsu ba...Bobby ya dan daga murya yace"Mummyy"..juyowa tayi da sauri tana kallonshi tace"aah har kun karaso?.."bai amsa mata ba sai cewa yayi"me kuke discussing ne haka?.."shareshi Mummy ta nufi wurin Aysha tareda kamo hannunta tana murmushi tace"sannu da zuwa daughter"..Aysha da taji wani irin nauyin Mummyn ya kamata tayi kasa da kai tace"Mama ina yini"..Mummy tace"lafia lau Aysha ya exams"..tace"Alhamdulillah"..Aunty sumy ma ta karaso inda suke da fara'a kafin tayi mgn Lamido tace"Aunty ina yini"..tace"lafia Aysha..ya azumi?.."kai a kasa tace"Alhamdulillah"..anty sumy ta juya ga Bobby daya wani daure fuska tace"wnn bata ran wai duk na menene?.."baice mata komai ba sai juyawa da yayi zai wuce flat dinshi Mummy tace"itama ka rakata ciki ta samu ta huta nasan tana tareda gajia kafin time din iftar ya karasa"..dakatawa yayi da tafiya baice komai ba..Mummy tace ma Aysha"jeki ya rakaki daki ki huta kinji?.."batayi musu ba tabi bayanshi zuwa flat din Mummy...kai tsaye dakinda ta taba kwana ya kaita tana shiga ya juya zai fita tayi saurin cewa"Sir ni yaushe zan tafi?.."baice mata komai ba ya sake taking two steps forwad kafin ya fita ta kuma cewa"to ni banida kayan sawa"..still baiyi mgn ba ya fita daga dakin...flat dinshi ya wuce direct ya shiga bathroom yayi wanka yana fitowa yayi changing zuwa kananan kaya snn ya dauki key din mota ya fita zuwa flat din aunty sumy..alwala ya samu tayo tana kokarin fita daga dakin ya shigo ganin zata fita yaui saurin dakatar da ita da cewa"aunty riga zaki dan bani in kaima yarinyar can tasa"..kallonshi aunty sumy tayi da mamaki tace" kayana ai sun mata yawa Bobby saidai ko na Miemie"..tun bata rufe baki ba yace"na Miemie matseta zasuyi nasan naki shine bazai fito da jikinta ba"..kallonshi ta sakeyi taga yanda ya wani hade rai kawai ta saki daria cikin ranta tana jinjina zafin kishi irin nashi..bata sake cewa komai ba ta isa gaban press dinta ta bude tareda dauko wani peach abaya daya mata kadan ta mika mashi..ya amsa yace"thank u"snn ya fita daga dakin..dakinda ya kaita ya nufa daidai lokacin ta fito daga bayi kenan ya shigo dakin...ta wani runtse ido tareda durkushewa nan kasa cikin wani irin tashin hankali tace"Noooo"..kallonta kawai Bobby ya tsaya yi daga ita sai towel a jikinta..gaba daya jikin nata na digar da ruwa alaman dai daga wanka ta fito..a take yaji wani irin faduwar gaba ya riskeshi...ya shiga kallonta with his eyes wide open tamkar wanda yaga abun tsoro..wani irin abu yaji yana gangarowa tun daga brain dinshi ya shiga yawatawa a cikin jinin jikinshi...gashi kuma ya kasa dauke idanun daga kanta duk kuwa da yanda yake son yin hakan...sai yaji kmr idanun ne suke controlling kansu da kansu ba wai shi yake controlling nasu ba..a hankali yaji legs dinshi sun fara motsi and he know for sure motsawa suke saidai kwata kwata baiyi tunanin tafia sukeyi ba saida ya ganshi a gabanta...hannu ya mika a nutse ya kamata tareda mikar da ita tsaye..ta sake runste idanu gabanta na tsananta faduwa sosai...kallon hannunta dake zagaye da chest dinta yayi har zuwa legs dinta da suke nan kusan duk a waje don towel din iya guiwarta ya tsaya...gabanshi yaji ya sakw faduwa lokaci daya idonshi suka canza launi..wasu baqin al'amura yakejin suna zagayawa cikin systems dinshi da shi kanshi baisan yana dasu ba sai this very moment...numfashi ma da kyar yake iya daukanshi sbd yanayin daya shiga...jin har yanxu baiy mgn ba kuma bai kai hannunshi jikinta ba sai tayi tunanin kilan tafiya yayi dan haka ta bude idanunta aikam tana budewa idanun suka fada cikin nashi...ta wani zare ido ra shiga ja baya kmr zatasa kuka tace"Sir..dan..Allah..ka fita"..bai iya ce mata komai ba sai takawa daya shigayi zuwa inda take...hankalinta ya sake tashi ganin yana biyota tacigaba daja baya har tajita jikin bango alaman taje karshen dakin knn..ta wani manne jikin bangon hawaye na ciko idonta tace"sir i beg of u plss"..ta karasa mgnr hawaye na silalowa fuskanta..da sauri ya sake matsawa dab da ita har jikinshi na gogan nata aiko ta bude baki zata kurma mashi ihu yay saurin dafe bakin da hannayenshi dan yasan tana sakin ihun nan ta cuceshi...fuskanshi ya matso dab da nata yana sakin numfashi da karfi..so yake ya bude baki yayi mgn amma yau sai yaji bakinshi ya kafe kaf ko word daya ya kasa furtawa...wani irin nauyi yakeji cikin heart dinshi tamkar wanda aka dorama mountain a ciki...soyayyarta yake ji yana sake zagawa cikin ilahirin jini da tsokar jikinshi tamkar zaiyi ajalinshi..lokaci daya ta fashe mishi da kuka baisan lokacinda ya lumshe ido tareda hadata da jikinshi ba..wani irin rauni yakeji tun daga cikin heart dinshi har zuwa lips dinshi hakan yasa har yanxu ya kasa bude bakin yayi mgn sai kyakykyawan runguma da yayi mata kmr zai ballata...only Allah knows irin soyayyan da yakema yarinyar nan..he loves her to the core..he loves her to the moon and back amma ita ya fuskanci sam bata kaunarshi...jin yanda kukanta ke kara tsananta sai ya dagota daga jikinshi yayi cupping fuskanta tareda hadata da nashi fuskan har yanxu ya kasa cewa komai...ji yake idan bai furta mata what he have in mind ba yau yana iya rasa ranshi dan abunda yakeji is beyond him..gaba daya oxygen din dakin yaji yayi mashi kadan sbd yanda breathe dinshi ke fita da kyar kmr asthmatic patient...sun dauki tsahon lokaci a haka tana kuka yana aikin share mata hawaye kafin a hankali cikin wani irin murya da shi kanshi baisan yana dashi ba yace"i just..can't hide it..anymore..mutuwa zanyi"..itadai kukanta kawai takeyi tana sheshsheka..a hankali ya sake dago fuskanta ya kuma hadewa da nashi yana kallon cikin idonta da nashi idon dake shinning yace"Lamido ki taimakamin plss..I LOVE U..i love u with my whole heart ki ceci rayuwata dan Allah"..duk kukan da takeyi yana furta kalmar i love u taji kukan ya tsaya cak..ta bude baki tana kallonshi da mamaki dan bata taba zaton abunda zai fada ba knn...ganin yanda take kallonshi kaman wanda yayi sa6o ya sake hade fuskansu pointed nose dinshi na gogan nata yace"yes ina sonki..ina sonki tun ranar dana fara ganinki"..tun kafin ya rufe baki tace"No plss..stop saying this to my face dan Allah"..murya a raunane yace"why..it's what i feel"..da sauri ta toshe kunnuwanta tana girgiza kai tace"stop it plss..bana sonji"..tausayinshi da taji ta faraji yasa batason yacigaba da fada don yana iya raunata mata zucia..kallon yanda take rusa mishi kuka yayi yace"then mutuwa zanyi..i will die for sure"..still kanta tacigaba da girgizawa tana kokarin durkushewa a wurin yayi saurin kamata ya rungume a jikinshi...idanunshi na cikowa da hawaye yace"Aysher ki taimakamin plss..ni kadai nasan yanda nakeji a kanki..inajin ciwon ganinki tareda wani fiyeda yanda nakeji idan kina wulakanta ni..i love u so much"..tureshi ta shiga yi daga jikinta tana dukan chest dinshi amma kememe yaki sakinta kmr wani magnet...saida ta gama dukan kirjin nashi dan kanta snn ya kamata suka zauna gefen gado ya sake hade fuskanshi da nata yace"stop crying plss..sorry if i hurt u amma it's what i feel..Aysher idan kikace bazaki aureni ba mutuwa zanyi..zucia ta bazai iya juran ganinki in the arms of another ba..ki taimakamin ki soni ko bai kai sonda nake maki ba wlh i won't complain..i promise to be the most perfect hubby plss"..dakatar da kukanta tayi tareda daddagewa ta janye jikinta daga nashi ta mike da gudu ta fada bathroom tana banko kofar da karfi..Bobby ya dafe head dinshi da yaji yayi wani mugun sarawa yanxun nan...ya kwashi almost 7 mins yana zaune nan kafin ya mike da kyar ya fita daga dakin...a bakin kofa suka kusa karo da Mummy tana ganinshi ta kama hannunshi har cikin bedroom dinta snn ta saki hannun nashi tace"Bobby kana hauka?..why zakaje ka tsare 'yar mutane haka?..baka tunanin shaitan ya shiga tsakaninku?.."kama hannunta yayi ya dora chest dinshi yana dubanta da eyes dinshi da sukaui jajawur yace"Mummy bazan iya cigaba da boyewa ba anymore.. zucia ta bugawa zatayi"..kama hannunshi Mummy tayi suka zauna kan sofa ta dan kwantar da murya snn tace"kuma sai kaje ka tsareta ba ko kaya a jikinta?..bakasan shaitan is real ba koh?.."dora kanshi yayi kan shoulder dinta yace"Mummy bazan taba aikata abunda kike tunani ba..a yanda nake kishinta bazan taba bari shaitan ya shiga tsakanina da ita kafin aure ba..kawai na kasa controlling feelings dina ne..Mummy ji nake idan yarinyar nan bata aureni ba bazan iya cigaba da rayuwa ba"..shafa kanshi Mummy ta shigayi without saying anything..bata ma san me zata fada ba..wnn wane irin so ne yakema yarinyar nan haka?..wane irin sone yake neman zautar mata da Bobby haka?..anya kuwa ya kamata tayi folding arms dinta tana gani yaronta ya shiga wani hali akan soyayya?..anya kuwa bai kamata tay making wani move da zai taimaka masa ba?..wnn tunane tunanen ne suka taru suka cika zuciyarta..zuwa yanxu ta gama tabbatar da yake cewa idan bai aureta ba mutuwa zaiyi...tsaf tasan hakan zai iya faruwa amma wane hanya ya kamata tabi don tayi preventing faruwar hakan?..duk brain dinta ya cunkushe tama rasa wane tunani ya kamata tayi...mikewa tayi da sauri tunawa da tayi lokacin iftar yayi itama ko ruwa bata sha ba tazo kiran Aysha shine ta iskeshi a dakin..kama hannunshi tayi tana kallonshi tace"yanzun ka tashi muje muyi iftar sai muyi mgn later"..baiyi mata musu ba ya mike don yasan idanma yace ya koshi Mummy ba rabuwa dashi zatayi ba dole sai yaci and shi kashi yanada buqatan yasha ko ruwa ne sbd yayi breaking fast dinshi...hannunshi na cikin nata suka fita daga dakin..a dinning suka samu Miemie da Sab har sun fara iftar dinsu sai aunty sumy da itama ta fito yanxu...Mummy taja mishi kujera ya zauna snn ta koma ciki don fitowa da Aysha..har lokacin tana bathroom bata fito ba saida Mummy tayi mgn taji voice dinta ne da gaske snn ta bude kofan..riganda ya wurgar a kasa Mummy ta dauka ta mika mata ta koma bathroom ta sakoshi abjikinta snn ta kama hannunta suka fita dinni g..da kanta taja mata seat ta zauna snn itamata zauna tayi serving dinsu..wurin sai yayi tsit banda karan spoons ba abunda ke tashi...daga Bobby har Lamido babu mai cin abincin kirki kowa tunanin da yake zuciyatshi daban..ita tsananin tsoro da kuma mamakin yanda har yakeda guts din da zai bude baki yayana sonta take yayinda shi kuma yaketa kallonta yana sauraran yanda zuciyarshi keyi mishi ihu tana sake jaddada mashi cewa matukar bai sameta ba mutiwa zaiyi..ya lumshe ido ya bude duk hankalinshi na kanta yaga a kasa cin komai a wurin banda jujjuyawa da take sai yaji sam hakan baiyi mishi dadi ba..ko kusa bayason ta kwana da yunwa especially not yanxu da ake azumi..Mummy yayi da ido yayi mata alama da tayi mata mgn..murmushi ta saki tareda juyawa tana dubanta tace"Aysha meyasa baki cin abincin ne?..idan kuma wani abun kikeso yamxu sai a shiga kitchen a dafa maki"..daukan yamballs tayo da sauri tana kaiwa bakinta tace"zanci"..daga haka ta shiga tunkuda yamballs din kmr an aikota..saida taci guda 4 snn ta dauki kunun gyada dake gabanta shima ta kafa a baki tanasha kmr mai shan magani...duk Bobby na lura da ita dan even for once bai dauke hankalinshi daga kanta ba..kawai jinshi yake yakai limit din da bazai iya cigaba da hiding feelings dinshi ba..idan kuma ya dage sai yayi hakan then definitely zuciyarshi zata samu matsala...Lamido kuwa dukda ba kallonshi take zata iya rantsewa taji pearcing idanun nan nashi a kanta..ajiyar zucia ta sauke har yanxu gabanta bai bar faduwa ba ta dauki drink dake gabanta tasha snn ta ajiye goran tareda mikewa zata bar wurin shima yayi saurin mikewa don ya koma daki Mummy tace"dawo ka zauna"..kallonta yayi da sauri yace"Mummy bafa binta zanyi ba"..bata bari ya karasa ba tace"i said sit"..bai sake mgn ba ya koma seat din da ya tashi ya zauna hade da dafe kanshi da hannu..Mummy da tasan yanda yakeji da batayi yunkurin hanashi tafia bawlh..shi ba wajenta zaije ba kawai yanaso ne yajishi a kwance ko zai samu saukin abunda yakeji. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 40 Tana shiga daki wayanta ta dauka ta sake dialing number Hamma amma bai shiga ba..ta kira na daddy shima bai shiga ba na Ammi ma bai shiga ba..duk hankalinta yabi ya tashi taji bata son zaman kanon ma gaba daya..ko ba yanxu zasu tafi Saudi ba itadai gara mata ta koma ko Bauchi ne gidan aunty fiddausi akan dai ta zauna gidansu wnn mutumin daya fara bata tsoro yanxu..gaba daya abubuwan da yayi mata sun kasa bajewa daga kwanyarta..yanda ya furta i love u din nan har yanxun bata denajin echo dinshi cikin ears dinta ba..kuma ta tabbata this time around da gaske yake..da gaske yake tunda har yanayinshi taga gaba daya ya sauya and she saw wani abu cikin idanunshi wanda ko kusa bata fatan sake ganin makamancinshi...ba Kano kadai ya fita daga ranta ba har FCNM din taji ta tsaneta da daddy zai yadda ya maidata Gombe da tafi kowa farin ciki da hakan amma tasan ko rasuwa zatayi daddy bazai canxa mata makaranta ba especially not yanxu da take dab da kammalawa...bayan sallah suna gama hutu zasu tafi Clinical posting daga nan kuma saura musu semester daya su gama ta huta da alakakai..duk ranan da akace ta gama FCNM kuwa tana tunanin bazata sake tako kafarata ta kawo Kano ba duk kuwa da tarin kaunar da takewa garin amma bazata iya da halin proprietor dinsu ba..she remember yanda Prof ya nace kan Bobby sonta yakeyi hakama Billy ita kuma tanata cewa ba sonta yakeyi ba ashe duk sun fita gaskia...abubuwa da dama sai yanxu suka shiga dawowa kwanyarta suna kuma sake tabbatar da lallai da gaske proprietor sonta yake saidai ita ko kusa ko alama bataji wai zata soshi ba saidai tausayi daya bata..kawai dai zaiyita wahalar da kanshi ne daga baya ya hakura tunda dai tasan da hankalinta da komai bazata fara zabanshi a matsahin miji ba bayan ba kalan bakin halinshi da bata sani ba. Bayan duk sun kammala iftar dinsu suka mike zuwa parlor kafin sallahn isha..ya rage daga Mummy sai Bobby da har yanxun ke dafe da head dinshi a dinning din...kama hannunshi Mummy tayi cikin tsananin tausayinshi tace"dan Allah ka ragema kanka damuwan nan Bobby"..tana rufe baki ya dago jajayen eyes dinshi dake nan kaman ana hura musu wuta yace"bansan yanda zanyi in dena ba Mummy..ya zanyi plss?.."yana rufe baki tace"ka fawwalawa Allah komai..ka kuma yi imanin cewa idan Aysha matar ka ce zaka aureta likewise idan ba matarka bace duk wnn kunchi da damuwan bai isa yasa ka sameta ba"..dagowa yayi yana kokarin boye tarin damuwar dake kan fuskanshi yace"shikenan Mummy amma pls can i see her this once?..i just wanted to make sure bata tareda yunwa ne kinga azumi akeyi and ina kallo daxun ba wani abincin kirki taci ba"..mikewa Mummy tayi tana cewa"don't worry i will take care of that"..da sauri yace"Mummy please..idan ban ganta ba bazan iya bacci ba wlh"..kallonshi Mummy tayi kawai ta ksa mgn..tausayi yake bata sosai..da ganin yanda ya jigata za'a san dama abun ya dade yana cinshi a zuci yanxun ne kawai ya fito sbd kasa cigaba da boyewa da yayi..bata sake hanashi ba ta kama hannunshi suka nufi flat dinta...a tare suka shiga dakinda take tayi saurin mikewa daga kwancen da take tana kallonsu...Mummy ce tace mata"anya kin koshi da abincin nan kuwa Aysha?..idan kina son wani abu ki fada a kawo maki"..girgiza kai ta shigayi da sauri tana cewa"Allah na koshi Mummy"..kallonta Mummy tayi kmr zata sake mgn sai kuma ta saki hannun Bobby tareda juyawa ta fita daga dakin..tana fita ya karasa ciki da sauri yana dubanta a raunane yace"if sbd mgnr dana fada ne yasa kika kasa cin abinci am sorry.. ki fadi duk abunda kikeso i will go out in samo maki yanxun"..girgiza mishi kai kawai tayi tareda komawa ta kwanta murya can kasa tace"na koshi"..legs dinshi yaji sunyi wani irin sanyi kmr bazasu daukeshi ba..murya a hankali ya kira sunanta ta mike tana kallonshi kawai sai ya juya ya fita daga dakin yana jin kanshi na sarawa da karfi...magani kadai ya iya sha snn ya hau gado ya kwanta tareda lumshe ido yana addu'an Allah ya kawo bacci ya daukeshi ko zai samu saukin halinda yake ciki...dukda maganin da yasha baccin bai samu daukarshi da wuri ba sai can kuma ya daukeshi ba tareda saninshi ba...ana kiran sallahn isha ya farka tareda sake dauro alwala ya wuce masjid..bai dawo ba saida suka idar da taraweeh still ya sake komawa daki ya kwanta tun daga nan kuma bai sake tashi ba saida alarm din wayanshi ya buga alaman time din sahoor yayi knn...mikewa yayi da sauri ya sauka daga gadon tareda fadawa bathroom yayi brushing ya fito kai tsaye ya fita zuwa flat din Mummy...yau ko nafilar dare bai iya tashi yayi ba sbd maganin bacci da yasha..a parlor sukayi karo da ita tana ganinshi tace"yauwa ka tashi?.."yace"na tashi..Mummy kin tasheta?.."murmushi Mummy ta saki tana kama hannunshi tace"na tasar maka ita Bobby..nama kai mata abincinta can dakin saida ta fara ci na fito"..ajiyar zuciya ya sauke gamida lumshe idonshi yace"Mummy kar kina fita taki ci fa"..hannunshi Mummy ta kama suka fita daga parlon tana ce mishi"zataci inshaAllah..believe me"..kai kawai ya gyada mata har suka fita...nashi abincin shima ta hada ta kawo mashi snn itama ta zauna cin nata..shi kuwa kasa cin abincin ma yayi gaba daya hankalinshi ya tafi wurinta..bayan mintina kadan ya mike yace ma Mummy zaije yayi nafilah kafin time din subhi yayi..batayi masa musu ba barshi dukda tasan kafin yayi sallahn sai ya fara zuwa inda Aysha tukunna...ilai kuwa yana shiga direct dakin da take ya wuce...ya sameta da mug din tea a hannu tana sha baisan lokacinda ya sauke wani ajiyar zuciya ba..kallonta ya danyi for like 5 mins snn ya juya ya fita don yasan ko yayi mata mgn ma zaiy wahala ta amsa mashi hakan kuma yana iya sa zuciyarshi ta hauro yazo yana mata abunda bai kamata ba. Karfe goma na safiyar ranar Aunty Munubiya tazo gidan tareda yaranta..gaba daya sun cika parlon Mummy suna labari har Aysha da Mummy tasa dole aka kirata ta fito itama ake labarin da ita..dukda ba wani abu take cewa ba tana sauraronsu tana murmushi..ga Miemie da Nusaiba da suka sanyata tsakiya sun cikata da surutu kmr ba azumi suke ba...dukda labarin da sukey hankalin Mummy na kanta taga yanda take dan smiling idan an fadi abun daria sai hankalinta ya dan kwanta at least dai bata cikin damuwa yanxu...Bobby na fitowa ta wani hade girar sama dana kasa kmr ba ita ke smiling a while ago ba.. ya karasa ciki ya zauna suna gaisawa da Aunty Munu kmr bazai ce mata komai ba shima nashi face din daure can kuma ya kasa hakura yace"come and speak to ur dad"..kallonshi tayi taga shima ya daure fuska saida gabanta ya fadi da ganin fuskan nashi...tayi kasa da kai kmr bata jishi ba shi kuma ya sake cewa"ba dake nake mgn bane?.."mikewa tayi a hankali tana turo baki shima ya mike maimakon ya hadata dashi din sai ya kama hanyar fita itama dole tabi bayanshi kafin ya zazzaga mata masifa kuma...Mummy da mamaki ta bishi da kallo ganin har yanxu bazai dena hade ma yarinyar nan rai ba bayan duk wahalan da yakesha kanta...yana fita kai tsaye motarshi ya nufa ya bude front seat yana kallonta har ta karaso ta shiga ya rufe kofar snn shima ya zagaya ya shiga tareda tayar da motar ya figeta da wani irin gudu suka fita daga gidan...cikin tashin hankali ta juya tana kallonshi taga fuskan nan ba sarari sai ma sake tamkeshi da yayi kmr namijin saniya..kasa cewa komai tayi ta dauke kai daga gareshi...gudu yakeyi sosai ba tareda yasan shi kanshi ina ya dosa ba..kawai haushi yakeji da zata dinga treating dinshi like this sbd yace yana sonta bayan ya tabbata ko bestynta baza tayi treating dinshi haka ba ballantana kuma ace wnn tsohon saurayin nata...ganin yanda yake tsere da motoci akan titi kawai ta fashe mishi da kuka..yanzu idan yaje ya zubar dasu ya zasuyi?..kuka takeyi wiwi yana jinta baice komai ba bai kuma dakata da gudun da yakeyi ba dukda yanda kukan nata ke neman karyar mishi da zucia amma haka ya dake...saida yaje can Arean Naibawa ya hau fly over yabi titinda zai maidashi hotoro snn ya samu silent area da ba motoci ke wucewa sosai ba yayi parking nan wurin yana kallonta...lumshe ido yayi jin kukan nan nata yake har cikin ranshi..duk wnn zafin da ya fito dashi sai ya nemeshi ya rasa kukan nan da takeyi duk ya wargaza su...a hankali yake dubanta murya a matukar raunane yace"do u want to kill me?..so kike kiga karshena koh?.."shiru batace komai ba..ya sake cewa"am asking u..kinaso kisamun ciwon zucia sbd kinga na damu dake ne?.."dagowa tayi tana wiping tears dinta ta girgiza masa kai alamar aah..yace"then why are u doing this?..why are u punishing me like this?..na fada maki if sbd abubuwanda na maki a baya ne u are free to punish me amma am begging u to stop giving me tough times haka nan..na wahala mana..ko a haka kika barni i've learnt my lessons and ko a mafarki bazan sake yunkurin hurting dinki ba plss"..kallonshi kawai take ba tareda tace komai ba..kamo hannunta yayi da sauri ya dora kan chest dinshi yace"feel my heartbeat kiji..bai sake bugawa normal ba tun daga ranan dana fara sonki"..dakatawa yayi tareda dora kanshi kan hannun data yace"Aysha help me plss..am about going crazy"..kallonshi kawai Aysha keyi gabanta na tsananta faduwa...for the very first time taji ya mugun bata tausayi yau..ta yadda da gaske son nata yakeyi amma ita fa tana sonshi?..hannunta taji ya fara sagewa sbd kanshi daya dora akai dan haka ta shiga kokarin kwatan hannun ya sake mata shi da sauri ya dago kai yana kokarin maida tashin hankalin dake fuskanshi yace" am sorry"..yarfa hannun ta shiga yi kafin a hankali tace"it's ohk"..shiru sukayi na wani lokaci kafin Bobby yace"zan baki enough time kije kiyi tunani akai..i promise bazan sake disturbing dinki da mgnr ba amma do help me plss..help me out of this whole mess"..kallonshi har yanxun takeyi tanajin zuciyarta na karyewa..tausayi yake bata fiyeda tunaninta amma ya zatayi?..tasan idan tayiwa baby haka bata mai adalci ba..koda tana son Bobby bai kamata ta wulakanta shi ba ballantana ba sonshi takeyi ba tausayi kawai yake bata...yana gama mgn ya gyara zamanshi snn ya dauki phone dinshi yayi dialing number daddy...yana fara ringing ya mika mata wayar ta amsa tareda karashi a kunne...tanajin yayi picking tayi saurin cewa"daddy ina kwana"..yace"lafia lau..meya samu wayarki ne Najeeb yace tun safe yake kira bai shiga ba"..a hankali tace"kilan network ne..nima tun jiya ina kira bana samunshi"..daddy yace"shknn..yanzu ki zama cikin shiri zuwa gobe flight dinku zai tashi inshaAllah..shima Najeeb din a gobe zai iso"..nan da nan face sinta ya washe da tsananin farin ciki tace"to daddy..Allah ya kawoshi lafia"..daddy yace"Ameen"..snn sukayi sallama..ta mika mashi wayarshi tana cigaba da murmushi tace"thank u"..kallonta kawai yayi bai iya cewa komai ba...ya amsa wayan ya ajiye snn ya tada motar suka cigaba da tafia...bakin wani mall taga yayi parking snn ya bude motar ya fita..after few minutes ya dawo da leda a hannunshi ya ajiye back seat snn ya shiga ya sake tada motar suka wuce..har yanxun babu mai cewa wani abu a cikinsu..shi gaba daya tunaninshi yanaga neman hanyar da zaibi don ya samu soyayyarta yayinda ita kuma nata tunanin ke ga tafiyar da zasuyi gobe zuwa saudi sai kuma asalin tausayinshi daya fara damunta...har suka isa gida ba wanda yayi mgn cikinsu..bayan ya gama parking ya dauko ledan da ya ajiye a baya ya mika mata ba tareda cewa komai ba..batayi gaddama ba ta amsa ta duba sai taga abaya ne a ciki da wani zundumemen hijab da ta tabbata sai yakai mata har kasa..da dan murmushi ta dubeshi tana fadin"thank u"..bude motar yayi ya fita ya saki dan guntun smile shima kafin yace"u are welcome"..daga haka ya wuce gaba tana binshi a baya har cikin gidan...har yanxu suna nan zaune a parlor ya karasa ciki ya zauna ita kuma Aysha gaishesu tayi snn ta wuce daki don Allah Allah takey ta kira Billy da besty ta sanar musu tafiyanta gobe ne...Aunty Munubiya ta bita da kallo har ta shiga flat din Mummy snn ta juya tana kallon Bobby dake zaune kusada ita..ya saki dan murmushi yana shafa kai baidai ce mata komai ba...itama bata ce komai din ba ta maida hankali ga hiran da suke wanda mostly na zuwa Gombe da zasuyi ne cikin sallah. Lamido na shiga daki daukan waya tayi ta shiga kiran Billy ta fesa mata zancen tafiyarta saudi gobe suna gamawa ta kira besty shima ta fesa mishi..tana shirin kiran Hamma taji karfe nawa ne flight din nasu kiran Prof ya shigo wayarta...dagawa tayi sukasha labari abunsu shima ta sanar mishi zata tafi Umrah gobe amma koda wasa bata fada mishi cewa tana gidansu proprietor ba don tasan for sure hakan zai bata mishi rai...saida suka gama hiransu snn ta kira Hamma shima dai labari sukasha bayan sun gama ta dauki wayan nata ta koma parlour. Washegari around 11 ta gama shirya kanta tsaf cikin dogon rigan daya siyo mata jiya blue black..tayi veiling da mayafin rigan ta dauki dan small bag daya hado mata dashi duk a jiyan tasa phone dinta a ciki da 'yan abubuwanta snn ta rataya bag din a shoulder dinta ta fito tanata baza kamshi...Aunty dake zaune tareda Mummy a parlor tana ganinta tace"fa tabarakallahu ah'sanul khaliqeen..sannu Aysha"..dan murmushi ta saki kanta kasa ta karaso cikin parlon tana gaishesu kowa na yaba irin kyawunda tayi yau din nan...Bobby da ya gama shiryawa shima yana fitowa daga flat dinshi idanunshi basu sauka ko inaba sai kanta..heart dinshi har wani irin tattarewa yayi ya koma can gefe guda ya cushe sbd tsabar kyau daya ga tayi..duk yanda yaso ya dauke idonshi a kanta kasawa yayi..tayi mishi kyai fiyeda duk tunanin mai tunani...lokaci daya kuma wani irin kishi ya lullu6eshi daya tuna jrgi zataje ta hau a haka har saudia..ranshi yaji ya baci da batasa hijabin daya hada mata dashi ba..a hankali ya karasa cikin parlon fuska a daure yace mata"shi hijabin laifin me yayi maki da bazaki sashi ba?.."kallonshi tayi taga yanda ya wani hade rai sai ta marairaice zatayi mgn ya katseta da fadin"ki koma kije ki daukoshi ki sameni a mota"..yana fadan haka ya maida dubanshi ga Mummy har yanxu ya kasa sakin fuskanshi yace"Mummy zan kaita airport in dawo"..Mummy tace"to saika dawo..Allah ya tsare"..yace"Ameen"..snn ya juya ya fita daga parlon..itama Aysha juyawar tayi ta koma inda ta baro hijabin ta dorashi kan veiling din da tayi snn ta fito ta sake sallama dasu Mummy da suka rakata har bakin kofa snn ta nufi inda motan nashi yake...ko kafin ta karasa ya gama tada motar yayi warming dinta dan haka tana shiga janta yayi suka fita daga gidan...suna hanya ta sake juyawa ta kalleshi har yanxu fuskanshi babu fus cikin ranta sai take mamakin hali irin nashi...jiya jiyan nan fa ya gama marairaice mata yana cewa ta taimakeshi amma yanxu shi yake wani daure mata fuska kmr ba shine yace idan bata aureshi ba mutuwa zaiyi..ita zuciyarta ya fara tantamar anya ma son nata yakeyi kuwa da gaske?..har suka isa airport baice mata ba itama batace mishi ba..duba agogon hannunshi yayi yaga time dinya kamata ace ya iso ma ya wuce dan haka yace mata"call him kiji idan ya karaso"..batayi musu ba tayi dialling number dinshi..yana dagawa tace"Hamma gamu a airport din fa"..daga daya bangaren Najeeb yace"yea gashi na hangoku yanxun nan..am coming"..daga haka ya kashe wayarshi ita kuma ta shiga dube duben inda zata hangoshi..can ta ganoshi yana nufowa inda suke sbd farin ciki kasa hakura tayi ya karaso inda suke saita tafi da saurinta kawai ta kama hands dinshi tana sakin smile...runtse ido Bobby yayi sbd saukan wani abu da yaji mai kamada saukan aradu a cikin zuciyarshi..shi kuma waye wnn da zataje ta cacime hannunshi haka?..anya kuwa Lamido tanada hankali?..Hamma janyeta hannunshi daga nata yayi yana dungure mata kai yace"zanga randa zakisan kin girma wlh"..wani murmushin ta kara saki har dimples dinta suka fito..Bobby kuwa ji yayi kaman zai hadiye zucia ya mutu...shin wai kowa haka yakeji idan yaga yarinyar da yakeso tareda wani ko kuwa nashi ne yake neman wuce gona da iri?..shidai tunda ya fara son yarinyar nan yayi bye bye da farin ciki..bai tsinci komai cikin son nata ba sai tarin damuwa da ciwon zucia...suna karasowa inda yake ta sake kama hannun Hamman nata tace"Hamma wnn shine proprietor dinmu"..kallonta kawai Bobby keyi yanaso yasan alaqar dake tsakaninta da wnn mutumin da taketa kwakwumarshi tun daxu sbd batada hankali..yasan dai zaiyi wahala ace daddy ne ya haifeshi..kallonshi Najeeb yayi yana murmushi ya mika mashi hannun damanshi tamkar yasan tunaninda yake cikin ranshi yace"sunana Najeeb Auwal Lamido"..Bobby ya runtse ido cikin zuciyarshi yace"shikenan cousin dinta ne..ai dama nasan ni na shiga uku"..a zahiri kuma kokari yayi sosai ya dora wani dan guntun murmushi akan fuskanshi snn ya mika mashi hannu shima kafin yace"Dr Bobby Attahir Waziri"..shaking hands dinsu sukayi Hamma na cigaba da murmushi yace"nice to meet u Dr Bobby"..shima wani murmushin ya kara saki da bai kai zuci ba yace"nice meeting u too"..Lamido dai na tsaye tana kallon faces dinsu idan ta kalli na wnn sai ta juya ta kalli na wnn...bayan sun gama gaisawa ya sake mishi godia kan riketa da yayi a gidansu har zuwa yanxu..Bobby bai iya cewa komai ba sai kai daya daga musu..ko tsayawa ganin tafiyarsu baiyi ba ya juya ya wuce abunshi...ciwo yakeji daya kasance shi din cousin dinta ne..yana bude mota ya shiga ya jingina kanshi da kujera murya can kasa yace"here is another threat"..yasan yanda cousins ke taka muhimmiyar rawa wajen ruining relationships..relationship da yake da kwari ma ruining dinshi suke ballantana nashi da ko fara building relationship din baiyi ba...ya tabbata daga shi har son da yake mata suna cikin tsaka mai wuya..on one hand akwai cousin dinta on the other hand kuma akwai bestynta..shikam ya shiga uku da Allah ya jarabceshi da son Lamido..ya tabbata jarrabashi ake sonyi shiyasa aka jarabceshi da matsanancin sonta saidai fatan Allah ya bashi ikon cinye wnn jarrabawa. Tun daga wnn rana Bobby bai sake mata mgnr yana sonta ba kmr yanda yayi alkawari..kawai jira yakeyi ta gama tunaninta ta fada mishi shi kuma yayi alkawarin zai dauki duk wani decision data yanke...sallah saura sati daya suma suka tafi Umrah gaba dayansu..ko a can ma ya sake haduwa da ita don daddy da kanshi yay inviting dinsu zuwa masaukinsu...duk halin da yake ciki bai bari daddy ya fahimci sonta yakeyi ba sbd yafison ta fara amincewa dash kafin yaji mgnr...kowa ya dukufa sosai da ibadarshi as goman karshe ne kowa yana fatan saduwa da lailatul qadr...addu'an Bobby kusan rabi akan Lamido yake..roko yake idan akwai alkhairi tsakaninsu Allah ya tabbatar idan kuma babu Allah ya cire mashi sonta daga zuciyarshi snn ya hada kowa da rabonshi...a nata bangaren kuma har ga Allah ba karamin tausaya mishi take ba..sau tari tana kamashi yana kallonta idan yaga zaa gani sai yayi sauri ya dauke kanshi..ko a waya ya dena kiranta sbd alkawarin daya dauka na bazai sake disturbing dinta ba har zuwa lokacinda zata gama nazari akan mgnr...ko Billy bata fadama yace yana sonta ba sbd batason yanda Billyn ke nuna dama can tasan yana sonta itace take raina masa hankali...a can sukayi sallah gaba dayansu sai washegarin sallah suka bar Saudi...jirginsu ya sauka a Kano inda daga nan su Aysha suka wuce Gombe yayinda su Bobby kuma suka wuce gida kowa ya fara shirin tafiya Gombe da zasuyi wajen Waziri. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 41 The following day karfe 10 suka dauki hanyan Gombe..mota biyu suka tafi dashi nashi dana aunty sumy sai kuma drivers guda biyu...tunda suka wuce wudil Bobby keta faman kallon hanya yana jinjina buwayar ubangiji wai yau shine ya dauki hanyan Gombe da kanshi kuma da son ranshi ba tareda anyi forcing dinshi ba..ikon Allah knn yafi gaban wasa..ada gani yake kome zai faru bazai iya yafewa waziri da yan uwan dad dinsu ba ballantana har ya dauki kafa yaje har Gombe da kanshi amma yanxu gashi nan kan hanyan zuwa Gomben kuma ba tareda wani ya takurashi zuwan ba...abubuwa da dama yaga sun canxa mishi a hanyar bai san ko sbd shekarun daya dauka baije bane..the more suna kusantar Gombe the more zuciyarshi ke kara sanar dashi cewa Lamido ma fa a Gombe take..to ta yaya zaayi ya ganta shida ba gidansu zaije ba...wani 6angare na zuciyarshi kuma na ce mishi ganin nata sai sanyaya mishi zucia amma sam yaki yadda da hakan sbd yasan ko yanason ganinta ma bashida yanda zaiyi tunda baida wani reason da zai fadama babanta na zuwa gidan nasu..besides so yake ya fara nesanta kanshi da ita don ya fara gajia da walakancinta..banda sharrin zuciyarshi ma data kasa hakura da ita ai da bata isa ta dinga masa wnn iskancin yana shanyewa ba da tuni yayi maganinta..da wadan nan tunane suka shigo garin Gombe..nan ya sake wara ido yana kallon garin da yaji wani irin attachment tsakaninshi da garin ya shigeshi..Allah ya sani shi koda can ba Gombe ya tsana ba..tsanar da yayiwa family dinshi ne yasa yakejin kmr ya tsani garin amma he never hated Gombe domin ko ba komai a nan aka haifeshi...kai tsaye adress da waziri yasa aka turo musu sukabi har kofar sabon gidanshi da bai dade da tarewa ba...bude musu gate akayi suka shiga ciki da motocinsu...waziri daya kagara da zuwan nasu kasa hakura yayi saida ya fito compound lokacinda suka shigo...gaba daya fitowa daga mota sukayi suka nufo wurinshi aiko ya buda musu hannu suna karasawa ya shiga hugging dinsu one by one yana sanya musu albarka..har su Miemie saida ya runguma snn suka dunguma zuwa ciki...Mummy dai na daga gefe tana kallon yanda yake cikin tsananin farin ciki sbd ganin jikokinshi..lumshe ido tayi ita ko a haka Allah ya dauki ranta ta cika burinta tunda ta shirya tsakanin yaranta da yan uwan mahaifinsu..har mamaki ma wazirin ya bata ganin yanda jikinshi yayi sauki sosai kmr bashi ne wanda yayi shekara da shekaru yana jinya ba...babban parlonshi da yake saukar baki ya shiga dasu nan aka shiga kawo musu abinci iri iri daga cikin gidan ana ajiyewa a gabansu...bayan sun gaisa an sake neman yafiyar juna yasa aka kaisu masauki domin su huta kafin 'ya'yanshi daya kira su karaso...Bobby da sab dakuna biyu aka basu dake nan cikin parlon nashi yayinda su Mummy kuma aka shiga dasu cikin gida...daki biyu suma aka basu Mummy da Miemie daya aunty sumy da Ilham suma suka dauki daya. Lamido's Palace... Da sauri ta fito daga dakinsu daga ita sai dan towel a jikinta ta shigo parlonsu da akayi decorating dinshi da flowers da baloons kmr dai wani shagali za'ayi a ciki...duba takai zuwa ga wasu set of baloons masu kyau da aka jerasu daga can saman wall din dakin an rubuta Happy Birthday Aysha a jikin baloons din batasan time din da ta saki murmushi tana karema decor din parlon kallo ba...abun ya karamin kayatar da ita yayi ba tun ma ba'a fara celebration din ba..rabonta da celebrating birthday tunda ta cika 15 sai yau kuma data cika 20 ta samu ta lalla6a Ammi da kyar ta amince mata tayi bayan ta gama kafa mata dokoki iri iri...Billy ce ta fito daga dakin nasu ta shiga duban Aysha daketa kallon decorations din parlon tana sakin murmushi tace"ikon Allah..yanxu Lamido bazaki zo ki shirya ba sai mutane sun cika gidan knn?.."juyawa tayi da sauri tana cigaba da murmushinta tace"Billy bazaki gane farin cikin da nake ciki bane..wai nice nake cika 20 years yau din nan..oh Allah Alhamdulillah"..tsaki Billy ta saki tana harararta tace"wlh da Ammi zan hadaki idan baki wuce kin fara shiryawa ba..yanzun mukayi waya da Sa'eed yace har sun kar6o cakes din suna hanyan dawowa fa"..juyawa tayi da sauri ta koma dakin tana cigaba da sakin murmushi kmr ta6a66iya...da kallo Billy ta bita itama tana murmushi cikin zuciyarta tace"Allah dai ya nunamin ranar da zaki girma Lamido"..daga haka itama ta koma dakin suka fara shiryawa. Karfe hudu da rabi ta gama shirinta cikin straight gown na wani black material sai walwali yakeyi tasa red turban a kanta gashin nan da yasha uban gyara yana kwance luf luf kmr na balarabiya..light make up da tayi applying ba karamin sake fito da kyawunta yayi ba..su Billy da sauran cousins dinta kuwa straight gown suma sukayi na wani red material kowa tasa black turban akai...Husna ce ta shigo cikin irin kayansu itama tasha kyau kmr babu gobe tace"Addah dan Allah kuyi sauri ku fito mutane sun fara zuwa fa"..hannun Aysha dake tsaye gaban madubi sai kalkale takeyi Billy ta kama tana fadin"zo muje dan Allah keda bakya gajia da kallon madubi"..binsu tayi suka fita daga dakin tana kokarin kwace hannunta...parlon yana nan cikeda cousins dinta mata wanda yawanci mates dinta ne sai mates din Husna suma duk suna sanye cikin nasu kayan iri daya dasu Husna suna ganinta suka hada baki suna fadin"happy birthday to you Lamido"..karasowa tayi cikin parlon tana kallonsu da murmushi tama kasa cewa komai...kowa sai yaba irin kyau da tayi yake kafin a fara tace Husna taje ta shigo mata da besty ciki...ba musu kuwa ta juya ta fita kmr dama jira take..jikin motarshi ta sameshi yanata danna wayarshi ta dan daga murya yanda zai jiyota tace"Hamma besty Adda tace wai ka shigo ciki"..maida wayarshi yayi aljihu yana murmushi ya shiga takawa zuwa inda take yana cewa"bazaki dena Hamma bestyn nan ba koh Husna Lamido?.."dan murmushi ta saki tace"to yi hakuri na dena fada..Hamma Sa'eed"..wani murmushin ya kara saki kafin yace"yauwa yanxu kikayi mgn"..daga haka suka shiga cikin parlon..daidai lokacinda Hamma Najeeb shima ya gama shiryawarashi ya fito suka karasa ciki a tare..can dinning suka nufa suka zauna yanda zasuna ganin duk abunda sukeyi daga nan wurin...Billy da Lamido suka karasa kusada table da aka cikashi da manya manyan cakes dinta guda biyu da snacks da drinks kala kala suka tsaya..kafin ta yanka cake din ta dago tana duban su Sa'eed dake dinning ta wani turo baki abunka da an riga an saba tace"Hamma to ku karaso a yanka cake din mana"...ba musu suka taso zuwa wurinda take..Hamma ya tsaya right hand dinta dasu Husna gefenshi..Sa'eed kuma ya tsaya left hand dinta sai Billy gefenshi..gaba daya sukayi extending hands dinsu bayan anyi counting to three suka shiga yanka cake sauran occupants din wurin nata singing mata"happy birthday to u..happy birthday to u..happy birthday dear Aysha..happy birthday to u"..tana gama yanka cake din ta dauko ta sama Hamma a baki tareda Husna da Yusra snn ta sake daukan wani ta sama Billy da besty suma duk a bakinsu..masu daukan pictures da videos nata yi daga nan kuma duk akabi aka shashshafa ma kowa cake din a fuska bayan duk ta basu sunci sai kuma aka cigaba da hotuna...Sa'eed sai so yake ya samu ya fita amma ta hanashi..yana juyawa zatace"besty dan dawo a daukemu da wance"..haka nan ya hakura har aka gama pics din snn suka koma dinning shida Hamma suka zauna...Husna da Billy ne sukaje sukayi mgn da Ammi wai tazo suyi pictures..saida suka hadata da Allah annabi snn ta yadda ta fito akayi nusu pictures din Lamido sai wani rungumarta take Ammi ta danyi kasa da murya yanda ita kadai zataji abunda take fada tace"zakici ubanki ne wlh..kici gaba da rungumana kmr wata sa'ar wasanki"..batasan lokacinda ta kwashe da daria ba...Ammi ta sake cewa"zanyi maganinki"..haka dai sukaita rungumarta suna daukan hotuna har Sa'eed saida Lamido ta kira wai yazo ayi musu hoto da Ammi..ba musu ya taso akayi musu...ana gama pictures din Ammi tayi komawarta daki su kuma suka kunna home theater suka sa kida suka fara dancing abunsu..ko ban fada ba nasan kunsan mutumiyarku gwanar rawa ce dan haka ta gyagije tanata dirkar rawa sauran suna tayata...a takaice babu kalan waqar da basuyi rawanshi ba..anyi naija anyi na hausa musamman Ado Gwanja Fav din nata..basu tashi daga partyn ba sai wajen magrib...nan cousins dinta duk suka watse bayan sun cikata da gifts iri iri..ya rage daga ita sai su Husna sai Billy da besty sai kuma Hamma...sallah suka farayi snn suka zauna suna duba gifts din data samu..Hamma da Sa'eed da suka dawo daga masjid kowa yayi presenting nashi gift din ta karba tana godia...na Hamm ta fara budewa latest jessy ne manchester da baby doll na pogba..sbd tsabar farin ciki batasan lokacinda taje ta rungumeshi ba..bayan ta dawo ta bude na besty shi kuma taga wani hand band mai kyau red color am rubuta besty a jiki..sai locket mai shape din heart shima an rubuta besty a jiki sai kuma wani hadadden diary da pen a jikinshi shima yana daukeda sunan besty...farin cikinta kasa boyuwa yayi sai kallonshi kawai takeyi kaman wata sokuwa..motsi daya biyu zatace"besty nagode sosai"..shi har saida ya gaji da godiyan nata ma wlh...kafin suyi dinner Hamma yaje ya roki Ammi kan yanaso ya fita dasu suyi dinner a waje idan ta amince knn..tace ba damuwa suje amma kada su dade...yana zuwa yace musu duk suje su shirya they are going out for dinner yanxun...ba Lamido kadai ba hatta Billy dasu Husna murna sukeyi...nan da nan kuwa sukaje suka sake shiri kowa ta fito suka fita compound.. Lamido da Husna suka shiga motan besty Billy da yusra kuma suka shiga na Hamma..haka suka fita daga gidan kai tsaye Hamma ya wuce dasu Blue lounge and resto...kai tsaye vip section suka shiga aka kawo musu menu kowa yayi ordern abunda yakeso...bayan few minutes aka kawo musu abunda sukayi order nan kuma suka fara ci suna dan taba hira...Husna ce ke basu labarin wani classmate dinta da yake sonta wai kullum itada friends dinta sai sun sashi ya kawosu nan wurin sunci abinci ko kuma yazo ya musu takeaway sai daria suke suna jinjina wulakancin Husna...a daidai wnn lokacin kuma Bobby suka shigo wurin tareda wani cousin dinshi daya dage kan lallai sai ya rakoshi yaci abinci...wani irin 6acin rai da faduwar gaba yaji sun riskeshi at once sakamakon tozali da yayi da ita tana zaune a tsakiyar maza tana cin abinci kuma tana daria...ranshi ba karamin baci yayi ba..wai yarinyar nan wace iri ce ita?..karasawa yayi ya samu table daga nan bayansu ya zauna yayinda cousin dinshi da sukazo tare ya shiga ciki wurin wani friend dinshi...daga nan inda yake yana iya hango gashin kanta dake waje..runtse ido yayi ya rasa dalilinda yasa batada burinda ya wuce tayi kwalliya ta fito da gashi..sam baisan wace irin fitinanniya bace ita...kamar ance ta juyo yaga ta mike daga seat din da sauri tana rikeda wayarta tazo ta wuce ta inda yake zaune tana amsa waya...riga da skirt ne a jikinta wnn karon ta daura dankwali amma mayafin nata akai ta dorashi dukda cewa ba mai girma bane..kallon yanda each and every part of jikinta ke moving as a resulf saurin da take yayi...wani irin zafi yakeji na fitowa da tayi a haka..yanxu yasan kaf mazan dake wurin nan ba wanda bai kalleta ba haka suma wanda take tare dasu kilan har taba jikin nata ma sunyi...tunanin haka yasa kanshi yai wani mugun sarawa da bai shirya masa ba...juyawa yayi ya kallesu yaga hankalinsu ba kanta yake ba snn yasake dubawa da kyau yaga kowa harkan gabanshi yake dan haka ya mike daga inda yake a hankali ya karasa inda take kawai saiji tayi an fizge wayar dake hannunta an jata da wani irin karfi an fitar da ita daga wurin...daddagewa tayi zata kwada ihu yayi saurin toshe bakinta da hannunshi..da yaga tana neman 6ata mishi lokaci ya wani hade rai ya zuba mata idanunshi da yasan dole su ladabtar da ita..lokaci daya ta hadiye wani yawu kafin yacigaba da janya har zuwa inda motarshi..budewa yayi ya zurata ciki snn shima ya zagaya ya shiga tareda locking kofar daga ciki...cikin tsananin tashin hankali ta sake bude baki zata kurma ihu yayi azamar janyota ya matseta a jikinshi yana kallon cikin idanunta...wara idon tayi sosai tana kallonshi tana mamakin me ya kawoshi Gombe kuma..kodai aljani tayi gamo dashi ne?..nan hankalinta ya sake tashi ta shiga zubda hawaye tana"wa innahu sulaimanu wa innahu..."kasa karasawa tayi saboda kallon da ya tsareta dashi...tabbas shine ba aljani bane don duk dunia babu wanda idan ya kalleta takejin irin haka sai shi..amma meya kawoshi Gombe?..bude baki tayi zatai mgn ya dora finger dinshi akan bakin tareda hade fuskanshi da nata cikin wata irin dacin murya yace"ke har yanxu bakida hankali bakisan ciwon kanki ba koh?.."lamgabewa tayi tana kallonshi a hankali tace"sir ms nayi?.."harara ya watsa mata mai kyau kafin ya nuna jikinta yace"take a look at yourself..ke ko kunya bakiji ba kika fito haka kuma tareda maza"..girgiza mishi kai tayi kafin tace"sir it's my birthday today shine amma ya fito damu muyi dinner amma ni ba haka nake fitowa ba"..kallonta yayi ya danyi yayi shiru jin tace its her birthday..wato tsanar da tayi mishi har yakai da zatayi birthday bata fada mashi ba..kawai sai yaji ranshi ya sake 6aci..nan take ya kuma daure fuska ya bude mata kofa murya cunkushe yace"fita"..kallonshi tayi da mamaki jik abunda ya fada..ta dan rausayar da kai tace"nifa.."bai bari ta karasa ba ya sake nuna mata kofar da har yanxun ke bude yace mata"ki fitamun a mota nace"..kin gita tayi kawai ta tsaya tana kallonshi..kallon nata shima yayi for like 2 mins kafin ya dauke idonshi..ta sauke numfashi kafin a hankali tace"am sorry"..juyowa yayi yana dubanta yace"for?.."tace"for everything..am sorry for everything plss"..kai ya gayada mata kafin ya sske pointing mata kofa yace"naji..now kije..ki tafi kawai bana son ganinki anymore"..idanu ta wara taa kallonshi da mamaki shi kuma ya sake hade rai ya juyar da kanshi gefe..ba yanda ta iya haka ta bude motar ta fita duk sai bataji dadin yanda yayi treating dinta ba..does this mean ya dena sonta?..aikam indai yanda yake nuna yana sonta da gaske bai isa yace ya dena sonta yanxun ba..dole ma tasan yana sonta walakancin ne kawai ya motsa mashi..kallonshi tayi ya lumshe ido tareda jingina kanshi da kujera..yanda ya rufe ido sai lashes dinshi suka kwanta kasan idon nashi kmr na mace...lips dinshi dake nan very thick ta kalla sai kuma idanunshi dake sata nutsuwa ko bata shirya ba...kyau na musamman taga yayi mata dama kuma tasan shi din mai kyau ne amma yau sai taga kaman karo mishi kyawun akayi...runtse idonta tayi da sauri cikin raunin murya ta kuma tace"sir am sorry plss"..bude idanunshi yayi a hankali jin yanda voice dinta ke cracking har yanxun face dinshi daure yace"i said babu laifin da kikamin..ko bakida kunne ne?.."a razane take kallonshi cikin tsananin mamaki..gaba daya sai taga ya birkice ya dawo mata asalin proprietor data sani mara mutunchi..ba shiri ta sauka daga motar tana cigaba da mamakin wnn masifa da yayi mata..duk yau sai bataji dadin sudden change din nashi ba..knn dai tafiso yayita chasing dinta tana walakantashi idan ba haka ba why zataji ba dadi sbd yayi mata abunda dama ba yanxun ya fara ba..masifa dai tun daya fara ganinta yake zazzaga mata shi don haka zuwa yanxu ya kamata ta saba amma sai taga wani daban tunda ta mance when last ya mata wnn bala’in nashi..haka tana tafe tana tunani har ta koma inda ta baro. Washegari Billy ta koma gida ya rage daga su sai su a gidan...Ammi na kitchen sunata shirin tarban daddy da zai dawo daga Abuja yau...hankalin Aysha duk ba jikinta yake ba as tunda sukayi waya da baby daxun ya daga mata hankali..cewa yake wai indai tana sonshi da gaske saita bashi daman yazo ya nemi aurenta kafin holidays dinsu ya kare idan kuma ta sake dakatar dashi zai dauki hakan da tayi as bata sonshi...hankalinta ya tashi sosai Allah ya sani bata san ta ina zata fara cema daddy za'azo neman aurenta ba..gashi duka duka hutun nasu saura one week ya kare..yanxun daga ina zata fara ne?..tun daxun take tunanin kota fara sanarda Ammi ita kuma ta sanar da daddy amma tsananin tsoro ya hanata tayi hakan dan Allah ya sani itadai tsoron abunda zaije ya dawo take..kilan ma cewa za'ay ba karatu takeyi a Kano ba soyayyanta kawau take..shi kuma baby duk yabi ya birkice mata ko wayanta ma ya dena dauka...a waya ta kira Billy tayi mata bayanin komai ita kuma ta bata shawaran taje ta fadama Ammi duk yanda sukayi da ita saita fadama babyn..tayi na'am da wnn shawara na Billy dan haka bayan ta fito daga kitchen kai tsaye ta bita zuaa bedroom dinta...tana kokarin shiga wanka Aysha ta shigo dakin..Ammi ta shiga binta da kallo ganin yanda tayi wani sanyi kmr ba ita ba tace"menene?.."karasawa tayi ta zauna gefen gado tana duban Ammin fuska a marairaice tace"Ammi mgn nakeso muyi"..komawa Ammi tayi ta zauna tana fuskantarta tace"to ina jinki"..a hankali ta sake dagowa ta kalleta sai kuma tayi kasa da idonta tace"Ammi dama..da akwai wani mutumi da muka hadu dashi a kano"..kallonta Ammi keyi tanaso taji inda zancen nata ya dosa tace"umhum cigaba mana"..saida ta hadiye wani yawu snn tacigaba"Ammi dama cewa yayi yana sona kuma da gaske aurena zaiyi..nace bazan kawoshi gida ba saina gama school shine daxu yace shidai dole yanaso ya turo ayi tambaya kafin na koma makaranta"..ta sakeyin shiru ta kurawa Ammi ido tanaso taga reaction dinta...ganin kallonta itama Ammin keyi tayi saurin cewa"kuma wlh Ammi bani nace mishi ya turo ba..da kanshi yace zaizo wai a fara saninshi a gida"..sauke ajiyar zucia Ammi tayi kafin tace"ke kina sonshi ne?.."shiru tayi tana kallonta..Ammi tace"magana fa nake miki"..a hankali tace"eh.."Ammi tace"shikenan kije zanyi magana da daddy idan ya dawo sai a fadama Lamido ya basu ranar da zasuzo..da yake ke mara hankali ce shine kikaje kika fara kulashi ba tareda ya turo gidanku ba"..itadai shiru tayi kanta kasa dan bata taba zaton Ammi ba fada zatayi mata ba..koda yake dama ance duk wata uwa mace da zarar yarinyarta ta girma batada burin da ya wuce ta sadata da dakin mijinta saidai idan lokaci baiyi ba...wnn mgn na mutane kuwa haka yake don ga alama nan ta gani wajen Ammi...mikewa tayi ta fita daga dakin bayan Ammi ta salameta..cikeda farin cikinta ta kira Prof ta sanar dashi yanda sukayi da Ammi..murna wajenshi tamkar bai taba aure ba...suna gama waya ta kira Billy itama ta sanar mata sai kuma ta jiye wayar tareda fadawa duniyar tunani..babu wanda ya fado mata a rai sai proprietor.. ta tabbata zai shiga mawuyacin hali idan yaji wnn labarin..to amma ita ba sonshi takeyi ba kuma bazata iya auren mai shekarunshi ba..tafi son babban mutum daya kusan haifanta yanda zataje taci duniyarta da tsinke...ta lumshe ido tana sake lafewa kan pillow incident dinsu ya shiga dawowa brain dinta...she remeber how he hold and tell her yana sonta morethan anything...how he made it clear cewa idan ta auri wani mutuwa zaiyi..then she remember his jealousy..ta tabbata level of jealousy dinshi yafi na baby sosai sbd yanda ko wani yaga yana kallonta kishi yakeji...abubuwa da dama ta shiga tunawa game dashi tun daga ranar daya fara mata allura har zuwa lokacin festival da Presentation da abubuwan da ya dinga nunawa a lokacin...ajiyar zucia ta sauke da gaske mgnr Billy haka yake kilan tun ranar daya fara ganinta yake sonta ganewa ne batayi ba...sai yanzu take ganin tsagwaron kishi cikin duk wnn abubuwan da yayi mata a baya...sake juyawa tayi tana rungumar pillow ta tuna how his Mom and siblings treated her time da taje gidansu..they are the most kind and nicest people she've ever come across..sunada karamci sosai likewise shi kanshi Bobbyn saidai shi yanada matsala daya which is masifa da shegen taurin kai...gaba daya tunaninta ranar sai ya tattara ya koma kanshi da ahalinshi kuma ta rasa dalilin hakan don dai ita bata taba tsayawa tunaninshi bama balle kuma na family dinsh..sai yanxu take ganin rashin dacewar amsan data bashi ranar..sam bata kyauta ba..ko bata sonshi bai kamata tana walakanta shi ba ko don sbd karamcinshi a gareta..yanada kirki sosai and yana sonta da gaske..duk sai taji wnn tunane tunanem sun addabeta sun hanata sukuni. Tun safe kowa ya fito parlon waziri suka gaidashi kmr yanda suka saba gashi har za'a fara breakfast Bobby bai fito ba...parlon nashi a cike yake da Uncles din su Bobby maza da yaransu sai Aunty Munubiya dasu Aunty Sumy suma duk suna nan...Waziri ne ya dubi daya daga cikin jikokinshi yace"Khalid je daki ka dubamun Attahir kaga meya hanashi fitowa har yanxu"..ba musu khalid din ya mike zuwa dakinda aka sauki Bobby..a kwance ya iskeshi can karshen gado ya wani dukunkune kanshi cikin duvet sai rawan sanyi yake...da sauri ya haura kan gadon tareda yaye duvet din yaji jikinshi akwai zafi sosai dan haka ya sauka da sauri ya fita daga dakin yaje ya sanar da waizir..hankalinshi ya tashi sosai dan ko Mummy bazata kaishi tashin hankali ba..mikewa yayi kai tsaye zuwa dakin nashi..ya zauna gefen gadon tareda kai hannu yayi feeling temperature dinshi yaji zafi sosai..dan haka yace a fito da mota su tafi asibiti..ba yanda wasu daga yaranshi basuyi ba kan ya bari a kira doctor yazo ya dubashi amma yace sam bazai iya jira har sai likita yazo ba..ba yanda suka iya dole haka aka fito da mota suka wuce asibitin daga shi sai Bobby sai daya daga cikin cousins dinshi da kuma Uncle dinshi. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 42 Suna shiga asibitin family doctor dinsu ya fara dubashi su kuma suka jira a waje..babu yanda khalid da wani uncle din su Bobby mai suna Lukman basuyi da waziri kan suje waiting room ya zauna ba amma yaki haka yayita kai kawo a reception cikin tsananin tashin hankali kai kace Attahir dinshi ne na asali baida lafia...after like 15 mina doctor ya fito daga dakinda yake..tun kafin ya karaso inda suke waziri yayi saurin juyawa yana dubanshi cikin tashin hankalin dake karuwa a tareda shi yace"ya jikin nashi?.."a nutse doc yace"ya samu bacci yanxu"..waziri yace"amma meyake damunshi?.."daga kafada yayi before yace"well da akwai tests daya kamata a mashi amma dole saiya tashi daga bacci..for now dai few examinations da nayi masa ya tabbatar mun da cewa yana tareda damuwa snn da akwai mgn da yake kokarin fada ban gane me yake nufi ba..ina ganin idan akwai mahaifi ko mahaifiyarshi a kusa ya kamata a kirasu ko su zasu fahimci me yakeso ya fada"..sbd tsabar tashin hankali waziri har wani jiri yaji ya daukeshi kaman zai fadi..uncle lukman dake bayanshi yayi saurin tareshi yana fadin"Dan Allah Baffa ka kwantar da hankalinka..zai samu lafia inshaAllah"..girgiza kanshi yakeyi cikin tashin hankali...bayaso ya rasashi kmr yanda ya rasa mahaifinshi..gani yake kaman wani abu zai faru dashi..ganin halinda ya shiga doctor yace u shiga dashi ciki shi kanshi yana bukatar hutu a yanzu..ba musu suka shiga dashi inda Bobbyn yake kwance..kujera ya samu ya zauna snn ya dubi khalid dake tsaye kusada uncle lukman yace"ka koma gida ka taho da Nadia yanxun nan..kace ma Munubiya da Sumayya suma ina son ganinsu a nan"..da sauri khalid ya juya ya fita don tahowa dasu din...uncle lukman ya karasa ciki ya zauna shima ya zubama Bobbyn ido yana kallo kmr yanda waziri ma ke kallonshi...yana kwance kan gado hannayenshi dafe da forehead dinshi..numfashinshi na fita da sauri dalilin haka chest dinshi keta sama da kasa...kana ganin yanda face dinshi ke a yatsine zakasan ba dadin baccin yakeji ba...bayan 30 mins khalid ya dawo asibitin tareda su Mummy kmr yanda Waziri ya bukata...a rikice suka shigo dakin gaba daya su ukun musamman aunty sumy da Aunty Munubiya duk a figirce suke kmr ance rasuwa yayi Bobbyn..Mummy kuma tayi kokari sosai wajen 6oye tashin hankalin da ta shiga na ganin halinda Bobbynta ke ciki sbd presence na waziri da kuma qanin mahaifinshi a wurin...karasawa ciki tayi ta zauna tana duban waziri kafin tayi mgn ya rigata"likita yace Attahiru na tareda damuwa..kinada masaniya akan abunda ks damunshi?.."shiru Mummy tayi tana tunani..duk dunia dai tasan damuwar Bobby guda daya ne kuma shine Lamido...amma ya kamata ta fadama waziri ba tareda sanin takamaiman dalilinda ya jefashi cikin wnn halin ba?..muryan waziri ya dawo da ita daga tunaninda take..yace"idan kinsan wani abu na damunshi ki fadamin..banaso shima in rasashi kmr yanda na rasa mahaifinshi"..ajiyar zucia Mummy ta sauke kafin tace"eh to da akwai wata yarinya da nasan yana sonta saidai ban saniba ko sanadinta ne ya fada wnn halin"...shima ajiyar zucia ya sauke kafin yayi mgn Bobby yayi wani irin mosti da saida gadon da yake kwance akai ya motsa...da sauri suka yi kanshi gaba dayansu kowa na kiran sunanshi amma sai sukaga ya sake komawa yacigaba da baccin..bakinshi ne ya fara mosti alaman yana cewa wani abu dan haka Aunty Munubiya ta kai kunnenta daidai bakin nashi amma bata fahinci abunda yake cewa ba..ganin hawaye ya faro zubowa daga cikin idanunshi dake rufe waziri yace Mummy takai kunnenta ita ko zata fahimci me yake fada...ba musu kuwa ta kara kunnenta a bakin nashi still itama bata ji me yake cewa ba..ga kuma idanuwanshi a rufe suna fidda hawaye sai kuma legs dinshi da suka fara mosti suma yanzu...hannunshi ta kama tareda zaunawa nan gefenshi ta shiga murza hannun nashi tace"Bobby.."da sauri ya bude idanuwanshi tamkar abunda yake jira knn..sake matsawa tayi kusada fuskanshi tana dubanshi tace"meya sameka?..me kakeso kace?.."lumshe idonshi yayi yayi kokarin dakatar da hawayen dake cikowa idonshi snn ya damke hannunta dake cikin nashi muryanshi na fita da kyar yace"bata sona Mummy"..dakatawa yayi hawaye na sake antayowa fuskanshi kafin yacigaba da cewa"mutuwa zanyi Mummy..wlh duk ranan da ta auri wani mutuwa za..."kasa karasawa yay sbd kukan Mummy daya cika dakin..mikewa yayi zaune da sauri yana kokarin goge mata hawayen yace"Mummy am sorry plss..ki bar kuka dan All.."still ya kasa karasawa sbd ganin sauran jama'an dake dakin..wara ido yayi yana kallonsu sosai..idonshi na tsayawa kan waziri yayi kasa da kanshi da sauri yana sauke numfashi da sauri da sauri...karasowa waziri yayi Mummy ta bashi wuri ya zauna nan kusada dashi shima ya kama hannunshi snn ya dubeshi fuska ba yabo ba fallasa yace"wacece ita Attahir?..wace yarinya ce kake neman kashe kanka sbd ita?.."runtse ido Bobby yayi yana salati shknn asirinshi ya gama tonuwa..baiso waziri yaji mgnr nan ta haka ba..so yayi ya sameshi yayi mishi bayani in person bayan sun daidaita da ita amma she ruined everything..tun jiya daya fahimci da gaske bata sonshi bai sake samun kwanciyar hankali ba..gani yake shknn ya rasata wanda damuwar hakan ya sanya mashi zazza6i da ciwon kai wanda baya ko tantama blood pressure dinshi ne ya hau..ganin yayi tsit baida niyyar mgn Waziri ya janyoshi jikinshi ya rungume ya shiga shafa bayanshi a hankali yace"ka fadamin 'yar gidan waye kuma a wane gari take?..nayi maka alkawarin duk inda take a fadin dunia ni da kaina zanje in nema maka aurenta"..lumshe ido yayi ya bude yanajin yanda zuciyarshi ke tsananta bugu still ya kasa cewa komai saida waziri ya sake cewa"Attahiru"..snn ya hadiye wani yawu daya cika mashi baki from no where yace"a..nan..Gombe take"..dagoshi waziri yayi daga jikinshi yana mishi duba irin na mamaki yace"Gombe?..wnn Gomben da muke ciki?.."gyada kai Bobby yayi idanunshi na kallon kasa yace"eh.."waziri ya sauke wani ajiyar zucia kafin yace"kaga faduwa yazo daidai da zama knn..fadamun 'yar gidan waye a Gombe take neman zautar min da abokina haka?.."ya karasa mgnr cikin sigar wasa sbd yayi cheering dinshi up..su Mummy dai suna daga gefe sun zama yan kallo a tsakaninsu...waziri ya sake kama hannunshi yace"ka fadamun waye mahaifinta a Gombe?.."saida ya runste ido snn ya iya bude baki yace"Col Ahmad Lamido"..wani irin tsit dakin yayi kmr babu masu rai a ciki...waziri da yayi dif shima yana kallonshi kallonda ya kusan sa zuciyar Bobby ya buga sbd wasu abubuwa da zuciyarshi ke saka mishi gameda kallon..lumshe idonshi yayi kmr daga sama yaji waziri yace"Ahmad Lamido fa kace"..a hankali Bobby ya gyada mishi kai..cikeda wani mamakin waziri ya kuma cewa"Lamido dai wnn Adnan Lamido nawa?"..nan ma kai ya sake gyada mashi...lokaci daya wani annuri da farin ciki suka mamaye fuskan waziri...hannu ya budawa Bobbyn shi kuma ya shige jikinshi ya rungumeshi yana sakin murmushi yace"yanzu akan jinin Lamido kake wahalar da kanka haka?..kasan alaqar dake tsakanina da Lamido kuwa?..shi kanshi Ahmad din mutumin mahaifinka ne sosai kafin Allah ya kar6i rayuwarshi"..dagowa Bobby yayi yana dubanshi da murmushi ya gyada mishi kai alaman ya sani..waziri daya kasa dena murmusawa yace"baka saniba Attahiru..daka sani da baka tsaya kana wahalar da kanka kan jinin Lamido ba domin kaima ahalin Lamido tamkar ahali yake a wurinka"...wani irin hamshakin dadi Bobby yaji yana saukan mishi from no where...ya kama duk hannayen waziri ya rikesu gam cikin nashi voice dinshi na rawa yace"yanxu..zan iya..samun..aurenta?.."tun kafin ya rufe baki Waziri yace"da izinin Allah zaka samu..nasan Lamido bazai taba hana jinin Waziri jininshi ba"..wani irin runguma Bobby yayi mashi yana fadin"nagode sosai Baffa Allah ya saka da alkhairi Allah ya kara girma"..waziri na shafa bayanshi yana cigaba da smiling yace"Ameen Ameen Attahiru..Allah ya jikan mahaifinka"..duk suka amsa da Ameen kafin ya dago yana sake duban waziri murmushin fuskanshi na raguwa yace"amma fa bata sona Baffa..da bakinta ta fadamin hak.."bai karasa ba waziri ya rufe mashi baki yana fadin"karka damu wnn a wurin Allah yake..nidai zanyi magana da Lamido da zarar mun koma gida"..gyada kai ya shigayi new tears na cikowa idonshi na farin ciki yace"Allah ya baka aljannah"...waziri ya amsa da Ameen snn yace khalid yaje ya kira doctor..ba musu ya juya ya fita su Mummy kuma har yanxun suna tsaye kowa tana goge hawaye tana kuma sakin murmurshi at the same time..musamman Mummy da take ganin Allah ne ya amsa addu'anta. Doctor na zuwa ya danyi gwaje gwajenshi kafin yace"da akwai stress a tareda kai so ina ganin zamu ajiyeka a nan for 1 or 2 days sbd ka samu enough rest"..yana rufe baki Bobby yace"don't worry i will take care of myself amma ayi discharging dina dan Allah"..kallonshi likitan keyi kafin yayi mgn Aunty Munubiya tace"he is a medical doctor"..tana rufe baki waziri yace indai yana ganin bai isa ayi discharging dinshi ba kada ya sallemshi har sai ya samu lafia...doctor yace ba damuwa zaiyi discharging din nashi sai ya dinga zuwa gida yana dubashi..yayi prescribing drugs da zaiyi amfani dasu ya bashi snn yayi discharging nashi yace zasu iya tafiya...a hankali yake takawa sbd jikinshi da baijin karfinshi kwata kwata...motan waziri ya shiga suma su Mummy suka shiga wanda aka kawosu snn suka bar asibitin...suna zuwa gida Aunty Munubiya ta hada mashi ruwa ya shiga yayi taking shower ya fito yasa kaya snn aka kawo mashi abinci...kasa cin komai yayi sbd shifa har yanzun hankalinshi ba kwantawa yayi ba sbd rashin sanin takamaimai halinda ake ciki...shin zai samu auren nata ne ko bazai samu ba?..shin zata hakura ta aureshi dukda bata sonshi ko bazata hakura ba..a soyayyan da yake mata shi gani yake ko bata sonshi matukar zata yadda ta aureshi he's ok..kawai yayi feeling kanshi cikin gida daya da ita ma ba karamin abu bane a wurinshi so muddin zata zauna dashi ko bata sonshi he won't complain...haka ya kasa taba komai cikin tarin abincin da aka jere a gabanshi saida waziri ya shigo da waya a hannunshi yace yayi sauri ya gama cin abincin sai ya kira Lamido ya fara sanar dashi abunda ke da akwai kafin yaje har gida ya sameshi...nan da nan kuwa ya shiga tunkuda abincin Aunty Munubiya na kallonshi tana mishi daria...yana gamawa waziri ya kira Lamido a waya as he promised saidai har wayan ya gama ringin baa daga ba..ya sake Kira nan ma no answer dan haka ya jiye wayar yace zuwa anjma zai sake kira kilan yana wani uzuri ne don dai yasan matukar babu babban uzuri ba yanda za'ayi ya kira wayar Lamido har sau biyu ba tareda ya dauka ba. A daidai lokacinda Waziri ya kira wayar Lamido shi kuma yana tareda daddy da bai jima da dawowa ba yana sanar dashi mgnr da Aysha sukayi da Amminta daxu na cewa wani wanda yake son aurenta yanaso yazo ya gana dasu...tunda daddy ya fara mgn Lamido yayi shiru yana sauraronshi har saida yakai aya snn ya numfasa yace"ka gama?.."a hankali daddy dake zaune nan kasa yace"na gama Baffah"..Lamido yace"to koma waye kace mata ta sanar dashi ba sai yazo ba"..da mamaki sosai daddy ke duban mahaifin nashi saidai baice komai ba...Lamido daya daure fuskanshi yace"saboda nayi mata miji"...sake dukar da kai daddy yace"Allah yasa hakane yafi alkhairi"..Lamido yace"Ameen..gobe idan Allah ya kaimu inaso ka kawomin ita Aishan da Maimuna inason mgn dasu"..cikeda ladabi ya sake fadin"InshaAllah za'a kawosu..Allah ya kara girma"..Lamido ya sake cewa"Ameen..kana iya tafia"..ba musu daddy yayi sallama dashi snn ya tashi ya fita...har ya isa gida bai dena tunanin mgnr da Lamido ya fada ba..ko waye mijin da yayi mata oho?..abu daya dai ya sani shine Lamido bazai ta6a yi mata za6en tumun dare ba don haka tun ma kafin yasan waye yayi na'am dashi domin sanin halin Lamido da kalamu waheed..zaiyi wahala ya fadi mgn kuma daga baya ya dawo ya canza ta..fatanshi dai bai wuce Allah ya daidaita kansu da Aysha ba don yasan muddin aka ce za'a aura mata mutuminda bataso za'aga tashin hankali..Aysha da kan abunda baikai ya kawo bama take kuka balle kuma wnn daya shafi rayuwarta na gaba..ai saidai Allah ya dorashi kanta kawai idan bahaka ba kam za'a ga rashin hankali. Koda ya koma gida sai ya kasa sanar da Ammi yanda sukayi da Lamido..kawai yana tunanin itama bai zama lallai taji dadin hukuncin na Lamido ba amma ya zaiyi?..bashida yanda zaiyi ne kmr yanda suma basuda yanda zasuyi dan haka ya zama musu dole su kar6i koma waye Lamido ya za6a mata da hannu bibbiyu...Ammi ta lura yana tareda damuwa kuma jikinta ya bata akan mgnr da yajema Lamido dashi ne..bata tambayeshi ba'asi ba saida dare yayi ta shigo dakin nashi cikin shirin bacci kmr yanda ta saba...daddy najin shigowarta yayi saurin rufe ido sbd tayi zaton yayi bacci amma abunda bai saniba shine duk wani 6oye 6oyenshi Ammi ta riga ta fahimci akwai damuwa a taredashi damuwan kuma baya rasa nasaba da batun auren Aysha da sukayi da Lamido...saida ta bari ya gama gyara kwanciyarshi shi bai yadda ba bacci yake snn a hankali tace"daddy.."daddy ya runtse ido yana addu'ar Allah yasa bata gano me yake 6oyewa ba kuma bai amsa mata ba...sake kiran sunanshi tayi still ba amsa dan haka takai hannu ta yaye duvet daya rufe dashi cikin raunin murya tace"wace mgn ce wnn da bazaka iya fadamun ba har kake baccin karya daddy?.."sake runtse ido yayi yana salati..Maimunatu badai fahimta ba..yanxun duk wnn 6oyewan da yake saida ta fahimci akwai wani abu a tattare dashi?..kasa cewa komai yayi sai mikewa da yayi zaune yana kallonta...kallon nashi itama take cikin sanyin murya tace"ka sanar dani abunda kw faruwa dan Allah..me Baffa yace?.."kallonta kawai daddy yake yana mamakin kwakwalwa irin nata..no wonder gaba daya yaransu sukeda brain especially Aysha data dauko komai da komai irin nata..itama bala'in kwanya gareta...kama hannunta yayi yana kallon cikin idonta yace"ki kwantar da hankalinki Maimunatu..ba wani babban abu bane"..tun kafin ya rufe baki tace"da wnn abun da kake yana sawa inyi tunanin babban abu ne daddy..kawai ka sanar dani ya kukayi da Baffa?.."ajiyar zucia ya sauke kafin yace"naje mishi da mgnr Aysha kmr yanda kika fadamin saidai tun ban karasa ba yace ace mata ta fada mashi ba sai yazo ba don yayi mata miji"..ya karasa mgnr cikin sanyin murya...dan murmushi Ammi ta saki tana kokarin 6oye dan rudanin data shiga tace"yanxu akan wnn mgnr kaketa 6oye 6oye bakaso ka sanar dani daddy?.."sake kama hannunta yayi yana dubanta da kyau yace"nasan Lamido bazai taba zaba mata mijin da bai dace da itaba saidai ina tsoron yanda ita Aishan zata dauki mgnr..kinsan halinta"..murmushi Ammi ta kara saki a kokarinta na ganin ta kwantarwa da mijinta hankali tace"wnn baikai dalilinda zai saka damuwa ba daddy..Ayshan nan fa 'yarka ce..da kai da ita kuma duk kuna karkashin Lamido ne so ya zama mata dole tayi mashi biyayya kmr yanda kaima ya zama maka dole"..kallonta daddy keyi yanajin wani irin sanyi a cikin ranshi...yaji almost 70%na damuwar da yake ciki ya gushe sbd maganganun nan nata..shiyasa dai ake cewa mace ta gari jin dadin rayuwa domin komai arziki da mulkin mutum matukar bashida mace ta gari bashida jin dadin rayuwa..duk wnn abunda take yasan itama baza'a rasa ko yayane dan damuwa a tareda ita ba amma ko kusa bata nuna mashi ba..yasan kuma koda za'a aura mata wanda bataso bazata ta6a bude baki tace mishi bataso ba ko kuma ta nuna wani alama da zai tabbatar da hakan...mace ce ita mai tsananin kara musamman akan Aysha data kasance 'yar fari..wnn dabi'un nata yasa a kullum sonta ke zama sabo fil a cikin zuciyarshi..bashida burinda ya wuce yaga ya faranta mata kmr yanda itama bata gajia da faranta mishi...(ubangiji ka azurta duk wani miji na gari da samun mata ta gari🙏🏻sisters kuce Ameen😂). The following morning tare sukay breakfast gaba daya a dinning dake nan parlor which is so unlike them..zaiyi wahala daddy da Ammi suyi breakfast tare dasu mostly su biyu sukeyin abunsu a can parlon daddyn...Aysha dai sai baza ido da kunne take tana jira taji yanda Ammi sukayi da daddy amma bataji komai ba..so take taji shin Ammi tayi masa mgnr ne kuma ya sukayi da Lamido?..baby gaba daya ya daga mata hankali sai rigima yakey mata wanda batasan sanda ya koya ba..kawai duk yabi ya sata cikin rudani itada takeso ta gama FCNM snn ta tafi abroad tayi furthering karatunta kmr yanda sukayi da daddy shine yanzun yake 6ullo mata da mgnr aure...Allah ya gani itadai ba shiryama auren nan tayi ba kawai ta yadda ne don batada yanda zatayi dashi...har suka gama breakfast dinsu ba wanda yace mata uffan hakan kuma yasa tasha jinin jikinta...Najeeb ne ya mike yayi sallama dasu snn ya fita tareda Husna da Yusra da zaiyi dropping nasu a islamiyya da sukayi resuming yau shima kuma ya wuce wajen aikinshi...itama Aysha mikewa tayi zata bar dinning din daddy ya kira sunanta...gabanta yayi wani irin faduwa na ba gaira babu dalili kafin ta juyo a hankali tana kallonshi tace"na'am"..ba tareda ya kalli inda take ba yace"kije ki sako hijab dinki yanxun nan kizo zamuje wajen Lamido"...wara idanu tayi gabanta na sake faduwa jin abunda ya fada..tabbas tasan akwai wata a kasa..babu yanda za'ayi ace ta shirya aje wajen Lamido a irin wnn lokacin..Innalillahi kawai take furatawa a ranta ta kasa ko mosti..Ammi da taga tayi wani tsaye kmr bada ita ake mgn ba tace"wai badake ake mgn bane?..wane irin iskanci ne wnn?.."juyawa tayi da sauri tana fadin"sorry Ammi"snn ta shige dakinsu...daddy ya mike daga dinning din yana duban Ammi cikin sigar wasa yace"fadanki ya fara yawa fa Maimunatu..inajin yanda kullum kike samun yara a gaba kina musu fada kawaici nakeyi maki"..mikewa tayi itama tana murmushi tace"yaran naka ne ai basajin mgn musamman ita wnn da har yanxu ta kasa fahimtan cewa itace babba"...murmushi kawai ya sakeyi ya wuce zuwa parlonshi tana mara mishi baya...car keys dinshi ya dauka itama Ammi ta zura hijab snn suka fito tare...daidai lokacin itama Aysha ta fito sanyeda katon hijab dinta har kasa...ficewa sukayi daga gidan daddy ya mikama Ammi makullin motar ba musu ta kar6a ta bude musu ya shiga front seat Aysha kuma ta shiga baya sai ita Ammin ta shiga driver seat..dama haka yake bai cika daukan driver zuwa gidan Lamido ha sai dai idan daga can zai wuce aiki bazai dawo ta gidan ba..itama Ammi duj zataje da kanta take driving kanta tareda yaran...motar shiru har suka isa gidan Lamido ba wanda yayi mgn cikinsu...a tare suka bude mota suja fito snn suka nufi entrance din gidan...daddy ne yayi sallama Lamido ya bashi izinin shiga snn suka shiga makeken parlon nashi...as usual yana zaune kan kujera yana kallonsu har suka karaso duk suka zauna a kasa snn suka fara gaisheshi..amsawa yayi cikin dattako da kamala irin nashi kafin yayi shiru yana kallonsu kmr bazaiyi mgn ba sai can kuma yace"Maimuna mgn ce nakesonyi dake"..kai a kasa Ammi tace"ina sauraronka Baffah"..yace"ina fatan Ahmad ya sanar dake yanda mukay dashi jiya"..kai ta daga tareda fadin"ya sanar dani"..Lamido yace"MashaAllahu...yanxu meye shawaranki akai?.."da sauri tace"ai ni banida wani shawara face bin umarninka Baffah..duk hukuncin daka yanke daidai ne Allah yasa haka shi yafi alkhairi"..cikin murmushin jin dadin kalamanta yace"to Madallah Maimuna Allah ya maki albarka"..ta amsa da"Ameen Ameen"..shiru dakin ya sakeyi kafin Lamido ya tsayar da idonshi kan Aysha da taji wani hadadden tashin hankali ya risketa yanxun nan..haka nan jikinta ya bata wnn kiran na Lamido bana lafia bane..gashi sai wani mgn sukeyi a kunshe ta kasa gane me suke cewa...ganin yanda duk tabi tayi tsuru tsuru tana rarraba ido Lamido ya saki murmushi wai tunma kafin taji mgnr da zai fada nata knn..dama yasan zaisha rikici ba dan karami ba da yarinyar nan amma saidai ko mutuwa zatayi bazai canxa mgnrshi ba..cikin muryar daya kusa sata fitsari yace"Aisha"..a firgice ta dago kai tana kallonshi har hawaye sun fara ciko idanunta..Lamido bai damu da hawayen nata ba yacigaba da mgn"kin turo mahaifinki jiya akan mgnr wanda kikeso koh?.."da sauri ta gyada mishi kai kmr mara hankali..Lamido yace"Alhamdulillah to inaso ki sanar dashi cewa ni Lamido na dade dayi maki miji"..wani irin zare idanu tayi tana kallonshi kmr bata gane me yace ba...ganin haka Lamido ya sake daure fuska yanda bata isa ta kawo mashi wargi ba yace"kinji abunda na fada ko in sake maimaitawa?.."nan take ta dawo daga suman zaunen da tayi hawaye suka shiga sauko kan fuskanta tace"na..ji"..yace"MashaAllah saiki kirashi ki fada mashi"..sake gyada mashi kai tayi hawaye na sake tururuwar zubowa fuskanta...har wani sarawa taji kanta nayi sbd tsabar tashin hankali..tunda take zata iya ranstuwa bata ta6a tsintar kanta cikin tsananin tashin hankali irin wnn ba..me Lamido yake nufi da yayi mata miji ne wai?..yanxu yana nufin bazata auri baby ba?..kuma waye shi wnn mijin da yayi mata?..lokaci daya ta kasa daurewa ta saki wani irin kuka tareda dora hannunta a kai kmr wanda uwa da ubanta suka mutu..shknn tasan ta riga ta gama yawo domin Lamido bazai ta6a canxa mgnrshi ba..abune wanda tasan ya zamar mata dole ta auri za6in da yayi mata amma shin waye wnn za6in nashi?..meyasa tun tuni bai ta6a furta yayi mata miji ba sai yanxu?..meyasa saida ta kawo wanda takeso Lamido zaiyi mata haka?..kuka takeyi wiwi tamkar wanda ta rasa iyayenta..Lamido sai yayi relaxing kan kujeran da yake yana kallon yanda take kuka kmr ranta zai fita..ganin haka daddy ya daka mata tsawa yana cewa"Aysha bakida hankali ne zaki tasa mu gaba kina mana kuka haka?..so kike ki nuna ba'a isa dake bane ko yaya?.."da sauri ta hau girgiza kai har yanxu hawaye basu dena ambaliya kan fuskanta ba ko mgn ta kasayi. Jama’a wa kuke ganin Lamido ya za6a a matsayin mijinda zata aura..Bobby ne?..ko kuma wani ne daban?..🙄 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 43 Kuka takeyi sosai cikin tsananin tashin hankali da rashin sanin tudun dafawa...yanxu wnn mgnr na Lamido na nufin auren dole za'ayi mata knn?..yanxu suna suna nufin ta rabu da baby knn?..innalillahi wa inna ilaihi rajiun...bude baki daddy ya sakeyi da nufin yayi mata masifa sai Lamido ya daga masa hannu alamar he shouldn't say a word..ba musu yaja bakinshi ya rufe yana kallonta..Ammi dama tana zaune ko kai bata dago ba balle tayi mgn...kallonta Lamido yayi fuska a daure ya sake kiran sunanta...ta dago tana kallonshi hawaye nata sintiri kan cheeks dinta...murya a dake yace"anyi maki wani abun ne kikema mutane kuka?.."shiru tayi kai a kasa..a fusace Lamido yace"ba mgn nake maki bane?.."girgiza kai ra shigayi da sauri tana runtse idanunta...yace"to kan wane dalili zaki zauna kina mana kuka?..ko kinga abokin wasanki a nan wurin,?.."nan ma kai ta sake girgiza alamar babu..yace"then wipe off those tears tun kafin raina ya 6aci..kika bari na sakejin kukanki kuma zakiga matakin da zan dauka"..tsit tayi tana toshe baki da hannayenta...shi kuma ya zuba mata ido har saida ta goge hawayen tas snn ya juya yana duban daddy yace"Ina Najeeb yake?.."kai a kasa daddy yace"yaje wajen aiki"..Lamido baiyi mgn ba sai wayarshi daya dauka nan kusa dashi yayi dialing number Najeeb..yana fara ringing Hamma Najeeb ya dauka da fadin"barka da safiya"..Lamido yace"barka dai..kana ina yanxu?.."Najeeb yace"ban dade da shigowa office ba"..yace"to ka dauki excuse ka dawo gida inason ganinka yanxun nan"..da sauri yace"Baffa lafia kuwa?.."katse wayarshi Lamido yayi bayan yace"ka hanzarta ba zaman jiranka zamuyi a nan ba"..su daddy dai na zaune sunajin me yake cewa amma ba wanda yace uffan...zaman kurame suka shigayi a parlon har Najeeb ya karaso...waje Lamido ya nuna mashi kusada Aysha ya zauna snn ya sake daure fuska yanda zai dauki mgnr da zai fada da muhimmanci kafin ya nuna Aysha da hannunshi yace"fadamun ya kake da wnn yarinyar?.."kallonta Hamma ya juya yayi snn ya dawo da kallonshi ga Lamido cikeda mamakin tambayar...cikin tsawa Lamido yace"bada kai nake mgn bane?.."da sauri yayi kasa da kanshi kafin yace"qanwata ce ita"..Lamido ya sake cewa"qanwarka kawai?.."juyawa Hamma ya sakeyi ya kalli su daddy snn ya kuna juyowa ga Lamido yaga yanda ya tsareshi da ido sai yace"kuma tanada sunan Mamana"..duk yanda Lamido yakai da daurw fuska saida mgnr nan ya bashi daria..wai tana sunan mamanshi..amma wnn yaro Najeeb ba dan karamin soko bane...hatta su daddy saida mgnr ya basu daria kuma duk basu kawo komai a ransu ba saida Lamido yace"to itace wadda na za6a maka matsayin matar da zaka aura kamar yanda kaima kaine na za6a mata matsayin mijinda zata aura"..wani irin diff dakin yayi kmr anyi ruwan sama an dauke...daddy da Ammi syka shiga kallon kallo dan ba wanda tunaninshi yazo nan wurin...Aysha kuwa wani irin darammm taji gabanta ya fadi ta shiga zare ido kmr wata zakanya ta juya tana kallon Hamman da shima idanunshi ke kanta yana zare ido...relaxing Lamido yayi yana kallon yanda suke kallon kallo a tsakaninsu..daga reaction dinsu ya fahimci mgnr a bazata yazo musu...har yanxu kuma parlon tsit an rasa mai kwarin guiwar da zai fara mgn cikinsu...baki Aysha ta bude zata sake rushewa da kuka Lamido ya daka mata wani tsawan da batasan sanda ta kankame Najeeb dake zaune kusada ita ba...ba shiri ta hadiye kukan tsaf tana cigaba sauke numfashi gamida rarraba ido kmr shege a rabon gado...wani shiru dakin ya sake dauka kafin Lamido ya juya yana fuskantar su daddy yace"Ahmad ko baku fahimci mgnr dana fada bane?.."daddy ta hadiye wani yawu daga bakinshi kafin cikin karfin hali yace"mun fahimta Baffa..kuma munyi na'am da haka ubangiji ya sanya alkhairi a ciki"...kasaitaccen smile Lamido ya saki ya dubi Ammi ita yace"kema kin amince Maimuna?.."har yanxu kanta na kasa tace"na amince..Allah ya tabbatar da alkhairi"..wanu murmushin Lamido ya kara saki kafin yace"Allah ya maku albarka"..suka amsa da Ameen snn ya sake juyawa ga iyayen gayyar wato Lamido da Hammanta...idanunshi ya tsayar kan Najeeb da yake ganin komai dake faruwa kmr a faraki yace"daga yau inaso ka fara daukanta matsayin matar da zaka aura ba wai qanwa ko mai sunan Mamanka ba..kema kuma ki tabbata kin bashi wnn matsayin don ko mutuwa daya daga cikinku yayi sai an daura wnn auren..kuje na sallameku"...mikewa Hamma yayi da kyar ya juya zai fita daga parlon Lamido yace"dawo ka tafi da ita"..ba musu ya dawo tareda durkusawa ya kama hannunta ya mikar da ita tsaye snn ya shiga janta kmr mara lafia suka fita daga parlon...juyawa yayi wajen su daddy yace"kuma kuna iya tafia Allah ya maku albarka"..bayan sun amsa da Ameen duk suka mike suka sake mishi sallama zasu fita Lamido yace"Ahmad ka tabbata ka fada masu suyi kokari su fahimci junansu kafin ta gama makaranta don wnn aure ko mutuwa nay banaso a fasa yinshi"...gyada kai daddy yayi before"zanyi kokari in Allah ya yarda..mun barka lafia"..daga haka ya juya yabi bayan Ammi suja fita daga parlon...basu samu su Aysha nan compound ba hakan ya nuna musu cewa kilan sun wuce gida dan haka shima ya bude nashi motar suka shiga wnn karon da kanshi ya jata suka bar gidan...a hanya Ammi tayi tsit ta kurawa waje daya ido tana tunani...gangarawa gefen titi yayi yai parking tareda jama hannunta ya rike cikin nashi...ta juyo da sauri tana kallonshi sai kuma ta sakar mashi smile dinta me kyau...kallonta yakeyi da damuwa yace"kiyi hakuri Maimunatu"..Ammi ta dan wara ido tana dubanshi tace"hakurin me kuma?.."yace"nasan bai zama lallai kiso wnn hadin nasu ba amma inaso kisan babu yanda zamuyi da Lamido tunda ya riga ya furta"..hannunshi itama ta rike tana sakin murmushi tace"ko kusa bana kin auren Aysha da Najeeb wlh..kawai mgnr ne yazomin a bazata kasan ban ta6a kawo a raina wai shine mijinda ya za6a mata ba...Najeeb yaron kirki ne mu muka raineshi sbd haka babu wanda ya dace da auren Aysha idan bashi ba..nasan zai riketa da kyau kuma zai iya bida ita a hankali sbd rashin jinta"...ajiyar zuciya daddy ya sauke yana kallonta da murmushi..gaskia Maimunatu matar arziki ce...da wnn maganganun nata sai yaji duk kokwanton da yake akan batun ya gushe..tabbas shi kanshi yasan Najeeb yaro ne mai hankali kuma bayada wani mugun hali da za'a hanashi aure sbd shi..dadin dadawa kuma danshi ne domin shi ya rikesh tun yana dan karami kuma kmr yanda ta fada zai iya da Aysha sosai sbd ya riga dama yasan halinta ciki da bai so basu da damuwar komai...tayar da motar yayi suka karasa gida kowa ranshi fess dan Allah ya gani sunyi na'am da wnn za6in na Lamido...a parlor suka iske Najeeb din zaune ya buga uban tagumi ga kukan Aysha daya karade dakin gaba daya...yana jin shigowarsu ya mike da sauri ya isa garesu yana cewa"dan Allah daddy babu yanda za'ayima Lamido ya janye mgnr auren nan?.."kallonsh duk su biyun sukeyi kafin su hada baki wajen cewa"baka sonta ne?.."wani irin kunya yaji ya rufeshi dajin tambayan nasu...shaf ya manta fa iyayenta ne and suna iya jin babu dadi idan ya nuna bai sonta..amma shi harga Allah ba kinta yake ba kawai abun ne yazo mishi unexpected sai kuma wnn uban kukan da take sai kace ance za'a aura mata dodo...girgiza kai ya shiga yi da sauri yana nuna kofar dakinsu yace"kawai..banaso ayi mata dole ne..rufe kanta tayi fa a daki taketa kuka daddy kada wani abun ya sameta"..kama hannunshi daddy yayi suka karasa cikin parlor suka zauna snn yace mishi"indai don wnn ne ka kwantar da hankalinka ai ka riga kasan yanda take dama..wnn kukan koma waye akace zan za6a mata sai tayishi so wnn kar ya dameka ko kadan..kawai kacigaba da addu'a"..kai kawai ya iya gyadawa cikin ranshi yana jinjina kalar darun da za'ay da ita don yasan dole ne sai tayishi wlh...mikewa yayi bayan yayi musu sallama ya koma wurin aikinshi yayinda Ammi ma ta shiga kitchen shi kuma daddy yai zaune a parlon yana sakawa da kwancewa..fatanshi kawai Allah ya daidata al'amura kada azo ana samun matsala...Aysha kuwa tana daki tanata rizgar kuka ba wanda yabi ta kanta don a cewarsu idan ta gaji dan kanta zata dena kuma zata bude kofa ta fito ko don yunwar cikinta kuwa. A hankali ya bude idonshi daga nannauyan baccin daya daukeshi as a result of drugs dinshi da yasha..duba yakai ga agogon dakin yaga it's almost five dan haka ya sauka daga gadon da sauri ya fada bathroom yayi alwala ta fito snn ya tada sallah yana jin haushin rashin tashinshi da sukayi har time din sallah ya wuce...yana idar da sallah Sab ya shigo dakin yana dubanshi yace"waziri yace wai ya jikinka?.."mikewa yayi daga inda yayi sallahn yace"da sauki..muje"..tare suka fita zuwa parlon waziri shi da Sab din...yana ganinshi ya saku murmushi tareda furta"jiki yayi kyau knn?.."murmushi shima Bobbyn ya sakar mishi har suka karasa ciki..nan kusada wazirin ya zauna yana dubanshi da murmushi..so yake ya tambayi ko sunyi mgn da Lamidon amma baisan ta yaya ba...bayan waziri ya sallami baqin dake tare dashi ya shiga duban Bobby fuska da murmurshi sosai yace"zaka iya rakani wani waje yanxu?.."a hankali Bobby ya daga mishi kai alaman zai iya..waziri ya maida dubanshi ga Khalid dake zaune parlon shima yace"kaje kace a fitomin da mota"..ba musu khalid ya juya ya fita shi kuma waziri ya mike tsaye tareda kama hannun Sab yace"kaima muje kayi mana rakiya mai sunana"..a tare suka fita duk su ukun zuwa motarshi da har an fito da ita...makullin motar ta kar6a daga hannun driver dinshi ya mukawa Sab yace yayi driving dinsu...ba musu Sab ya amsa key din dukda cewa baisan kan garin sosai ba...ya bude driver seat ya shiga su kuma suka shiga baya snn ya tada motar suka fita daga gidan...saida suka hau babban titi Waziri yace"zaka iya gane Gra?.."a hankali Sab yace"da kyar zan gane gaskia"..gyada kai waziri yayi yace"to muje zanyi directing dinka"..haka kuwa Sab yaja motar suna tafe yana nuna mishi hanya har suka shigo Gra...suprise yakeso yaima Bobby shiyasa bai sanar mishi inda zasuje ba..yaso ace yareda uncles dinsu sukazo amma bazai iya jira har su dawo daga aiyukansu ba shiyasa yaga gwara ya fara zuwa shi kadai suyi mgn gemu da gemu da Lamido inyaso daga baya sai su sake dawowa tareda 'yan uwan mahaifinshi don kawo dukiyar aure...waziri nacigaba da nuna ma Sab hanya har suka iso Lamido's Palace...wani irin bugu zuciyar Bobby yayi da yaga an rubuta The Lamido's 6aro 6aro a can saman gate din estate din...duk fadin Gombe kuma yasan Lamido ne kadai mutuminda yayi suna da sunan sosai dan haka ba tareda wani tantama ba brain dinshi ya fada mashi cewa wnn estate dinsu Lamido ne...lumshe ido yayi tareda jingina da kujera knn hakan na nufin Waziri zuwa yayi suyi mgn da Lamido?..wani irin faduwa gabanshi ya sakeyi daya tuna cewa fa tayi bata sonshi..yanxu idan sukaje ta sake tozartashi tace bata sonshi fa?..hankalinshi yaji ya tashi har wani zufa ya faraji na ba gaira babu dalili amma yayi kokari bai bari waziri ya fahimta ba har aka bude musu gate suka shiga ciki...tafia sukayi ba wani mai nisa da yawa ba suka karaso gidan Lamido...daga nan waje Sab yayi parking motar snn duk suka bude suka fito...suka sanya waziri a tsakiya suka shiga cikin gidan...daidai entrance suka hadu da wani brother din daddy ya fito daga parlon Lamido yana ganin Waziri yayi saurin dunkule hannu tareda risinawa yana fadin"Allah ya taimaki Waziri...barka da zuwa"..Waziri ya amsa da"barka dai Mahmoud..ya iyali?.."Mahmoud Lamido yace"suna lafia lau Waziri..a fito lafia"..Waziri ya gyada mishi kai yana murmushi..sai a snn Bobby da Sab suka gaishe da mutumin snn sukabi bayan Waziri zuwa cikin parlon...Lamido na ganinsu ya fadada murmushin fuskanshi yace"Waziri ne a tafe?.."Waziri daya karasa ciki ya zauna kan one of kujerun dake parlon yace"wlh nine Lamido"..Lamido yace"to barka da isowa"..Waziri yace"yauwa..ga jikokinka nan na kawo makasu har gida"...kallonsu Bobby Lamido yayi yana cigaba da murmushi yace"yaran Attahiru koh?.."Waziri ya gyada mash kai shima yana murmushi...Bobby ne ya fara gaisheshi kai a kasa sai Sab shima ya gaisheshi...bayan gaisuwa Waziri yace"jiya na kira wayarka ai"..Lamido yace"na gani wlh..lokacin ne ina tareda Ahmad kan batun auren 'yarsa daya taso shiyasa banga kiran naka bama sai daga baya"..waziri na gyada kai yace"ikon Allah watace zatayi aure cikin yaran nashi?.."Lamido yace"babbar ce wai ta turo a sanar dani wani dake neman aurenta yanaso ya turo shine nace ta dakatar dashi dan na riga nayi mata miji tun tuni"...wani irin faduwa gaban Bobby yayi kirjinshi sai up and down yake fatanshi bai wuce Allah yasa ba akanta ake mgn ba...shi kanshi waziri zuwa yanxu gaban nashi faduwa yake yace"wacce daga cikin yaran wai?.."kai tsaye Lamido yace"Aisha mana..ina wnn yaro Najeeb?.."Waziri yace"dan wajen marigayi Auwal koh?.."Lamido yace"yauwa to shine wanda na za6a a matsayin mijin nata..kasan ubanta shi ya rike Najeeb din kuma nasan ba wanda zai iya zama da ita sai shi shiyasa na tarasu na fada musu ko bayan raina ban yadda a fasa wnn auren ba"...wani irin tari ne ya sarke Bobby kaman wanda ya kware da wani abun...hankalinshi yakai kololuwar tashi har wani zufa ya faraji all of a sudden ga kuma coughing da taketa faman yi non stop..nan take hankalin Waziri ya tashi shima..Sab ya rikoshi yana yana shafa bayanshi amma kmr tunzurashi suke don cough din sai karuwa ma da yayi...da sauri Waziri ya mike yana duban Sab hankali a tashe yace"kamoshi muje asibiti"...Lamido ya mike shima yana dubansu yace"ina zuwa"..daga haka ya shiga wani corridor dake nan cikin parlon..bayan few minutes ya fito rikeda goran zamzam da akayima addu'a a hannunshi..yana karasowa ya bude tareda kafa goran a bakinshi nan da nan kuwa ya shiga shan ruwan kaman an aikoshi...saida tasha almost half snn ya cire baki tareda yin kasa da ido yana sauke numfashi...hawaye ne sosai suke cikowa idonshi amma bayason su zubo...bayason ko waziri yaga wnn tears din sbd ya gaji da zubar da hawaye a gabansu...zuciyarshi wani irin rauni tayi mashi wanda bata ta6ayi masa irinshi ba...kokari yake sosai na ganin ya 6oye abunda yakeji amma abun yaci tura sbd bashi keda control din kanshi ba...runtse ido yayi yana maimaita innalillahi a cikin zuciyarshi har yanxu kuma bai denajin hadadden zufa na lullu6eshi ba...kallonshi Lamido yake cikeda mamaki yace"meya sameshi ne haka?.."Waziri ne yayi karfin halin cewa"dama baida lafia don daxun aka sallamoshi daga asibiti..ina ganin zamu tafi kawai a sake maidashi can"...da sauri Lamido yace"a maidashi gaskia don wnn tarin nashi bana lafia bane..Allah ya baka lafia Attahiru"..ya karasa mgnr referring to Bobby dake dafe da chest dinshi da hannu daya dai kuma daya hannun ya dafe head dinshi da yaketa jujjuyashi from side to side...Sab har ya fara hawaye shima a haka ya kamashi zuwa inda yayi parking mota..bude baya yayi ya sashi ciki snn yayi saurin zagawa zuwa driver seat Waziri kuma ya shiga baya suka tafi...kai tsaye asibitin da suka baro daxu ya shiga nuna masa suka maidashi. Aysha kuwa yini tayi daki tana kuka ba wanda yabi ta kanta saida su Husna suka dawo..sune sukaita tambayanta meya faru amma ta kasa ko bude baki balle tayi musu bayani...ganin abun nata bana kare bana kare bane gashi har dare zaiyi bata fito taci abinci ba daddy dake parlonshi ya kira Ammi yace mata"Maimunatu je ku duba yarinyar can don Allah..wnn kukan da take ai saiya haifar mata da ciwon kai"..ajiyar zucia Ammi ta sauke Allah ya sani itama tun daxu takejin kmr taje ta rarrashi kayarta amma sbd kara irin nasu na fulani kasa zuwa tayi...yanxu kuma da daddy yayi mgn da kanshi ko musu batayi mashi ba ta kama hanyar dakin nasu...su Husna na zaune sun sanyata tsakiya tana fada musu cewa Lamido ne yace zai hadata da Hamma Najeeb aure..Husna da bataga wani abun tayar da hankali a mgnr ba tace"to Adda wnn ne abun kuka kuma?..Hamman da kinfi kowa sanin halinshi ne kike kuka sbd zaki aureshi?..ai murna ya kamata kiyi ma"..Husna na rufe baki Ammi data shigo dakin tace"Husna kuje parlor ku jiramu zamuyi mgn"..ba musu Husna ta kama hannun Yusra suka fita...suna fita Ammi ta zauna nan kusada ita tareda kama hannunta ta rike kafin tace"ki tsayar da kukan nan mgn zamuyi"..ba musu takai hannu tana share hawayenta...Ammi na dubanta da kyau tace"bakya son Najeeb din ne?.."da sauri ta shiga gyada mata kai alamar eh..janyota Ammi tayi ta rungume a jikinta tana shafa bayanta tace"to ki dena kukan nan indai baso kike kisama kanki ciwon kai ba..so nake ki kwantar da hankalinki zamuyita addu'a inshaAllah idan ba alkhairi bane Lamido da kanshi zaice ya janye mgnr"..luf Aysha tayi jikin mahaifiyar tata tana sauke numfashi..wato dai duk dunia babu inda ake samun irin wnn nustuwan sai wurin uwa...hankalinta taji ya dan kwanta unlike daxun da take ganin duk tashin hankalin dunia a kanta ya kare...kawai har yanxu ta kasa picturing itada Hamma matsayin mata da miji...jin yanda tayi tsit Ammi ta dagota daga jikinta tana sake rike hannunta tace"kinji abunda na fada maki koh?.."gyada kai tayi a hankali Ammi tace" yauwa kuma banaso shima Najeeb din kice zaki nuna masa wani abu..kucigaba da mu'amalarku kmr da inshaAllah indai ba alkhairi bazaki aureshi ba"..sake gyafa kanta tayi tana fatan Allah yasa ba alkhairi din...mikewa Ammi tayi itama ta mikar da ita tsaye tana cewa"muje to kici abinci..haka nan yau duk kinbi kin dorama kanki damuwa ko abincin bakici ba"...daga haka Ammi ta shiga janta suka fita daga dakin..Lamido dai mamaki fal cikin zuciyarta na ganin yanda Ammi take lalla6ata yau..anya kuwa ba kofar rago ake shirya mata ba?..tasan dai yanda Ammi take da zafi zaiyi wahala tazo ta rarrasheta haka kawai...sai kuma wata zuciyar tace mata kilan sbd tasan ba'a kyauta mata bane shiyasa take haka...ko su Husna dake zaune parlor abun ya basu mamaki ganin Ammi rikeda hannun Addarsu har dinning...ba wai Ammi bata sonta bane no kawai dai basu cika jituwa bane sbd halayen Ayshan da kusan gaba daya basu mata ba..ga kuma kasancewarta 'yar fari shiyasa abun ya hade mata biyu amma yau ga Ammi rikeda hannun 'yarta sai sukay kaman wasu qawaye...daddy daya fito don tafia masjid ya hangosu a dinning Ammi na kokarin serving dinta sai ya saki murmushi hade da girgiza kai snn ya fita daga gidan...Maimunatu sarkin kara yau an ajiye karar a gefe knn...yaji dadin yanda yaga Ayshan har ta dan sauko shiyasa akace dai duk fadin dunia mutum baida wanda ya wuce mahaifiyarshi...babu wanda zai soka kaman ita haka kuma babu wanda zai ji tausayinka ya kuma damu da damuwarka kamar mahaifiyarka...itace zata soka kilan fiyema da yanda kake son kanka..(Rabbi ya sakawa iyayenmu da alkhairi ya basu aljannah).🙏🏻 Saida Ammi ta tabbata taci abincin da yawa snn tace taje tayo alwala ta sameta dakinta...ba musu ta wuce dakinsu tayi alwalan snn ta fito..su Husna suma duk alwalan sukayi snn suka wuce bedroom din Ammi kamar yanda tace musu su sameta a can...a tare sukayi sallahn nasu gaba daya bayan sun idar Ammi tace duk su sa 'yar uwarsu a addu'a idan akwai alkhairi tsakaninta da Najeeb Allah ya tabbatar idan kuma babu Allah ya kawo mafita..Aysha dai sam ba wnn addu'an takeso ayi ba tafiso kawai suce Allah ya kawo hanyarda fasa auren inyaso sai kowa Allah ya hadashi da alkhairin nashi a gaba...zata iya hakura da auren baby amma bazata iya auren Hamma da take mishi kallon dan uwanta da syka fito ciki daya ba. Washegari ta tashi da dan dama dama don batayi kuka ba kwata kwata saidai yawan tunani...tun jiya taje tunanin yanyar da zatabi wajen sanar da Prof halinda ake ciki amma ta kasa...hakan yasan ta sanar da Ammi ita kuma tace idan daddy ya dawo fada mashi sai ya kirashi da kanshi yayi mashi bayani sbd kada ma yayi zaton ko yaudaranshi zatayi...da wnn shawara na Ammi ta dan samu nustuwa amma dukda haka tana tunanin halinda bawan Allahn nan zai shiga duk ya samu labari...daddy na dawowa Ammi ta fada mishi yanda sukayi yace ta kawo numbershi ya kira da kanshi suyi mgn..ba musu ta bashi number nashi snn ta zauna nan parlon daddy ya kira number...yana dagawa daddy yace shine mahaifin Aysha sai kuma ya dora da fadin yanda sukayi da Lamido kan batun zuwa neman aurenta da yace zaiyi...hankalinshi ya rashi sosai wanda hatta daddy saida yaji tausayinshi...ya kwantar mashi da hankali tareda cewa sucigaba da addu'a idan Allah yayi akwai rabo a tsakaninsu zasu auri juna idan kuma babu rabo sai kowa ya rungumi kaddara...Aysha dai na zaune tana sauraronsu tanajin tausayinshi na kamata sosai..bawan Allah dama tasan zai shiga mawuyacin hali...nasiha daddy ya sake mata snn yace ta tashi ta tafi Allah ya mata albarka. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 44 A hankali Bobby ya bude ido daga nannauyan baccinda ya daukeshi as a result of alluran bacci da aka bashi...a take maganganun Lamido suka shiga dawowa kwanyarshi..."shine wanda na za6a mata a matsayin miji..ko bayan raina ban yadda a fasa wnn auren ba"...wnn words zai iya cewa tunda yake bai ta6ajin words da suka tayar mishi da hankali kamarsu ba..kalmomi ne marasu yawa a baki amma tabbas yasan sunada nauyin da zasu iya tarwatsa duk wani farin ciki da yayi saura cikin rayuwarshi...kalmomi ne dake kokarin nesantashi da macen da yafi so duk dunia idan aka dauke Mummy...hakan kuma yana nufin rabuwa da ita na har abada..runtse idonshi da yaji har wani yaji yake mishi sbd tsabar tashin hankali..har yanxun heart beat dinshi bai dawo daidai ba..yanxu shknn Lamido aure zatayi ta barshi?..sake runtse ido yayi zafin da idonshi keyi na karuwa kuma ko alamar hawaye babu a cikin idon..wato shi kanshi kuka ma rahama ne..kawai the taught of her getting married to someone yasa yaji another zazza6i yana son rufeshi...dama tun farkon ganinshi da Najeeb din nan yaji bai kwanta masa ba ashe shine wanda zai zama silar rabashi da ita..dukda ba sonshi take ba yana fatan watarana zata soshi and now Lamido yayi ruining komai...Mummy ce ta shigo dakin tareda Aunty Munubiya da basket din abinci a hannunta..Waziri kuma tin daxun doctor yace a maidashi gida because yana bukatan hutu shima if not yana iya faduwa sbd damuwan daya daurama kanshi..dole haka ya hakura ya koma gidan don shi kanshi yasan idan bai samu hutun ba kaman yanda likita yace yana iya komawa gidan jiya..gaba daya yaron ya tsaya mashi a rai matukar tausayinshi yakeji..ashe dama har yanxun ana samun irin wnn soyayyar?..shikam wane taimako ya kamata yayima yaron nan matsayinshi na kaka kuma waliyyinshi?..wane kokari ya kamata yayi don ganin ya samu wnn jika ta Lamido daya kwallafa rai a kanta?...Mummy na isa ta zauna nan kusada shi tareda kamo hannunshi ta rike cikin nata kawai ta shiga binshi da ido...a hankali yasake bude idonshi a kanta kafin ya kuma maidasu ya lumshe muryanshi na fita da kyar yace"mu..koma gida..Mummy pls..i don't want to stay here anylonger"..damke hannunshi Mummy tayi hawaye na ciko idanuwanta tace"zamu tafi..amma first ka fara kwantar da hankalinka ka samu sauki tukunna"..tun kafin ta rufe baki ya shiga girgiza kai still idonshi a kulle yace"bazaki ganeba Mummy..aure za'a mata..aure zatayi ta barni..kakanta yace ya za6ar mata miji Mummy bazan iya cigaba da zama garin nan ba mu koma kano please!."kuka ne sosai yaci karfin Mumny dake rikeda hannunshi ta kasa cewa uffan...Aunty Munubiya kanta saida kwalla ya cika mata ido..karasawa tayi kusa dashi bayan tayi dropping basket dake hannunta tace"dama sbd ita kazo Gombe ba sbd grnadfather dinka ba?..kana tunanin idan kuka tafi yanxu waziri zaiji dadi ne?.."mikewa ya shiga kokarin yi zaune da sauri Mummy ta taimaka mashi ya jingina da pillow..har yanxun ya kasa bude idanunshi don yana budewa zafin da yakeji cikinsu ke sake karuwa..yakai duk hands dinshi ya dafe forehead dinshi dasu cikin muryanda ke nuni da tsagwaron damuwar da yake ciki yace"Aunty bazan iya zama ba..bazan iya zama bayan nasan zata auri wani ba"..yana rufe baki Aunty Munubiya tace"to idan ka koma kanon kana tunanin ka dena ganinta ne?..karewa ma naga a college dinka take karatu kuma hutu na karewa zata koma tunda ba gamawa tayi ba shima sai kace zaka bar college din sbd ita?..get a grip of yourself mana Bobby..be a man inshaAllah Allah bazai barka haka ba"...sauraronta kawai Bobby keyi without saying anything..bazasu gane bane..bazasu ta6a gane halinda yake ciki ba shiyasa duk zasuyi wnn maganganun...a yanda yakejin zuciyarshi yasan dab take da samun matsala shi kuma baison yacigaba da zama yana dorawa Waziri damuwa kada hakan yayi sanadin da hawan jininshi zai sake tashi...gaba daya Gomben ta fita a ranshi and matukar ba komawa Kano yayi ba yana iya samun matsala...da za'a taimakeshi a cireta daga college din ma shi da yafi mashi yanda idan ya tafi ya dena ganinta kenan for good...sake komawa yayi ya kwanta zuciyarshi na cigaba da bugawa da gudu...Mummy takai hannu tana shafa uban gashin kanshi da bai cika askewa ba tace"ko tea bazaka sha ba Bobby?.."gyada mata kanshi yayi alamar bazai sha ba..da sauri Aunty Munubiya tace"aa ya kamata kaci wani abun gaskia..doctor yace kafin medication ya zama lallai kaci abinci"..banza kawai yayi da ita idonshi rufe don gani yake bazata gane halinda yake ciki ba...da kyar da sidin goshi suka samu yasha tea din snn ya sake komawa ya kwanta before time din medication. Washegari ma haka ya tashi ba walwala dukda cewa fevern da yakeji ya sauka amma har yanxun bai dena ciwon kai da jiri ba...tunda ya tashi baiyi mgn ba duk yanda aunty sumy taso yace wani abu kin kulasu yayi sai binsu da yake faman yi da ido kmr bai sansu ba..fuskan nan nashi kuwa a tamke kamar na shanu shi kadai yasan abubuwan da yakeji a cikin ranshi...da yamma sai ga Lamido yazo dubash tareda daddy da baima san yana garin ba saida Lamido yace yazo ya rakashi duboshi...mamaki sosai ya kama daddy ganin yanda ya koma cikin lokaci kankani dukda cewa a haka kokari yake yaga bai nuna musu asalin damuwar da yake ciki ba..da yake sun samu waziri a asibtin basu suka tafi ba sai dab da magrib...daddy na zuwa gida yace Ammi ta shirya ita dasu Aysha yanaso Najeeb ya kaisu asibiti su dubo jikinshi a daren...haka kuwa duk suka shirya suka fita inda Hamma ke jiransu...tana ganin shine a motar ta wani hade rai tana muzurai..baice mata uffan ba ya bude motar Ammi da su Husna suka shiga baya aka barta a tsaye alamun ita suke nufi ta dhiga front seat knn...budewa tayi ta shiga tana wani kumbura kamar kububuwa..shikam Najeeb daria ma abubuwan nan nata suke bashi wlh...wai shi Maama takema wnn iskancin kawai sbd ance za'a hadashi aure da ita...ya tada motar suka tafi kuma har sukaje asibiti ba wanda yayi mgn cikinsu sai Yusra daketa damun Ammi da tambaya kaman 'yar jarida...bayan ya gama parking Ammi ta bude mota ta fita yaranta sukabi bayanta...itama hannu takai zata bude yayi saurin danna lock yana kallonta...juyawa tayi tana dubanshi fuskan nan a kwa6e tace"Hamma meye haka?..ni ka budemun mota in fita"..tana gama fadin haka sai kuma ga hawaye ya shiga silalowa kan fuskanta shidai yayi shiru yana kallonta baice komai ba...kamar wanda aka tsikara ta dago tana kallonshi tace"Hamma wai dama kana sona ne?..meyasa Lamido ke cewa zai hadani aure dakai?..dan Allah Hamma kayi wani abu bazan iya auranka ba wlh"..matsawa kusada ita ya kamo hannunta yana cewa"ki nustu mgnr da zamuyi knn amma ki tsaida kukan nan first"..ba musu ta hadiye ragowar kukan tareda kai hannu tana goge hawayenta...saida ya tabbata ta dena kukan snn yace mata"haka kika tsaneni dama ban sani ba?.."da sauri ta hau girgiza tace"ni ban tsaneka bafa"..yace"idan ba tsanana kikayi ba meye wnn?.why kike bani attitude sbd ance zan aureki?.."langabar da kai tayi tana dubanshi a hankali tace"Allah ban tsaneka ba Hamma..kawai ban ta6a picturing kaina matsayin matarka ba..kallon dan uwa na jini nake maka Hamma ba kallon mijina ba"..sake kama hannayenta yayi ya rike shima yana dubanta da kyau yace"na sani Maama..hasali nima kallon qanwata nake maki ba kallon matar da zan iya aure ba amma ya zamuyi?..idan kaddaranmu yazo a haka dole haka zamuyi hakuri mu kar6eshi tunda bamuda yanda zamuyi"..hawaye na sake taruwa idanunta tace"kai bakada wadda kakeso ne?.."shiru yayi yana kallonta kmr bazaice komai ba sai can kuma yace"inada..akwai wadda nakeso Maama amma bankai ga sanar da ita ba wnn mgnr na Lamido ya 6ullo"..da sauri ta sake rike hannunshi tace"then muyi mgn da daddy plss..ka fada mashi kaima kanada wadda kakeso nasan inshaAlla bazai rasa yanda zaiyi ba"..hannu yakai yana goge mata hawaye yace"naji i will think about it amma yanxu ki bari mu shiga muyi dubiyan nan tukun..kada su Ammi su gama bamu je ba"..da sauri ta shiga gyada kai tana karasa hawayenta tace"toh na dena"..murmushi ya sakin mata tareda bude motar ya fita itama ta fita suka nufi cikin asibitin...saida ta kira Ammi ta fada mata room number snn suka isa zuwa dakin...Najeeb ne ya fara shiga snn itama ta shiga kai a kasa...Bobby idonshi ke kallon kofa tun daxu yana jiran shigowanta kasa dauke idanunshi yayi a kanta..yanajin zuciyarshi tayi wani tsalle ta dire sbd ganinta da yayi tareda wanda yasan shi zai aureta baisan lokacinda ya runtse ido yana salati sbd zafin da yaji ba..ba kowa dakin sai shi kadai don haka Hamma ya kara karasawa kusa dashi yana dubanshi da murmushi yace"sannu ya jikin"..kai kawai Bobby ya iya daga mash ba tareda ko bude idonshi yayi ba..a yanda yakeji yasan tsaf zai iya kasa controlling anger dinshi na ganinsh da yayi tareda ita shiyasa ko idan yaji budewa balle yayi mashi kallonda zai jefashi tunani...Najeeb bai kawo komai ba a tunaninshi ko jikin nashi ne shiyasa daya gama dubashi ya juya ya fita daga dakin...wani irin shiru dakin ya dauka har suna iyajin numfashin junansu...kallonshi kawai take ganin yanda ya kara haske ga dan rama da yayi sai taga kaman karo mishi kyau akai don sosai taga yau dai yayi mata kyau...shiko bude idanunshi yayi jin har yanxu batace komai ba sai gashi karaf idanunsu sun sarke cikin na juna..da sauri ta dauke nata tana zare ido sbd wani irin abu da taji ya shiga cikin idanun nata har zuwa zuciyarta..bata taba jin irin wnn game dashi ba tadai san for sure idonshi na sata jin wani iri amma ba irin wnn feeling din bane kwata kwata...lumshe idon ya sakeyi kafin ya budesu fes a kanta yanajin kmr ya mike ya sanyata a jikinshi ko zai samu saukin wnn ja'iban da yake ciki...idanunshi sun kada sunyi jajir ga zuciyarshi daketa faman bugawa da mugun sauri...ido ya sake lumshewa yanajin yanda gaba daya ganin nata ya dirar mishi da wani kasala na musamman...wani irin weird feeling yakeji irin wanda bai ta6a ji a kanta ba...addu'a ya shiga karantowa a ranshi wai ko feelings din zasu ragu amma kmr sake hankado mishi su akeyi...sun dauki kusan mintina biyar a haka kafin ta karasa kusa dashi a hankali har yanxu bata bar kallon face dinshi ba tace"ina yini"..bai bude idonsh ba kuma bai amsa ta ba..ta sake cewa"Sir ina yini"..still bai amsa ba sai takai hannu ta dora kan nashi da nufi ta jijjagashi wai ko bai jita bane aikuwa ya kama hannun nata da sauri kmr magnet ya damke cikin nashi...wara ido tayi tana kallonshi da mamaki ashe idonsa biyu dan rainin hankain...kokarin kwace hannunta ta shiga yi nan take yaji wani karfi yazo mishi kawai sai ya mike zaune yana dubanta da idonshi da ya bata tsoro sbd jajir din da yayi...kallonta yakeyi cikin ido eyes dinshi na shinning as a result of hawaye da cikoshi..tunda abun nan ya faru sai yanxun tears suka samu damar zuwa idanunshi amma jiya sai zafi da idon suke ba hawaye ko kadan...kallonshi itama take tana karantar abubuwa da dama cikin idanun nashi wanda bata ta6a tsaiwa ta karance su ba ada..abubuwa ne masu wuyar karantuwa snn kuma masu wuyar fassaruwa amma dukda haka taji ta kasa dauke idanunta a kanshi...hawayen dake idanuwanshi yayi kokarin maidawa kafin yace"can..i hug..u plss?.."wara ido tayi tana kallonshi without saying anything..voice dinshi na rawa ya sake cewa"for this once Aysher plss..mutuwa zanyi"...lokaci guda itama hawaye suka ciko idanunta ba tareda tasan dalilin su ba...ganin kallon da take mishi ya janyota jikinshi tareda wrapping dinta da hannayenshi ya saki ajiyar zucia mai karfin gaske...tana iya jiyo yanda heart dinshi yake bugawa da mugun sauri nan take hawayen dake idonta suka gangaro fuskanta...Bobby ko wani irin sanyi yaji yana ratsa tun daga kwakwalwarshi har zuwa tafin kafafunshi..idanuwasnhi rufe yayinda hawayen dake ciki suka wanke mishi fuska..ji yake inama zasu dawwama a haka shikam daya gama samun komai na dunia...a hankali yayi breaking hug din tareda kamo fuskanta da hannayenshi ya hada da nashi fuskan still idanunshi rufe saidai ba hawaye yakeyi ba yace mata"ina sonki sosai Aysher..morethan any other thing..you are my whole world..my whole heart..you are my.."kasa karasawa yayi ya sake runtse ido sbd wani abu da yaji ya tokare mishi wuya..sake manne face dinshi yayi da nata yana kallon cikin idonta yace"i will die without you.. i will die for sure"..ya karasa yana sake lumshe ido at the same time yana sauke numfashi...Lamido kuwa kuka ta fara wiwi kai kace uwa da ubanta ne suka rasu suka barta a doron kasa...ita kanta kuma bazata ce ga dalilin kukan ba amma for sure tasan akwai tausayinshi sosai a cikin ranta...ta kuma san da gaske yana sonta fiyeda komai kmr yanda yace...sake rungumeta yayi yana shafa bayanta yace"sorry i made u cry...i just feel like saying what i have in mind but am sorry"..girgiza kai ta shigayi alaman ba reason din kukanta knn ba tace"aure za'ai min"..yace"i know"..tace"Hammana zan aura"..nan ma kai ya sake gyadawa yace"i..know"..a hankali ta bude ido tana kallonshi cikin sigar lallashi tace"am sorry"..yace"u don't have to..i forgave u already"..kai ta shiga gyadawa tana sakin smile da wet face dinta tace"thank u..thanks for loving me"..kallonta kawai Bobby keyi yanajn wani abu na zagayawa cikin jininshi and he couldn't help it saida ya kai lips dinshi goshinta ya manna mata peck a wurin snn ya saketa tareda komawa kan gadon ya kwanta yana fadin"thank you"...kallonshi ta tsaya yi tanajin wani bakon abu na zagayawa cikin jikinta...karasawa tayi kusa dashi idonta akan fuskanshi tace"Allah ya baka lafia..zan tafi"..kai kawai ya iya daga mata tareda dan sakin murmushi wanda baikai zuci ba...saida ta juya zata tafi ya bude ido yana kallonta har ta fita daga dakin snn ya sake lumshe idon tareda kai hannu yana dafe saitin heart dinshi dashi. Kwananshi biyu a asibiti aka sallameshi a ranar kuma ya dage sai sun wuce kano waziri yace bazasu tafi a ranar ba.. dole suka bari the next day shima kuma bada son waziri ya bari suka tafi ba..ba yanda zaiyi ne kawai sbd yanda yaga Bobby ya daga hankalinshi ne amma da bazai bari su tafi ba musamman daya kasance har yanxu ba gama warkewa yayi ba...shi kuma yayi hakan ne sbd yanaso ya nesanta kanshi da ita and hakan bazai yiwu ba don idan yana Gombe jin kanshi yake yana kusa da ita amma idan ya koma kano zai samu sauki ya sani...idan ta dawo college kuma tsaf zai iya dena shiga makarantan ma gaba daya balle watarana ya ganta abunda yake kokarin 6oyewa ya tona masa asiri...da wnn shawara na zuciyarshi yayi na'am ya kumayi tawakkali tareda mika lamuranshi ga Allan don yasan shi kadai yakeda ikon canxa al'amura a lokacinda yaso. Kwana biyu da tafiyarsu Aunty Munubiya da bata koma tare dasu ba ta shirya ta tafi gidan Uncle Lukman wanda yake mazaunin babba cikin 'ya'yan waziri tunda shi yakebin mahaifinsu Bobby...bayan sun gaisa dashi ya shiga dubanta da alamar tambaya yace"Munubiya lafia kuwa naganki gidane irin wnn lokacin?.."cikeda damuwa tace"wlh ba lafia ba Yaya Lukman..mgn ce nazo da ita akan Bobby"..shiru yayi yana kallonta kafin yace"to meya faru?.."a nutse ta shiga koro mishi bayanin kaunar da yakema jinin Lamido da yanda sukaje tareda Waziri akan batun neman aurenta sai kuma sukaji Lamidon da bakinshi yace ya riga ya tsayar mata da miji...tunda ta fara bayani yayi shiru yana sauraronta baice komai ba saida ta kammala yace"to yanxu me kikeso ayi Munubiya?..da bakinki fa kikace Lamido ne yace ya mata miji kuma a yanda nasan Lamido dai zaiyi wahala yayi mgn ya canxa musamman mgnr aure"...yana rufe baki tace"na sani amma bai kamata mu nade hannu mu kasa yin komai matsayinmu na 'yan uwan mahaifinshi ba...so nake dan Allah yaya Lukman kaje ka samu mahaifin yarinyar nan in person ka nuna bakasan da waccan mgn ta Lamido ba kace nemawa Bobby auren yarinyar kazoyi wata kila zai iya cewa ya hadaka da Lamido..daga nan nasan shi kanshi Lamidon zai sake nazari musamman idan ya kasance yarinyar ba son wancan auren take ba..ko don alaqar dake tsakaninshi da Waziri nasan zai iya janye waccan mgn da yayi"...shiru Uncle Lukman ya sakeyi yana sauraronta...tabbas gaskia ta fada amma shin zai iya kuwa?..gani yake kmr zasu fahimci drama suka shirya musu tunda ai Lamido yasan Waziri yasan da mgnr amma meye abunyi?.Allah ya sani shi kanshi yaji yana son taimakon yaron ko don ya samu damar goge tarin laifukan daya aikata musu a baya ciki harda kin amincewa ya nemosu bayan rasuwar mahaifinsu...yayi nadama sosai yanxu ya kuma ji gaba daya ahalin Attahir sun shiga ranshi matuka ko don sbd yanda basu nuna wani alama na har yanxu suna rike dasu ba dukda yasan zaiyi wahala ace sun manta duk abubuwan da suka aikata masu a baya...ganin yanda yayi nisa cikn tunani Aunty Munubiya ta sake lankwasa murya tace"dan Allah yaya Lukman ka taimakawa yaron nan a matsayinka na qanin mahaifinshi...ko don zumunchi ka daure kayi hakan bakasan tarin ladan da zaka samu ba"...ajiyar zucia ya sauke kafin yace"shknn zanje inshaAllah..zan fara bincikawa inji yaushe Ahmad din yake gida sai inje in sameshi"..nan take Aunty Munubiya ta shiga washe baki tana cewa"Allah ya saka da alkhairi yaya..Allah kuma yasa muji alkhairi"..shima yana murmushi yace"Ameen..duk yanda mukayi dashi zakiji"..tace"to shknn yaya..bari inzo in tafi Allah ya saka da alkhairi"...ya amsa mata da Ameen snn tayi mishi sallama ta tafi..cikin gida ta shiga wurin matarshi itama tayi mata sallama snn ta koma gidan waziri don gobe take shirin komawa kano itama dama ga dalilinda ya tsayar da ita nan. Washegari around 4:30 Uncle Lukman ya iso gidansu Aysha bayan sunyi mgn da daddy ya tabbatar mashi da cewa yana gida...daddy ya bude kofar parlonshi ta waje ya shiga dashi nan ciki suka fara gaisawa...bayan gaisuwa kai tsaye Uncle Lukman ya fadi mgnr dake tafe dashi saidai bai 6oye mashi komai ba har yanda Lamido sukayi da waziri kan batun aurenta da Najeeb da kuma yanda shi Bobbyn ya shiga wani hali sbd jin mgnr auren nata...bayani sosai yake mashi dalla dalla kaman yanda ya samu labari wurin Aunty Munubiya...daddy kuwa rsabar mamaki kasa kwakwaran mosti yayi a wurin...gaba daya kanshi ya kulle knn all these while yaron nan yana sonta bai ta6a nunawa ba?..tausayinshi yaji ya kamashi matuka yaji inama yanada hanyar dazai taimaka mashi da yayi haka..inama ikon bayar da aurenta a hannunshi yake da ya bashi ita ko bataso saidai mgn a hannun Lamido yake ba hannunshi ba...har Uncle Lukman ya gama bayani tareda rokon idan akwai taimakon da zai iyayi don a samu sauyin al'amura ya taimaka yayi ko don a ceto rayuwar yaron...hankalin daddy ya tashi sosai ya kumaji tausayinshi ya kamashi fiyeda tunaninshi...yasan yaron baida matsala sam and yanada duk wani quality da iyaye ya kamata su duba wajen za6ama yaransu miji kuma zaifi kowa son ace ya hada jini da Mentor dinshi Col Attahir saidai hakan da kmr wuya tunda bai zama lallai Lamido ya tankwaru ba...hakuri yaba Uncle Lukman sosai tareda alkawarin zaiyi bakin kokarinshi yaga abunda Allah zaiyi saidai suci gaba da addu'a...har ya tafi daddy bai dawo cikin hayyacinshi ba...mamaki kawai yakeyi da har yake mata so irin wnn kuma ya iya 6oyewa har na tsahon lokaci haka...sosai yaji yana son hada zuri'a dashi a daya bangaren kuma yana tunanin shima Najeeb din idan sonta yakeyi fa?..itama kuma Ayshan wanda takeso daban shikam ya zaiyi ya kwance wnn kullin ne?..ya zaiyi ya daidaita al'amuran nan?.."kira Najeeb din zakayi ka tambayi ko shima yanada wadda yakeso"..amsar da wani sashe na zuciyarshi ya bashi knn nan take kuma yayi na'am da ita dan haka ya dauki waya ya dannawa Najeeb din kira yace lallai lallai yanason ganinshi idan ya dawo daga office. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata yafitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 45 Da dare misalin karfe takwas Najeeb yayi sallama parlon daddy kmr yanda yace yazo yana nemanshi...ya karaso ciki ya gaisheshi kafin a hankali ya kira sunanshi"Najeeb"..kai a kasa ya amsa da"Na'am"..daddy yace"tambaya ne nakeson yi maka amma inaso kayi alqawarin zaka fadamun gaskia"..still kanshi na kasa yace"nayi alqawari daddy"..daddy yace"so nake ka fadi tsakaninka da Allah kana son Aysha ko baka sonta?.."shiru Najeeb yayi kai a kasa as tambayar ya masa nauyi sosai..taya zai kalli tsabar idanun mahaifinta yace ba son aure yake mata ba..kai abun da kmr wuya...daddy kmr yasan tunanin da yakeyi knn yace"ka daukeni matsayin mahaifinka ba mahaifin Aysha ba..wata mgn aka zomun da ita mai girma wadda nake sa ran zata iya sa Lamido ya janye mgnr hada aurenku amma fa idan baka so..matukar kana so to ka fada nayi maka alqawarin ko bata sonka zata aureka"..kanshi ya sake dukarwa kasa murya can kasa yace"ni ba son aure nake mata ba daddy...sonta nake tamkar wadda muka fito ciki daya"..wani ajiyar zucia da baisan daga ina ya fito daddy ya sauke cikeda jin dadin wnn amsa ta Najeeb..yanxu dai yasan baya sonta sbd haka zai kai mgn direct to Lamido yaga ko Allah zaisa a dace...nan take ya sallami Najeeb ya tafi tareda ce mishi idan bukatar sake nemanshi ya taso zai kuma nemanshi...haka ya tashi ya wuce yana mamakin wane mgn ne yace ya taso mai girma kuma?..fatanshi dai Allah ya dorasu akan Lamidon ya bar kowa ya auri wanda yakeso. Daren ranar daddy har sallahn dare yayi yana rokon Allah ya dorashi kan Lamido ya amince da mgnr da zaije mashi da ita..Ammi dai na kwance tana kallonshi har ya idar snn ta sake tambayanshi abunda ke faruwa...bai 6oye komai ba ya fada mata duk yanda sukayi da Uncle Lukman ya kuma fada mata yanda sukayi da Najeeb daxu..ita kanta Ammi tayi mamaki sosai jin wai sbd ita ma ya kwanta rashin lafia..bawan Allah ashe haka yake sonta ba'a sani ba...ita kanta zataso kasancewarshi sirikinta ko don yanda kullum daddy ke yabonshi yana fadar kyawawan dabi'unshi...tana duban mai gidan nata tace"amma daddy kana ganin Aysha tana sonshi kuwa?..naga wanda tace zai turo ai kmr bashi bane"..daddy yace"rabu da ita ko babu wnn mgnr ma bazata auri wancan din ba..wai ashe tsoho yarinyar nan taje ta dauko kusan age mate dina wai shi zata aura?.."wara idanu Ammi tayi da mamaki tace"u mean wanda tace zai turo din ba yaro bane?.."daddy yace"babban mutum ne wlh..wai sunanshi Professor Ahmad Kurawa"..Ammi tace"amma duk a ina ka samu wnn labarin?.."yace"Bilkisu na kira daxun..na kasa nutsuwa ne tun bayan mgnr mu da Alhaji Lukman sai na kira nace ta fadamun idan tasan wani abu tsakaninsu tace ita bata fada mata yace yana sonta ba ta kuma bani labarin shi wnn da takeso din"..ajiyar zucia Ammi ta sauke mai karfi tana fadin"wnn yarinya dai bansan irinta ba wlh..sbd rashin hankali duk cikin masu sonta ta rasa wanda zata kawo as wanda zata aura sai dattijo?..Allah ka shirya yarinyar nan"..daddy yace"Ameen..gobe in Allah ya yadda zan kai mgnr Attahir wajen Lamido muji ko zai hakura da wancan mgnr"..gyada kai Ammi tayi tana fadin"to Allah ya kaimu..Allah kuma ya tabbatar da alkhairi. The next morning daddy ko breakfast baiyi ba ya tafi wurin Lamido..as usual ya sameshi tareda jama'a saida ya jira ya gama sallamansu tsaf snn ya matsa kusa dashi yana gaidashi...Lamido ya amsa yana dubanshi cikin mamakin abunda ya kawoshi wurinshi da sassafe haka..mostly sai rana ta farayi yake shigowa amma yau gashi da sanyin safiya...bayan shiru na wani lokaci daddy ya gama tattaro duk wani karfin halinshi kafin ya fara mgn kai a kasa"wata mgn ce dama ta kawoni Baffah"..Lamido yace"dama tunda na ganka wnn lokacin nasan akwai dalili..meke tafe dakai?.."kai tsaye daddy yace"akan batun auren yaran nan ne..kayi hakuri ba nufina inyi jayayya dakai ba amma wata mgn Alhaji Lukman Waziri yazomun da ita jiya wanda yasa nayi tunanin in sake kawota gabanka ko za'a samu maslaha"...kai Lamido ke gyadawa yace"ina sauraronka..wace mgn ce wnn?.."daddy yace"ina wnn yaro dan wajen Col Attahir marigayi?.."Lamido ya gyada kai alamar ya ganeshi..daddy yacigaba da cewa"shine wai ashe yake sonta..ya dade yana sonta fada ne baiyi ba sai yanxun..ranar da sukazo nan tareda waziri mgnr ce ta kawosu sai kuma suka ji cewa ka riga ka fidda mata miji..wnn dalilin nema yasashi rashin lafia har ya kwanta asibiti"..wani irin tsit Lamido yayi kmr baya dakin..tabbas biri yayi kama da mutum..shi kanshi yayi mamakin yanda yanayin yaron ya sauya lokaci guda..tausayinshi yaji ya kamashi meyasa Waziri bai sanar dashi ba?..ga kuma shi wancan yaron Najeeb ya zaiyi dashi?..bayan dogon tunani ya dawo da dubanshi ga daddy dake zaman jiran tsammani yace"shi kuma wancan yaron Najeeb ya zamuyi dashi"..da sauri daddy yace"saida na fara tuntu6arshi kafin na kawo mgnr gareka..ya kuma tabbatar mun da cewa akwai yarinyar da yakeso"...numfashi Lamido ya sauke kafin yace"idan Allah ya kaimu dare kazo mun da iyalan naka gaba daya"..cikeda farin ciki ganin ya kusa cin nasara yace"zan kawosu in Allah ya yadda..na barka lafia"...daga haka ya mike ya sake mashi sallama snn ya tafi...koda yaje gida ya sanar da Ammi yanda sukayi dashi ita kanta ba karamin farin ciki tayi ba..sai a lokacin ya samu yayi breakfast din da bai samu yayishi ba daxu. A can Kano kuwa tunda suka koma Bobby bai sake walwala ba...shi ba mara lafia ba kuma shi ba lafiyayye ba gashi nan ne kawai..gaba daya duniar yake ganin tayi juyin waina dashi daga farin cikin da yake ciki kafin ya santa zuwa baqin cikin da yake ciku yanxu bayan sanin nata...bakin kokarinshi yakeyi wajen ganin bai bar ciwon da yakeji ya kwantar dashi ba amma ko Allah yasan ba karamin wahala yake ciki ba..rabonshi da samun isashshen bacci har ya manta...kullum idan ba sedative yasha ba bai iya yin baccin...yana zuwa hospital dinshi kullum saidai ba wani iya aikin yakeyi ba mostly idan yaje kwanciya yake shima yaji da kanshi...Mummy tayi fadan tayi nasiha tayi magiya kan ya dena dorawa kanshi damuwa amma kwata kwata ya kasa yakice abun a cikin ranshi...kawai imagining yake wai ga Aysha an daura mata aure da wani shikam yasan da kyar idan ba wnn ce ranarshi na karshe a dunia ba...shi kadai yasan halin da yake ciki sai kuma Nur daya fadama duk abunda ya faru...Nur yaji tausayinshi matuka sbd yasan yanda ya kwallafa rai a kan Lamido..ya kuma san irin son da yake mata ba gama garin so bane..so ne wanda zaiyi wahala ta samu maiyi mata irinshi a dunia indai ba iyayenta ba...so ne wanda idan ta kuskura ya su6uce mata to ta tafka babban asaran samun masoyi kamarshi...wnn dalilin yasa kusan kullum Nur na tare dashi tunda har yanxu students basu dawo hutu ba and suna dawowa clinical posting zasu wuce..shike kwantar mashi da hankali tareda assuring nashi cewa komai zaiyi daidai...jinshi kawai yake don yasan zaiyi wahala ace an fasa auren nata. Yau da wuri ya dawo gida sbd ciwon kai da yake fama dashi...yayi nisa cikin tunani har bai lura dasu Mummy dake zaune a parlor ba kawai ya wuce flat dinshi...gaba daya suka bishi da kallo ganin har yanxu Bobby bazai dangana ya mika komai ga Allah ba...ko Sab da zai koma school wnn karon aunty sumy ce ta maidashi madadin shi da yake maidashi koda yaushe...gaba daya Mummy itama cikin tashin hankali take don ganinshi a wnn halin ba karamin daga hankalinta yake ba...mikewa tayi zuwa dakin nashi..yana zaune kan sofa ya zabga uban tagumi da hannayenshi har ta karaso ta zauna nan kusa dashi baisani ba saida takai hannu ta dafa shoulder dinshi ya dago da sauri yana kallonta...kallonshi takeyi itama kafin tace"so duk mgnn da nake fada maka baka dauka ba knn koh?.."ya wani kwabe fuska yana kallonta yace"Mummy to me nayi?.."tace"kaki ka mika lamuranka ga Allah mana..do u think wnn damuwan daka daurama kanka shi zaiyi sorting things out?..baka yadda da ikon ubangiji ba ne?.."hannayenta ya kama ya rike yana dubanta in a calm voice yace"na yadda da ikon Allah mana kawai zuciata ta kasa daukan rasata da nake shirinyi..inama kokari Mummy Allah kadai yasan halinda nake ciki..ciwo nakeji sosai a zuciata Mummy ban san me zanyi ya dena ba"..kama hannunshi tayi tana cigaba da kallonshi tace"na fada maka ka kwantar da hankalinka jikina yana bani cewa ita din matarka ce..idan Allah ya yadda kuma kai zaka aureta ba wani ba"..kallonta kawai yakeyi kmr bai gane me take fada ba..cikeda assurance ta sake cewa"yes..ina nan ina maka addu'a and bi'iznillah Allah bazaiki amsan addu'a na ba"..dan murmushi kawai ya saki without saying anything..gani yake Mummy na son kwantar mashi da hankali ne kawai amma taya al'amura zasu canxa bayan Lamido da kanshi yace ya tsayar mata da wanda zata aura...shidai fatanshi bai wuce Allah ya cire mashi ita daga zuciyarshi ba koya samu ya huta. Zaune suke cikin parlon Lamido gaba dayansu kmr yanda ya bukata...Ammi,daddy sai Aysha da Najeeb..gaba daya suna zaune a kasa while Lamido da tun shigowarsu ya kasa cewa uffan yana zaune a usual seat dinshi...kawai tunanin ta inda ya kamata ya fara yake..kmr bazaiyi mgn ba sai can yace"Najeeb"..a hankali Najeeb da har yanxun kanshi ke kasa ya amsa mashi...Lamido ya gyara zama before saying"tambaya nake son maka kuma inaso ka bani amsa iyakar gaskiayarka"..a hankali ya daga kai tareda fadin"InshaAllah"...Lamido yace"shin akwai wadda kakeso kafin wnn mgnr ya 6ullo?.."shiru dakin ya dauka kowa na jiran yaji amsar da zai bada...ganin yanda yayi shiru kai a duke Lamido yace"ko bakaji abunda na fada bane?.."da kyar ya bude bakinshi yace"ina dashi"..Lamido yace"a ina take?.."shiru ya sakeyi ba mgn a fusace Lamido yace"idan ina maka mgn kanamun shiru zakasa in canxa ra'ayina wlh"..tun kafin ya rufe baki yace"kayi hakuri..a nan Bauchi take"..kallonshi duk sukeyi before Lamido ya sake cewa"Bauchi a ina?..bude baki fa zakayi kayi bayani don idan ba gamsuwa nayi da yarinyar ba bazaka aureta bane"..har yanxun shidai kanshi na kasa yace"sunanta Bilkisu Ibrahim Muqaddas..tare suke makaranta da Maama"...wani irin zare ido Lamido tayi kai kace wani mugun abu ya fada..lokaci guda fuskanta ya washe da murmushi cikin tsantsan farin cikin da taji ya diro mata all of a sudden tace"Hamma are u for real?..da gaske Billyna kakeso?.."dakatawa tayi da mgnr tareda matsawa kusa dashi sosai hadda su kama hannunshi tace"bani labari Hamma yaushe ka fara sonta?..ya akayi ma kana son Billy amma ban sani ba..Hamma dan Allah ka..."bata karasa ba Lamido ya daka mata wani tsawan da batasan sanda ta koma inda take ba da sauri tana rarraba ido..sam ta manta wai a gabanshi suke..farin ciki yasa ta manta da hakan jin wai Hamma da kanshi ne yakeson Billynta..knn hakan yana nufin tun tale tale yana son Billy basu sani ba..shin Billyn tasan yana sonta ta 6oye mata kmr yanda itama bata fada mata Proprietor na sonta ba ko kuwa itama bata san yana son nata ba..duk zaman wurin sai taji ya gundureta Allah Allah take su bar wurin ta samu ta kira Billy taji ya wnn batu yake...Lamido dai maida dubanshi ga Hamman yayi yana cewa"kace mene sunanta?.."a hankali ya sake cewa"Bilkisu Muqaddas"..Lamido yace"jikar Inuwa Muqaddas ce knn?.."kai ya gyada mishi..Lamido yace"to Alhamdulillah 'yar manyan Mutane ce ai..shi Alhaji Muqaddas din was a very goon friend of mine and zan tuntu6eshi da mgnr"..da sauri yace"ai bamu gama daidaitawa da ita ba"..yace"wnn duk ba matsala bane zanyi mgn dashi dai..Allah yasa albarka"..duk suka amsa da"Ameen"..daga nan kuma ya maida hankalinshi kan Hajia Indo mai gayya mai aiki..ta sake sinne kai tamkar tana gaban surkai dukda cikin ranta murna ce fal na jin wnn labarin na Hamma da kuma warware wnn auren da Lamido keson hadawa da akayi..she's super excited kawai sai murmusawa takeyi ita kadai kmr munafuka...ganin bata ma san kallonta yakeyi ba yace"Aisha.."da sauri ta dago tana kallonshi kmr mutumiyar kwarai..kofa ya nuna mata tareda fadin"kina iya tafia"..da sauri ta mike ta kama hanya zata fita tace"Nagode Allah ya saka da alkhairi"..Lamido baice mata komai ba har ta fita snn ya dawo da dubanshi ga Hamma yace"kaima kana iya tafia duk yanda mukayi da Muqaddas din zakaji"..kai a kasa shima ya mike tareda yi masa godia ya fita...ya rage daga daddy sai Ammi a parlon..Lamido na duban Ammi yace"Maimuna kin amince da mgnr dan wajen Attahir?.."kai a kasa tace"na amince..Allah yasa haka shi yafi alkhairi"..yace"to madallah zanyi mgn da wazirin anjima..ita kuma Aisha ina sane naki fada mata sbd nasan hauka zataimn..idan kunje sai ku mata bayani"..daria sosai mgnrshi ya basu haka suka mishi sallama suka fita suna sake darian mgnr daya fada...suna fita Lamido ya dauki wayanshi ya kira Waziri suka fara mgn. dadi sosai daddy yaji da Allah ya sauya al'amura haka?..ya tabbata Attahir zai kasance miji na gari a gareta ko don son da akace yana mata. Aysha na fitowa daga parlon ta shiga kiran number Billy bata dauka ba..sake dialing tayi tana tafiya tana fadin"Billy pick up the call mana..pick up pls"..har ya gama ringing dinshi Billy bata dauka ba ita kuma bata gaji da jera mata missed calls ba...Hamma Najeeb daya biyo bayanta da sauri ya karasa inda take kawai sai ji tayi ya fizge wayar daga hannunta yana kallonta...juyawa tayi tana dubanshi itama sai kuma ta saki murmushi tace"Hamma dan Allah mgnr daka fadama Lamido gaske ne?..da gaske Billyna kakeso?.."harara ya watsa mata mai kyau kafin yace"ban saniba..kiranta kikayi zaki fada mata kou?.."murmushi ta Kara saki tace"of course mana..so nake inji labarin komai in detail amma batayi picking call dina ba"..ta karasa mgn tana turo baki...hannu ya kai ya dan bugi bakin nata before saying"to ban aikeki kije ki fada mata ba dan itama ba sani tayi ba..idan kika barni da kaina zanje in sanar da ita when the right time comes"..kallonshi take tana murmushi sosai tace"to bazan fada mata ba Hamma..amma dan yaushe ka fara sonta?..does she loves u too?.."girgiza kai kawai yayi yana murmushi jin wai tambaya take if tana sonshi..sai kace ba yanxu yace mata bata ma san yana son nata ba shine take mishi wnn tambayan kmr ba itane ta dauke mishi wuta sbd ance zai aureta ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 46 Zaune suke office din Nur tun safe ya baro nashi office din yazo ya tasa shi a gaba shi baije yayi aikinshi ba kuma shima bai barshi yayi nashi aikin ba...kawai yazo ya mishi kwance a office kaman wani mara lafia...for the fifth time Nur ya sake cewa"kaga malam if zaman office din nawa ke maka dadi tell me insan inda dare yayi mun..haka nan kazo Kamin wani kwance office sai kace mara lafia"..banza Bobby yayi dashi kmr baiji abunda yace ba..Nur ya tsaya kallonshi cikeda takaicin wnn iskancin da yake mai...murmushin iskanci ya saki tareda fadin"dont worry nasan maganinka ai..da Lamido zanje in hadaka tunda yanxu naga duk dunia ba wanda kake jin mgnrshi kmr nata"..still Bobby banza yayi dashi idanunshi lumshe sai karkada legs dinshi yake..Nur ya mike tareda tattara papers daya baza kan desk dinshi ya dauki makulli da wayanshi snn ya kama hanya fita yana cewa"to in ka gama saika rufe office din..naga kaman kwana zakayi a ciki"..sai yanxu ya bude ido yana kallon Nur dake neman barin office din yace"wai meyasa bakada mutunci ne Nur..baka ga halinda nake ciki ba da zaka dameni da surutu?.."juyawa Nur yayi yana kada kanshi yace"nine ma Lamido da naki accepting soyayyarka zakazo har office dina ka faramun hayaniya..na tabbata ko ita da tayi turning dinka down bakayi mata irin wnn wulakancin ba sai ni daka gama rainama wayo..don't worry nasan maganinka"..dafe head dinshi yayi yanajin yanda wnn iskancin na Nur ke neman kara mashi tension kan wanda already yake ciki..wayanshi ne ya fara ringing ya dauka da sauri ganin Mummy ce yayi picking tareda kaiwa ears dinshi before yace"Mummy"..a daya 6angaren full of excitement Mummy tace"Bobby guess what?.."dan shiru yayi kmr me tunani kafin yace"Mummy kinsan am not a good guesser kawai ki fadamin"..murmushi ta kara saki before tace wani abu another kira ya sake shigowa wayanshi..dubawa yayi sai yaga Waziri dan haka da sauri yace"Mummy hang on for a minute plss..Waziri ke kira"..Mummy bata ce komai ba tayi hanging call dinta shi kuma yayi picking na waziri tareda fadin"Baffa barka da rana"...Nur da yaji ya ambaci waziri yayi saurin komawa cikin office din ya zauna nan kusa dashi ya tattara duk attension dinshi a kanshi yana son yaji me wazirin zaice?..cikeda farin ciki shima wazirin yace"barka dai Attahiru ya jiki ka?.."yace"na samu sauki"..waziri yace"to Alhamdulillahi haka akeso..Allah ya kara lafia"..Bobby ya amsa da"Ameen"..suka yi shiru na dan lokacin kafin waziri yace"wani albishir ne zanyi maka mai dadi wane tukuici zaka bani?.."dan murmushi Bobby ya saki jin abunda ya fada..to wane albishir ne wnn?..shifa gani yake a halin nan da yake ciki matukar ba cewa za'ayi an bashi auren Lamido ba ba wani albishir da za'ayi ya faranta mashi rai..kawai gani yake ba wani albishir ne da zai sashi farin ciki ba amma dukda haka bai gwale Kakanshi ba yace"duk abunda kakeso Baffah"..waziri yace"to an baka auren Aisha...yanxun nan muka yi Waya da Lamido yake sanar dani yanda akayi"...wani irin diff Bobby yayi kaman baiji abunda yace ba...meyasa waziri zaiyi playing mashi such an expensive joke?..why zaiyi wasa da zuciarshi akan lamari irin wnn..duk sai yaji ranshi ya 6aci yama rasa abunda zaice...jin yanda yayi shiru waziri yace"ko bakaji abunda na fada bane?.."a hankali ya kakalo murmushi tareda fadin"nasan da wasa kake Baffah"..da sauri Waziri yace"na ta6a maka wasa da irin wnn mgnr dama?.."shiru ya sake yi yana tunani lokacin daya wani bright smile yazo kan fuskanshi yana cewa"da..Allah da gaske kake Baffah?.."cikeda assurance Lamido ya sake fadin"da gaske nake wlh..yanxun Lamidon ya kirani muka yi mgn"...lumshe ido Bobby yayi ya bude yana jin wani irin sanyin dadi na cika zuciyarshi kawai sai ya shiga karanta duk abunda yazo bakinshi kmr wanda ya zauce...addu'a kawai yakeyi ba tareda ya bude ido ba kuma ba tareda ya ajiye wayan dake makale kunnenshi ba..banda murmushi ba abunda yake saki sai kuma bakinshi dake motsawa a hankali sbd addu'a da yake...Nur dake zaune yana kallonshi wnn smile da yake saki kadai ya isa ya fahimci dalilin hakan...lokacin daya ya bude idon nashi sbd mgnr waziri da yaji ya mike tsaye yana shafa gashin kanshi still bai dena murmushi ba yace " yanxu Baffa u mean ni zan aureta knn?..i can't believe this?.."murmushi waziri ya kara saki before saying"kai zaka aureta insha Allah sbd haka rashin lafia ya kare"..murmushi kawai yake saki yana gyada kai yama kasa bude baki yayi mgn...kawai mamakin yanda al'amari ya canxa yake..is this really happening ko kuma day dreaming yake?..a hankali ya zauna kan sofa dake nan kusa dashi bayan sunyi sallama da waziri ya sake lumshe ido yayi relaxing kan sofa din murya can kasa yace"i can't believe this?..Allah kasa ba mafarki nake ba"..Nur dake zaune yana kallonshi tasowa yayi daga inda yake ya karaso nan kusa dashi ya zauna yana dubanshi da murmushi shima yace"ba mafarki kake ba Dr Bobby..it's reality..Lamido dai ta kusa ta zama matarka congratulations to u"..tun kafin ya rufe baki Bobby yayi mishi wani runguma cikin excitement yace"i still can't believe this Nur..Anya ba mafarki nakeba?.."Nur yace"i told u ba mafarki kake ba da gaske ne..Allah ne ya amsa addu'anka"..dagowa yayi yana kallonshi har yanxu bakinshi kaman go at auduga yace"Allah Alhamdulillah..Alhamdulillah Rabbi am forever grateful"..yana gama fadan haka kuma ya mike tareda zura wayanshi a aljihunshi yace"lets get going I need to talk to Mummy about this"..Nur baice komai ya mike bayan ya day car key dinshi suka fita daga office din...Motan Nur suka shiga don dama da ita suka zo..kai tsaye ya kama hanyan gidansu kmr yanda Bobby yace..ko a hanya Bobby bai dena hamdala ba..kawai gani yake Allah yana matukar sonshi daya canxa mgnr aurenta a lokacin da ya gama giving up..gaskia ne da masu iya mgn suka ce duk wani tsananin yana tareda sauki kmr yanda duk mai hakuri yana tareda nasara...shidai yayi hakuri ya kuma fawwala Allah lamuranshi dai gashi ya kawo mashi canji a lokacin da bai ta6a tsammani ba..Lallai Allah abun godia...har suka isa gidansu bai dena godia wa wnn ni'ima ta ubangiji ba..gani yake an gama mashi komai a dunia saidai kuma yayi fatan gama wa lafia...ko parking Nur bai gama ba ya bude motar da sauri ya fita zuwa cikin gidan...Nur ya bishi da kallo yana girgiza kai yace"wa yaga ba sabon ba"..karasawa yayi ya gyara parking dinshi snn ya bude motar shima ya fita zuwa ciki...yana shiga yaci Karo da Mummy dake kokarin Shiga parlonta kawai sai ya rungumota ta baya yana cewa"Mummy I can't believe this..waziri yace wai ni zan aureta yanxu..am super excited Mummy Allah yasa ba mafarki nake ba"..juyawa Mummy tayi ta dagoshi daga jikinta tana kallonshi da murmushi a fuskanta itama tace"ba mafarki bane..duk wani da kaji a gaske yake faruwa ba mafarki ba..dama ba nace maka jikina na bani kai zaka aureta ba?.."da sauri ya shiga gyada kai kafin ya lumshe idanunshi ya sake rungume Mummy yace"Mummy nagode sosai..nagode da addu'arki gareni Allah ya saka da aljannah"...hannunshi Mummy ta kama suka karasa parlorn suka zauna tana dubanshi tace"Ameen..kaima Allah ya maka albarka..waziri yace mun gobe zasuje su samu Lamido tareda uncles dinka akan mgnr auren naku"..sake rungumeta Bobby yayi yama kasa cewa komai...Nur dake tsaye tun daxun yana kallonsu sai yanxu Mummy ta lura dashi tace"Nuru karaso ciki mana"..yana murmushi ya karasa cikin parlorn ya zauna yana gaishe da Mummy...kmr wanda ya tunada wani abu sukaga ya mike da sauri ya kama hanyar flat dinshi duk suka bishi da kallo suna daria..daidai lokacin Aunty Sumy ta shigo wayanta rike a hannunta tace"yanxun muka gama mgn da Aunty Munubiya tace tana nan zuwa gobe inshaAllah"..Mummy tace"to Allah kawota lafia". Yana Shiga parlonshi ya zauna kan three seater tareda dialing number ta yana lumshe ido..har ya gama ringing bata dauka ba ya sake kira still no answer kawai sai ya ajiye wayar tareda mikewa ya shiga bedroom direct ya fada bathroom ya daura alwala ya fito ya shimfida carpet ya tayar da sallah don ya nuna godia wa ubangijinshi for such a blessing da yayi mashi na bashi auren Lamido...har azumi ya kamata yayi don nuna godiyarshi wa Allah...har dare ya tsala bai dena Kiran wayanta ba ita kuma bata dauka ba..ganin ba daga wa zatayi ba yayi sending mata"thank u..thanks for accepting me..I love you"..daga haka ya jiye wayar ya lumshe ido yana tuna duk moments da yayi spending da ita..kaman yayi tsuntsu yakai kanshi Gombe haka yakeji amma ba zaiyi wnn rashin kunyan ba matukar ba cewa akayi yazo ba..afterall saura baifi 4 days suyi resuming school ba so zai na samun daman ganinta duk time din da yaso..he prays Allah ya shirya mashi ita yasa bazata na aikata abubuwanda dole zaisa yayi mata masifa ba. Gombe.. Tunda Lamido ta samu labarin yanda reshe ya juye da mujiya sai abun yazo mata a bazata sosai..wani irin sanyi taji jikinta yayi zuwa yanxun for sure tasan she does not hate him amma ya zatayi da Prof ne kam?..ba wai aurenta da Bobby ke 6ata mata rai ba..kawai yanda baby zai dauka kaman dama can yaudaranshi take shiyasa ta hanashi zuwa ga parents dinta da wuri..and shi kanshi proprietor nan ba sabawa tayi dashi ba..ita bata San ma ta ina zata fara zama da wnn mutumin as her hubby ba..tasan yana sonta da gaske amma har ga Allah itadai gani take kmr bayan auren zai sake rikidewa ya dawo asalin proprietor data sani a baya..gaba daya ranar yini tayi a daki tana faman kunchi ko abinci bataci ba kuma ba wanda yace mata don me...conference video call ta hada musu itada Billy da besty tana tuttura baki ta fada masu duk abunda ke faruwa ga mamakinta sai taga gaba daya sunyi farin ciki da mgnr don har lissafin biki suka fara kawai ta kashe wayarta tana huci..ita fa har yanxu bata ga ta inda ita da proprietor za’ace suyi aure ba..to ta inama za’a fara?..kawai gani take kmr abun ba mai yiwuwa bane..gashi tun jiya take kiran wayan Prof a kashe har zuwa yanxu kama a kashen yake ta rasa dalilinda yasashi kashe waya..so take ta sanar dashi an samu turn of events ya gwada turowa wai ko Lamido zai sauraresu amma bata samun wayan nashi..duk tabi ta zama wata iri ita ba mai lafia ba kuma ba mara lafia ba..tana gani tun daxun yake kiran wayanta taki dauka don batasan abunda zai fada mata ba kmr yanda itama batasan abunda zata fada mashi ba...kunayanshi ma taji tanaji wlh..tana nan kwance a daki har dare daddy ya turo Yusra ta kirata..ba musu ta mike tareda maida hulan kanta ta nufi parlon nashi..suna zaune tareda Ammi ta karasa ciki a nutse ta zauna a kasa..daddy yace"nasan kin samu labarin abunda ke faruwa wajen Amminki koh?.."ta daga kai alamar ta sani..daddy yacigaba"to inaso ki kwantar da hankalinki kiyi mana biyayya a wnn auren..a yanda yaron ke sonki nasan kema bazaiyi taking naki long time kafin ki fara sonshi ba..kuma ban yadda ki mashi wani rashin kirki ba Aisha..inaso ki girmamashi kmr yanda kikeyi a baya snn kar in sakeji ance kin hadu da wnn mutumin ko waya ban amince kiyi dashi ba..idan Allah ya kaimu gobe zasuzo a tsaida ranar aurenku..Allah yasa haka shine alkhairi a tare daku Allah kuma ya maku albarka baki daya"..a hankali ta gyada kai idonta a kasa..saida ta tabbata ya gama snn tace"daddy dan Allah ina son zuwa Bauchi gidan aunty fiddausi"..daddy yace"ba wnn sunday zakuyi resuming school ba?.."a hankali tace"eh amma kafin sunday din zan dawo..ko kuma a daukemu daga can tareda Billy kawai mu wuce"..shiru daddy yayi kmr bazaiyi mgn ba sai can yace mata"shknn saiki shirya gobe da safe a kaiki..Allah maki albarka"..ta amsa da"Ameen daddy"..snn ta mike ta fita daga parlon..Ammi ta bita da kallo bayan fitar nata tace"ikon Allah..wai Aysha ce tayi wnn nustuwa haka sbd mgnr aure ya 6ullo..wonders shall never end"..ta karasa mgn tana daria yayinda daddy ke girgiza kai shima yana murmushi..shi kanshi yaga wnn canjin tattare da ita fatanshi dai Allah yasa auren nasu shine alkhairi a tareda kowannensu. Washegari da safe ta shirya kmr yanda daddy yace driver dinsu ya dauketa zuwa Bauchi..tana zuwa gidan ta fashewa small mom dinta da kuka wai za’a mata auren dole..Aunty Fiddausi nata aikin rarrashinta tace"ni banga abun tada hankali anan ba Aysha bayan kowa ya shaida irin son da akace yana maki"..tun kafin ta rufe baki tace"Aunty inyamuri ne fa..kuma wlh bashida mutunci masifaffe ne na bugawa a jarida..shknn ni sai a hadani dashi salon yayitama mutum masifa komai fa shi abun fada ne a wurinshi"...daria aunty fiddausi ta kunshe kafin tace"to kiyi hakuri ni da kaina zanyi masa fada ya dena maki masifa gaskia..kuma shi da yake jikan waziri ta ina ya zama inyamuri kuma?.."da sauri tace"babarshi inyamura ce kuma shima yanayin inyamurancin..kawai sai in haifi ‘ya’ya a dinga koya musu igbo..wlh an cuceni"..daria sosai small mom dinta ke mata don ita bataga abun daga hankali a nan ba...idan ta fahimceta ba ma rashin auren wancan saurayin ne damuwarta ba kawai damuwarta an hadata dashi kuma wai masifaffe ne..ta lura iskanci ne kawai yasa take wnn abun amma ba kiyayya ba don bisa ga dukkan alamu itama tana sonshi kilan ganewa ne kawai batayi ba. Sha biyu da wani abu tayi sallama da aunty fiddausi ta wuce gidansu Billy..ta iske Ummansu a parlor tareda sauran siblings din Billy maza..ta karasa ciki a hankali kaman wata mara lafia ta shiga gaisawa da Umma..Umma dake dubanta with smile tace"ashe kuma proprietor dinku zaki aura?..dazu Bilkisu ke fadamun..to Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokacin Aysha Allah yasa albarka"...juyawa tayi tana kallon Billy kmr zata fashe da kuka kafin ta sake juyowa ga Umma tace"Umma masifaffe ne fa"..daria Umma da sauran brothers din Billy suka sa jin abunda tace...Umma tace"banda abunki Aysha ai ba’a cika son namiji ya zama mara fada ba sbd raini"..turo baki kawai tayi bata sake mgn ba..wani elder brother din Billy mai suna Mubarak yace"naji ance jikan wazirin Gombe ne koh?.."mikewa tayi still tana turo bakinta tace"kuma babarshi inyamura ce"..daria suka kara saki Billy ta mike da sauri zuwa inda take ta kama hannunta tana kokarin kunshe dariar dake cinta itama tace"ki kyale Yaya best friend tsokanarki yake..yanxu mu shiga ciki ki bani labari in detail"..kwace hannunta ta shiga kokarin yi Billy bata sakeshi ba saida suka shiga dakinta..tana sakin hannun nata ta sake fashewa da daria har tana clapping hands dinta tace"wlh ba karamin dacewa kikayi dashi ba..dama garinku daya"..kallonta Aysha take har ta gama iskancinta snn ta karasa ciki ta zauna gefen gado tana duban Billy da wani murmushin mugunta tace"dadin abun dai kema naki yana nan zuwa..kwanan nan na samu labarin wani yana sonki har turowa ma zaiyi gidanku ayi mgn"..tsaki Billy ta saki tareda zama nan kusada ita tace"matsala na dake karya..uban wa ya baki wnn labarin?.."Aysha tace"ba labari aka bani ba kan idona komai ya faru..da gaske kema very soon zakiji ance an fidda maki miji sai ki zama cikin shiri"..kallonta Billy take kmr mai son gano gaskia..sake matsawa jikinta tayi tana marairaicewa tace"bani labari dan Allah..da gaske kike ko da wasa?.."Aysha tace"da gaske nake wlh..Hammana ne yake sonki"..wani kwalo idanu waje Billy tayi kmr taga abun tsoro tace"Lamido kiji tsoron Allah"..Aysha tace"Allah kinji na ranste maki da gaske nake..a gabana ya fadama Lamido ke yakeso shi kuma Lamido yace zaiyi mgn da grandpa dinku”..dakatawa tayi tareda kamo hannayenta tace"Billy i cant believe this wlh..abun yayi mun dadi wai ace Hamma na zai aureki..dan Allah Billy kema ki soshi kinji and kada kije ki fada masa na sanar dake dan cewa yayi bai yadda in fada maki ba"...murmushi Billy ta saki tareda zame hannunta daga nata tace"banza ‘yar rainin hankali"..ta fashe da wani daria tana cewa"ni dake za’a ga dan rainin hankali a ciki..yarinya tanaso tana kaiwa kasuwa"..da sauri Billy tace"ai kema kina son proprietor kuma kina kaiwa kasuwa"...haka dai sukaita tsokanar junansu Aysha bata bar gidan ba sai dab da magrib tayi sallama dasu ta koma gidan aunt dinta. Washegari Waziri da Uncles din Bobby biyu suka je nema mashi aurenta wajen Lamido...Waziri da kanshi ya bada kudin aure inda Lamido,daddy da uncles dinta suka karba tareda tabbatar musu da cewa an bashi ita halak malak..Lamido yasha godia wajen waziri kaman wani gagarumin abun yayi mashi..an tsayar da mgn kan baza’ayi biki ba sai ta gama makaranta amma zai iya zuwa duk time da yakeso yayi mgn da ita wnn kam an bashi izini batun aure ne dai akace sai ta kammala. Washegarin ranar suma sukaje Bauchi nemawa Hamma auren Billy a hannun kakanta babu wasting of time suma suka amince suka kuma ce an bashi aurenta lokaci kadai ya rage a shafa fatiha. Lokacinda labari ya iske Bobby ji yayi kaman yayi tsuntsu ya tafi Gombe sbd farin ciki..bai taba tunanin komai zai faru cikin sauki haka ba..matsala daya da yake fuskanta yanxu shine rashin samunta a waya..ba wai bai samun wayan nata bane aah yana shiga dauka ne kawai batayi wanda baisan dalilin haka ba..duk iya dauriyarshi kasa cigaba yayi sbd yanda take neman ta tarwatsa mashi dan farin cikin daya samu yanxu a dalilin aurenta da yasan an bashi...daukan wayanshi yayi ya kira waziri sukayi mgn dashi yace shidai yanaso yazo Gombe a gobe sbd ya samu ya ganta..Waziri bai hanashi ba yace babu damuwa yazo ya ganta ko don su fara fahimtar junansu. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba... masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 47 Da wuri ya gama shirinshi don ko breakfast bai fitoyi ba saida ya gama..flat din Mummy ya fara shiga ya sameta zaune tana mgn da waziri a waya..karasawa yayi ciki ya zauna kusada ita yana jira ta gama..sun dauki lokaci mai tsayi suna discussing kan mgnr da bai fahimci inda ya dosa ba kafin su gama..Mummy na ajiye wayanta ta jiya tana dubanshi tace"so ka gama shiryawa?.."yace"na gama Mummy..Nur kadai nake jira"...Mummy ta mike tace"to muje kayi breakfast kafin Nur din ya karaso"..mikewa yayi ya matairaice yace"Mummy am not hungry plss..kinsan idan zanyi tafia ba son cin abinci nake ba"..hannunshi ta kama zasu fita daga dakin tace"ko tea ne sai kasha in ba haka ba kuma u will not step out if this house"..bai sake yi mata musu ba yabita har dinning..aunty sumy itama daidai lokacin ta fito don da wuri zata fita aiki...su Miemie ne bai gani ba ya tambaya Mummy ta wani hade rai tace sun tafi gidan kakarsu..baice komai ba sbd yanda yaga ta hade rai..batasan ko bata hade rai ba ba mgn zaiyi ba sbd shima yanxu na gabanshi ya isheshi..Allah Allah yake ya ganshi a gaban yarinyar nan yaji dalilinta na ignoring calls dinshi..koma me zatayi dai daga baya ne tunda an rigada an bashi aurenta so duk ihu bayan hari takeyi ya sani..tea Mummy ta hada mashi ya dauka ya shiga sha cikin ranshi yana tunanin yanda zasu kwashe da ita...kafin ya gama sha Nur ya iso gidan dan haka ya mike da sauri bayan ya ajiye mug dake hannunshi yana duban Mummy yace"zamu wuce Mummy..tafiyan akwai nisa"..murmushi kawai Mummy tace"Allah ya kiyaye hanya..ina gaida ‘yar tawa"..murmushi yayi tareda fadin"zataji"..snn ya koma zuwa flat dinshi don daukan keys..Nur kuma ya karasa yana gaisawa dasu Mummy..aunty sumy dake cin abincinta tace"wnn abokin naka zalamamme ne wlh..haka ake zuwa zance tun sassafe sbd rashin hakuri"..daria Nur yasa kafin yace"ai aunty kinsan qanin naki halinshi sai shi..ita kanta Lamidon fa wai haushinta yakeji bata daukan mishi waya..so nake muje dai inga iya inda fushin nashi zai kare"..daria itama aunty sumy tayi tana cewa"ai matar Bobby ta shiga uku da masifa..koda yake ita wnn yana sonta bazai iya mata masifan ba kila"..Nur yace"ina ya isa ya mata?..daidai dashi ya samu ai"..daria suka kara saki Mummy dai na jinsu tana murmushi..ita kanta wani lokaci takanyi tunanin yanda Bobby zai kare da matarshi da wnn temper din nashi..saurin hawa gareshi kmr farashi gashi kuma da wuyar sakkowa..amma ta bakin na Nur ta lura yarinyar daidai dashi ce snn kuma uwa uba soyayyan da yake mata wanda bazai barshi yanayi mata anyhow ba..sbd wnn fadan nashi yasa a kullum addu’arta Allah ya bashi macen da yake mutuwar so ba wadda ke mutuwar sonshi ba don idan ya auri macen da baiso matsala za’a samu gagaruma..Allah almusawwir kuma sai ya amsa addu’anta ya bashi wadda sonshi yafi nata..fitowa yayi daga dakinshi yanata baza kamshi..Nur ya kalleshi yana wani kashe ido yace"bakaga kyan da kayi ba wlh..manyan kaya na suiting dinka and da wnn wankan nasan dole Lamido ta ajiye ego dinta ta bada kai don zata fahimci kai din fa ba kmr kowa bane"..harara Bobby ya watsa mashi baice komai ba..yana karasowa yayima Mummy da aunty sumy sallama snn ya juya ya fita Nur yabi bayanshi yana kunshe daria...driver na ganin su ya karaso suka gaisa Bobby ya bashi key din motar da zasu fita yana sake trying number dinta bata dauka ba..driver ya kawo motar inda suke snn suka bude suka shiga shi kuma ya tayar da ita suka fita already dama ya sanar dashi cewa Gombe zai kaisu...ko a hanya saida ya sake trying number still no answer sbd tsabar haushi baisan sanda ya wurga wayan nan gefenshi yana fadin"to hell with you"..juyawa Nur yayi yana kallonshi then back to wayarshi dake yashe a tsakiyarsu...hannu yakai zai dauki wayan Bobby yayi saurin daukan kayarshi shima yace mishi"fuck you"..Nur ya kwashe da daria hadda kyakyatawa...Bobby ya kulu iya kuluwa amma baice komai ba..gaban driver dinshi zai dinga mashi irin wnn iskancin?..zaiyi maganin Nur wlh...bai sake ce mishi komai ba har shima ya gaji da daria don kanshi ya bari daga karshe ma baccinshi yayi hankali kwance..a kufule Bobby ke kallon yanda ya wani yi bacci a mota kmr karamin yaro..shiko tunanin dake ranshi ma bazai iya barinshi baccin ba..gani yake kaman ba tafia suke ba don Gomben yaga tayi nisa sosai baisan ko don sbd matsuwar da yayi ya hadu da ita bane...haka yayita sake sake har suka shigo Gombe around 11:45..saida ya fara zuwa suka gaisa da waziri snn suka wuce estate dinsu...suna zuwa bakin gate gabanshi ya fara faduwa da baisan dalilinshi ba...gidan Lamido suka sauka kmr yanda waziri yace daga nan kuma Lamido yasa aka rakasu har kofar gidansu..tun jiya da waziri ya sanar dashi zaizo dama yasa da sassafe akaje aka daukota daga Bauchi don daddy baya gari ya koma wurin aiki...a bakin gate sukayi parking Bobby sai kallon gidan yake cikin ranshi yace"so this is their house?.."ya karasa da wani murmushi kan face dinshi...yaron da ya rakosu ne ya shiga ciki yace ma Ammi sun iso ita kuma ta tura Husna tace ta shiga dasu parlon daddy..babu wasting of time kuwa Husna ta fito tana hangosu ta karasa kusa dasu ta washe musu baki tace"sannunku da zuwa"..Nur ne ya fara cewa"yauwa sannu yanmata..ke qanwar Lamido ce koh?.."gyada mishi kai tayi still smiling tace"nike binta ai..sunana Husna Lamido"..Nur dake gyada kai yace"MashaAllah Husna Lamido"..juyawa tayi tana kallon Bobby daya rungume hands dinshi yana kallonsu..suna hada ido ya sakar mata smile tareda cewa"Sannu Husna Lamido"..murmushinta ta kara fadadawa kafin tace"Ammi tace ku shigo ciki"..daga haka tayi gaba sukabi bayanta har cikin gidan..parlon daddy ta shiga dasu as instructed by Ammi snn ta gaidasu ta fita...Nur ya shiga kallon parlon yana yaba kyau da yayi mashi...shiko Bobby idonshi bai sauka ko inaba sai kan wani picture dinsu gaba daya lokacin suna kanana..ita da Ammi ne a pic din daddy ya dauki Husna Ammi kuma ta dauki Yusra aysha kuma tana tsakiyarsu...tayi murmushi a picture din har dimples dinta sun fito..murmushi da bai shiryaba ya saki yanajin wani weird feeling tattare dashi..sake maida dubanshi yayi ga dayan picture din shima gaba dayansu ne amma wnn sun girma gaba daya snn akwai Hamma Najeeb a jiki..dan hade rai yayi ganin yanda take zaune kusa dashi gaba daya suna daria kawai sai yaji baiji dadin zama kusa dashi da tayi ba..da sauri ya dauke idonshi daga hoton don gudun kada ya karasa spoiling mood dinshi da dama ba daidai yake ba...wani fitinannen kamshi ne ya bugi hancinshi kafin ta shigo parlon a hankali tamkar kazar da kwai ya fashewa a ciki...kallonta kawai Bobby yake yanajin zafin a yanayin da ta fito..is she mad zata sanya turare haka ta fito kuma ba tareda hijab ba?..juyawa ga Nur yaga sai wani kallonta yake yana murmushi nan take yaji 6acin ranshi ya karu akan wanda yake ciki..shi baima san kaddarar data kaishi daukan Nur ya taho dashi ba gashi nan sai kalle mashi ita yake a banza kmr yaga matarshi...karasowa ciki tayi ta zauna hankalinta gaba daya kan Nur fuskanta ba yabo ba fallasa tace"sir good afternoon"..Nur da har yanxu ke murmushi yace"good afternoon amarya Lamido ya hutu?.."dan murmushi kawai tayi tareda cewa"Alhamdulillah”...Bobby daya cika yayi fam ya shiga dubanta da angry eyes dinshi yace"bakida hijabi ne?.."daure fuska tayi ba tareda ta kalleshi ba tace"bani dashi"..yace"then tashi muje a siyo"..banza tayi dashi tana sake dinke fuska..shi wnn irin masifaffe ne wai?..a nan dinma sai ya mata bala’i bazai bari su rabu lafia ba?..mikewa yayi hands dinshi a aljihun wandonshi yace"ki tashi muje a siyo nace"..ko motsawa batayi ba Nur dai da yaga abun na Bobby azimun ne sai ya mike ba tareda ya kalli inda yake ba yace"i will wait for u in the car"..daga haka ya fita daga parlon shi kuma ya shiga takawa a nuste zuwa inda take yayi kata wani tsaye yana kallonta kmr soldier...dan dagowa tayi a hankali ta kalleshi taga kallonta shima yake kmr an aikoshi nan da nan ta sauke nata idon tana kunkuni...zama yayi nan kusa da ita still yana dubanta yace"and wa ya fada maki ana sa turare haka a shiga cikin mutane?.."kallonshi ta juyo tanayi kmr zata sanya kuka..ya lumshe ido tareda jingina da jikin kujerar yana maimaita innalillahi a cikin zuciyarshi..kada kuma ta fara tunanin yana overacting amma Allah ya san ba karamin kishi yake dashi a kanta ba..ganinta a haka shi kanshi saida yaji wani abu balle kuma Nur da bai hada komai da ita ba..shi bayason ana ganin beauty dinta ne and fesa turare ko Allah ya haramtawa mata su fesa su fita sbd kamshi ba karamin fitina yake haddasawa ba..a hankali ya bude idon nashi tareda gyara zama yana dubanta yace"why are you ignoring my calls?.."tace"ba komai"..girgiza kai ya shigayi yana dubanta cikin ido yace"karya kikeyi"..ta wani zaro ido tana kallonshi saura kiris daria ya subuce mata tace"sir karya kuma?.."kai ya sake gyadawa alamar haka yake nufi...ta dan turo baki tace"nidai ba karya nake ba"..kallonta ya tsaya yi kawai kmr baiji abunda ta fada ba...riga da skirt ne a jikinta na lace da yayi matukar amsarta..ta daura dankwalinta as usual saidai wnn karon bata fito da gashi ba don tasan sai yayi mgn sai kuma veil dinta data yafa a kafada...gani yake duk dunia babu macen da zata kaita kyau a idanunshi..ita komai ta sa kyau yake mata shiyasa a kullum kishinshi karuwa yakeyi a kanta...lumshe ido yayi tareda sauke ajiyar zucia cikin voice dinshi da yaji ya dashe all of a sudden yace mata"i love u so much Aysher..plss i beg of u ki bar kin answering calls dina..am about going crazy.i..i am..."kasa karasawa yayi kawai yayi shiru yana sauraran heart beat dinshi...kallonta yacigaba dayi voice dinshi na rawa sosai yace"have mercy on me plss..i promise to love u till my very last breathe..I promise to be a good husband..i will never rufuse u anything in the world just wanted u to love me nor matter how little i wont complain..kawai ki soni ki zauna dani for i dont think i can live without u..i love you dearly"..lumshe idanu Aysha tayi tana sauraran words din nan nashi..bata san why ba amma words din really galddens her heart..sunyi mata dadi sosai ba kadan ba..kawai mamaki take yanda the whole Dr Bobby ke pouring mata love words haka..bata san ita ko tana sonshi ba amma this very moment taji ya burgeta matuka..da dadewa dama tasan son da yake mata ba gama garin so da ake iya samu a ko ina bane sai wanda Allah ya zaba yake bama masoyi mai matukar sonka kamarshi..kawai gani take Allah knows best shiyasa ya hada aurenta da nashi..idan kuwa haka ne ita bazata ja da ikon Allah ba saidai tayi fatan hakan ya zama alkhairi a garesu baki daya...ganin yana mata wnn kallon nashi mai sawa taji wani iri ta mike da sauri har veil dinta yana faduwa ta dauka da sauri ta fita daga parlon ta bar Bobby da lumshe ido yana saqan kamshin da ta tafi ta bar mashi...yana nan zaune after few minutes ta dawo dauke da tray a hannunta ya mike da sauri ya amsa tray din ya ajiye kan table ita kuma ta sake fita ta dawo da wani..a takaice saida ta cika musu gaba da kayan ci dana sha snn ta kama haya zata fita yayi saurin cewa"where are u going to?.."tace"zan kira provost ne yazo kuci abinci"..girgiza mata kai ya shiga yi yana zaro wayanshi yace"don’t worry i will call him..amma haka kike fita Aysher duk mazan dake gidan nan suna kallonki?.."juyawa tayi ta koma ciki ba tareda tace komai ha don bata ma san abunda ya kamata ta fada ba..shi kuma yayi dialing number din Nur yana dagawa yace ya shigo suci abinci..ba musu Nur ta dawo parlon ita kuma ta mike tana fadin"bari inyi excusing naku idan kun gama sai in dawo"..kai kawai Bobby ya iya daga mata yabi bayanta da kallo har ta fita snn ya sauke ajiyar zuciya ya fara cin abincin...sai yanxu ya samu kwanciyar hankalin cin abinci amma daxu ji yake gaba daya tension din dunia kanshi ya kare. Bayan sun gama cin abincin ta dawo tareda Yusra data dage sai taje ta gaishesu...kanta a kasa har ta karaso ciki ta zauna..Bobby daketa kallon Yusra ganin kamar Ilham dinshi yace mata"hey cutie"..washe baki tayi tana gaisheshi yace"ya sunanki?.."tace"Yusra Lamido..kaine wanda zaka auri Addah?.."dan wara ido yayi yana kallonta da murmushi yace"yeah nine..waya fada maki ni zata aura?.."da sauri Yusra tace"Adda Husna ce tace wai kai proprietor dinsu ne kuma wai kai inya..."Aysha bata bari ta karasa ba ta toshe mata baki...Bobby sai yayi relaxing yana kallonsu..dukda bata bari ta karasa ba yasan inyamuri zata ce..girgiza kai kawai yayi yana murmushi..Aysha ta mike rikeda hannun Yusra suka fita daga parlon tace"ni zaki tonawa asiri Yusra?.."a hankali tace"kiyi hakuri Adda mantawa fa nayi"..Aysha tace"oya wuce ki koma wajen Ammi kar na sake ganin kafarki a nan"..ba musu ta wuce ta bar wurin ita kuma ta sauke ajiyar zucia tareda komawa ciki...bata samu Nur a parlon ba sai shi kadai...tana karasawa ta zauna yace mata"daddy baya gari ne?.."tace"eh yana Abuja"...gyada kai yayi kafin ya sake cewa"inyamuri kike cemin koh?.."wani irin zare idanu tayi hadda su dafa kirji tace"Nii😳"..murmushi ya kara saki yana gyada kanshi yace"yes ba gashi zata fada kin hanata ba"..turo baki tayi tana kawar da idonta daga wnn kallon nashi tace"nidai ba haka nake cewa ba ba ruwana"...daria mgnr nata ya bashi aiko ya shiga yinta kmr me..saida ya gama don kanshi snn yace"ko haka kika fada ma ba wani abu ke bakaya laifi ai..and niba igbo bane..ni bafulatani ne just like you"..shiru tayi tana wasa da fingers dinta..shi kuma kallonta yakeyi yanajin tamkar ya janyota jikinshi yace"ko har yanxu baki yadda nima dan Gombe bane?.."sake turo baki tayi cikin gajiya da tambayoyin nan nashi tace"na yadda"..shiru ya sakeyi for some minutes kafin kuma yace"so yanxu dai ni zan aureki?.."sake sunne kai tayi tanajin wani irin faduwar gaba..shi kuma har yanxun ya kasa dena murmushi yacigaba da fadin"i just can’t wait for ranar da za’a daura mana aure..am eager in ganki cikin gidana as my wife"..wnn karon rufe fuskanta tayi da hands dinta don wani irin kunya taji ya rufeta..shiko murmushi kawai yake saki non stop murya can kasa ya kira sunanta"Aysher"..dagowa tayi a hankali tana kallonshi..shima kallon nata yakeyi kafin yace"i love you..to the moon and back..kuma nagode sosai for agreeing to marry me insha Allah bazakiyi regretting decision din nan ba"..kasa ta sakeyi da idonta tanajin wani baqon al’amari na zaga jikinta...banda yake ba abunda take yau duk uban surutunta nemanshi tayi ta rasa kuma ta rasa dalili..duk wnn rashin kunya data gama planning zata mishi saita kasa sbd kwarjini na musamman da taga ya mata uwa uba kuma wnn words da yake sake kashe mata jiki dasu...duk sai taga ya sauya kaman ba proprietor data sani mai dan karen masifa ba...shiko murmushi yaki yankewa a face dinshi sam sai wani jin dadi yake kmr anyi mashi bushara da aljannah...sake kasa da murya yayi kafin yayi mgn wayanshi dake ajiye kusa dashi ya fara ringing..dubawa yayi yaga wanda ke neman katse mashi wnn jin dadin sai yaga Mummy dan haka yayi picking da sauri yana cigaba da murmushi da igbo yace"Hello Mummy"..da igbo din itama ta amsa mashi da"tun daxu nake kiran wayoyinku bai shiga..ka bani ita mu gaisa idan kuna tare"..mika mata wayan yayi yana binta da wani kallo mai wuyar fassarawa yace"Mummy"..ba musu ta amsa wayan tareda kaiwa kunne..a daya banagaren Mummy tace"daughter"Aysha ta sake sinne kai tana murmushi tace"Mama ina yini"..Mummy tace"lafia lau ya hutu"..tace"Alhamdulillah"..Mummy tace"maasha Allah dama so nake in maki godia for accepting him..Allah maku albarka yasa haka ne alkhairi a tareda ku"..kasa tayi da kanta ta kasa amsawa..ita duk bata san yaushe kunya ya shigeta har haka ba wlh..bata taba zaton zataji wani abu wai shi kunya ba a rayuwarta amma yau gashi tanaji kuma batasan dalili ba...godia sosai Mummy ta sake kwararo mata snn tace ta gaida Mamanta..ta amsa mata da zataji snn ta mika mashi wayar...yana karba ya sake maidawa kunne yana sauraran abunda take fada yanata murmushi...baice komai ba har saida ta gama snn ya ajiye wayar...agogon hannunshi ya duba yaga time na wucewa gashi yau zasu koma Kano dan haka ya wani langabar da kai yana kallonta in a pleading tone yace"tafia zamuyi Aysher..amma dan Allah i beg of u ki bar fesa turare haka da yawa idan zaki fita kuma ki taimakamun ki dinga sa hijabi please"...dagowa tayi ta kalleshi ya sake narke mata idonshi aikuwa ta dauke nata da sauri jin wani abu ya fito daga cikin idon nashi ya shiga nata..itadai ta shiga uku da idanun nan nashi da ba dama ta kallesu ko ya kalleta dasu sai ya sata jin wani iri..ganin har yanxu batace komai ba ya sake kasa da murya yace"kinji?.."kai kawai ta iya daga mashi ba tareda ta kalleshi ba..shiko bai dauke idanunshi a kanta ba ya sake cewa"And dan Allah ki taimaka ki dinga daukan wayana..hankalina tashi yake idan ina kira baki dauka ba kinji?.."nan ma kai ta sake gyada mashi without saying a word..gaba daya yawun bakinta ma taji ya kafe mata all of a sudden..kallonta yake yana so ya samu eye contact da ita amma taki dagowa..yace"to kiyi mgn da Ammi zamu gaisheta kafin mu wuce"...ba musu ta mike ta fita daga parlon shi kuma ya bita da kallo yanajin sonta na sake zagaya duk wani system na jikinshi...after like 5 mins ta dawo tace Ammi tace su shiga dan haka ya kira Nur a waya ya dawo snn suka shiga main parlor gaba dayansu...Ammi na zaune kan one of kujerun parlon sanyeda hijab sai Yusra a gefenta...suka karasa ciki duk suka zauna a kasa Ammi nata cewa su koma kan kujera amma basuyi hakan ba suka fara gaisheta a haka...ta amsa da fara’a tareda tambayan iyayensu duk sukace suna lafia..nasiha sosai tayi musu kafin su mata sallama su fita Bobby na sakejin matar ta kwanta mashi a rai sbd kamalarta..wato ba daddy kadai ne dattijo a gidan ba ita kanta Ammi dattijuwa ce..sunada halin girma sosai ba kadan ba..ya kuma san yayi dace da Allah yasa zai auri diyarsu don mutanen kirki ne..shi sai yau ya samu ganin tsananin kamar da Aysha takeyi da Amminta..irin kama sosai wanda ko mgnrsu ma kusan iri daya ne likewise dimples dinsu...halayyan su ne kawai ya bambamta don yasan da kyar idan wnn fitinan na Aysha a wurin Ammi ta dauko..ita batayi kala da fitinannu ba sam amma ita indo a kallon farko da mutum yayi mata yana iya gane tsantsar rashin jin dake tattare daita dukda ma dai yanxu ta girma ta rage kiriniya...ita kadai ta rakosu har compound don Husna ta wuce islamiyya...suna gama sallama da Nur ya bude mota ya shiga yayinda shi kuma Bobby ya karasa inda take tsaye ya zaro kudi a aljihunshi ya mika mata yana cewa"sorry ban kawo maki komai ba..hankalina ne duk ba daidai ba lokacinda zamu taho amma ga wnn kisai duk abunda kikeso"..girgiza mishi kai tayi alaman bazata karba ba..ya wani langabar da kai yana kallonta yace"dan Allah accept it..bazanji dadi ba in kikamun haka"..shiru kawai tana kallonshi..ya kamo hannunta yasa kudin a ciki snn ya sake kasa da murya still bai bar kallonta ba yace"shknn zamu wuce..ai ranan sunday zakuyi resuming school koh?.."kai a kasa ta amsa da"eh..zamu tafi clinical posting"..gyada kanshi yayi yana murmushi don tuna zai samu damar ganinta son ranshi a asibiti yace"i can’t wait for sunday..i love u sosai"..kasa ta sakeyi da kanta batace komai ba..yace"Aysher look at me mana"..dan dagowa tayi ta kalleshi suna hada ido ta juya zuwa cikin gida da sauri har tana tuntu6e shi kuma ya shiga shafa kanshi yana sakin murmushi ba kakkautawa...shi kanshi baisan ya iya murmushi ba har haka..gaba daya 6acin ran daya kwaso tun daga kano yana zuwa gareta sai ya nemesu ya rasa sai farin ciki daya baibayeshi kuma.."oh Allah nagode maka..Allah Alhamdulillah bazan gaji da godia kan wnn kyauta da kayimun ba..i will be forever grateful"..abunda yake fada knn yayinda ya karasa inda motarshi yake ya bude ya shiga snn driver ya tada ita suka fara tafia...ko a cikin motar relaxing yayi kan kujera yana shafa kai yana murmushi kamar sabon kamu..Nur dai na zaune gefe yana kallon ikon Allah..a fili yace"muma dai mun kusa isowa wurin nan...lokaci karami muke jira muma mu shigo sahun manya"...Bobby dai kala baice dashi ba yacigaba da murmushinshi..idan yace zai biyewa Nur yasan tsaf zai iya harxukashi suzo suna rigima gaban driver shiyasa bazai kulashi ba ko don ma farin cikin da yake ciki a yanxu haka. Wnn dai page din gobe ne na dawo muku dashi yau so koda kun jini shiru gobe ga abunku nan na baku.😄 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 48 Ranar sunday around 11 suka baro Gombe zuwa Kano sbd posting da zasu fara..saida suka fara tsayawa Bauchi sukayi picking Billy da duk ta kasa sakin jikinta da Hamma sbd mgnr so daya 6ullo tsakaninsu..yana ankare da ita shiyasa tun farko baiso tasan yana sonta ba sai sun kammala school amma mgnr da Lamido yayi shi ya hargitsa komai..tana zaune back seat sai sunkuyar da kanta take kmr munafuka..ita kuma Aysha banda daria ba abunda take mata..shidai yana jinsu baice komai ba sai kallonta da yakeyi ta mirror time to time...karfe biyu da wani abu suka shigo Kanon Dabo kai tsaye kuma suka wuce FCNM kmr ko yaushe dai...sai yanxu hankalin Aysha ya dawo jikinta ta shiga tunanin rayuwar da zatayi da proprietor yanxu kuma..a dan wnn lokacin ta fahimci ba karamin mara kunya bane shi..yanda yake nuna yana sonta gaban uban kowa abun har tsoro yake bata kada yaje yayita nunawa har kowa ya fahimci abunda ke tsakaninta dashi...a 6angarenta dai har yanxu tasan ba sonshi take ba kawai dai taji zata iya aurenshi ne sbd son da yake mata da kuma kasancewarshi za6in iyayenta...ga mamakinta suna shiga premises na makarantan sukaci karo da motarshi parke wajen parking space alaman yana cikin makarantan knn..tuj daxu yazo yana so ya ganta shiyasa ko office dinshi bai shiga ba yayi zaune nan cikin mota tunda yanafa tint so ba wanda zai ganshi...kmr ance ya dago suna shigowa kuwa ya juya yana kallonsu..ranshi yaji ya 6aci da ganin wanda ya dawo dasu..to meye hadinta da wnn kuma yanxu?..har abada bazai manta shine wanda akaso bashi aurenta ba kawai Allah ya rubuta bashine mijinta ba amma da yanxu wani mgn akeyi ba wnn ba...yana kallon lokacin da ya fito ya rakasu zuwa inda zasu duba posting..da kanshi ya duba masu gaba daya ya kuma ce Freedom aka sake posting nasu again wnn karon Aysha ko kadan batayi mamaki ba don dama tasan abunda zai faru knn kuma da bakinshi ya fada mata bazai bari tayi nesa dashi ba wai kada taje inda doctors da sauran health workers zasuyi caa akanta da sunan suna sonta..ita bata ta6a ganin mutum mai kishi ba irinshi..kishinshi har tsoro yake bata wataran don akan kowa da komai ma kishi yake shi kam..bayan sun gama duba posting din suka koma jikin motarshi nan kuma Aysha ta shiga tsokanar Billy wai kunyanshi takeji sai faman kyalkyala mata daria take ganin yanda duk ta wani nustu kmr ba Billynta mai masifa ba..Hamma dai sauraronta yake yana kuma tare mata don yasan iskancin Aysha ba dan karami bane tsaf zata saka mishi ita a gaba da tsokana har saita tunzurata...tsabar takaici Bobby kiran driver dinshi yayi yace yazo su wuce don idan yacigaba da zama nan kilan yana iya jin abunda yafi wanda yakeji yanxu..yasan dole bai isa ya rabata dashi ba tunda cousin dinta ne cousin dinma kuma wanda suka tashi a gida daya dan haka dole yayi hakuri dashi tunda yasan dai bai isa ya rabata dashi ba..shiyasa dai maza da yawa suke tsoron cousins sbd ba karamin ruining relationships sukeyi ba..lokaci guda sai besty ya fado ranshi har ya tambayi kanshi ko suna tare dashi har yanxu ko kuma sun dena friendship din oho..ya tuna ma tare dashi ya gansu a Gombe ranar birthday dinta kuma hakan na nufin yana nan matsayin bestynta ba abunda ya sauya...driver na shiga tayar da motar suka fita bayan an bude musu gate...da kallo Lamido tabi motar kmr idanunta zasu fado kasa..knn dama tun daxu yana cikin motar tunda dai ita bataga lokacinda ya shiga sai kawai gani tayi anja motar an tafi...ta6e baki tayi data tuna bama abunda ya shafeta bane...saida Hamma ya shiga dasu har hostel snn ya juya zai koma Gombe su kuma suka shiga daukan kayansu zuwa cikin apartment dinsu. Karfe takwas da wani abu ya iso hostel dinsu cikin motan aunty sumy don yasan idan yazo da motarshi masu gadi suna iya ganewa shi kuma baiso su ganshi sbd dare yayi shiyasa yayi disguising kanshi da motarta..so yayi ma ya hakura da ganin nata sai gobe sai kuma yaji bazai iya ba at leat ko ganinta ya samu yayi ya danyi mgn da ita yasan zai samu bacci mai kyau shiyasa baiyi ka sa a guiwa ba..yana gama parking yayi dialing number dinta..lokacin suna zaune sun hadu a room 1a gaba dayansu sai labari suke suna daria kowa tana bada labarin hutunda tayi a gida...Lamido na zaune daga gefe tana sauraronsu tana sakin smile ita nata holidays din dai la ba’asa zatace don kwata kwata ba wani enjoying dinshi tayi sosai ba..suna tsaka da wnn hira wayanta ya fara ringing ta dauka da sauri tana zare ido ganin Proprietor akan screen..mikewa tayi ta fita daga dakin sbd hayaniyarsu bazai bari taji ba..kiran na katsewa wani ya sake shigowa dan tayi picking tareda cewa"sir ina yini"..bai amsa gaisuwar ba sai yace mata"ki fito in ganki ina bakin gate dinku plss"..dan tura baki tayi kmr yana ganinta tace"sir dare fa yayi"..a hankali yace"i know..bazan iya bacci bane tunda nasama taina saina ganki nasan matsala zan samu idan ba ganin naki nayi ba..ki daure kizo kinji"...bata sake mgn ba ta kashe wayarta tareda dora babban hijab akan three quarter da rigan dake jikinta..wayanta na rike hannunta ta fita daga hostel din..idanunshi na kanta yana kallo kmr bai taba ganinta ba har ta karaso inda yake..da sauri ya bude mata kofa ta shiga snn ta rufe kofar..kanta a kasa tana wasa da fingers dinta tace"ina yini"..maimakon ya amsa sai ji tayi yace"i missed u"..sake sinne kanta kasa tayi tanajin wani irin yanayi tattare da ita..shi kuma kallonta yakeyi kmr an aikoshi..wani abu yakeji mai kamada magnet ko kuma ince maganadisu yana kokarin janshi gareta amma bai bari yayi tasiri ba ya dan janye jikinshi kadan ya sauke wani ajiyar zuciya mai karfi tareda relaxing jikin kujera yana cigaba da kallonta..shi baiqi su kwana a haka yana kallonta ba wlh..he can’t get enough of her..komai nata abun kallo ne a wurinshi shiyasa wani lokaci shi kanshi yakan ba kanshi mamaki...ganin yanda suke zaman kurame yayi breaking silence ta hanyar kiran sunanta"Aysher"..amsawa tayi da"na’am"..ba tareda ta yadda ta dago idonta ba..shikuma yana cigaba da kallonta murya kasa kasa yace"i missed u so much..can i hug u plss"..da sauri ta shiga girgiza kai tace"Noo"..hannunshi ya daga alaman surrender yace mata"shknn i wont touch u tunda bakiso..amma da gaske am missing u sosai..ko bacci bana iyayi"..lumshe idanunta tayi tanajin wnn baqon yanayin daya tsiri bijiro mata a duk sanda take tare dashi..gabanta har wani faduwa yake na rashin dalili...sake matsowa yayi yana kallon cute face dinta da kyau har breathe dinshi na sauka direct akan fuskan nata sbd kusancinsu yayi mata wispering"i love u"..sake runtse idanun tayi tanajin faduwar gabanta na sake tsananta..wai wane irin mutum ne shi kam?..yana gama fadin haka ya sake komawa ya kafe jikin seat din da yake har yanxun yana kallonta yace"bari in barki ki tafi saida safe..dama kawai nace izo in ganki sbd in samu bacci sosai"..kai kawai ta iya gyada mashi ta kasa cewa komai..dan marairaicewa yayi yana dubanta yace"Aysher this is not fair mana..kin kulle idanunki kin hanani ganinsu snn mgn ma bazan samu ayimun ba?.."da kyar ta iya bude bakinta tace"saida..safe"..kallon bakinta kawai ya tsaya yi and he couldn’t help it but closed his eyes sbd yanda yakejin kmr ya kama dan bakin yayita sha..hannunshi ya mika baya ya dauko wani shopping bag mai kyau ya mika mata ganin idanunta a kulle ne yace mata"take mana"..sai yanxu ta bude idanun tana kallon bag da yake miko mata..sbd tsabar bazata iya masa musu ba don ko bude baki bata sonyi ta amsa bag din kawai batareda tace komai ba..bayan ta amsa yace"Mummy tace in kawo maki"..gyada kai ta shigayi kafin a hankali ta sake cewa"nagode"..yayi murmushi tareda daga mata kai kawai duk mood dinshi ya sauya wanda har yayi affecting idanunshi...cire mata lock yayi ta bude motar ta fita snn ta sake sukuyowa ba tareda ta yadda sun hada ido dashi ba tace"thank u..saida safe"..yana kallonta kasa kasa shima yace"saida safe..love u"..bata sake gigin cewa wani abu ba ta bar wurin da sauri rikeda bag din daya bata..shiko lumshe ido yua sakeyi kafin ya bude ya tayar da motar snn yayi reverse ya fita daga hostel din. The next morning da wuri suka gama shiryawa kowa cikin well ironed uniform dinta da dan mini hijab dinsu as usual..kafin su fita daga room dinsu Lamido ta dauki wani pink veil dinta mai dan girma ta yafa akan uniform din nata don tasan idan ma bata sa ba saiya mata mgn..Billy sai daria take mata itama tana rama tsokanarta da taitayi jiya haka su fita daga dakin..kmr kllum yauma school bus dinsu ne ya kwashesu kowa za’ayi dropping nashi hospital da akai posting dinshi..Freedom suka fara zuwa and abun da ya basu mamaki bai wuce ganin su biyu kadai akai posting Freedom din ba dan gaba daya sauran dake cikin bus din ba wanda take a nan...suna fita suka nufi cikin asibitin kai tsaye...office din CNO suka nufa as usual don yayi masu posting sai yace suje office din Dr Bobby yace shi da kanshi zaiyi musu posting bashi ba..wani irin kallon juna sukai suka hada ido suna fita Billy ta sake rushewa da daria..Lamido bata kulata ba har suka isa office dinshi..kafin suyi knocking wani messenger dinshi dake zaune gefe da alaman su yake jira ya tashi ya bude musu office din yana cewa"doctor yace ace ku shiga ciki ku jirashi..sun shiga theater ne tun daxu"..basuyi masa musu ba suka shiga office din Lamido sai binshi takeyi da kallo tana tuna abubuwa a dama da suka faru cikin office din nan nashi..ta tuna ranar farko data fara shigowa office din lokacinda sukaje bikin Aneesa ta bar ward dinsu ba kowa har hakan yayi sanadin rasuwar wata mata..ranar ne ta fara shigowa office dinshi yayita sata aiki snn ya hanata zama for almost 5 hours..ta tuna lokacinda batada lafia ya kawota nan ya dubata sai kuma lokacinda Provost ya kawota sbd yayi fushi da ita..she remembers how he hugged her at that time..how he wrapped her with his hands..batasan lokacinda ta lumshe ido tareda zaunawa nan kujeran dake kusada ita ba..nan take komai daya taba faruwa a office din ya shiga dawo mata daga masu dadi har masaru dadin..ta tuna randa yake cewa bazaiyi posting nata inda takeso ba until she promised to stay far away from doctors da duk wani staff namiji and her reply was"bazan kulasu ba ai dama bana da interest kan doctors da health workers sbd son matansu yayi yawa"..sake lumshe ido tayi tana tuna yanda komai ya faru a office din...bit by bit ta shiga remembering duk wani moment da ta taba spending a office din har zuwa time dinda taji ciwo a kafa..how he treated her..da yanda ya daukota cak tun daga parking space zuwa cikin office din..tayi nisa sosai cikin tunani har batasan wayanta dake cikin bag dinta nata ringing ba saida Billy ta daddage ta kwada mata duka a cinya snn firgigit ta dawo hayyacinta..ta wani hade rai tana kallon Billy yace"wnn wane irin mugunta ne..kinji zafinda naji kuwa?.."murmushi Billy ta saki tana fadin"yi hakuri Ammi keta kiranki tun daxu fa kina can kina tunani"...daukan wayan tayi da sauri taga two missed calls from Ammi dan haka tayi dialing number dinta tana kara wayar a kunne...Ammi na dagawa tace"ina kika shigane naketa kira baki dauka?.."da sauri tace"Ammi ban ganiba wlh..ina kwana"..Ammi tace"lafia lau..ya makarantan"..tace"fine Ammi..yau mukayi reporting asibiti"..Ammi tace"to Allah ya taimaka..dama tuna maki zanyi karki yadda kiyi abunda bashi knn ba..ki nustu ki kama kanki yanxu kinga dai mgnr aure ne tsakaninki da mutumin nan idan kikaje kikayi abunda mutuncinki zai zube a wurinsa ke zakizo daga baya kinajin kunya sbd haka ki kula sosia"..gyada kai takeyi tace"insha Allah Ammi zan kula..i will be a goo girl"..Ammi tace"to Allah yayi albarka..ina Bilkisu?.."tace"gata"..snn ta mika mata wayar..Billy na amsa itama ta gaisheta kafin ta amsa da fadin"so nakd kisamun ido akanta sosai duk kikaga zatayi wani abu daba shknn ba ki kira ki fadamin"..da sauri Billy tace"zanyi haka inshaAllah Ammi"..daga haka sukayi sallama ta mikama ma Aysha wayarta..ta karba tana sake dinke fuska tace"sbd mugunta kika dakeni Billy..kinji zafin da nakeji kuwa"..kallonta Billy keyi tana kunshe daria tace"to Allah baki hakuri nidai"..ta daddage zata fara masifa aka turo kofar office din aka shigo nan take ta hadiye masifar da takeson saukewa tareda kasa da kanta kmr mara gaskia..kamshin perfume dinshi kawai taji ta gane shine don a jikinshi kadai tasan irin wnn kamshin...shigowa cikin office din yayi waya kare a kunnenshi idanuwanshi kuma kyam akanta har ya isa seat dinshi ya zauna..kallonta yacigaba dayi yana sauraron abunda ake fada mai ta wayar banda gyada kai ba abunda yake itadai Lamido tayi wani tsit ko numfashi ma a nutse take daukanshi sbd kada ace tayi ba daidai ba...muryanshi taji yace"abunda zai faru yanxu ki turota tazo ta sameni zuwa anjima sai ik duba maki ita inyaso duk yanda ake ciki i’ll let u know"..shiru ya sakeyi kafin kuma yace"alright sai anjima"..daga haka ya ajiye wayar yana kallon yanda ta dage wasa da fingers dinta kmr ‘yar yarinya..juyawa yayi yana kallon Billy da ido ya tambayeta"what happened to her"..Billy ta bude hannayenta alaman she have no idea..sake juyawa yayi gareta still kanta a kasa Billy ta gaisheshi ya amsa ba tareda ya dauke idon daga kanta ba.."Aysher"..ya kira sunanta a hankali..maimakon ta amsa sai cewa tayi"ina kwana"..komawa yayi yai relaxing kan kujera yana dan rotating dinshi yace"yau bazan amsa gaisuwan nan idan baki dago kin kalleni ba"..sake sunkuyar da kanta tayi tana turo baki..yace"bazaki kalleni ba?.."kin dagowa tayi shi kuma yacigaba da kallonta yana shafa gemu zuwa sajenshi yace"then yau zamu yini office din nan knn"..juyawa yayi ga Billy dake kallon love iya love yace mata"kice ta bude idonta idan baso take mu kwana office din nan ba"..ajiyar zucia Billy ta sauke before saying"Lamido open ur eyes mana"..banza itama tayi mata taki dago kan nata..ganin haka ya juya ga Billy ya sake cewa"ina kikeso ayi posting dinki tunda naga ita zaman office din nawa takeso"..da sauri ta dago idanunta tace"ni ba zaman nan nakeso ba"..yace"then look into my eyes"..shoulder ta makale mashi tace"ni banason kallonsu"..yace"why?.."tace"suna sani jin wani iri"..murmushi kawai ya saki tareda gyara zama yace"to ku fadi inda kukeso ayi posting naku"..da sauri Billy tace"sir ni theater nakeso"..tana rufe baki Lamido tace"nidai bazanjd theatr ba gaskia"..bai sake mgn ba yayi posting Billy theater ta tashi ta tafi..ita kuma yace ta fadi inda takeso yayi posting dinta tace maternity..baiyi musu ba yayi posting dinta can itama ta mike zata tafi yace"banda mgn da maza dan Allah"..kai kawai ta gyada mashi ta fita tana sakin ajiyar zucia..batasan meyasa these days duk take taredashi take jinta kaman a prison ba..hatta numfashinta ba daidai yake tafia ba ta kuma rasa dalilin wnn abu haka..mutuminda ba tun yau ta sanshi ba ta rasa meyasa sai yanxu takejin wnn bala’i a kanshi..shikam da kallo ya bita har ta fita snn ya janyo wasu files dake kan desk dinshi ya fara dubawa yanata zabga murmushi..saida ya gama going through the files snn ya ajiyesu ya fita daga office din zuwa maternity don yin ward round. Kwanaki nata tafia yayinda Dr Bobby ke gwada mata tsantsar soyayya..gaban kowa nuna mata so yake babu ruwanshi saida ita ya barta dajin kunya..har mamakin yanda baida kunya take wlh..koda yake ba abun mamaki bane idan akayi duba da ya hada jini da inyamurai...kullum ta shigo asibiti sai ta fara zuwa office dinshi don idanma bata je ba shi zuwa yake har inda take ya bata kunya..haka zai ajiye duk wani abu da yakeyi ya tashi ya rakata har maternity tun abun na bata kunya har tazo ta denaji..daga karshe ma hanata bin school bus yayi yasa driver dinshi ke zuwa ya daukosu daga hostel snn ya maidasu idan sun tashi aiki..Lamido tun tana ignoring abunda takeji game dashi har ta fara saduda..soyayyan da yake gwada mai tsayawa a rai ne don kullum ta koma hostel tayita tunaninshi knn har wani lokacin ta tsinci kanta tana murmushi..tana jin dadin yanda yake kulada ita sosai da kuma yanda bai iya 6oye abunda yake feeling gameda ita..duk wanda yayi zama 10 mins dasu saiya fahimci ba dan karamin so yakeyi mata ba...abu daya da watarana yake bata haushi shine kishinshi da yayi yawa..gaba daya yabi ya takureta a asibitin ta yanda ko mgn yaga tanayi da namiji shknn ta shiga uku don saiya mata fada..har mamakin yanda yake daure face dinshi take sai kace bashine ke mata mahaukacin so ba amma kan kishi gaba daya idanunshi rufewa suke..snn ga dokar saka hijab daya kafa mata shima ba karamin takura bane a wurinta amma haka nan ta hakura take sakawa dan ko by mistake ya ganta ba tareda hijab din nan ba sai an samu matsala..a 6angaren Billy da Hammanta kuwa soyayya ce mai karfi suke yinta don yanda suke son juna abun har mamaki yake bata..wani lokaci idan Billy na waya dashi saidai tayi zaune tana kallonta a daidai lokacin sai itama soyayyan da sukayi da Prof ya shiga ya dawo mata..ta tuna itama fa da haka takeyi da saurayinta amma with Proprietor komai ya canxa mata..dukda zuwa yanxu ta rage jik kunyanshi amma har yanxun bata iya sakewa tayi mashi mgnr daya shafi love kmr yanda shi yake mata..bata sani ba ko har yanxu bata fara sonshi bane amma dai ta tabbata ya samar ma kanshi special place a cikin zuciyarta. Yau Friday da safe ta shigo asibitin ita kadai kasancewar Billy evening duty gareta..bata je office dinshi ba kai tsaye ta wuce maternity sbd ta danyi latti..tana shiga ta cire hijab dake jikinta ta bar iya na uniform dinta snn ta shiga cikin labour room bayan ta gaisa da sauran staff dake dakin..Nurses station ta shiga ta ajiye bag dinta snn ta shiga ciki..mutum biyu ta samu kwance a dakin..daya daga cikinsu nata fama don har anyi rupturing membrane..karasawa tayi tana dubata sai taga head ya fara tahowa dan haka tayi saurin daukan hand glove ta saka snn ta shiga assisting matar..cikin ikon Allah ta haifi yaronta lafi..bayan tayi musu duk wani necessary abu tace ma matar ta fadi sunanta wanda suka kawota aje a karbo kayan baby a wurinsu..ba musu matar ta fadi sunan mijinta ita kuma ta fita don sawa a karbo kayan sai bataga ko daya daga cikin messengers dinsu ba dole ta fita da kanta ta amsa kayan ta dawo..tana cikin shirya babyn ya shiga cikin labour room din sbd kiranshi da akayi ya duba daya matar dake cikin dakin..abunda ya bata mamaki shine yanda yayi kamar bai ganta ba ya wuce inda matar take fuskan nan nashi a daure kmr an aiko mashi da saqon mutuwa..dakatawa tayi da abunda take ta juya tana kallonshi still taga ko inda take baya kallo ya fara aikin gabanshi..ranta taji ya 6aci sosai..to uban me tayi kuma da zai wani dinga shareta dan rainin hankali kawai. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 49 Kallonshi ta tsaya yi da mamaki bayan ta gama shirya yaron ya dorashi jikin mamanshi da aka wuce da ita post natal..yanxu laifin me tayi kuma?..ko dan sbd bataje office dinshi bane yau?..karasawa tayi inda yake bayan sauran Midwives din sun fita..murya can kasa tace mishi"ina kwana"..wani kallo daya sakar mata saura kiris ta fadi kasa sbd tsabar rudata da yayi..ta tabbata wnn fushin ba iya na rashin zuwa office dinshi bane dole da akwai wani abu to amma menene?..duk jikinta yayi sanyi taji bataji dadin wnn cold treatment dinba tunda ba haka ya saba mata ba..tafiso yacigaba da kulawa da ita yana nuna mata so kmr dai yanda yakeyi a baya..ganin har yanxu bai kalli inda take ba aikin gabanshi kawai yake sai ta juya ta fita daga labour room jiki a sanyaye..lumshe ido yayi bayan fitan nata yana sauke numfashi..jiya ko baccin kirki kasawa yayi sbd labarin da aka bashi wai tsohon saurayinta yaje har hostel wurinta kuma ta fito ta sameshi sbd batada hankali..abun yayi mashi ciwo sosai ta yanda har zata iya zuwa ta kula wani bayan alqawarin aure dake tsakaninsu..snn kuma da zai shigo nan ya hangeta tareda wani suna mgn kuma ko hijab babu a jikinta haka ta gama nuna mishi jikinta ta juya ta tafi yana ganin yanda mutumin yabita da kallo..a yanda yasan halinta da shegen rashin jin mgn tabbas idan ba zafi zafi yayi mata ba bazata shiga hankalinka ba shiyasa dole ya dake ya nuna mata abunda tayi ba daidai bane sbd ta kiyaye gaba amma shi kanshi bajin dadin fushin da yakeyi da ita yake ba..kawai dauriya yake amma Allah kadai yasan halinda yake ciki...a takaice har ya gama aikinshi ya bar ward din baibi ta kanta ba hakan kuma ya sake daga mata hankali fiyeda tunani..lokacin tashi nayi ya tura mata text saying tazo office dinshi idan ta tashi ya maidata hostel..ba bata lokaci ta nifi office din nashi bayan tasa katoton hijab dinta..tana shiga ko zama batayi ba ya dauki wayoyinshi dake kan desk dinshi ya bude kofa yana kallonta fuska daure yace"muje"..kai a kasa ta ra6a ta fita daga office din shima ya fita suka wuce parking space..amsan key yayi hannun drivernshi snn ya bude mata front seat ta shiga shima ya shiga snn ya tada motar suka wuce..ko a hanya sai satar kallonshi take taga fuskan nan a cunkushe kamar na shanu..sun danyi nisa da tafia wayanta ya fara ringing ta duba screen sai taga thesame number ne da baby ya kirata dashi jiya dan haka tayi daurin silencing wayar tareda turata cikin jaka tana rarraba ido..Bobby dake ankare da duk abunda take hannu yakai ya dauki bag din nata tareda zaro wayar daga ciki snn ya ajiye mata jakar ta..kallon wayar ya tsayayi kafin wani kiran ya sake shigowa bai tsaya wata wata ba kuwa yayi answering tareda sawa a speaker..on the other hand Prof na jin tayi picking call din ya fara cewa"baby girl listen to me plss..i will explain everything..lokacinda.."kitt Bobby ya katse kiran tareda kashe wayar gaba daya yasa a aljihunshi saura kiris kan motar ya kwace mashi Allah ya taimaka yayi saurin daidaitashi..Lamido kuwa banda kwalo ido ba abunda take shknn ya gama tona mata asiri..kodai ya samu labarin yazo hostel jiya?..tunanin hakan yasa taji kaman fever na neman rufeta..yanxu idan ya fadawa daddy ai ta shiga uku..shidai yana driving yana kokarin cooling temper dinshi don idan ta zuciyarshi zai bi yana iya gaura mata mari a wurin..kawai zafi yakeji na wnn tsohon mutumin da bazai bar mashi ita ya huta ba..idan ba iskanci bama baiga dalilinda zaisa yace yana son ‘yar cikinshi ba wlh..duk ranshi ya sake 6aci kafin su isa hostel ya cika yayi fam kiris yake jira ya fashema wanda keda rabon shan masifa..daurewa tayi ta tattaro duk karfin halin da take dashi ta kira sunanshi a hankali"Sir"..bai kulata ba kuma bai kalli inda take ba..ta sake juyawa taga yanda yake cin kuna sai kawai ta kauda kanta tana turo baki..tun asali fa wnn baqin halin nashi ne yasa bata wani so aurenshi ba..kan a very minor abu zaizo ya nemi daga mata hankali..har suka karasa hostel batace ba shima baice mata ba..bayan ya gama parking ta juya tana kallonshi kafin tayi mgn taji yace"sauka"..ko minti daya bata kara na cikin motar ba ta bude tayi ficewarta ko sallama bata yi dashi ba..da kallo ya bita zuciyarshi na tafasa yayi reverse ya bar hostel din..direct gida ya koma don yana bukatar mgn da Mummy a halin yanxu..ya fuskanci idan ba wani mataki ya dauka ba tsaf tsohon mutumin nan zaiyi snatching dan attention dinta daya fara samu yanxu..direct bedroom din Mummy ya shiga ya sameta zaune tana karatun Qur’ani ya karasa da sauri ya zauna kusada ita yana kallonta kmr wanda ke shirin fashewa da kuka..Alqur’anin hannunta ta ajiye bayan takai ayah snn ta shiga dubanshi tace"kai lafia kuwa?..why zaka shigomin daki a zabure haka?.."kama hannayenta yayi yanayi mata puppy eyes yace"Mummy akwai matsala wlh"..kallonshi Mummy keyi tace"matsalar me?.."yace"Mummy so nake ayi mgn da Lamido ya tsayar mun da rana nidai..bazan iya jira har saita gama karatu ba wlh"..zare idanu Mummy tayi tana kallonshi tace"rashin kunya Bobby?.."girgiza kai ya shiga yi yace"ba mgnr rashin kunya ba..wani mayen mutumi ne ya makale ma yarinyar nan yake kokarin rabani da ita ni kuma hankalina bazai kwanta ba tunda kinga ba wani sona takeyi ba har yanxu"..ajiyar zucia Mummy ta sauke kafin tace"sai kaje kayi mgn da Waziri sune masu nema maka aure bani ba"..da sauri yace"kunyarshi nakeji wlh..kiyi masa mgn da kanki"..girgiza kai Mummy ta shigayi tana murmushi..ya sake kama hannunta yace"Mummy please mana..ba tuntuni kikeso inyi aure ba?.."kai ta gyada alamar eh..yace"to yanxu nakeso nayi auren Mummy kiyi wani abu plss"..kai ta gyada mashi tareda fadin"zanyi mgn da wazirin"..da sauri ya rungumeta yana cewa"nagode sosai mother..Allah ya baki aljannah"..kai kawai ta iya gyadawa tana shafa kanshi..har yanxu bata dena mamakin wnn so da Bobby kema yarinyar ba...sallama yayi da ita ya sake komawa hospital don bai kammala aiyukanshi ba. Bai baro hospital din ba sai after magrib..yaso ya wuce gida amma yaji bazai iyaba sai yaje yayi mgn da ita..so yake fushin nashi ya dore amma yasan bazai iyaba don wahalar da kanshi zaiyi..gashi ita ko text message batayi masa irin na bada hakuri ba balle yasa ran kira..jikinshi duk yayi sanyi yasan dama shi kadai yake sonta ita ba sonshi take ba..bayan driver ya gama parking ya bude motar ya fita shi kuma ya kira wayarta tana dauka yace ta fito waje yana jiranta...hijab ta dora akan dogon rigan dake jikinta ta fita..kafin ta karaso ya bude mata kofa dan haka tana zuwa ta shiga tareda maida kofar ta rufe..kamshinshi duk ya cika motar ga kuma sanyin ac da driver ya bari a kunne..kallonta Bobby yake yanajin ciwon tsayawa da tayi kula tsohon saurayinta..kmr tasan tunanin da yake knn tayi kasa da murya tana dan kallonshi a hankali tace"sir nidai dan Allah kayi hakuri"..kallonta yacigaba dayi kafin yace"why are u doing this?.."a hankali ta sake cewa"am sorry"...lumshe ido yayi tareda jingina kanshi jikin seat din da yake yana sauke numfashi..dama yasan wnn fushin ba wani wurin zaije ba tunda ba iya fushi zaiyi da ita na lokaci mai tsaho ba..bude idon yayi yana kallonta ita kuma ta sake narkewa cikin shagwa6an da ta manta yaushe rabonta dashi tace"nidai kayi hakuri bazan kara ba"..kallonta kawai Bobby yake gabanshi har wani faduwa yake..yau dai itama ta tsayar da idonta a kanshi tana kallonshi da puppy eyes don da gaske bata son yana fushi da ita..wani irin sanyi da kasala Bobby yaji sun dirar mashi at once..gaba daya joints din jikinshi sukayi wani irin weak kaman wanda yayi shekara da shekaru ba lafia..lumshe ido yayi ya bude yana sake kallon yanda har yanxu bata dauke idanu akanshi ba..baisan wane force of attraction ne ya matsar dashi kusada ita ba kawai shidai yaji yana iya zaucewa yau idan baiji yarinyar nan a jikinshi ba..Allah kadai yasan yanda yake kokarin fighting wnn feeling dake bijiro mishi duk yake tareda ita amma wnn is different and beyond his control..a hankali yakai hands dinshi yayi cupping fuskanta dasu yana sauke numfashi da sauri kmr wanda yayi aikin karfi..da sauri ta lumshe eyes dinta gabanta na faduwa..fuskanshi ya dora kan nata yana kallon the most cutest and attractive lips daya taba coming across duk rayuwarshi..a hankali ya bude bakinshi yace"i..i..want"..kasa karasawa yayi kawai saiya rungumeta a jikinshi yana sauke ajiyar zucia..wani irin azababben so da qaunarta suna sake zaga kowane kafa na jikinshi..shidai yasan yarinyar nan idan bata soshi ba mutuwa zaiyi for sure..wnn son da yake mata bana lafia bane ya sani..wani irin dif Lamido tayi tanajin yanda heart dinshi ke beating da karfi..ga wani irin force da yayi applying a hug din kaman zai maidata jikinshi...batayi mosti ba kmr yanda batayi kokarin kwace kanta ba..heart beat dinshi da taji kadai ya isa ya tabbatar mata da ba karamin so yake mata ba..wani tausayinshi taji ya kamata...shiko Bobby har yanxun eyes dinshi lumshe yanajin wani extra hot feeling na sake rushing into him..gashi duk kokarinshi na yaga ya rabata da jikinshi ya kasa sbd ko energy baidashi..saida ya daddage snn ya iya raba jikin nata da nashi idanunshi kumshe ya jingina kanshi da kujera..kallonshi Aysha keyi ba tareda tace komai ba har ya dan samu nutsuwarshi snn ya bude idonshi da sukayi jaa sbd abunda yakeji voice dinshi na fita da kyar yace mata"i will die without u..i love u"..kallonshi kawai Aysha keyi batace komai ba..shi kuma yana dubanta ya gyada mata kai yace"yes..i love u to the core..duk wnn abunda kike ba karamin daga hankalina yake ba..am sure yanxu if za’ayi diagnosing dina baza’a rasani da high blood pressure ko kuma cardiac problems ba and it’s all because of u"..kallonshi har yanxu takeyi fana langabar da kai kmr zata sa kuka..hannunta ya kama ya dora saitin heart dinshi yace"zafi nakeji a ciki duk lokacinda namiji ya ra6eki..inajin kmr zata fasa kirjina ta fito idan kika fita ba tareda covering jikinki completely ba..snn inajin ciwo idan kika nuna baki damu dani ba"..shiru ya sakeyi yana sauke numfashi..itama tayi tsit tana sauraran heart beat din nashi..hannun nata ya cire daga chest dinshi ya rikeshi gam da nashi hannun yana yi mata kallon da ya kusa tafia da imaninta in a pleading tone yace"i beg u in the name of almighty ki bar wahalar dani haka..all i want from u is love and care..ko baki soni yanda nake sonki ba i will manage and i will live a happy life for as long as ina tareda ke..i love u so so very much Aysher..i love u to the moon"..kai kawai ta shiga gyada mashi hawaye har ya ciko idonta tace"kayi hakuri ban karawa"..dan murmushi ya saki tareda matsawa ya manna mata peck a forehead dinta yace"thanks love..i love u"..lumshe ido tayi hawayen dake cikeda idon suka zubo kan fuskanta..kmr an fizgi mgnr daga bakinta tace"and i..i..i.."kasa karasawa tayi ta sake lumshe ido..da sauri Bobby ya sake kama hannayenta yana kallonta cikeda son yaji abunda zata fada"say it..say it plss it’s what i have been longing to hear from u..please say it in samu saukin zuciata"..sake runtse idanu tayi voice dinta na rawa tace"i..love..u"..tun kafin ta karasa ya cike gap din dake tsakaninsu ta hanyar yi mata kyakykyawar runguma...wani irin bright smile ne kwance kan fuskanshi yaji kalmar i love u din nan tafi diamond da gold a wurinshi..wani irin sanyin dadi yaji yana kamashi ashe haka akeji idan masoyi ya furta kalmar so?..ashe haka feeling din yake?.."oh Allah thank u..Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah yaa rabb"..sun dauki lokaci mai tsaho a haka kafin yayi breaking hug din ya dagota sai yaga hawaye take wani nabin wani..hannu yakai yana share mata hawayen yace"don’t cry okay?..stop crying i love u"..kai ta gyada mashi tana wani turo baki..ita kanta batasan wai ita zata iya bude baki tacema proprietor she loves him ba amma gashi tayi..it happened all of a sudden..kawai batasan yaushe ta fara sonshi ba amma for sure yau ta tabbata she loves him too and she doesn’t want to share him with any other woman..ido ya kuma lumshewa tareda pecking forehead dinta yana dubanta da bright smile nasa yace"thank u so much love..thanks for loving me"..murmushi kawai ta saki dimples dinta suka fito..Bobby dake kallonta yau dai yakai fingers dinshi ya aza bisa dimples din nata..hannunta tasa ta dafe nashi hannayen snn ta dan bude ido kadan ta kalleshi sai kuma ta sake maidawa ta rufe..sunkuyawa yayi ya hade fuskanshi da nata yace"open ur eyes mana ki sake maimaitawa inji"..shoulder ta makale tana wani turo baki tace"oh oh"..daria sosai Bobby ya saki har yanxu fuskanshi hade da nata..wani irin mashahurin nishadi yaji yana saukan mishi ta ko ina kmr bashine dazu kunci suka mai zucia ba..wato Allah dai shine mai yanda yaso kuma a lokacinda yaso..bayan ya gama dariarshi ya raba jikinshi da nata tareda duba agogon hannunshi nan take ya wara ido cikeda mamaki ganin time ya wuce har haka..juyawa ya sakeyi yana kallonta har yanxu bata bude eyes dinta ba..shi duk bai gaji da ganinta ba wlh..ya zama dole ma yaje ya hura wuta shidai asa rana ayi ayi a daura a kawo mashi ita gidanshi don bazai iya jurewa ba anymore..hakurinshi ya kare don haka kawai asan yanda za’ayi dashi shidai..hannunta ya kama yana kallon yanda har yanxu eyes dinta ke rufe yace"love to ki bude idon naki muyi sallama mana"..shoulder ta sake makalewa tana girgiza kai..hands dinshi ya hada wuri daya alaman begging yace"Aysher please mana..ki tausaya min please"..bude idanun tayi a hankali tana kallonshi sai kuma ta bude kofar da sauri ta fita daga motar har tana hada hanya..wani kunyanshi taji ya rufeta wlh..sam bazata iya hada idanuwa dashi ba ita dai..Bobby kam relaxing yayi nan cikin motar yana binta da kallo har ta shige gate dinsu...ajiyar zucia mai karfi ya sauke yana sake godia wa Allah daya nuna mashi wnn rana..shikam babu abunda zaima Allah sai godia..hakika an gama mashi komai na dunia saidai fatan cikawa da imani kuma..driver na ganin fitarta ya koma ciki ya tada motar suka tafi yayinda Bobby ke jingine da seat yana ayyana yanda zaije ya takurama kowa har ansa mashi ranarshi..kuma bada nisa yakeso asa ba shi in ta nashi ne ma nan da two months yakeso ayi komai a kawo mashi matarshi. Yana shiga gida ko flat dinshi bai shiga ba ya fara shiga flat din Mummy..har ta fara bacci shigowan nashi ta farka ta shiga dubanshi da mamaki tace"lafia dai koh?.."zama yayi a gefenta yace"ba lafia ba Mummy..mgnr sa ranar nan ne dai"..da mamaki Mummy take kallonshi tace"Bobby yaushe ka zama mara kunya ne wai?.."turo baki yayi yace"Mummy ba rashin kunya bane kawai nidai na gaji da jira ne..nidai dan Allah kiyi mgn dasu in two months time nakeso ayi komai plss"..tace"shi kuma ginin gidanka daka ajiye ka denayi fa?..kana ganin zaka iya karasa shi in two months time?.."da sauri yace"Mummy ai finishing ne kadai ya rage and in 4 weeks time nasan za’a gama kawai kice musu nidai banaso ya wuce two weeks"..ha6a Mummy ta kama tace"innalillahi wainna ilaihi rajiun"..sake marairaice mata yayi yace"Mummy please"..kallonshi kawai Mummy keyi tace"ikon Allah"..ya sake bude baki zaiyi mgn tace"tashi ka barmin daki kafin ranka ya 6aci wlh..yaushe ka zama mara kunya haka ne"..mikewa yayi yana turo baki yace"Mummy ni ba rashin kunya nake ba"..tace"to wuce ka barmin daki idan ba haka ba ince shekara guda za’a sa ba wata biyu ba"..ya sake bude baki zaiyi mgn tace"nace ka fita daga dakina Bobby"..sum sum ya juya ya fita daga dakin yana kunkuni..shifa duk basu san halinda yake ciki bane..da sun san abunda yake going through da basu tsaya yi masa kwane kwane ba wlh..he’s kind of desperate..he’s eager..shi gane yakeyi idan ba’ayi komai da wuri ba tana iya dawowa nan gaba tace bata sonshi kuma..har yanxun there is this insecurity a tare dashi amma sun kasa ganewa. Lamido kuwa da gudu gudu ta koma hostel kai tsaye ta shige room dinsu tareda fadawa gado tanata doka murmushi kai kace mahaukaciya ce sabon kamu..wani irin excitement taji ta tsinci kanta a ciki all of a sudden..wato Allah yayi ma Proprietor baiwar iya kalamai sai kace abunda ya karanta knn..yanda yake tsara mata love words abun har mamaki yake bata yanda baya taba running out of them..gashi da kirki da iya kula da mace snn kuma uwa uba yana yi mata sonda tasan duk dunia babu maiyi mata irinshi idan aka dauke parents dinta..bata san how and when ta fara sonshi ba kawai lokaci daya taji tana sonshi itama kuma zata iya auranshi ko don sbd wnn son da yake mata..ta lura he is super romantic dan yanda yayi wrapping dinta a chest dinshi daxun kadai ma abun tsayawa a rai ne balle kuma wnn maganganun da yayita fada mata wanda sune suka bijiro da nata son itama har ta kasa rikewa ta sanar dashi..she remember the smile on his face lokcinda ta furta tana sonshi..she remember how he pecked her kawai saita saki murmushi mai sauti..gaskia Dr Bobby is amazing..he is one in a billion and duk macen data aureshi will be considered as a lucky girl..tayi zurfi sosai cikin tunaninta har bata san yaushe Billy ta shigo dakin tana mata mgn ba..saida ta daddage ta daka mata duka snn ta dawo hayyacinta..ta mike zaune tana waji daure fuska tace"meye haka?.."zama Billy tayi nan kusa da ita tana kallonta with smile tace"bestie bani labari dan Allah..what’s the good news?.."murmushi Aysha ta saki tana wani kallonta ta gefen ido tace"who is ur bestie?.."Billy tace"to yi hakuri bestyn Sa’eed..bani labari inji what’s the secret behind wnn beautiful smile din naki?.."gyara zama Lamido tayi tana dubanta still face dinta da murmushi tace"hmm Billy u wont believe this..wai nice yau da kaina na bude baki nace ma proprietor ina sonshi..can u believe this?.."tagumi Billy tayi tana dubanta da murmushi tace"ai dama kin dade da fara sonshi ganewa ne bakiyi ba..bani labari in de tadail plss"..Lamido tace"aikam dai daxu bansan ya akai ba kawai sai jin bakina nayi yana furta i love u..kuma wlh Billy da gaske sonshi nake..ya samar ma kanshi special wuri a cikin zuciyata har mamakin abun nake..it happen so fast"..murmushi Billy ke saki kai kace itace Proprietor tace"ai dama na fada maki mutumin nan karshe ne..ni tun daga yanda naga yana miki a hospital nasan ba karamin sonki yake ba sbd bai iya 6oyewa a ko ina"..zama Lamido ta gyara ta shiga bata labarin komai daya faru in detail..Billy tayi tsit tana sauraronta banda murmushi ba abunda take saki..Allah ya sani ita dama ta dade tanama qawat tata sha’awar auren proprietor sbd mutum neshi na kwarai..yanada duk wasu qualities da mace take nema a wurin namiji and above all yana sonta fiyeda yanda yake son kanshi..labari sosai Aysha ke bata tana yi tana blushing ita kanta mamakin yanda farat daya ya mamaye ilahirin zuciyarta take..ko daxu da safe bataji wnn feeling din game dashi ba amma yanxu gasu nan sai rushing sukeyi zuwa heart dinta kmr zasu fasa ta..so sosai taji tana mashi kusan fiyeda wanda tayi ma Professor Ahmad...saida ta gama labarinta tsaf Billy ta dauki waya tana searching contact din Sa’eed tace"Sa’eed needs to hear this..i cant believe Lamido is in love with Proprietor..what a miracle!.." Jama’a biki dai ya kusa sbd haka kowa ya fara shiri zamuje har Gombe mu gwangwaje💃🏻💃🏻💃🏻 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 50 Soyayya mai karfi ya shiga tsakaninsu tun daga wnn ranan..Lamido har mamakin yanda take mugun sonshi take..she loves him to the moon and back kmr yanda yake fada mata..kawai gani take babu macen da ta kaita sa’a data sameshi..yana sonta sosai and ya iya kula da mace sosai ba kadan ba..yanda yake treating nata yasa ko kusa bataso taga wata ta ra6eshi don yanxun zasu samu matsala..kulawa takeyi da abunta yanda ya kamata don da gaske bazata so ta rasashi ko tayi sharing dinshi da wata ba..duk wani abu da tasan bayaso ta bar yinshi wanda yakeso kuma tanayi don ta faranta mishi..sbd tsabar nutsuwa yanxu su Lamido kullum hijab ake sawa babba idan an shigo school ta cire..tana sonshi sosai kusan duk wanda ke tareda ita sun san da haka ga kuma kishi da take dashi don akwai ranar da kiri kiri tace bazai duba wata mata ba wai tunda ta shigo sai kallonshi takeyi..haka nan ya hakura bai dubatan ba saida ta bar office yasa aka sake kiranta..farin ciki sosai yake ciki na samun soyayyarta da yayi shiyasa har kullum bazai gaji da yima Allah godia ba...before su gaka Clinical Posting kusan yan asibitin kadan ne basu san Dr Bobby zai auri Lamido ba sbd yanda suke nuna tsantsar caring wa junansu is something else..wani lokaci kota rigashi tashi bata tafia har saiya gama da patients dinshi snn ya maidata hostel..abun nasu is so so interesting sai ma wanda ya gani..a haka har suka kammala posting suka koma makaranta. A hankali ta turo office dinshi ta shiga fuskan nan ba fus ganin yana tareda secretary dinshi da kuma wata da bata san wacece ba a office din..sake tamke fuska tayi ta karasa ciki rungume da hannayenta ta karasa ciki..tunda ya dago idonshi ya kalleta yasan akwai daru yau..yanda ta hade ran nan yasan drama ne zasuyi shi ba karami ba..File dake hannunshi ya mikawa matar dake gabanshi tareda sallamarta yace suje zai sake namants..ba musu suka bar office din Lamido ta shiga karasowa ciki har yanxun fuskan nan ba sarari..tsayawa tayi gaban desk dinshi tana mishi kallon tuhuma tace"who are they?.."dan wara ido yayi yana kokarin danne daria yace"secretary dina ce baki gane ba kuma?.."yana rufe baki tace"to na meye zasu wani shigo office dinka su zauna?.."kallonta kawai yake yana kunshe daria yace"to yi hakuri"..harara ta watsa mashi mai kyau tana sake dinke fuska tace"Kuma dayar hadda wani zuwa da dingilallen skirt..nidai bana so kana tara irin wayan nan mutanen a office dinka bakasan ‘yan iska bane koh?.."yana kallonta yace"baby ba tarasu nakeyi bafa..bakiga aiki ne ya kawosu ba?.."sake rungume hannu tayi ta zauna tana turo baki tace"nidai banaso..dama da aiki suke fakewa suzo suyita kallonka mana"..daria sosai ya saki jin kalamanta..har gobe wani extraordinary farin ciki yakeji idan yaga tana kishinshi haka..abun na qayatar dashi sosai..yanxu matsalanshi daya shine bikinsu da akace dole saita gama makaranta za'ayi..waziri da kanshi yace bazai ma jema da Lamido mgnr ba sbd yasan amincewa zaiyi bayan kuma ba haka sukaso ba..kokarin dakatar da dariyarshi yayi yana kallon yanda saura kiris ta fashe ya kama hannunta yace"to kiyi hakuri baby insha Allah bazasu sake zuwa ba..babu mai sake kallon miki ni kinji"..baki ta murguda tana hararanshi shi kuma yacigaba da kallonta full of affection yace mata"C'mon smile mana..da gaske sun dena zuwa daga yau and ko suna zuwa ma babu ruwana dasu you'll always be my one and only woman..baby I love u so so very much..i love u alot"..murmushi itama ta saki dimples dinta suka fito sai wani blushing take tace"nima da gaske Ina sonka..ban ta6a son wani namiji kaman yanda nake sonka ba Allah..i love u sosai"..gyara zama yayi yana marairaice mata yace"yanxu ya mgnr mu na daxu?.."itama marairaicewa tayi kafin tace"Sir ni bazan iyaba"..tun kafin ta karasa ta katseta da fadin"i told u ki bar kirana da sir din nan bakiji koh..am not ur sir for God's sake am ur partner..ur life partner so please ki bar kirana da wnn sir din is so irritating"..murmushi ta saki tana kallonshi ta wani kashe murya tana karkata kai tace"can i call u partner then?.."murmushi ya saki shima yana kallon eyeballs dinta yace"U can call me anything amma banda sir"..yana rufe baki tace"alright then daga yau ka zama partner kuma kaima dole kace mun partner"..makale mata shoulder dinshi yayi yace"No u are my baby..yanxun enough talking about that..ya mgnr mu na daxu?.."sake langabewa tayi tace"partner bazan iya bafa..kawai sai inje incema Lamido ayimun aure kafin na gama school"..tasowa yayi daga inda yake ya dawo kusada ita ya zauna suna facing din juna yace mata"partner yanxu bazaki tausaymin ba?..for how many months kikeso muyita zama a haka for God’s sake..if ke zaki iya jurewa ni bazan iya ba pls..na gaji da zama wothout u i want to get married"..baki ta rufe tana daria tace"partner rashin kunya fa"..yace"ba wani rashin kunya am saying the truth..ke baki ganin kokarina ma?.."..kama hannunshi tayi tana kallonshi in a pleading tone tace"nidai kayi hakuri dan Allah..bazan iya ba"..hannunshi ya zame daga nata tareda mikewa ya koma seat dinshi..kawai bazata gane bane shi kadai yasan halinda yake ciki..idan saita gama makaranta nan da almost four months fa ake mgn..dole ma yasan matakinda zai dauka gaskia..ita Mummy da anyi mgn kullum sai tace bai gama gidanshi ba amma yanxu ai ya gama gidan nashi tunda dama fininshing kadai ya rage to me ake jira kuma idan dai baso suke another sugar daddy yazo ya sake mishi gaba da ita ba..marairaicewa ta sakeyi itama kafin tayi mgn Nur ya shigo office din da files a hannunshi..yana ganinta nan zaune yayi wani saurin juya baya kmr wanda yaga abun kunya yace"A’uzubillahi Subhanallahi na shigo at the wrong time"..wani kallo Bobby ya bishi dashi yanajin kmr yaje ya rufeshi da duka..Lamido dai na zaune tana daria dan da gaske draman dake tsakaninshi da abokin nashi ba karamin daria yake bata ba..sake juyowa Nur yayi yana kallon Bobby da wani shegen smile yace"sorry for the interruption guys..will come back some later"..har ya juya zai fita Aysha tace"Sir ka dawo plss..dama ni tafia zanyi"..tana rufe baki Bobby yace"you won’t go anywhere until we finished our discussion"..kallonshi tayi taga ya hade giran sama dana kasa dan haka bata sake mgn ba ta gyara zama tana kallonsu..ta fuskanci shima ba karamin rigimamme bane wlh..at times ma sai taga kmr yafita rigima..juyawa yayi ga Nur da har yanxun yake tsaye rikeda files a hannu shi bai shigo ciki ba kuma bai koma waje ba..saida ya sakar mashi wani harara kafin yace"if u like ka karaso muyi abunda zamuyi as u can see ba zaman banza nakeyi ba"..da sauri Nur yace"ni din banza ince kana zaman banza bayan da idona naga babban aikin da kakeyi..ai ka wuce a kiraka da mai zaman banxa mr romeo"..sake daure fuska Bobby yayi baice mishi komai ba har ya karaso seat dake opposite to her ya zauna ita dai kanta na kasa sai ji tayi gogan nata yace ta koma kan sofa ta jirasu..dan dagowa tayi ta kalleshi tace"sir please..sorry i mean partner please inje anjima sai in dawo"..kallonta yayi yana jajjada mata ki dawo fa da idanunshi..murmushi ta saki tareda gyada kai hadi da lumshe ido meaning she will definitely come back..daga haka tayi sallama da Nur ta bar office din..tana fita Nur ya sauke wani ajiyar zucia yana shafa gemunshi yace"muma dai muzo mu fara love din nan..very soon zakaji nima na hau network wlh..bazanyita zama kuna kasheni da salon love dinku ba kaida Lamido"..harara Bobby ya watsa mashi kafin yace"abunda ya kawoka knn dama?.."girgiza kai Nur yayi tareda daukan files daya shigo dasu ya mika masa ya fara dubawa..shi Kuma Nur banda kallonshi yana murmushi ba abunda yakeyi..mamaki sosai yake na yanda abokinshi ya zama mastern soyayya kmr dai ba shine da yake cewa bazai iya soyayya da diyar kowa ba wai it's a waste of time and resources..yanxun sai gashi tsumu tsumu yana soyayya da Lamido kmr ba Dr Bobby ba shiyasa har kullum bazai dena mamakin yanda ta shigo rayuwarshi farat daya kuma ta canxa mishi ita ba. Da dare ya shigo parlon Mummy cikin wani baqin yadi daya haska skin dinshi sosai sai baza qamshi yake abunshi...Mummy da aunty sumy na zaune sai faman listing abubuwan da zasu fara siya na lefe suke don shirye shirye sosai sukeyi na biki da baifi saura few months ba..ya karaso ciki ya zauna yana kallon list din da suke yace"Mummy har yanxu list din bai kare bane?.."Mummy tace"ai list bazai kare ba Bobby kasan sha'ani irin wnn wahala ne dashi..idan ba list din akayi ba sai kaga anxo an manta da wasu abun ba'a siyo ba"..dakatawa tayi tareda dagowa tana kallonshi kafin tacigaba"wait..tun yaushe ma nace ka kawota inason mgn da ita kaki?.."shafa kanshi yayi yace"Mummy ba laifina bane bafa..wai kunya takeji bazata iya zuwa ba"..girgiza Kai Mummy tayi tace"to zan kirata da kaina in fada mata"..mikewa yayi ya zuba hannunshi cikin aljihu yace"zan dan fita Mummy"..Mummy tace"to a dawo lafia"..aunty sumy dake ta sauraronsu tun daxun tace"duk wnn wankan nata ne knn?.."dan 6ata rai yayi yana kallonta yace"ke waya fada maki haka?..ni ba wurinta zanje ba"..aunty sumy ta dago tana kallonshi da murmushi tace"ai ba zama zanyi har sai kazo kace aunty na tafi wajen Lamido snn zan gane wajenta zakaje ba"..zuyawa tayi tana duban Mummy tace"dan Allah Mummy baki lura duk yasa manyan kaya wajenta yake zuwa ba?.."dagowa Mummy tayi tana murmushi tace"nima dai na lura Sumayya..ni bansan yaushe ma ya fara sa manyan kaya ba shida kullum cikin suits yake kaman ba bahaushe ba"..Mummy na rufe baki Bobby daketa faman smiling ya dan kwabe face dinshi yace"Mummy ni ba bahaushe bane mana..am Igbo"..hararanshi Mummy tayi tace"for where?..kai bafulatani ne"..aunty sumy tace"rabu dashi Mummy..kaje ka fadawa Aysha haka kaga idan bata fasa aurenka ba"..murmushi yake yana girgiza kai yace"nasan maganinki ai..babansu Miemie kawai zan kira ince ya dawo daga England ya daukeki ku koma gidanku tunda takura mana kikeyi"..daria kawai tasa tacigaba da aikin gabanta jin ya ambaci baban su Miemie..Mummy ma bata sake mgn ba shi Kuma yayi musu sallama ya fita yanata smiling..da mgn daya yayi maganinsu...yana fita ya nufi motarshi da yasha car wash sai kyalle yake ya bude driver seat ya shiga tareda tayar da ita ya fita daga gidan..these driver dinshi ba karamin hutawa yake ba sbd almost everyday shi yake driving kanshi yanxu especially idan yasan wajenta zaije..shifa gani yake ana daura musu aure ma driver office kadai zan dinga kaishi amma duk wani personal al'amuranshi da kanshi zai dinga zuwa yanayi ko don sbd matarshi..shi bazai iya bari driver ya tuka mashi mata ba har ga Allah..kawai gani yake zaiyita kallonta ne ta mirror shi kuma da wani namiji ya kalleta gwara shi a kwana ana kallonshi bai damu ba...driving yake yana murmushi gami da shafa Kai sbd tunowa da ita da yayi..har kullum sonta karuwa yake a cikin ranshi musamman yanxu da yake receiving equal treatment daga wurinta..daxun rigima sukayi sosai sbd tayi mgn a sauko musu da biki tace bazata iya ba shine yayi zucia har ya baro school din bai nemeta ba yasan tana can ta cika fal tana jiran yaje ta sauke mashi...har ya isa college dinsu bai bar tunawa da ita yana murmushi ba..daidai gate dinsu yayi parking snn ya dauki waya yayi dialing numberta don ko sanar da ita zaizo baiyi ba..tana dauka ko jira tayi mgn baiyi ba yace"baby am outside"..ta wani hade rai ita bata yadda ba ya 6ata mata rai tace"ni banida lafia"..murmushi yakeyi yace"eyya meya sameki?.."a shagwabe tace"fever"..yace"alright let me come inside in dubaki"..tun kafin ya rufe baki tace mishi"nidai No..salon ka shigo duk suyita kallonka"..yace"then indai bakiso in shigo ki fito..na baki 3 mins idan ban ganki ba am coming inside"..daga haka ya kashe wayar yana cigaba da murmushin wnn rigiman nata...suna gama wayar ta juya tana kallon Billy dake kunshe daria tace"munafuka"..daria Billy ta fashe dashi harda su tafa hannaye tace"munafurcin me Kuma nayi Lamido?.."harara ta watsa mata tareda mikewa zuwa wardrobe dinsu ta dauko zumbulelen hijab ta dora kan jean da Jessy dake jikinta as always snn ta fita daga dakin bayan ta Maka ma Billy harara..ita dai da kallo ta bita tana cigaba da murmushi tace"wai Ina matsayin matar yayanta takemun wnn iskancin..Lamido Allah ya shiryeki". Tana fita Kai tsaye inda ta hango motarshi ta nufa..shi Kuma yana zaune ciki yana kare mata kallo don wurin akwai haske dal kmr ba dare ba..hijabinta yakai qasa amma Saida ya fahimci jean da riga ne a jikinta sbd fitowa da wandon yayi ta kasa..lumshe Ido yayi ya bude tareda jingina kanshi da kujera yana cigaba da kallonta har ta iso inda yake..ta bude motar ta shigo snn ta maidashi ta rufe tanata wani ciccin magani ta juya tana kallonshi..murmushi ya Kara saki tareda kama both hands dinta ya rike yana kallon eyeballs dinta yace"menene?."turo baki tayi tace"Pogba"..idanu ya ware da kyau a kanta cikin mamaki yace"Pogba Kuma?.."Kai ta daga mishi akamar eh nan take kuma ranshi yaji ya 6aci..shi duk tunaninshi sbd ya wuce bai nemeta bane daxun take fushi ashe abun nata ne ya motsa bai saniba..sake hannunta dake cikin nashi yayi snn ya sake dubanta cikin kokarin 6oye 6acin ranshi yace"what about him?.."a dan fusace tace"wai mutumin nan mu zai wani tozarta ya bar Manchester United..kasan yanxu wai Juventus..."bata samu sararin karasawa ba sbd wani kallo da ya shiga binta dashi ita sai yanxu ma ta tuna ashe fa tayi kato6ara..innalillahi wainna ilaihi rajiun ta fada cikin ranta.."wane ruwa na kuntowa kaina ni Aisha?.."ta fada a hankali yayinda take kallon yanda yanayinshi ya sauya lokaci daya..dunia idan akwai abunda ya tsana bai wuce wnn Pogban ba..ya tsaneshi to the extent that yakejin duk wani dan Manchester da Yan ball din ma kaf ya tsanesu..dukda cewa shi Pogban musulmi ne amma da gaske tsanarshi yakeji sbd wnn son da yaga tana mashi.. marairaicewa tayi sosai kmr wadda ke dab da fashewa da kuka tace"partner am sor"..bata karasa ba ya dora finger dinshi kan lips dinta yana kallon cikin Idonta yace"u don't have to apologize"..girgiza kai ta shigayi tana kallon 6acin rai Karara kan fuskanshi tace"nidan am sorry plss..wlh mancewa nayi"..baice mata kala ba ya dauke finger dinshi daga bakinta tareda komawa yayi relaxing kan seat din da yake..hankalinta taji ya tashi sosai tasan duk yayi irin wnn fushin da ita to abu ba karamin 6ata ranshi yayi ba..shaf mancewa tayi da wnn kishin nashi wlh da bata ma fara ambaton Pogba a gabanshi ba sbd yanda ya tsaneshi..matsawa tayi jikinshi sosai tareda Kai hannu ta kama left hand dinshi murya can kasa tace"partner"..banza yayi mata baice komai ba..ta sake cewa"partner talk to me manaa..nace am sorry fa"..still baiyi mgn ba sai ma hannunshi daya zare daga cikin nata ya shiga kokarin bude motar zai sauka kawai yaji ta rungumoshi ta baya tana cewa"partner am so very sorry plss..am sorry I hurt u amma ba da gangan nayi haka ba kasan I love u"..lumshe Ido Bobby yayi yanajin heart beat dinshi na sauyawa lokaci guda..kawai sai yaji wasu irin abubuwa sun shiga zagayawa cikin jini da tsokar jikinshi baisan lokacida ya sauke wani gauron numfashi ba..yana jinta a jikinshi yaji duk 6acin ran nashi yayi disappearing sai Kuma wani shauki daya tsinci kanshi a ciki na musamman...tunda yake da ita bata ta6a hugging dinshi haka ba sai yau..this very moment..wani additional sonta yaji yana sake ciko zuciarshi kawai sai ya juya tareda dagota daga jikinshi yayi cupping fuskanta yace"Love why plss..why do u always wants to talk about him..why do u love him this much?.."hannu takai itama tayi cupping nashi face din tana girgiza mashi Kai tace"I do not love him..I love u..only u baby..I love u more than any other person in this whole wide world..u are my soul partner,my future husband,my babies daddy and I love u so much"..sbd tsabar jin dadin kalamanta baisan lokacida ya sake maidata jikinshi yana sauke ajiyar zucia da mugun karfin gaske ba..wani irin sanyin dadi yaji yana ratsa zuciarshi tamkar an sauke mashi mountain daga ciki..these words means the entire world to him..it means a lot to him and he wouldn't mind tacigaba da fada mashi irinsu daga nan har mahdi ya bayyana..kawai baiso ta dena fada ba..sai yaji kaman su dawwama nan wurin tana fada mashi the most sweetest words daya taba saurara all his life..rumgumeta yayi sosai sai sauke numfashi yake kafin ya dagota a hankali yakai lips dinshi ya manna mata peck a forehead dinta yana kallonta wearing a very wide smile kan fuskanshi yace"I love u more baby..I love u like..."kasa karasawa yayi sbd gani yake babu wata kalma da zatayi daidai da son da yakejin yanayi mata a mizani saidai in zuciyarshi zai bude mata ta shiga ta gani kawai idan ba hakaba duk yanda zaiyi bayani bazata ta6a ganewa ba..hade fuskanshi yayi da nata idanunshi rufe yace"I beg u in the..."bata bari ya karasa ba itama ta dora two fingers dinta akan lips dinshi tana kallonshi tace"I promise not to talk about him ever again..am sorry"..sake rungumeta yayi yana sauke ajiyar zucia..bayan few minutes ya rabata da jikinshi yanata doka murmushi ya kalleta kafin yayi mgn tace"I love u"..ya lumshe Ido ya bude shima yace"I love u more baby..and ba na hanaki fitowa da wando ba?.."kallonshi tayi ta kalli jikinta tanaso taga ta Ina ya gane wando ne a jikinta amma bata ganiba don hijabinta ya rufe har kasa ne.. dan marairaicewa tayi tana dubanshi tace"partner naga ba wani wajen zanje ba ai..wajenka zanzo"..yace"ko wurina ban yadda kina zuwa anyhow ba manaa.. don't u know u have this beauty and figure da bai kamata kina fita da anyhow dressing ba?.."langa6e Kai tayi a hankali tace"to kayi hakuri na dena"..sake pecking goshinta yayi tareda komawa seat dinshi ya zauna yana cigaba da kallonta with a smile yace"thank u so much love..I love u"..murmushin takeyi itama kafin tace"I love u more"..girgiza kai yayi yana kallonta yace"no I love u more"..itama ta makale shoulder dinta tace"nima I love u more"..murmushi kadai Bobby keyi ya kasa dena kallonta..itama kallonshi takeyi this time around ba tareda wani tsoro ko fargaba ba..bayan almost 10 mins of silence and starring yace mata"Mummy nata damuna fa in kaiki wajenta..yaushe zaki shirya muje?.."dan karya wuta tayi tana dubanshi har yanxu tace"partner kunyanta nakeji nidai"..yace"then kiyi mgn da Billy kuje tare amma da gaske Mummy tace she wants to see u..kilan akwai abunda takeso kuyi discussing da ita"..gyada mishi kai tayi a hankali alamar ta amince. Sorry for the late update pls..kunsan sallah ya kusa so ina can ina kujiba kujiba😅 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 51 Washegari da around 4 ya gama shiri tsaf don zuwa daukosu kamar yanda sukayi da ita jiya..tun daxun yake tsaye gaban mirror sai faman kalkale yakeyi kamar mace..wayanshi ne ya shiga ringing yana dubawa yaga Rayhan kan screen dan haka ya saki tsaki tareda ignoring call din har ya gama ringinshi dinshi bai dauka ba..wani kiran ya sake shigowa still bai dauka ba yana gama ringing ya dauki wayan da nufin sawa a silent sai kuma kiran Nur ya shigo..fasa sawa silent din yayi tareda answering call din yana cewa"what?.."daga daya 6angaren Nur yace"dole kace haka mana dan rainin hankali kaman ba kaine Lamido tayita ladabtar mana da kai ba"..tsaki Bobby ya saki yana ta6e baki yace"is this why u called?.."da sauri Nur yace"no plss..ina cikin matsala ne wlh almos similar to wanda ka shiga a kwanakin baya and i need ur help"..ajiye comb dake hannunshi yayi tareda daukan keys dinshi ya fita daga dakin kafin yace"then ka bari idan hadu gobe sai muyi mgn amma ba a waya ba"..yana rufe baki Nur yace"no plss nidai kayi alqawari zaka taimakamin"..dan girgiza kai yayi yana mamakin wnn sudden behavior na abokinshi yace"wai kayi gamo ne hala?..wane irin alqawari zan daukan maka kuma?.."Nur yace"alqawari dai kmr yanda kaji na fada"..gyada kai yayi yace"then nayi alqawari shknn?.."Nur yace"shknn sai munyi mgn tomorrow"..yace"ohk"..snn ya kashe wayar yana girgiza kai..wani lokacin Nur sai yayita behaving kaman wani karamin yaro wlh..kai tsaye yana fita parlon Mummy ya shiga yayi sallama da ita snn ya fita don zuwa dauko su Aysha daga hostel..yana hanya ya kira ya sanar da ita tahowarshi don haka kafin ya karasa sun gama shiryawa tsaf shi kawai suke jira..bayan ya isa ya sske kira ya sanar mata ya iso basu 6ata lokaci ba suka fito tareda Billy..relaxing yayi nan cikin mota yana kare mata kallo as usual duk yazo wurinta dama kafin ta isa gareshi sai ya gama kalleta tsaf shiyasa ko hijab tasa yake iya gane abunda take sanye dashi ta ciki..doguwar riga ne a jikinsu iri daya saidai color daya banbanta amma daidai da hulunan dake kansu iri daya ne likewise takalmansu..ya fuskanci qawance ne tsakaninsu na gaske bana wasa ba and suna son juna tsakani da Allah ba wani mai zucia biyu a cikinsu..kafin su karaso as usual ya bude mata front seat suna karasowa ta shiga Billy kuma ta shiga backe seat bayan sun rufe kofa ya sake tada mota suka bar cikin hostel din...suna daukan haya ta juya tana kallonshi da wani smile daya kusa sashi zubar dasu a titi sbd tsabar rikitashi da yayi tace"partner kayi kyau"..kallonta ya danyi sai kuma ya saki murmushi yana cigaba da driving dinshi ita baima san yanda zai bayyana irin kyawun da tayi mashi bane..kawai shidai baison tana yin shiga irin haka tace zataje wani wurin amma bazai iya hanata ba yau tunda anko yaga sunyi ita da Billy amma ko Allah yasan shidai baso yakeyi ba..sam baison tana fita babu hijab sbd yanda yake ganin kmr idanun kowa kanta zasu dawo don a ganinshi babu namijin da zai kalleta baiji ta birgeshi ba ko don kyawun fuskarta ko kuma surar jikinta...dan turo baki tayi tana kallonshi tace"bazaka ce nima nayi kyau ba koh?.."juyawa yayi ya kalleta for like 2 secs kafin ya sake maida hankalinshi ga driving da yakeyi yace"kinyi more than kyau"..harara ta dan watsa mashi alaman bata gamsu da abunda ya fada kuma har yanxu bata bar turo mishi baki ba..Billy dake sauraronsu tana murmushi tace"sir ina yini"..kallonta ya danyi ta mirror kafin yace"lafia lau Bilkisu meyasa bakiyi mata fada ne?.."Billy tace"Allah inayi mata sir kawai dai halin nata ne sai ita..batajin mgn wlh"..tana rufe baki Aysha ta juya tana kallonta tace"kiji tsoron Allah wlh..haka kikaje kika hadani da Ammi ma kikasa taitamun fada ba tareda laifin komai ba"..murmushi kawai Billy tayi batace mata komai ba shima murmushin yayi hade da girgiza kai ba tareda cewa wani abu ba..ganin yanda suka maidata kamar wata yar iska tayi mgn sunyi banza da ita sai taja bakinta ta tsuke itama tana harare harare ita a dole anyi mata ba daidai ba..har suka isa gida ba wanda ya sake mgn cikinsu..ciki ya shiga yayi parking kmr ko yaushe snn Billy ta fara budewa ta fita don ta basu space..itama tana kokarin budewa ta fita ya kama hannunta da sauri yana langabar mata da kanshi yace"bana hanaki fitowa a haka ba?.."langabar da nata kan tayi itama kafin tace"kaga anko fa mukayi da Billy ai babu dadi ince mata bazan sa ba"..janyota yayi jikinshi sosai yana kallon eyeballs dinta yace"sai kice mata na hanaki fita a haka ai zata fahimta amma kin kama kin fito a haka yanxu Allah kadai yasan adadin mazan da zasu kalleki kafin mu koma"..kallonshi take a hankali tace"partner kaima fa dan bakaga kyau da kayi bane nima sai ince mata zasuna kallonka mana"..hannunta ya kama ya dora saitin heart dinshi yace"ko sun kalleni it won’t change a thing sbd my heart beats for only u and u alone..i don’t think har dunia ta tashi zan samu macen da zan sota kmr yanda nake sonki..ina sonki sosai nefa..try and understand mana"..kallonshi kawai Aysha keyi tana sakin murmushi cikin ranta kuma tana godia wa Allah daya bata shi a matsayin miji..dukda basu riga sunyi aure ba tana da tabbacin za’a jima ba’a samu macen da tayi dacen miji dake sonta irin yanda yake sonta ba..soyayyanshi is genuine wanda ta tabbata yafi wanda ita take mashi nesa ba kusa ba...ganin kallon da take mishi tana smiling ya dan hura mata iska a ido yana kallonta yace"what are y thinking about?.."a hankali tayi pointing nashi da finger dinta tace"you"..kallonta yayi kafin ya samu damar cewa wani abu yaji saukan warm lips dinta akan forehead dinshi ta manna mishi kiss that last for almost 3 mins kafin ta janye bakin a hankali tareda bude motar ta fita tana sake kasheshi da wnn smile din nata...Bobby mutuwan zaune yayi a wurin yana bin bayanta da kallo har suka shiga cikin gidan itada Billy..lokaci guda moo dinshi ya sauya gaba daya sai kace wanda yasha wani abun...wnn kiss da tayi mashi ba karamin hargitsa mashi lissafi yayi ba..jikinshi ya mutu murus wanda hatta numfashi da kyar yake shaqansa..lumshe ido yayi tareda komawa yayi relaxing kan kujera yana sauke ajiyar zucia..wani irin yanayi yakeji tattare dashi wanda yafi duk wanda yasan yanaji a baya..jikinshi yayi sanyi qalau da har ya kasa daga legs dinshi balle ya samu ya fita daga motar..haka yake fama da wnn desire din these days ko kallonta ya fiye yi saiya samu matsala ballantana kuma yanxu da tayi mashi abunda bata ta6a yi mashi ba tunda suke tare..kawai addu’a yake Allah yasa bata ta6a yiwa wani namiji haka ba don a yanda yakeji tsaf zai iya kauce hanya sbd yanda dan abu karami daga gareta yake kai mishi karo..effect sosai wadan nan abubuwan suke dashi a kanshi wanda ya zama mishi dole yayi baya baya da ita don gudun kada azo ana samun matsala..saida ya gama tattara sauran energy dinshi kaf snn ya bude motar ya fita yana takawa a hankali ya nufi cikin gidan..a central parlor suke zaune da Mummy da friend dinta maman Rayhan sai kuma Rayhan din dake zaune gefen Mom dinta tana karema su Aysha dake gaisawa da Mummy kallo...karasowa cikin parlon yayi a hankali bayan ya daure fuska ya shiga gaida Mom din Rayhan kafin itama Rayhan din ta mike da sauri tana kallonshi da wani murmushi tace"Uncle Bobby sannu da zuwa..tun daxun nake jiranka"..kai kawai ta iya gyada mata yana satar kallon Aysha da ko ba’a fada ba yasan kallonsu take..Mom dinta na murmushi itama tace"tun tuni take damuna da mgnrka Bobby kusan kullum haka zamu yini tana kiran Uncle Bobby shiyasa yau dai nace bari mu samu muzo dan ni kaina rabona da mahaifiyarka tun bikin Zahraddeen"..murmushin yake ya iya saki yana gyada kai duk yabi ya diririce sbd presence na Aysha a wurin..Mummy ma ba karamin kunya maganganunsu suka bata ba gashi ta rasa yanda zatayi tayi stopping nasu don haka da sauri tace"to ka wuce ciki idan mun gama gaisawa sai ka maidasu"..kmr abunda yake jira knn ya kama hanyar flat dinshi da sauri..Itama Rayhan da saurin ta mike tabi bayanshi tana cewa"Mommy bari inyi mgn dashi plss"..daga haka itama ta shiga flat din nashi..Mummy ta juya a hankali tana kallon Aysha data kasa jurewa ta shiga binsu da kallo har suka shiga flat din nashi kawai saiji tayi hawaye sun ciko idanunta..wnn kuma wace irin masifa ce?..da sauri tayi kasa da kanta tana kokarin maida hawayen da suka ciko mata ido amma Mummy ta riga ta gani and hakan kuma ya bala’in tada mata hankali..kada fa yaran nan suzo suna samun matsala ta dalilin wnn abun..mikewa tayi da nufin binsu flat din nashi sai ga Miemie da aunty sumy sun shigo parlon tareda ilham da alama unguwa sukaje...Miemie na ganinsu ta karasa kusa dasu da fara’arta tana gaishesu haka ma ilham da hugging Aysha saida tayi sbd farin cikin ganinta..ganin haka Mummy ta dubi aunty sumy dake gaisawa da Mom din Rayhan tace"wuce dasu parlonki su samu su huta kafin na shigo"..ba musu aunty sumy ta kwashesu zuwa flat dinta tareda su Miemie da suketa murna kamar basu ta6a ganinta ba..Billy dai sai kallonsu takeyi tana sake yabawa da kirki irin nasu..ta tabbata Lamido ba karamin dacen samunsu matsayin dangin miji tayi ba basuda matsala ko kadan..Lamido kuwa ji take kaman ana hura mata wuta a cikin jikinta sbd tsabar zafin da taji ya rufeta..ita bataso suka bar parlon ba so tayi su zauna taga iya tsahon lokacin da zasu dauka a dakin nashi basu fito ba..har wani jiri taji kaman zai dauketa sbd tashin hankali..bata ta6a sanin haka takeda kishi ba sai this very moment..kawai ayyanosu takeyi wai suna can suna abunda bai kamata ba kilan ma har kissing juna zasuyi and iya tunanin haka kadai yasa ta kware da yawun bakinta nan take kuma tari ya sarketa kmr zata shide..Miemie daketa faman zuba ma Billy surutu hankalinsu yayi kanta gaba daya suka shiga kokarin taimaka mata..aunty sumy ta dauko ruwa da sauri ta kawo musu Billy ta amsa ruwan ta bata a baki tasha sai kuma tarin ya sake karuwa sbd another kwarewa da tayi da ruwan data sha din..nan take hawaye suka shiga kwararowa fuskanta wanda ko kusa bana kwarewa da tayi bane kawai na ciwon ganin wata mayya tareda namijin da duk dunia batada kamarsa a yanxun idan aka dauke iyayenta...yayi mata ciwo sosai yanda yarinyar ta iya binshi har flat dinshi kuma bai koreta ba..da sauri aunty sumy ta dauko waya ta shiga dialing number dinshi sbd batason dagawa Mummy hankali tunda tana tareda bakuwa..kamar jiran kiran nata yakeyi yana dagawa tace mishi"come to my parlor plss..ur Aysha bansan meya sameta ba"..ai tun bata kai karshe ba ya katse wayar tareda fitowa zuwa flat din nata da sauri..tana shiga yayi toxali da yanda take shaqan numfashi da kyar baisan lokacinda ya karasa tareda zaunawa nan kusa da ita ba..yakai hannu yana kakarin janyota jikinshi da karfi tace"don’t..touch..me"..tsayawa kawai yayi yana kallonta kmr bai gane me tace ba..hannu ya sake kaiwa zai zare nata hannun data rufe hanci da bakinta dashi still ta sake cewa"i said don’t touch me"..kama hannun nata yayi ya janyeshi daga fuskar ita kuma ta daddage ta make hannun nashi tana wani sauke numfashi tana muzurai tarin kuma sai ya tsaya cak kmr dama dai zuwanshi yaje jira..kallonta ya shiga da puppy eyes dinshi ita kuma ta dauke kai tana kokarin maida hawayen da suke sake ciko mata idon..kawai gani take kilan ya dade yana raina mata hankali akan yarinyar...aunty sumy da batasan dawar garin ba sakin baki tayi tana kallonsu da mamaki haka ma su Miemie..kallonta yayi yana marairaicewa yace"aunty kice tayi hakuri plss"..yana rufe baki itama tace"aunty baimin laifin komai ba"..galala aunty sumy ta tsaya tana kallonsu da sabon mamaki..Bobby ya kori su Miemie da yaga sun wani tsaresu da ido kafin ya sake maida dubanshi ga aunty sumy da ido ya shiga yi mata alamar ta rokar mishi ita aunty sumy kawai tasa daria..daria suka bata daga shi har Ayshan wlh..idan akace kuruciya na damun mutum dai sai a hankali wlh..juyawa tayi da nufin ta basu wuri suyi rigimarsu su gama Mummy ta shigo parlon hankalinta gaba daya kan Aysha tace"daughter meya sameki?.."dan murmushi ta kakalo kai a kasa ta girgiza kai alamar ba komai..Mummy tayi shiru tana kallonta kafin tace"to ku taso mu koma parlor tuna baqin sun tafi"..mikewa sukayi ba musu suka sake komawa wancan parlon..shidai Bobby har yanxu hankalinshi bai bar kanta ba...bayan sun zauna Mummy ta danyi kasa da muryanta tace"kiyi hakuri da abunda ya faru kinji?..ba abunda kike tunani bane"..kai kawai ta iya gyadawa Mummy amma Allah kadai yasan me takeji..Allah Allah take kawai su tafi yanda zata samu wankeshi tas da soso da sabulu..nasiha sosai Mummy ta shiga yi musu wanda duk akan abunda ya faru ne tana sake assuring dinta cewar ba komai ba wani abu ne tsakaninta da Bobby ba amma kishi ya rufe mata ido kwata kwata bata yadda ba kawai gani take itama Mummyn yana raina mata hankali ne kmr yanda itama ya raina mata kilan yana soyayya da ita a bayan idanunsu..idan ba haka ba why zai bata such freedom?..why zata samu damar binshi har flat dinshi kuma ba tareda wani shakku ko tsoro ba idan har ba soyayya suke ba?..a takaice sun 6ata lokaci sosai Mummy nata faman musu nasiha ko dalilin da yasa tace tana son ganin nata ma bata fada mata ba..shidai Bobby yana zaune yana kallonta yasan duk wnn 6a6atun da Mummy take da kyar idan tanaji don a yanda yake ganin fuskanta kadai ya isa yasa yasan yau fa mai rabata dashi sai Allah...bayan ta gama musu nasihan da suka zo tafia har ita akayi musu rakiya bakin mota su A’i sai yake ake ana washe hakora irin komai normal din nan nan kuwa basu san ta ciki na ciki ba..ta bude front seat ta shiga Billy ta shiga back seat kafin shima ya shiga ya tada motar su tafi gabanshi har wani faduwa yake sbd tunanin yanda zaiyi ya fitar da kanshi daga wnn gundumemen zargi...har suka isa hostel babu Wanda yayi mgn cikinsu..ita Billy tana zaune back seat tana danna waya yayinda Lamido da Bobby ake kallon kallo a tsakanin juna shi yana tunanin yanda zasu kwashe da ita yanda yaga tana hade rai ita Kuma tana tunanin Kalan rashin mutuncin da zata mashi sbd raina mata hankali da yayi...yana gama parking a gate din hostel Billy ta bude motar ta fita bayan tayi sallama dashi ta shiga cikin hostel din shi Kuma ya juya a hankali yana kallon Aysha data shiga kici kicin bude motar zata fita amma yasa lock don haka ta kasa budewa..matsowa yayi yana dubanta a hankali yace"baby listen to me plss..I will explain"..tun bai rufe baki ba ta kama masa wani kallo Idonta har ya ciko da hawaye tace"ka cuceni"..juyawa tayi zata fita yayi saurin janyota ya sakata jikinshi murya can kasa yake ce mata"am sorry..am so sorry ki bari inyi maki bayani plss"tureshi ta shigayi tana dukan chest dinshi da duk karfin da Allah ya hore mata ta kasa cewa komai..ganin ba sakinta zaiyi ba kawai ta sake kankameshi tana fashewa da matsanancin kuka..kishi takeji sosai na wnn shegiyar inyamurar yarinyar..bata ta6a sanin kishi bala'i bane sai yanxu..knn shima haka yayita ji duk lokacinda yake ganinta tareda wani?..idan haka ne ma yayi kokari sosai dan ko Allah ya San ita bai zama lallai ta iya irin wancan hakuri da yayi da ita a baya ba..wani irin zafi takeji tamkar an dau zuciarta ansa shi cikin frying pan ana soya mata shi...Bobby dai banda shafa bayanta ba abunda yakeyi..bashi yake kukan ba amma zai iya rantsuwa yana jin sautin kukan da zuciarshi takeyi sbd nata kukan da takeyi..hankalinshi tashi yakeyi sosai..yasan yanda mutum keji idan irin wnn kishin ya motsa and ko kadan baya mata fatan sake experiencing wnn feeling din sbd yasan exactly how it feels..ba fatanshi ta dena kuka kadai ba fatanshi kada Allah ya sake kawo dalilinda zai tada kishinta haka sbd ciwo yakeji idan yana ganinta a irin wnn halin..he loves her to the extent that duk wani abu da zai daga mata hankali baya son yazo kusada ita..gashi dai yanxu ita take kukanta amma yanda yakeji yasan ko ita dake kukan bazata kaishi shiga damuwa ba...dagota yayi a hankali yana share mata hawaye gami da girgiza kai shima kmr zaisa mata kukan yace"stop crying plss..nace maki ba wani abu nefa tsakanina da ita ba"..ture hannunshi tana sauke ajiyar zucia sbd kukan da taci ta sake juyawa zata bude motar yayi saurin dawo da ita yana kallon tsakiyar idanunta a hankali yace"please!..please I beg u"..lumshe Idonta tayi tana goge hawayenta shi Kuma ya matsa jikinta sosai har suna shaqan numfashi juna yace mata"when i say u i mean u baby..only u..duk dunia idan kina tunanin akwai wata mace cikin rayuwata apart from u then u are mistaken..I love only u and u alone..you are the best of all the precious things that have ever happened to me..you owns my heart completely and I love u so much..please allow me to explain things to u"..tunda ya fara mgn kawai ta lumshe Ido tana sauraran yanda yake pouring mata love words din nan ya kamata taji dadi amma Sam kishin dake cinta ya hana mata jin dadin kalaman nashi..kawai imagining take dama sun dade tana shiga flat dinshi kilan har ganinshi ta ta6ayi babu kaya ajikinshi..tunanin haka yasa ta sake kwa6e fuska hade da tale baki zata fara kuka kawai taji saukan warm and cute lips dinshi akan bakinta..ta kwalo idanuwa waje da sauri tana rarraba su kmr dai shege a rabon gado..lokaci daya ta hadiye kukan nata tsaf ta zuba ma face dinshi Ido yanda ya lumshe nashi idon yayi holding dinta da two hands dinshi makes him loos so cute a Idonta..lumshe idon ta sakeyi tanajin yanda ya kasa raba lips dinshi da nata ga heart dinshi dake bugawa very fast kawai saita daddage iya karfinta ta janye bakinta daga nashi tana sauke numfashi...bata sake yadda ko kallon inda yake tayi ba ta bude motar ta fita da sauri har tana hadawa da gudu...Bobby ya dafe head dinshi tareda hada Kai da starring yana sauke numfashi da sauri kmr Wanda yayi tsere..lokaci daya regretting abunda ya aikata ya shigeshi..baisan yanda akayi har hakan ya faru ba kawai shidai yaji bakinshi cikin nata anda daga nan Kuma bai sake tantance komai ba sai abunda yakeyi...shknn yanxu kilan kallon dan iska zata fara mishi amma ba laifinshi bane..Allah ya gani he tried his best abun ne yafi karfin tunaninshi..shi da yake kokari bata hakuri ya sake aikata wani laifin da kilan sai yasha wahala kafin ya damu kanta again...lumshe Idonshi yayi yana furta"innalillahi wainna ilaihi rajiun"a hankali..gaba daya yama kasa tashi balle ya tayar da motar ya tafi..driver dinshi ya kira da kyar yayi mashi bayanin inda yake yace yazo yayi picking dinshi..babu wasting of time yazo wurin Bobby ya bashi keys tareda komawa back seat shi Kuma driver ya tashi motar suka tafi bayan yace gida yskeso ya kaishi. To habibties ina ganin zamu dakata a nan sai Allah ya kaimu bayan sallah. Ina ma kowa barka da sallah in advance Allah ya maimaita mana..Allah kuma yasa muyi azumin arfah lafia mu gama lafia.❤️💫 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan diya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 52 Driver na gama parking a gida ya bude motar ya fita yana takawa a hankali zuwa cikin gidan..bai ko lura da Mummy da aunty sumy dake parlor ba yayi wucewarshi flat dinshi..yana shiga ya fada kan gado ba tareda ko takalman kafanshi ya cire ba..haushin kanshi yakeji sosai na abun da yayi..Sam bai kamata yayi hakan ba yanxun gashi baisan ta Ina ya kamata ya fara bata hakuri ba...yana cikin wnn tunani kiran Nur ya shigo wayanshi..ya dauka tareda sashi a speaker ya ajiye daidai face dinshi kafin yace"what?.."tsaki Nur yaja before yace"kaidai kanada matsala wlh banza..are u at home?.."Kai ya gyada tareda cewa"yes"..katse wayar Nur yayi ba tareda yace komai ba shi Kuma ya sake gyara kwanciya tana tunanin abunyi..yasan da kyar idan Nur ba zuwa zaiyi ba tunda ya tambayi ko yana gida amma yasan idan ya fada masa abunda ya faru shknn ya shiga uku da walakancinsa dan tsona ne zaisha a wajenshi tunda yasan halin kayanshi. Lokacinda Nur ya shigo dakin ya fito daga wanka knn ya shiga closet zai canxa kaya..yana jinshi baice mishi kala ba har ya gama shiryawa ya fito..Nur ya juya yana kallonshi da wani murmushi yace"na Lamido bada kanka a sare idan kaje gida kacewa Mummy ya Fadi"..murmushi Bobby ya saki tareda zama nan kusa dashi yana dubanshi yace"bansan a inda kaji Hausa ba Nur.. duk wani mgn na hausawa ka iya sai kace dai ba inyamuri bane Kai"..daria shima Nur din ya saki yana shafa Kai yace"sai kace dai ba inyamurai bane mu..kaima ba kace kai ba bahaushe bane?.."harara Bobby ya watsa mashi yace"to yanxu nace bahaushe ne ni.. bafulatani ma kuwa"..tun kafin ya rufe baki Nur ya kwashe da daria kmr ta6a66e.. Bobby na jinshi bai kulashi ba Saida ya gaji don kanshi ya bari snn ya sake dubanshi yana cewa"wai Dr Bobby ne yau yake kiran kanshi bafulatani..wonders shall never end"..banza Bobby ya sake yi dashi yanata danna wayarshi..Saida Nur ya gaji da iskancinshi don kanshi snn ya dan rage murya yace"sorry abokina wasa nake Maka"..shidai baice dashi komai ba..shi Kuma Nur dan nustuwa yayi tareda maida hankali gareshi yace"wata yarinya ce nake tsananin sonta wlh Kuma na kasa fada mata"..kallonshi Bobby ya danyi for like 3 secs kafin ya maida duba ga wayarshi dake hannunshi yace"Ina jinka"..dan shiru Nur yayi kmr bazai ce komai ba sai can yace"Bobby pretty nakeso"..dagowa Bobby yayi da sauri yana dubanshi cikeda mamaki sosai yace"are u even listening to ur self?..kaji abunda kace kuwa?.."Nur yace"na sani mana..ce Maka nayi Ina son pretty and I want to marry her"..girgiza Kai Bobby ya shigayi har yanxun yana binshi da kallo irin na mamaki yace"yanxun of all mata dake garin nan ka rasa wadda zakace kanaso sai Miemie da ko secondary school bata gama ba?.."dan daure fuska Nur yayi yace"kasan I don't tell my heart whom to love..kawai idan bazaka taimakamin ba its ok ba sai ka biyo ta wnn hanyan ba"..murmushi Bobby ya saki ya sake duban Nur da mamaki yace"ikon Allah..when did i say that?.."Nur yace"gashi nan ka fara cewa bata gama secondary school ba..ai ba cewa nayi zan fada mata Ina sonta tun yanxu ba..I just want u to know sbd kada a samu matsala nan gaba amma its ok".. daria sosai Bobby ya fashe dashi Wanda rabon da yayi irinshi har ya manta...he can't believe Nur da gaske yake..yanxu of all yammatan Kano ya rasa warce zaiso sai yar karamar yarinyar da batafi 17 years ba..abun ba karamin daria bane..shi Kuma Nur ya cika yayi fal kiris yake jira ya fashe ganin sbd rainin hankali daria ma yake mashi...Saida ya gaji da daria dan kanshi snn ya dan dakata ya kama hannun Nur kafin yace wani abu Nur ya fizge hannunshi yana zabga mashi harara..daria Bobby ya sake yi kafin yace"C'mon sorry mana abokina..sorry sirikin aunty sumy"..yana gama fadan haka ya sake kwashewa da daria..Nur dai na zaune yana kallon tsabar walakanci kawai sai ya mike ya kama hanyar fita daga dakin Bobby yayi saurin mikewa ya isa inda yake suka fita dakin a tare yana cigaba da murmushi yace"to ka tsaya mu karasa mgn mana"..girgiza Kai Nur yayi ba tareda ya tsaya da tafiyar da yakeyi ba yace"don't bother"..kama hannunshi Bobby yayi ya dawo dashi cikin parlor suka zauna snn ya dan daidaita dariar da yakeyi yace"to yanxu ya kakeso ayi?.."marairaicewa Nur yayi yana dubanshi yace"kawai nidai kayimin kokari akan mgnr..ba sai ka fadama kowa Ina sonta ba amma daga nan zuwa ta gama secondary school kada a bari ta kula kowa dan Allah sbd banaso wani yazo ya rigani"..murmushi Bobby keyi yana gyada kai yace"baka da matsala da wnn..dama bata kula kowa and bazata fara ba har ta kammala secondary school din"..ajiyar zucia Nur ya sauke tareda fadin"thank u..wnn year din zata gama Koh?.."Bobby yace"mene?.."Nur yace"secondary school din mana?.."murmushi ya Kara saki yace"yeah this year zata gama"..Nur ya sake cewa"ohk Allah ya kaimu..and thanks for ur understanding"..murmushi kawai Bobby keyi yana shafa kanshi..har yanxun mamakin abun yakeyi ne..saidai Kuma ba abun mamaki bane idan akayi duba da how love is..kwata kwata baisan wani dacewa ko cancanta ba..snn Kuma baya duba kan abunda ke iya zuwa ya dawo duk kan wanda yaga dama kawai fadawa yake..yasan Nur husband material ne sosai and tunda har ya furta yana son to lallai fa gaske son nata yake..shi Kuma zaiyi bakin kokarinshi wajen ganin itama Miemien ta soshi ko don sbd abotar dake tsakaninshi dashi. Da dare yayi dialing number dinta praying Allah yasa ta dauka sai Kuma gashi ta dauka din..ya lankwasa muryanshi in a pleading tone yace mata"Love am sorry"..shiru tayi bata amsa mashi ba shi Kuma ya sake cewa"Aysher"..a hankali tace"umhum"..yace"am sorry for kissing u..nasan I shouldn't have done that amma ba laifina bane..u couldn't control my self am sorry"..ajiyar zucia yaji ta sauke ita bama wnn ne damuwarta ba..Kai tsaye tace"wacece ita?.."yace"Mom dinta friend din Mummy ne..and.."kasa karasawa yayi yai shiru tana tunanin yanda zaiyi mata bayani...jin yayi shiru tace"and?.."a hankali yacigaba"tana Sona sosai amma believe me I never loved her..infact na tsaneta"..dan daure fuska tayi kmr yana ganinta tace"i don't believe that..baka sonta shine kake bata daman binka har flat dinka?.."tana rufe baki yace"wlh da gaske nake maki Aysher bana sonta..koda ta shiga flat din nawa explaining mata nayi cewa ni ke nakeso Kuma kece zan aura..dan Allah kiyi hakuri mana plss..u are the only person that matters to me and i love only u"..shiru tayi batace komai ba..shi Kuma ya sake marairace mata yace"love please!.."ajiyar zucia ta Kara saki before saying"nidai wlh ta sake zuwa inda kake ban yafe ba..and I mean it"..ya saki wani murmushi yana cewa"baza ma ta sake zuwa ba believe me..I Love u"..shiru ta sakeyi kafin yace"Love say u love me too mana plss..i want to hear that"..dan turo bakinta tayi kafin tace"I love u too".. tun kafin ta rufe baki ya shiga blowing mata kisses ta cikin wayar yana cewa"thank u..thank u..thank u so very much baby..thank u". Tun daga wnn rana masoyan suka shirya abunsu..soyayya Kuma sai sake karfi yakeyi a tsakaninsu ta yanda basa iya complete 2 days ba tareda ganin juna ba..abun har mamaki yake bata yanda takejin sonshi a kowane lungu da saqo na zuciarta..kullum yana kan hanyan zuwa ganinta don kullum sai ta fara shiga college ya ganta kafin ya wuce hospital..zuwa yanxu hatta students daidai ne basu san irin soyayyan dake tsakaninsu ba...a daya 6angaren kuma shirye shiryen council sukeyi sosai don few months yanxu ya rage musu su fara..kowa ya maida hankali matuka wajen karatu sbd yayi passing...specialist aka dauko ta fannoni daban daban suke musu extra lesson kullum a cikin college din kan duk wani abu daya shafi council exam tun daga kan theory har zuwa kan practical..sosai Kuma suka maida hankalinsu suna koya wnn dalilin yasa har weekends suna shiga school sbd lessons din da sukeyi. A 6angaren shirye shiryen bikinsu nan na ba'a cewa komai don both bangarori nata shiri sosai na bikin da baifi saura 4 weeks ba yanxu...su Mummy sun gama hada lefe lokaci kadai suke jira su dauka su kaisu wajen waziri da yace har ita Mummyn yakeso suzo wai da akwai mgnr da zaiyi da ita. A 6angaren bride and groom Kuma za'a iya cewa ba wani shiri da suke don ita tana fama da karatu exams dinta dake sake approaching yayinda shi Kuma ya maida hankali sosai wajen ganin tayi passing exams din nata..har extra lesson yakeyi musu ita da Billy kan duk wani abu daya shige musu duhu..sosai Kuma suke fahimta dan da gaske ya iya koyarwa..wani lokaci har class din nasu yake zuwa yana koyar dasu wani abun during weekends haka sbd ya taimakawa Nur da shima duk wani attention dinshi ya dawo garesu. Yau ma kmr kullum bayan sun gama lesson da yayi musu office dinshi Billy tayi sallama dashi ta fita ita Kuma Aysha na zaune tana kallonshi ganin ya zuba mata ido ya kasa cewa komai..turo baki tayi tana rufe fuska da hannaye ta tace"ni ka dena kallona"..dan murmushi ya saki yana shafa gashin kanshi yace mata"gobe zamuje Gombe"..bude idon tayi da sauri tana kallonshi lokaci daya ta kwabe fuska kmr zata sa mishi kuka tace"partner nima inaso inje plss"..girgiza Kai yayi yana cewa"kiyi focussing kan exams dinki dan Allah"..tun bai rufe baki ta make kafada tana turo baki tace"nidai i want to follow u plss"..kama hannunta yayi ya dawo da ita kusa dashi ta zauna yana facing dinta yace"kinga fa bani kadai zanje ba..tare dasu Mummy zamuje..Kuma ba daddy yace ki bari ki gama exams dinki ba"..baki ta sake turowa tace"to shine Kai zakaje ka barni?.."yace"ai ba jimawa zamuyi ba love believe me..ba dan Waziri da kanshi yace yana nemanmu ba da bazan iya zuwa in kyaleki a nan ba kema kin sani"..kallonshi kawai takeyi hawaye na ciko idonta ta dora kanta a shoulder dinshi tana rikeda hannunshi tace"am going to miss u"..shafa kanta yayi yace"nima i will miss u amma ko kwana biyu bazanyi ba zan dawo trust me"..Kai kawai ta gyada mishi tana sake lafewa a jikinshi..hannu yakai ya dagota daga jikin nashi sbd wasu abubuwa da suka fara kai kawo a cikin jinin jikinshi ya shiga goge mata tears dinta yace"to yaushe zamuje kiga kayan naki?.."makale kafada tayi alaman bazata jeba..yace"to gidanki fa shima bazaki je ki gani ba?.."sake makale kafada tayi tana wani turo baki..Bobby daketa kallonta with adoration lumshe ido yayi tareda matsawa yayi pecking forehead dinta kafin ya dago yana rike da hannayenta yace"I love u so much"..murmushi ta saki itama da wet face dinta tace"i love u too"..kallon dimples dinta yayi kafin yakai fingers dinshi a dora both dimples din nata yana kallon tsakiyar idanunta yace"suma ina sonsu sosai"..murmushi ta kara saki dimples din ya sake fitowa baisan time din da ya lumshe ido ya sake pecking cheeks din nata ba..he loves this girl to the core..yana jin sonta a duk wani numfashi da yake shaqa a doron kasa..soyayyarta a cikin jininshi yake. Washegari da safe suka dauki hanyan Gombe su uku..Mummy,Bobby sai aunty sumy..sai da suka fara tsayawa Police Academy Wudil wajen Sab snn suka wuce Gomben...lokacinda suka isa was around 12..bayan sun isa gidan Waziri yasa aka fito da kayan da suma mota guda akayi musu suka shiga dasu parlonshi..Saida ya gama ganin uban kayan snn yace da Mummy"kunyi kokari sosai Allah ya saka da alkhairi..amma banaso ku sake yin komai kan harkar bikin nan..duk wani abu da yayi saura tun daga kan sadaki har zuwa duk wani abu da za'ayi spending lokacin biki ni na dauki nauyinshi..kaima Attahiru ban yadda ka sake yin komai ba ni da kaina zanyi maka duk abunda ya kama in Allah ya nuna mana"..cikeda farin ciki Mummy tace"Muna godia Baffa Allah ya saka da aljanna"..Waziri yace"Ameen..mgnr kai lefe kuma nayi mgn da Baffaninka da kansu zasu dauki kayan su kaiwa Lamido dan haka ba sai mata sun shiga lamarin ba"..nan ma godia suke sakeyi Bobby ji yayi ya rasa inda zai sa kanshi sbd farin ciki..wato dai zumunchi ba karamin abu bane a rayuwa..dunia mutum baya da tamkar 'yan uwanshi shiyasa no matter the situation bazaka ta6ajin ance wane ya canxa 'yan uwa ba..dan uwanka dole dan uwanka ne komai rigimar da zakuyi dai bazai canxa wnn suna ba shiyasa ake son mutum ya kasance mai juria da Kuma hakuri da 'dan uwanshi..(Allah ka bamu ikon rike zumunchi har karshen rayuwarmu). Bayan sun dan nisa Waziri ya sake cewa"sai Kuma mgn ta biyu da nakeso muyi"..Mummy ce tace"Muna sauraronka"..Waziri ya gyara zama tareda maida duba ga aunty sumy ya kira sunanta"Sumayya"..a hankali tace"na'am"..yace"kinada masaniyar zuwan tsohon mijinki wajena kan batun maida aurenku?.."girgiza kai aunty sumy tayi alamar aah..Waziri yace"to yazo nan ya sameni tareda wani kawunshi..ya sanar dani duk abunda suka faru a tsakaninku ya kuma bani hakuri tareda neman alfarmar in roka masa ke ki amince ki koma dakinki..nace masa bazan yanke hukunci ba saina farajin ta bakinku dan haka kuje kuyi shawara a tsakaninku idan kun amince ta koma Alhamdulillah idan kuma baku amince ba wanda zaiyi mata dole"..gaba daya shiru sukayi tamkar basuji abunda yace ba..Mummy ce ta fara breaking silence din da cewa"nidai ta 6angarena banida wani matsala da haka domin mahaifiyarshi har gida tazo ta nemi gafarar mu kuma muka yafe mata..dan haka indai taga zata koma din nima zanfi son haka ko don sbd zuri'a dake tsakaninsu"..gyada kai Waziri ya shiga yi yace"wnn haka yake..kai kuma Attahiru menene shawararka akan haka?.."dan murmusawa yayi yana shafa kanshi yace"Baffa nima indai ta amince shknn"..da mamaki aunty sumy ta juya tana kallonshi jin yace ya amince kmr dai ba Bobby da har sim card yake canxa mata sbd Isma'il din ba..lallai Bobby ya canxa sosai ba kadan ba..ta tabbata da ada ne akayi mashi wnn tambayar kanshi tsaye zaice bai amince ba amma wai shine da cewa in ta amince shknn..lallai wonders shall never end..har gobe bata dena mamakin sudden change din nan nashi ba..ta fuskanci tun da ya fara son Lamido zuwa haduwa da Waziri ya sauya daga Bobby mai kafiya,taurin kai da kuma riqo zuwa Bobby mai sauki da kuma sanyin hali kan abubuwa da dama ciki hadda yafiya da kuma mancewa da tarin laifukan mutun da tunawa da alkhairinsa komai qanqantarshi...ganin tayi shiru ta kasa cewa komai Waziri ya sake Kiran sunanta..ta amsa kanta a kasa duk bata San ma amsar daya kamata ta bashi ba..shi Isma'il din na meye zai wani xo har wajen waziri ba tareda ya fara mgn da ita yaji ta bakinta ba..Waziri yace"na baki nan da sati biyu kiyi tunani akai..idan kin amince sai a hada auren naki dana 'dan uwanki a daura rana daya"..ba tareda ta dago kanta ba tace"na amince Baffah..Allah yasa haka shine yafi alkhairi"..cikeda farin ciki Waziri yace"Ameen Allah ya maku albarka..Allah Kuma yasa ayi lafia a gama lafia"..duk suka amsa da Ameen..daga nan kuma suka shiga cikin gidan don su huta kafin gobe kuma su sake daukan hanya su koma Kanon Dabo. Kmr yanda Waziri ya fada Baffanin Bobby su hudu tareda shi wazirin na biyar sukaje suka kai lefe wa Lamido inda shima ya kar6a tareda saura uncles dinta..farin ciki sosai sukayi da ganin uban kayan kowa yana Allah sambarka..daga nan Kuma suka tsaida biki bayan sati hudu da gama council exam dinsu..sosai su waziri sukayi na'am da da ranar sbd ita kanta amaryar tabada buqatar hutawa kafin lokacin bikin nata...dukda Lamido yaso hada bikin dana Hamma Najeeb amma hakan bai yiwu ba sbd wani special assignment da aka turashi yi a Cameroon and bazai gama ba sai bayan shekara daya..wnn dalilin yasa dole suka bar nashi bikin har zuwa lokacinda zai dawo shi kuma Bobby tunda ya matsa lallai so yake ayi nashi sai a fara yinshi kafin zuwan na Najeeb din..lokacin da labarin sa ranar ya iske Bobby Saida yaji ba dadi..yanxu bayan duk wnn jiran da yayi so suke ya kara cinye wani month bayan exams dinsu snn ayi biki?..Sam baiji dadin wnn four weeks din ba..shi da zasu gane ma da dawo da bikin sukayi ya dawo one month din amma ba su sake Kara mishi another month akai ba...yana zaune office dinshi tun daxu sai jujjuya mgnr yake yanajin haushi kmr tasan halinda yake ciki saiga kiranta ya shigo wayarshi..daukan wayan yayi tareda relaxing kan kujera yayi answering call din ba tareda yace komai ba..a daya 6angaren Lamido najin yayi picking ta wani kashe murya tace"partner nah"..dan turo baki yayi exactly yanda take tura mishi nata bakin yace"stop calling me that"..wara ido tayi da mamaki tace"why?..what happened?.."sake marairaicewa yayi kmr zaisa mata kuka yace"wai bakiji ma abunda ke faruwa ba?.."dan rausayar da Kai tayi itama kmr yana ganinta tace"meya faru?.."tun bata rufe baki ba yace"two months..sbd Allah wane hutawa akeso kiyi har na tsahon one month bayan kammala exams..ya kamata aji tausayina mana"..Saida ta bari ya gama haqilonshi snn ta saki wani murmushi tana cewa"Partner its just four weeks fa..before u know it zakaga har lokacin yazo"..girgiza kai kawai yake yana dafa head dinshi alaman she won't understand..ita Kuma jin baice komai ba ta sake lankwasa murya tace"sati hudu ai kaman yau n..."bata karasa ba katseta da fadin"idan kika sake kiramin four weeks din nan zakiga other side of me wlh..a tunaninki four weeks din kmr four days yake?.."dan daure fuskanta tayi tana turo baki tace"nidai kayi hakuri..ai bani nasa maka biki ba zaka wuce a kaina"..shiru yayi kmr bazai sake mgn ba yace"haka kikace?.."with full confidence dinta tace"yes"..yace"ohk then"..sai kuma ya dakata ya shiga sakin murmushi yana shafa gemu zuwa sajen fuskanshi murya can kasa yace"don't worry my turn will soon come..and yes ya kamata ki samu enough hutu sosai for what u are about to face"..dan daure fuska tayi tana muzurai tace"what are u insinuating?.."yana cigaba da shafa uban gashin kanshi yace"nothing oo..it's nothing"..shiru tayi tana ture turen baki sai kace ganinta yake..shi kuma har yanxu bai dena smiling ba ya sake cewa"kullum Ina cewa zakiga other side of me baki ta6a gani ba koh?..to a wnn ranan zakiga the real definition of my other side"..tun kafin ya rufe baki tace"banaso"..yace"badai ni kike cema its just four weeks ba?..zakiga it's just four weeks duk ranan da kika shigo hannuna..a ranan zaki gane Attahir nake ba proprietor ko Dr Bobby ba"..ya karasa mgnr da wani killer smile a fuskanshi..yanda yake mgn kadai says it all domin duk wanda yaga how he's talking yana lumshe ido zai gane da mace ne yake waya..kawai baqin cikin da yake na Kara mishi one month duk yayi disappearing sbd tunawa da wani abu da yayi..hakan kuma yasa yaketa sakin murmushi yana shafa kai kmr wani sabon kamu...Alhajia indo kuwa jikinta ba karamin sanyi yayi da wnn kalaman nashi ba..ta lura fa dama these days wani sabon iskanci yakeji dashi haka zaiyita 6aro mata mgn yana sata jin kunya shi kuma ko a jikinshi..ita bata ta6a sanin there is this side of him ba sai yanxu..duk ya wani dawo mai dabi'un 'yan iska shiyasa yake bata tsoro ma...jin yanda tayi dif kmr bata jinshi ya sake relaxing yana lumshe ido kafin yace"baby"..banza tayi mishi tana turo baki kmr yana gabanta..ya sake cewa"partner"..still taki tankashi kawai sai ya saki murmushi yana girgiza kai yace mata"duk wnn abun fa love wasa nake maki..ke bakisan wasa bane?.."murguda baki tayi tana sake dinke fuska tace"ba wani wasa..Allah idan kacigaba da tsokana na fasawa zanyi"..Bobby ya dan wara ido yana sake murmusawa yace"baby idan kika fasa kuma ai mutuwa zanyi"..tace"to ka dena tsokana na nidai"..tun kafin ta rufe baki yace"na bari..ban karawa believe me"..ajiyar zucia ta sauke kafin tace"shknn"..ajiyar zuciyar shima ya sauke tareda lumshe ido yana sake relaxing kan seat dinshi yace"I..love..you..and i can't wait to..marry you". Bayan sati hudu... Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 53 Bayan sati hudu... Yau Friday sukayi final laper dinsu and tun da suka fito daga exam hall around 11 kowa yaje ya sake shiri cikin sign out shirts da sukayi iri daya kowa nashi dauke da sunanshi a jiki..hall da suka saba gabatar da celebrations aka bude musu suka shiga nan sukaita celebrating kammala exams dinsu saura fitowa results kuma..har dj suka kira yaketa playing musu waqoqi iri iri masu rawa nayi masu daukan pictures ma sunayi...a extreme end of the hall Lamido zaune tana kallon su Billy daketa dirkan rawa kan stage da sunga wani da bai musu signing jikin shirts dinsu ba zasu bar rawan suje ayi musu signing din suma suyima wanda basuma ba snn su sake komawa dance floor..haka suketa yi tun daxun ita tana nan zaune tana kallonsu..kawai tunanin yanda zasu kwashe da Bobby takeyi idan yaga shirt dinta da signing musamman ma signing na namiji sai kuma rawa Kiri kiri da takeso tayi amma sbd tsoron kishi irin nashi ta kasayi..har sha'awan Billy da sauran colleagues dinta dake wurin takeyi sai taji inama ba'a college din nan yake ba itama da ba abunda zai hana mata enjoying wnn ranan amma yanxu bata isa ba...Billy ce ta nufo inda take zaune da sauri tana zuwa ta Mika mata wayanta dake hannunta tana cewa"Ur Hamma wants to speak to u"..ba musu Aysha ta karbi waya suka fara mgn dashi ita Kuma Billy ta dauki bottled water dake ajiye nan kusa da ita ta zauna tana sipping ruwan tana sauke numfashi...after like 4 mins suka gama mgn da Hamma Aysha ta shiga mikawa Billy wayanta kafin tace"Billy dan Allah zan danyi rawa ko kadan ne kinga fa ba zuwa zaiyi ba nasan yana hospital wlh"..girgiza kai Billy ta shigayi tace"aah fa ba ruwana Lamido bazaki hadani da wnn rigimammen mijin naki ba..haka nan kisa yazo yana tsareni da idon nan nashi da dadine dasu ba"..langa6ewa tayi tana kallonta kmr zata sa kuka tace"yanxu knn kinfi sonshi akaina Billy?..dan girman Allah in dan shiga inyi Allah ba dadewa zanyi ba"..girgiza Kai Billy ta sakeyi saidai kafin tace wani abu Aysha da ta riga tazo wuya sbd haushi tace"ko baki yadda ba sai nayi wlh saidai kije kiyita fada masa din i don't care"..daga haka ta mike zata bar wurin Billy ta dawo da ita da sauri tareda mikewa itama tana kallonta tace"amma banda signing kou?..kinsan fa halin mutumin nan Lamido banson kuxo kuna samun matsala akan haka"..kwace hannunta Aysha tayi ta bude bag dinta ta fito da wani shirt din sabuwa sak irin na jikinta tana nunawa Billy rigan tace"indai ba kece munafukar da zaki fada masa ba ba yanda za'ayi ya sani..ana gama min signing kafin mu fita hall din nan ma zan cire in saka wnn"..kallonta kawai Billy keyi ita wnn abun bai gamsheta ba..a yanda taga yake mgn jiya tasan wlh da kyar idan basu samu matsala kan haka ba tunda he made it clear cewar bayason wnn abun...ganin har ta kama hanyan dance floor ta daga shoulder alaman ba ruwanta snn itama ta bita a baya...tana hawa kan stage din sai kuma ta juya zata sauka da sauri colleagues dinta suka kamata suka maidata wurin..daya daga cikinsu taje ta samu dj tace mishi class rep dinsu ta shigo don haka ya samu Waqar favorite dinta mai azabar dadi yayi playing musu zasu cashe yanxun nan..dj kuwa ba musu ya sakar musu waqa mai dadi nan suka shiga rawa suna janta wai itama dole sai tayi..tun tana nokewa tanajin tsoro har dai daga baya ta saki jiki ta dilliqi rawar ta son ranta..at that moment gaba daya mantawa ma tayi da wani warning dinshi na jiya kan baiso tayi rawa and bai yadda wani ya taba rigarta da sunan signing ba..enjoying dinta takeyi kawai tana cashiya kmr ba Lamido ba...saida tayi me isarta snn ta fara zuwa ana mata signing jikin shirt dinta duk wanda ta gani da sauri take zuwa wurinshi yanayi mata zatayi sauri ta rufe wurin da kimono din jikinta wai duk sbd kada ya samu labari idan yazo...a takaice har after five suna cikin hall din nan suna abu daya..ganin yamma ya farayi hankalinta ya dawo jikinta tasan yanxu duk inda yake ya kusa shigowa college din don haka baki alekum ta fita daga cikin hall din zuwa wani dan small room dake kusada wurin ta shiga ciki da sauri ta zare kimono dinta tana kokarin cire sign out shirt din kawai taga mutum a gabanta..batasan sanda gabanta yayi wani irin yankewa ya fadi ba..lokaci daya ta saki rigar tana yarfa hannayenta hawaye har ya ciko eyes dinta tace"wayyo Allah na"..kala bai ce mata ba sai kimono daya dauka ya mika mata..da sauri ta kar6a ta maidata jikinta tana kallonshi..tana gamawa ya kama hannunta a fusace suka fita daga room din..direct office dinshi ya nufa da ita mutane nata kallon yanda ya riko hannunta amma kobi ta kansu baiyi ba don abunda ya dameshi kadai ma ya isheshi..yana bude office din ya turata ciki snn shima ya shiga ya maida kofar ya rufe ya shiga kallonta da eyes dinshi da sukayi jaa sbd bacin rai...kuka sosai ta fara tana yarfe hannayenta shi Kuma baice mata komai ba sai tsareta da yayi da eyes dinshi da taji sun dawo mata eyes dinshi data sani a baya masu sanya mata firgici da nutsuwa ba tareda ta shirya ba..da sauri ta matsa zuwa kusa dashi ta dan daga Kai tana kallonshi sbd yafita tsayi sosai kawai sai ya lumshe eyes dinshi don bazai iya juran kallonta a haka ba karyar mishi da zucia zatayi...ba zato ba tsammani kawai yajita fada jikinshi ta kankameshi tana sakin wani kukan da koshi yasan na shagwa6a ne kawai muryanta na rawa tace"am so..rry"..lumshe idanu ya sakeyi yana sauke ajiyar zucia..baisan ya zaiyi da rashin jin Aysha ba amma ko Allah yasan ba karamin wahalar dashi take ba..bude idanunshi yayi tareda dagota daga jikinshi ba tareda ya kalleta ba yakai hannu ya bude kimono dake jikinta nan take uban signings din dake jikin riganta suka bayyana..kallonsu kawai Bobby keyi ranshi na sake 6aci..duk Wanda yayi signing din nn yasan ya ta6a masa jikinta Kuma shidai Allah ya isanshi wlh..da iya class mates dinta ne ma da sauki tunda mata ne amma yasan baza'a rasa 'yan nursing a cikin Wanda sukayi mata signing din ba...runtse Ido yayi da karfi da yaga har wurin chest dinta saida akayi signing..ya juya bayanta nan ma yaga har waist dinta signing ne kaca kace kawai sai ya juya tareda zaunawa kan sofa yana date head dinshi da yaji kaman zai 6alle sbd ciwo..karasawa tayi ta zauna kusa dashi tareda dora kanta a shoulder dinshi tana hawaye sosai tace mishi"dan Allah kayi hakuri partner..zaka iya punishing dina da any kind of punishment amma don't be mad at me plss..am sorry"..hannunshi yakai a hankali yana shafa kanta sbd yanda kukan ke ta6a zuciarshi kwarai...sake langabewa tayi tana sauke numfashi..shi Kuma murya can kasa yace mata"you danced right?.."shiru tayi tana rarraba ido kmr munafuka shi Kuma ya saki murmushi mai ciwo dama ya tambaya ne wai ko hasashenshi zai zama ba gaskia ba amma shirun da tayi ya tabbatar mishi da cewa tayi rawa..zafi sosai yakeji cikin ranshi Wanda inda zai fito dashi ya nuna mata yanda yakeji kilan tsorata zatayi ta gudu shiyasa yake kokarin dannewa kawai..zuwa yanxu ya fuskanci zafi da takura babu abunda zai kara mata sai kangarewa so it's better ya fara binta da lallami da nasiha kilan Allah yasa ya dace..sake Kai hannayenta tayi ta zagaya bayanshi zuwa stomach dinshi dasu dukda ba gama zagayawa sukayi ba tace"partner am sorry please"..Kai kawai ya iya gyadawa yana shafa kanta a hankali yana karanta duk addu'an da yazo bakinshi..inshort sun duki lokaci mai tsaho a haka tana bashi hakuri kafin ya samu saukin abunda yakeji..Saida ya dan nustu snn ya shiga nata nasiha sosai Wanda har kusan kuka yasata sbd yanda yake mgnr shows ba karamin zafin abun da tayi yakeji ba..bata bar office din ba saida ta tabbata he is no longer upset with her snn yayi dropping nasu a hostel da kanshi bayan sun sha love dinsu. Washegari da safe bayan sun gama 'yan koke kokensu na rabuwa da juna Hamma Najeeb yazo ya kwashesu dasu da komai nasu sai jihar Gombawa diban fari..ba'a kwana daku ba wai sai a tashi daku. Wnn knn.. Kwananta biyu da komawa small mom dinta tazo ta dauketa suka wuce Bauchi wai za'a fara mata gyaran jiki and stuffs dai da akeyi na gyaran amarya..dukda Ammi bataso haka ba sbd zaman Fiddausi da Aysha a cewarta ba abunda yake karawa sai lalata Ayshan sbd ba wani fada take iya mata ba..amma da daddy yasa baki haka nan ta hakura suka tafi Bauchin bada son ranta ba..ita fa so tayi a dan zaman nn da zatayi ta gyara mata zama sosai ta yanda bazata je gidan miji tana basu kunya ba don tasan halin kayarta tsaf har yanxu ba cikakken hankali ne da ita ba. Tunda ranan da suka isa Bauchi ko kofar gida bata sake fitowa ba wai idan ana gyara ba'a son shiga rana...mai gyaran jiki sosai auntyn nata ta dauko takanas take gyara mata ita ciki da waje don komai daya danganci gyaran amarya ana mata and ita da kanta ta fara ji da kuma ganin canji a jikinta..biki ya rage saura 3 weeks Billy ta dawo gidan aunty Fiddausi da zama sbd shirye shiryen biki da suka fara ka'in da na'in...events sosai Billy suke shiryawa ita da Provost don sune Organizers na komai da zasuyi a bikin..dama Kuma halinsu ya kusa zuwa daya dan haka suketa planning events kala kala hadda na shirme dan kusan week guda za'a kwashe ana bikin..ko Lamido da take mayyar biki Saida tace ma Billy events din sunyi yawa da taga uban abubuwan da suka rubuta za'ayi amma sai Billy tace mata babu ruwanta nata kawai zuwa ne amma ko event guda baza suyi cancelling ba. Shirye shirye sosai akeyi ta kowane 6angare..baga ahalin Lamido da Waziri ba..ba Kuma ga ahalin hajia Mummy da aunty Sumayya ba...bride and groom dai nasu Ido ne kawai almost komai na bikin shirya musu akeyi so nasu kawai suyi attending ne..lokacinda aunty sumy ta fada mishi events da zasuyi cewa yayi a rage that shi bayason big wedding wai gajia zaiyi ma da attending events din..amma aunty sumy tace ko event daya bazasuyi cancelling ba idan yaga dama kar yazo su zasuyi abunsu tareda amarya...murmushi kawai ya iya sakar mata ya wuce flat dinshi yana dialing number amaryarshi da rabonshi da sanyata a ido tun ranar da tabar Kano..kiri kiri yanason zuwa ya ganta yarinyar nan ta hanashi wani wai aunty Fiddausi bazata bari ba which he knows she's lying of course..kawai shima sai ya rabu da ita cikin ranshi yace zaiyi maganinta ne idan ta shigo hannunshi..ganin har Kiran ta katse bata dauka ba ya ajiye wayar ya shiga wanka don dawowarshi knn daga clinic. Aunty Fiddausi ta shigo dakin da take kwance hannunta rikeda bottled water mai sanyi sai sachet na inflanil a hannunta ta karaso ciki ta zauna gefen Aysha dake kudundune cikin bargo tace"oya mike ki samu Kisha maganin nn yanxu zaki samu sauki inshaAllah"..dan bude Ido Aysha tayi tana ganin magani a hannunta ta wani yatsine fuska tana marairaicewa tace"aunty dan Allah kiyi hakuri da kanshi zai dena wlh"..a fusace aunty Fiddausi tace"kinsan Allah zan kira Adda in fada mata wnn iskancin da kikeyi..Shan magani kawai ya gagareki kuma don walakanci har likita na kira tazo ta dubaki kememe kina hana ta maki allura yanxu maganin ma Kuma bazaki Sha ba sbd kin maidani yar iska"..sake marairaicewa tayi tana duban small mom din tata tace"aunty na rantse da Allah idan nasha bakina sai yayi sati yanamin daci..shi Kuma allura fa kinsan dai yanda yakemun ba saina fada maki ba"..a fusace aunty Fiddausi ta ajiye drug da ruwa dake hannunta tace"sai kiyita zama da ciwonki har bikin naki yazo ni ba ruwana"..daga haka ta mike tayi ficewarta daga dakin..a waje suka kusa karo da Billy zata Kai mata tea tasha..ganin yanda ta fito rai a 6ace Billy tace"bata Sha maganinba Koh?.."aunty Fiddausi tace"inafa tasha..yarinya dai shege taurin kai kmr mutanen farko"..girgiza kai Billy tayi tace"bari in kai mata tea din nan inzo aunty nasan wanda ko bataso zai iya mata allura"..daga haka ta wuce dakin ta dire mata tea din gabanta ko kallonta batayi ba ta juya ta fita Aysha ta bita da harara kmr Idonta zasu Fadi kasa..kawai batada lafia ma bazasu daga mata kafa ba kowa sai yayita nata masifa kmr an gaji da ita...Billy na fita ta iske aunty Fiddausi zaune a parlor samun wuri tayi itama ta zauna snn ta dauko wayanta tana searching contact dinshi tace"aunty proprietor ne kadai zai iya mata allura komai isakancin da zatayi"..kallonta aunty Fiddausi tayi kafin tace"sai Kuma mu tasoshi tun daga Kano sbd yazo ya mata allura Bilkisu"..Billy tace"zaizo wlh aunty shima nasan da kyar idan ba son ganinta yake ba yanxu..rabonshi da ita fa tun da mukayi graduation"..ajiyar zucia aunty Fiddausi ta sauke tana cewa"to kirashi ki fada mishi yazo yasan yanda zaiyi da ita nidai..dan wlh idan ta kaini bango ubanta zanci babu ruwana da ita amarya ce tunda batada mutunci"..Billy na murmushi tayi dialing number dinshi tana fadin"bama za'a Kai ga hakaba zaizo yayi maganin kayarshi"..yana daukan waya bayan ta gaisheshi tace mishi aunty Fiddausi tace idan zai iya zuwa Bauchi yazo ya duba musu ita batada lafia as usual Kuma taki yadda ayi mata allura snn taki tasha magani..Bobby da yaji abun kmr gaba ta kaishi nan take yace zai taho yanxun nn don shima son ganinta yakeyi musamman yanxu da akace batada lafia yasan ko yace sai gobe ma ba iya baccin kirki zaiyi ba so gwara ya taho yanxun..suna gama waya ta sanar da aunty Fiddausi yanda sukayi dashi dan haka tasa aka fara shirya mishi abinci kala kala yayinda hajia Ai ke kwance daki tana bacci bata ma San abunda ke faruwa ba. Bobby na gama waya da Billy ya shirya kanshi sharp sharp ya dauki duk wani abu da yasan zai bukata tareda key din mota ya fita ka tsaye ya shiga flat din Mummy ya mata sallama kan zaije Bauchi wai Aysha batada lafia..Mummy batayi yunkurin hanashi ba ta bishi da addu'an dawowa lafia don tasan yanda duk ya rikice din nn idan ma ba'a barshi ya tafi ba hankalinshi ba kwanciya zaiyi ba...yana fita ya fada mota direct ya wuce gidan su Nur haka ya azalzaleshi ya shirya sharp sharp snn suka shiga motanshi suka kama hanyan Bauchi..Nur sai mita yake mishi wai daga dawowa gida ko hutawa bai barshi yayi ba yazo ya wani jajibeshi zuwa Bauchi sbd rashin hakuri ba yanda baiyi dashi akan ya bari sai gobe ba amma ya dage sai yau sai kace dai a kanshi aka fara soyayya. Karfe hudu da wani abu suka shigo cikin Bauchi..driver aunty Fiddausi ta tura ya taho dasu daga inda suke har zuwa gidanta..shi ya fara shiga ciki kafin suma su shiga da nasu motan..parking Bobby ya karasa ciki yayi yayinda driver daya rakosu ta shiga cikin gidan ya sanar da aunty Fiddausi karasowarsu..Jim kadan ya dawo yace musu tace su shiga ciki..basuyi musu ba suka fita daga mota dukabi bayanshi har zuwa cikin gidan..a main parlor suka zauna shi Kuma driver ya fita..bayan few minutes Billy ta shigo parlon rikeda tray din su juice a hannunta..ta karaso ciki ta ajiye tray akan table snn ta zauna kan one seater tana dan sunkuyar da kanta tace"barkanku da zuwa"..Nur ya fara cewa"barka Bilkisu..ya jikin Lamidon?.."tace"da sauki sosai"..juyawa tayi tana kallon Bobby ya sakar mata murmushi..murmushin itama ta saki snn ta shiga gaishesu..bayan sun gaisa ta mike ta bar parlon can sai gata ta sake dawowa da wasu dirka dirkan warmers ta ajiye snn ta sake komawa ta kawo wasu ta kuma ajiyewa snn ta wuce don kiran aunty Fiddausi..tare suka dawo da ita parlon ta karaso ciki ta zauna opposite to them tana dubansu da murmushi sosai fuskanta tace"sannunku da hanya"..durkusawa sukayi har kasa suka gaisheta dukda ko zata girmesu ba irin sosai din nan ba..aunty Fiddausi ta amsa gaisuwarsu tana murmushi bayan sun zauna tace"ku fara cin abinci sai raka ku inda take..bacci ma takeyi don batasan da zuwanku ba"..tana rufe baki Bobby da ya matsu ya sanyata Idonshi yace"am..ni bana tareda yunwa aunty"..dan murmushi aunty Fiddausi ta saki kafin tace ma Billy"ki rakashi dakinda take"..ba musu Billy ta amsa da toh ta juya ta kama hanyar dakin Bobby yabi bayanta yayinda oga Nuruddeen ya baje ya shiga bama cikinshi haqqinshi don a cewarshi soyayyar Bobby bazai hanashi cin abinci ba shikam...Billy na nuna mashi dakin ta juya ta bar wurin yayinda shi Kuma ya tura kofar dakin a hankali ya shiga da sallama...wani irin sanyi dakin ya dauka sosai sbd ac dake kure ita Kuma tana kwance can karshen gado ta kudundune kanta cikin blanket tana bacci peacefully kmr ba mara lafia ba..a hankali ta shiga takawa har zuwa bakin gadon ya tsaya yana kallon yanda tayi coiling kanta a kan gadon kmr ba mutum ba..stool ya janyo ya zauna dab da gadon yana facing dinta kafin yakai hannunshi a hankali ya janye blanket din..da uban gashin kanta dake tsefe ya fara cin karo sai kuma cute and beautiful face dinta da yaga har wani glowing yakeyi a Idonshi..baisan ko sbd ya jima bai ganta bane amma yaga ta Kara kyau sosai ba kadan ba...janye blanket din yayi daidai stomach dinta sai yaga tayi motsi tareda jan blanket din zata sake rufewa dashi yayi saurin janyeshi tareda daukan remote ya kashe air condition din dakin gaba daya...kallonta yacigaba dayi yanajin wani abu mai matukar karfi yana kokarin fizgarshi zuwa gareta baisan lokacinda ya lumshe ido tareda sunkuyawa yayi pecking forehead dinta ba..hannunta ya kama ya rike yana cigaba da kallonta kmr Wanda keson gano wani abun..left hand dinshi da yake free ya mika yayi feeling temperature dinta yaji jikinta normal babu wani zafi kawai sai ya saki wani hadadden murmushi yana shafa gemu zuwa sajen fuskanshi Kuma still hannunshi na cikin nata..a hankali ta fara motsawa sbd zafi data faraji as a result of kashe ac da yayi..lokaci daya Kuma ta bude Idonta tar tana kallonshi shima sai ya tsayar da nashi idon a kanta yana kallonta...mikewa tayi zaune da sauri tana Mirza idonta to make sure ba dreaming take ba Kuma sai taga its real ba mafarki bane..wara idon tayi da kyau tana kallonshi kallo irin na mamaki kafin tace wani abu ya rigata da fadin"ya jikinki?.."hadiye yawu tayi da sauri tana gyada kanta tace"naji..sauqi..amma ya akayi kazo nan?.."murmushi ya saki yana kallonta yace"kirana sukayi wai bakida lafia kuma kinqi yadda ayi allura and kinqi shan magani"..turo baki tayi tana hade rai lokaci guda tace"to nidai bazaka mun allura ba wlh"..murmushi yakeyi har yanxu yace"baby bakida lafia fa?.."rau rau tayi da Ido kmr zata fara kuka tace"Allah kamun allura fasawa zanyi"..daria ta bashi sosai jin abunda ta fada..ya fuskanci these days rigima takeji dashi dan abu kadan zata ce mishi fasawa zatayi..Saida ya gaji da dariarshi kafin yaja dogon hancinta yana cigaba smiling yace"da yake fasawan a hannunki yake Koh?.."turo baki tayi tace"nidai kada kamin allura dan Allah"..gyada mata kai yayi alamar bazaiyi ba..dan kura mata ido yayi for like 3 mins sai Kuma ya saki murmushi yana kallon eyeballs dinta yace"meke damunki?.."a hankali tace"fever"..tun kafin ta rufe baki ya shiga girgiza kai yana cigaba da kallonta yace"ba fever ba dai..ki fadi gaskia"..daure fuska tayi tana harare harare tace"nidai fever ne ke damuna"..shiru yayi yana kallonta kawai sai ya girgiza kai..Aysha da gaba daya ta gama tsarguwa da wnn abun nashi tace"and what does that mean?.."shoulder ya daga mata alamar nothing..da sauri tace"ban yadda ba wlh..da akwai wani abu cikin ranka"..girgiza mata kai yayi alamar ba komai ita kuma ta wani hade rai zata kwanta baisan lokacinda ya janyota jikinshi yana danne dariarshi ba..murya can kasa yace"kawai ki fadamun period kike ba sai kina wani 6oye 6oye ba mana..am ur soon to be husband"..tun kafin ya rufe baki ta daddage ta tureshi daga jikinta ta sake juyawa zata kwanta yayi saurin dawo da ita jikinshi yana cigaba da dariarshi yace"nifa bada wani abu na fada ba..am sorry"..banza tayi dashi ta shiga kokarin kwace kanta..ya dagota tareda cupping fuskanta still yana murmushi yace"bafa laifi kukayi ba ni kyautamun ma kukayi keda period din naki da kukeyin abunku tun yanxu ba sai..."bata bari ya karasa ba ta toshe mishi bakin da hannu daya tana dukan chest dinshi da dayan hannun tace"banaso..banasoo"..sake rungumeta yayi yana sakin daria sosai yace"to kuyi hakuri na dena"..sake dukan chest din nashi tayi yace"to kiyi hakuri love..am sorry ba period kike ba"..daga haka ya dagota daga jikin nahi yana kallonta da kyau yace"yanxu kici abinci sai muyi allura"..girgiza kai ta shigayi tana cewa"No pls"..da sauri yace"ohk to ki samu kici wani abu sai kisha magani"..gyada mishi Kai tayi alamar toh..shi Kuma ya mike daga inda yake zaune ya mika mata hannunshi yace"tashi muje parlor kici abinci"..girgiza kai ta sakeyi tace"rigana baida tsayi kaje zan fito"..yace"U sure?.."Kai ta gyada mishi meaning she's sure..bai sake cewa komai ba ya fita daga dakin ita Kuma ta mike da kyar ta janyo hijab ta zura snn ta shiga takawa a hankali ta fita zuwa parlon..itadai tsoronta Allah tsoronta kada yace zaiyi mata allura dan bataso wlh..haka kawai salon azo bikinta allura nayi mata ciwo. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 54 Biki ya rage sati daya Aunty Fiddausi ta tattara su gaba daya suka wuce Gombe sbd preparation na biki da zata taya yayarta...zuwa lokacin sosai amarya Aysha ta canxa tayi wani 6ul 6ul da ita kaman ba amarya ba don ba wani stress na biki data daurama kanta..duk wani abu daya kamata ayi Billy ce takeyi tareda sauran cousins dinta sai kuma Aunty Fiddausi...sbd cika fa gidansu ya farayi da mutane na nesa da suka fara zuwa Ammi tace ita da Billy suje can gidan wani small uncle dinta da bai dade da aure ba su zauna tareda sauran friends dinsu da zasuzo idan an fara biki...haka kuwa akayi suka tattara duk wani abu da sukasan zasuyi amfani dashi har a kammala biki suka wuce can gidan uncle din nata dake few houses away from nasu gidan...sun rage yawan events da suka tsara zasuyi sbd Lamido ne yace lallai lallai duk yawan events dinsu kada ya wuce kwana uku dan haka sun bar Henna Party ranar Wednesday.. Thursday Cocktail party..Friday kuma Kamu da Mother's Eve wanda Ammi ta shirya..Saturday ayi daurin Aure by 11 daga nan kuma a wuce da amarya Kano inda zasu gabatar da nasu events din a can. Yau Tuesday tun safe sukayi shirin tafia saloon Billy na zaune parlor tana waya da Hamma bai Kai ga dawowa Gombe ba ita kuma amarya Aysha tana daki tana karasa shiryawa don su wuce saloon din da wuri..tana zaune gaban mirror tana kokarin parking gashinta kiran ango ya shigo wayarta..ajiye comb dake hannunta tayi tareda daukan wayan tana marairaicewa tayi picking tana cewa"partner dan Allah kayi hakuri mu tafi plss..wlh daga ni sai Billy zamu tafi ba wani ne zai kaimu ba"..girgiza kai Bobby yayi kmr tana gabanshi yace"baby i told u Sab is coming to take u guys ku Kara hakuri mana..ban yadda ki shiga motar wani ya fita dake ba wlh"..da mamaki sosai tace"u mean tun daga kano ka tasoshi sbd yazo ya kaimu saloon?.."girgiza kai ya sakeyi yana shafa kanshi yace"no yana Gomben dama tun jiya Mummy ta aikoshi bai dawo ba..yanxun yacemin ya fito daga gida so u guys should wait for him"..a hankali tace"partner kishinka yayi yawa mana..an kusa bikin ma bazaka dena wnn abun ba"..tun kafin ta rufe baki yace"duk abunda zaki fada ki fada amma da gaske bazan saki matata sakaka kowane Kato yana kallon min ita ba..ubangiji da kanshi yace ya tsine ma wanda bai kishin matarshi so bazan zama among wayanda tsinuwan Allah zai tabbata a kansu ba"..murmushi tayi tana girgiza kai tace"dukda haka naka yayi yawa partner..ya kamata ka rage plss"..shiru taji yayi kmr bazaiyi mgn ba sai can taji yace"kinsan wani abu?.."girgiza mishi before saying"aah"..wani munafukin murmushi ya saki yana shafa gemunshi murya can kasa yace"i can't wait to be with you..Allah kadai yasan yanda nakeji kaman in janyo Saturday ya dawo yau"..ya karasa mgn yana lumshe ido kai kace a gabanta yake..Lamido dai diff tayi tana sauraronshi jin ya fara sauka daga layi..ita ta rasa dalilinda yasa ya dawo bashida kunya yanxu..gaya mata duk maganan da yazo bakinshi yake ita ya barta da jin kunya..turo baki tayi tareda mikewa daga inda take zaune tace"nidai tafia zanyi Ammi na kirana"..da sauri yace mata"hang on plss"..shiru tayi tana sauraronshi..shi kuma ya wani kwantar da murya yace"bakice kina Sona bafa"..murmushi mai kyau ta saki tana kallon kanta ta mirror kafin a hankali tace"Partner"..murya can kasa shima yace"yes partner"..sake kashe murya tayi tana wani kashe ido cikin wani irin siga tace"Ina sonka sosai..i love u"..lumshe ido Bobby yayi yana safe chest dinshi still smiling yace"i love u more wlh..son da nake maki Allah kadai yasan amount dinshi"..har yanxu bata bar smiling ba itama tana lumshe ido..batasan why har yanxu bata gajia da sauraron words din nn nashi ba..she loves him to the extent that duk wani word da zai furta mata means the entire world to her..she loves him to the core...kafin wani cikinsu ya sake mgn kiran Ammi ya shigo wayanta..tana dubawa taga itace sai tayi saurin maidawa kunnenta tana cewa"partner excuse me plss..Ammi naga ke kira tun daxu bansan ko nemana take ba"..gyada kai yayi tareda kashe kiran ita Kuma tayi saurin daukan call din Ammi tana cewa"hello Ammi"..a fusace Ammi tace"wai zaman uban me kukeyi a gida baku fito ba tun daxu?.."da sauri tace"yi hakuri Ammi cewa yayi ya turo Sab yazo ya kaimu shiyasa bamu fito ba"..tsaki Ammi taja kafin tace"to yana zuwa ku tafi and ki tabbata kin biyo ta nan don akwai baqin da zaku gaisa dasu"..a hankali tace"to Ammi"..daga haka Ammi ta kashe wayarta ita kuma tayi saurin karasa parking gashinta ta dauki bag dinta da veil dinta a hannu ta fita daga dakin..har yanxu Billy na nan parlor suna waya da Hamma..Aysha ta karasa ciki tana yafa veil dinta akai tace"su Laila da Majnoon har yanxu ba'a gama wayan bane?.."harara Billy ta watsa mata before tace"inace kema wayan kika gamayi da Romeo dinki yanxu?.."girgiza kai Aysha tayi tana karasa veiling dinta..daidai nan Kuma kiran Sag ya shigo wayarta and ko bata dauka ba tasan karasowa yayi dan haka a hanakli ta isa inda Billy ke zaune ta fizge wayar hannunta tareda kaishi kunnenta tana cewa"Hamma a dan daga mana kafa plss..zamuje saloon"..murmushi Hamman nata ya saki tareda kashe wayarshi..Billy da already ta gama shirinta kafin ta fito ta mike tana rataya bag dinta a shoulder dinta tace"to muje amaryar proprietor"..murmushi kawai Aysha ta saki tareda juyawa suka fita daga gidan..suna fita ta hango motar Sab Parke a gefe dan haka suka nufi can direct..yana hangosu ya fito daga motar ya bude musu kofa yana kallonsu da murmushi har suka karaso..Aysha na kallonshi with a smile tace"haka nan ya tasoka daga aikinka Koh?.."girgiza kai Sabeer yayi yana murmushi shima yace"duk aikin da nake ai muhimmancinshi baikai wnn ba aunty"..murmushi ta kara saki ta shiga cikin motar Billy ma ta shiga snn shima ya zaga ya shiga ya tayar da ita suka bar wurin..Saida suka hau titi Lamido tace"dukda haka nidai banji dadin tasoka da yayi kana zaman zamanka ba..Saida fa nace mishi daga ni sai Billy zamu tafi amma bai yadda ba"..Sab dake jinjina zafin kishi irin na dan uwanshi yace"haka nan fa yake aunty..tareda wani cousin dina da zamu zo yace bai yadda in tahoda kowa ya kalleki ba shine na saukeshi a gidan Waziri nace mishi yanxu zanje in dawo"..murmushi Aysha keyi tana girgiza kai tasan halin kayanta tsaf zai aikata hakan shiyasa batayi mamaki ba..har yanxu tana murmushi tace"ni kaina kishin Partner har tsoro yake bani fa..inaga shi baiqi ace babu wanda zai sake kallona ba har karshen rayuwa"..daria Sab ya saki yana cigaba da driving dinshi yace"zai iya aikata hakan wlh"..Billy dai na zaune baya tana jin conversation dinsu..tun bata sa baki ba har daga baya itama ta shiga suka farayi da ita..bayan ya saukesu yace idan sun gama sai su kirashi ya maida su gida shi Kuma ya juya kan motarshi ya koma gidan Waziri. Lokacin da Sab ya maidosu gida was around 3..kofar gidansu tace yayi parking sbd amsan da kiran da Ammi keyi mata tun safe dan haka daga nan sukayi sallama dashi ya wuce su kuma suka shiga cikin gidan da yake nan taf da mutane...saida suka tsaya suka gama gaishe gaishe a parlor na baqin dake ciki kafin suka wuce bedroom din Ammi..daga ita sai aunty Fiddausi a dakin sai wata cousin dinsu suna lissafa cards din mother's eve da dole Ammi tasa aka karo sbd wanda akayi da farko har ya kare..karasowa ciki sukayi suka zauna suna gaisawa dasu..cousin din Ammi mai suna Rahina tace"aah su amare an samu shigowa knn"..Lamido tayi kasa da kai tana sake gaisheta..Aunty Fiddausi ta debo cards kusan guda 40 ta mikama Billy tace"ungo wnn koda na hannunku zaku kare sai kuyi amfani dasu"..Billy tasa hannu ta amsa tana counting dinsu tace"wlh kuwa kmr kinsan wanda kika bani har sun kare"..Aunty Fiddausi tace"nasan za'ayi hakan ai shiyasa na kwasan maku wnn"..daga haka ta kwashi wasu da suka ware na 'yan uwan daddy ta fita daga dakin don kai musu nasu..Ammi ta gyara zama tana duban Aysha tace"zauna muyi mgn"..ba musu ta zauna kusa da Billy tana kallonta..daure fuska Ammi tayi tana cewa"mgn dama zanyi Miki akan African time..wlh Aysha kika sake na tara jama'a a wuri kikaje kikayi zamanki bakizo da wuri ba da sunan make up zakiga yanda zanyi dake a gidan nan..dama da wuri ku fara make up dinku don bazan dauki a 6ata mana lokaci ba kin sani"..gyada kai tayi tana dan marairaicewa tace"wlh da wuri zamu fara Ammi"..Ammi tace"good..saura kuma kiqi nutsuwa kizo kina wnn raye rayen naki da kika saba"..sake marairaicewa tayi tana duban Ammin nata bata dai ce komai ba..Ammi tace"kika wani tsareni da ido ko bakiji abunda na fada bane?.."kasa tayi da kanta kafin a hankali tace"naji..amma to Ammi nidai dan Allah kice kar asa waqoqin gwanja kinga bansan sanda zanyi rawar bafa"..rai a 6ace Ammi ke kallonta tace"qanin ubanki ne Ado Gwanjan?.."da sauri ta girgiza kai tana turo baki..Ammi tace"to kije kiyi rawar kiga idan banci mutuncinki ba..ki bar ganin aurenki za'ayi wlh idan kikayi ba daidai ba Ina iya zuwa har gidan mijin naki inyi maganinki"..har yanxun kanta na kasa tace"to kiyi hakuri"..Ammi bata sake tankata ba ta dauki wasu cards cikin wanda ke xube gabanta ta mikama Billy tace"idan Kun fita ki nemi Husna ki bata..kuma kice mata idan batayi sauri ta kawomun abunda na aiketa ba itama zataci ubanta"..murmushi Billy ta saki tareda mikewa ta amsa cards din Aysha ta mike suka fita..suna fita cousin din Ammi dake sauraron draman nasu tana daria tace"yanxu Maimuna har yanxu baki dena wnn fadan naki ba..yarinya tana amarya kin wani sanyata a gaba da fada bayan ba laifin komai tayi ba"..murmushi Ammi tayi tareda mikewa daga kan gadon da take zaune tace"Adda bakisan halinta bane idan ba haka nayi mata kunya zatazo tana bani a gaban jama'a..shegen rawar kai gareta kmr ba bafulatana ba". Suna bar gidan direct gidan uncle dinta suka wuce da kafa tunda ba wani nisa ke tsakaninshinda nasu gidan ba..suna shiga ta hadu da wata cousin dinta ta 6angaren Ammi mai suna Walida da taba dade da zuwa ba..aikam suna ganinta suka rungume juna suna murnan zuwanta..abinci kadai sukaci bayan sallahn la'asar wanda zatayi musu red henna tazo tunda gobe iya black za'ayi a wajen henna party..daga ita sai Jessy da gajeren wando ta zauna aka fara mata lallen yayinda Billy da Walida keta faman dirkan hira kaman wanda suka shekara da sanin junansu..kafin a gama mata wasu daga cikin cousins dinta dake nan cikin estate din suma duk sun karaso dan haka sukayi reras sunata hira da labari abunsu sai tsokanar amarya suke Billy na tare mata...bayan ita suma duk sauran wanda suke son red din akayi musu ciki harda su Hajia Bilkisu kirjin biki da kuma wasu daga cousins dinta na wurin...har matar gidan saida mai lallen tayima daga nan kuma Ammi ta turo aka dauketa zuwa can gidan nasu don tayi musu nasu lallen suma. Henna Party... Tun safe mutane keta shirin tafia henna party da za'ayi a makeken compound din gidan wani uncle dinta dake nan cikin estate din..anyi decorating wajen in a traditional way wurin yayi kyau sosai da gani traditional event za'ayi a wurin...masu kidan kwarya tuni sun fara aikinsu yayinda wasu da suka fara zuwa wurin suketa tikar rawa. Amarya Aysha bata iso wurin ba sai around 5 tayi matukar kyau cikin wani saqi army green kasancewarta fara sai duhun kayan ya sake fito da ainihin hasken skin dinta..dinkin straight gown akai mata da head dinta da aka daura ya tashi sosai kmr dai na amare..tun daga kan shoes har purse dinta duk sunyi matching da kayan jikinta...tayi kyau sosai da light make up dinta daya sake fito da kyan nata..su Billy da sauran cousins dinta sai few friends dinta ne sukayo mata rakiya har zuwa wurin event din...kafin su shiga da ita ciki Billy dake sanye da ankonsu na bridesmaids tayi kyau sosai itama kasancewarta best friend din amarya ta matso kusada ita da sauri tana daga musu hannu tace"you people should wait inyi video din shigan nan in turama angonta don da gaske idan bai ga wankan nan ba yau da kyar zai iya bacci"..daria gaba daya suka saka itadai Billy ta dauko wayanta ta shiga yi mata pictures da videos saida ta gama snn ta maida wayarta cikin jaka daga nan Kuma suka sake jeruwa suka shigo da ita ciki bayan an sakar musu kida na musamman domin shigo da amarya..bayan sun kaita inda aka tanadar mata ta zauna sai suka koma tsakiyar fili suka dan taka rawa daga nan kuma kowa ta nemi wuri ta zauna..su Billy table guda suka cika na yan FCNM da suka zamu zuwa bikin kowacce tayi shar da ita exactly yanda qawayen amarya keyi idan ana bikin qawar su..each table yana cike da kayan ciye ciye iri iri na gargajia bayan sun gama ciye ciyen henna artists da sukazo suka fara aikinsu...lalle sosai akeyi musu baqi kusan duk Wanda tazo wurin babu wanda hannunta ba lalle a jiki..amarya dai na zaune inda aka ajiyeta duk zaman wurin ma ya isheta kafin a gama nata lallen...tun kafin a gama photographers keta aikinsu..masu daukan pictures nayi masu video coverage suna suna nasu..a takaice har akayi sallahn magrib suna abu daya..dakatawa akayi sukai sallah bayan sun dawo Kuma aka sake sakar musu kida suka cigaba da rawa wnn karon har amarya Lamido kasa cigaba da zama tayi don haka ta taso ta shiga cikin qawayenta sukaita rawa suna nishadinsu a cewarta dai Ammi ba zuwa zatayi wurin ba...bayan wani lokaci su Aunty Fiddausi da sauran aunties da mata uncles dinta suka zo wurin nan ma kida aka sake sa musu sukaita rawa suna 6arar da kudi kmr basu sa zafin nemansu..Aunty Fiddausi ta kama hannun Aysha sukaita rawa abunsu kmr wasu qawaye aikuwa yan uwan Ammi sukayi caa a kansu suna watsa musu kudi..inshort dai basu suka tashi taron ba sai after 8..zuwa lokacin kowa jiki yayi liqis don rawar da sukayi a wurin bana wasa bane..motoci aka kawo musu suka dauki amarya da friends dinta zuwa gidan uncle dinta yayinda su Aunty Fiddausi suma suka nashi motocin da sukazo dasu suka wuce. Suna komawa gida Aysha ta cire kayan jikinta ta shiga wanka don yanda takejin kayan duk sun takura mata..tana fitowa ta dauki sabon jessy dinta na Man u as usual ta saka ta hada da gajeren wandon rigan snn ta zura katon hijab ta tayar da sallah..tana idarwa ta cire hijabin kanta ko hula babu ta dauki waya ta fita parlor inda qawayenta suke sunata maida zance suna daria...gaba dayansu suma sun canxa shiga zuwa na bacci kowa kuma ta gabatar da sallahn da ake binta kafin su zauna..tsakiyarsu ta shiga ta zauna Billy dake kallon wayarta tace"Lamido kinsan ya mukayi da mijinki kuwa?.."girgiza kai tayi tana kallonta meaning bata sani ba..Billy tace"hmm ai Ina tura masa videos din nan na daxu ya kirani wai amma bamuyi masa adalci ba..nace sir rashin adalcin me mukayi wai da muka bar masa ke kika fita a haka nace dole fa yayi mana hakuri har a gama bikin nan"..daria gaba daya suka saka suna tsokanarta ita dai tayi gum babu bakin mgn.. kmr kuwa yasan mgnrshi sukeyi sai ga kiranshi ya shigo..ta mike da sauri ta fada daki hadda su rufe kofa snn ta zauna kan gado ta dauki wayar..ko sallama baiyi ba yace mata"lets video call"..tace"ohk"..shi Kuma ya kaste Kiran sai gashi ya kirata video call..dauka tayi tana kallon screen sai ta ganshi zaune a bedroom dinshi yana sanye da white shirt da three quarter fuskan nn nashi a shagwabe kmr zaisa mata kuka..kallon yanda yayi da face dinshi tayi sai ta saki smile tana karema beard dinshi da yayi mata kyau sosai sbd gyaran fuska da akai mashi kallo..kawai sai taji dama kusa da ita yake yaudai takai hannu ta taba wnn sajen nashi da take ganin kmr duk dunia babu wanda gemu da saje kema kyau kamarshi..lumshe ido tayi tana sake fadada smile dinta..yayinda take kallonshi shima kallon nata yakeyi ganin jessy a jikinta ya dan bata ranshi yace"love meye wnn kike wearing?.."kallon jikinta tayi kafin ta maida kallon gareshi tace"riga ne mana partner"..tana rufe baki"of all rigunan da kike dasu ki rasa Wanda zaki sa sai na 'yan ball..what is wrong with you?.."kallonshi ta tsaya yi har ya gama mgn snn tace"ka cika rigima wlh..riga ne fa kawai ba wani abu ba"..tana rufe baki yace"nidai banasonki da kayan Manchester din nan seriously"..gyada kai tayi tana cewa"to na dena sawa daga yau..are u happy now?.."girgiza mata kanshi yayi yana turo baki yace"Kuma gashinki a bude"..murmushi tayi tareda mikewa ta ajiye wayar jikin mirror yanda zai na kallota daga nan tace"to bari in dauko hula in sa"..daga haka ta juya zuwa wardrobe ta shiga neman hula ko dankwali da zata rufe gashin nata dashi..tana juyawa ya bita da kallo ganin dan wandon dake jikinta ya lumshe ido jin gabanshi har faduwa saida yayi..wandon ya kamata ne sosai gashi kuma gajere baifi iya guiwarta ba..sake bude idon yayi daidai lokacinda tayi bending tana kokarin zaro hula daga cikin kayan Billy kawai sai ya kashe kiran da sauri yana sauke numfashi..tana gama daukan hulan ta juya tana kallon wayan sai taga ya kashe dan haka ta saka hulan a kanta da sauri snn ta sake kiranshi video call din amma har ya katse bai dauka ba..sake kira tayi still no answer tana shirin sake kira sai kuma kiranshi ya shigo amma voice call ba video call..picking tayi ta Kai kunnenta kafin tayi mgn yace"let's not video call again plss..matsala za'a samu"..wara idanunta tayi tace"matsala kuma partner"..gyada kanshi yayi tareda fadin"yes ko a yanxu nasan na gama samun matsala..Allah yasa dai ba haka kike fita kowa yana kallonki ba"..sauke ajiyar zucia tayi kafin tace"da hijab nake fita..amma what's wrong naji kace ka samu matsala"..shiru yayi kmr bazaice komai ba sai can yayi kasa da murya ya shiga furta mata mgnr da tunda suke dashi bata ta6ajin such words daga bakinshi ba..ai da sauri ta kashe wayar tana kwalo idanu waje kmr munafuka..har wani seizing taji numfashinta nayi kmr zai dauke..wai meyake damunshi ne these days?..gaba daya ya canxa mata wlh..sai yayita furta mata duk abunda yazo bakinshi shi ko kunya bai dashi...Billy ce ta shigo dakin taga yanda take kwalo idanu waje tace"what?.."girgiza mata kai tayi alamar ba komai..Billy ta saki smile tareda karasawa ta dauki charger dinta ta juya kafin ta bar dakin tace"yarinya ta kusa jin mazaaa..wlh har tausayi kike bani Lamido"..harara ta Maka mata mai kyau tana wani daure fuska tace"kinga banason irin haka Billy..meye wani na kusa naji maza sai kace yar iska"..juyowa Billy tayi tana kallonta da wani dan iskan murmushi a fuskanta tace"wnn mijin naki dai da gani ba hakuri zaiyi ba yaseen..Proprietor da ko kallonki yakeyi sai an fahimci wani abu..yarinya idan ma zaki shirya ki shirya don aiki ne gagarumi yake tunkaroki"..tana gama fadin haka ta fice daga dakin tana kyalkyala mata daria ita Kuma Aysha komawa da baya tayi ta zauna gefen gadon tareda dafe chest dinta idanu a waje sosai tace"na shiga uku ni Aisha..anya kuwa ba fasawa zanyi ba?.." Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 55 Cocktail Party... Karfe shidda da wani abu aka gama wa amarya make up dinta..tana sanye cikin gown na wani sky blue material..head dinta ma da akayi mata turban style blue sai su earrings da rings silver likewise takalmi da purse dinta..light simple make up da akayi mata ba karamin amsanta yayi ba dama ga lalle tasha red and black da suka sake haska pure white skin dinta...Billy ce ta shigo dakinda take cikin ankon da sukayi na dark blue material itama tayi kyau har ta gaji da haduwa..wayanta ne ya fara ringing ta koma gefen gado ta zauna ganin besty ke kira..daukan wayan tayi tana wani daure fuska kmr yana gabanta tace"besty what is it again?..why are u disturbing me?.."daga daya 6angaren Sa'eed ya saki murmushi yana shafa kanshi yace mata"wai yanxu besty har yanxun mgn bai wuce bane?..nace maki fa gobe zan taho inshaAllah"..sake 6ata rai tayi tana turo baki tace"amma ai ba gobe mukayi dakai zakazo ba yau kacemun zakazo"..yace"to nidai dan Allah kiyi hakuri..i promise idan nazo gobe bazan dawo kd ba har sai an kaiki gidan Proprietor".. murguda baki tayi tana cewa"dole kace haka dama ai..kuma idan bakazo gobe ba dena kulaka zanyi wlh"tana rufe baki yace"bazai ma kaimu ga haka ba Hajia besty amaryar Proprietor"..dan murmushi ta saki kafin suyi sallama abd jiranta da aka fara yi..tana gamawa ta mike make up artist ta sake gyara mata face dinta snn ta fito daga dakin hannunta rikeda purse dinta..qawayen ta dake zazzaune parlor suna ganin fitowarta suka saki ihu suna yaba irin kyawun da tayi..banda murmushi ba abunda take musu ganin kusan kowaccensu ta fito da waya tana daukan pictures..suna cikin daukan pics din Husna ta shigo parlon itama taci ado har ta gaji da haduwa..kallo daya zakayi mata ka gane sister din amarya ce sbd tsabar kyau da tayi..ta karaso ciki tana duban yanda suka wani baibayeta suna hotuna tace"Adda jiranku akeyi fa tun daxu..ga motoci can a waje duk ku suke jira"..da sauri suka karasa pictures dinsu suka fita..ko a wajen ma duk wanda ya kalli amarya saiya furta MashaAllah sbd tsabar haduwan da tayi..mota aka bude mata ta shiga sauran friends dinta ma suka shiga aka kwashesu zuwa hall da za'ayi event din..tun suna hanya Bobby ke kiranta tana gani bata dauka ba dan da gaske ita dai tsoro yake bata yanxun..haka nan ta dauki wayanshi yazo yana kunyatata a gaban qawayenta. Yau ma dai kamar jiya event yayi kyau sosai Kuma ya qayatar da mutane..idan kaga yanda Aysha ta dirki rawa bazakayi zaton she's the bride ba..da yake babu manya Kuma ba maza daga ita sai qawayenta sukasha sha'aninsu..pictures da video coverage yau ma sunyi su kmr ba gobe..inda Billy tana gama daukan nata ta turama Bobby da tun daxun yake sake jaddada mata ta turo mishi hoton amaryarshi ya gani...event yayi dadi sosai sunci sunsha Kuma sunyi rawa kmr yanda sukeso..Lamido ji take ko event din jiya bai Kai na yau yi mata dadi ba..sunsha sha'aninsu ne itada friends dinta abun ba'a cewa komai...a takaice basu bar wurin ba sai around 9 o'clock..kai tsaye ana daukansu gida aka wuce dasu kowacce jiki yayi laushi sbd rawan da sukayi. Yauma kmr jiya suna komawa gida ta sake yin wanka ta saka sleeping dress suma su Billy duk sun sauya kaya zuwa na bacci Wanda zasuyi wanka sunyi wanda baza suyi ba kuma sun wanke make up dinsu bayan sun rama sallolin da ake binsu..ta jona wayarta caji snn ta fita parlor inda sauran suke nan sukaita maida yanda akayi suna darawa abunsu...kusan raba dare sukayi suna labari a parlor sai wajen 1 suka mike kowa ta nemi makwancinta...tana daukan wayanta ta zare Ido ganin missed calls dinshi kusan 20 a wayar..komawa kan gado tayi da sauri ta zauna tana dialing number nashi..har ya kaste bai dauka ba tana shirin sake dialing kuma sai gashi ya kira..tana dauka tun ma tayi mgn ya shiga tambayarta inda taje ta bar wayarta haka..hakuri ta bashi tareda mishi bayanin ta fita parlor wayan kuma ta barshi daki yana caji..hira sosai suka shigayi irin na masoya Billy na kwance tana jinsu har bacci ya dauketa basu dena wayan nan ba inda yawanci hiran nasu bai wuce akan tahowa shima da zasuyi a gobe ba don dashi za'ayi Mother's Eve..daga nan zasu kwana Saturday bayan daurin aure zaa wuce mishi da amaryarshi..sosai yake farin cikin hakan sbd abunda yake hange daga nesa ne yake dab da karasowa kusa dashi...ga su Mummy suma da suketa faman shiri wai zasuyi traditional event dinsu na Igbo ranan da aka kawota..shi gaba daya ba son harkan events din nan yake ba wlh..a takaice Bobby bai kashe wayarshi ba saida yaji ta fara bacci snn ya saki smile tareda kashe wayar cikin ranshi yana ayyana very soon shima zata fara bacci a kusa dashi kilan ma a jikinshi..tunanin hakan da yayi saida yasa ya saki wani murmushi na musamman yana shafa gashin kanshi. Mother's Eve... Misalin karfe 12 da wani abu Mummy da jama'arta gaba daya suka sauka garin Gombe..gida guda Waziri yasa aka ware musu ita da 'yan uwanta da kuma sauran mutanenta..Aunty Sumy ma gayya guda tayi na kanta abunka da babbar yayar ango. A 6angaren oga Bobby kuma gida suma Waziri ya bashi ya sauka tareda abokanshi..duk yanda yaso Waziri ya bari suje hotel hanawa yayi yace dole saidai su zauna gidan daya basu tunda yanada girma zai daukesu gaba daya shi kuma basu gane ba hayaniya ne baiso shiyasa yaso suyi lodging a hotel tunda kowa separate room za'a kama mishi so babu wanda zai dameshi amma nan ko bai hada daki da kowa ba yasan dole zai hada da Nur da yakeda shegen tsokana da rawar kai kmr shine angon..shi duk randa akace yau ana auren Nur baisan irin giggiwar da zaiyi a matsayinshi na groom ba..gaskia idan haka ne Miemie ta shiga uku..kawai sai ya saki murmushi yana girgiza kai. Karfe shidda da wani abu suka gama shiryawa duk suka shiga motocinsu wasu suka fara tafia hall da za'ayi event din shi Kuma ango da some of friends dinshi irin su Nur suka tsaya gidan da zasuyi picking amarya..dama tun kafin zuwansu an kammala mata shirinta tayi kyau sosai cikin coffee lace dinta daketa walwali..daurinta yayi daidai dana amarya ga kuma gashin goshinta da aka sa musu gel akayi wani coiling dinsu suka kwanta luf a goshin nata..fuskanta na rufe da wani net da ake iya hango fuskan nata daga ciki..Billy ce ta fito da ita tareda walida cousin dinta..ita tana daga baya tana dage nata gown dinta dake jan kasa walida kuma na daga side dinta suna tafia a tare...tun daga cikin mota Bobby ke kallonta gabanshi har wani faduwa yayi sbd kyau da yaga tayi..she looks extremely gorgeous har baisan da wane kalma ma ya kamata ya danganta kyawun da tayi dashi ba..relaxing yana cigaba da kallonta hannunshi daya dafe da saitin heart dinshi da yaji fitowa zaiyi daga kirjinshi sbd mugun bugawar da yake...Nur dake zaune driver seat yana ganin sun fito ya fita daga motar da sauri yana kallonsu baki a washe yake fadin"MashaAllah Tabarakallah..Lamido kece kuwa?.."murmushi tayi tana sunne kai daidai lokacinda suka karaso wurin..Nur da kanshi ya bude mata baya inda Bobby ke zaune har yanxun yana dafe da zucia ta karasa a hankali ta shiga cikin motar kafin ya kulle kofa shima ya koma driver seat..Walida da Billy suka shiga motar Hamma Najeeb da bai dade da zuwa ba suka farayin gaba kafin shima Nur ya tada nashi motan su tafi...wani irin tsit cikin motar yayi yanda kasan babu wani abu mai rai da motsi a ciki..ga kuma kamshin perfumes dinsu da ya baibaye ko ina a cikin motar..ta mirror Nur ya kallesu yaga yanda har yanxun Bobby ke jingine jikin kujera ya wani lumshe ido ita kuma tayi kasa da kai tana wasa da purse dinta..murmushi ya saki yana girgiza kai cikin ranshi yace"strange couple"...har suka isa hall din babu wanda yayi mgn cikinsu..shidai Nur yana gama parking ya bude motar ya fita don ya basu space su dan tattauna before azo a shiga dasu ciki kuma..kmr abunda Bobby ke jira knn ya bude idon a hankali tareda karkatawa gaba daya yana kallonta...dagowa itama tayi ta kalleshi sai kuma ta saki murmushi tareda dauke kanta..a hankali ya matsa kusada ita tareda kai hannu ya yaye net da aka rufe face dinta dashi..nan take beautiful face dinta da yasha light make up ya bayyana..Bobby lumshe ido yayi ya furzar da iska kafin ya sake bude idanun a kanta..hannunshi yakai ya kamo nata da yasha red and black henna ya shiga shafa lallen a hankali yana kallonta..dagowa itama tayi tana kallonshi sai kuma ta kasa cigaba da kallon nashi sbd faduwar da gabanta yayi..idonshi taga yayi wani iri shiyasa bazata iya juran kallonsu a haka ba...hannun nata yakai bakinshi ya manna mishi peck a hankali kuma yana cigaba da kallonta yace"u look..."kasa karasawa yayi ya dago fuskan nata yana kallon eyeballs dinta yace"u look.. extraordinary..beautiful..kishi nakeji wasu su kalleki a haka"..hannunta takai itama tayi cupping nashi fuskan tana binshi da kallon da tasan bazai iya resisting ba tace"kayan hakuri it's just for today"..kai ya shiga gyada mata yana murmushi yace"yes.. it's only for today..daga gobe ana daura mana aure shknn u have become mine"..kai itama ta sake gyada mishi tana murmushi alaman yes..kasa hakura yayi saida ya janyota ya hadata da jikinshi sbd yanda yaji kmr fizgarshi akeyi zuwa gareta..hannu takai itama ta zagaye bayanshi dasu a tare suka sauke ajiyar zucia..voice dinshi na breaking yace mata"I..love..you"..lumshe ido tayi itama a hankali tace"I love u too"..dagota yayi daga jikinta yana sake kallon face dinta da har yanxu baiji zai iya gajiya da kallonta ba..itama kallonshi tayi sai taga ya kara haske yayi wani irin kyau da tunda take dashi bata ta6a ganin yayi mata kyau haka ba..shadda ne a jikinshi getzner sai sheqi yake milk colour da aikin coffee a jiki..hula da shoes dinshi suma duk coffee hatta links dinshi coffee colour ne..kallonshi kawai take tana sakin murmushi cikin ranta tana godia wa Allah daya mallaka mata such a handsome man as her hubby..he's looks so cute da har ta kasa dauke idanu a kanshi saida Nur yayi knocking musu kofa duk suka dawo hayyacinsu...bude kofar tayi da sauri ta fita don wani kunya da taji ya rufeta..shima ya bude side dinshi ya fito yana sakin murmushi dake sake fito da annurin face dinshi...su Billy da abokan ango ne sukayi arranging kansu suka sanya bride and groom a tsakiya snn aka sakar musu sauti suka fara shiga ciki...wajen ya cika ya tumbatsa da mutane ba daga brides family ba ba kuma groom's family ba dan suma sunzo da yawansu ne tamkar dama a Gomben suke da zama...tun da suka shigo idanun kowa ya dawo kansu kmr dai yanda ya saba kasancewa a every gidan biki amarya da ango na shigowa all attention yake komawa kansu..duk Wanda ya kallesu sai ya sake sbd tsabar haduwan da sukayi..hannunta na rike cikin nashi suke takawa a hankali ita kanta a kasa yayinda nashi kan ke daidai sai sakin murmushi yake..sunyi matukar dacewa da juna ne sosai ba kadan ba..hatta Mummy da Ammi da kowa take zaune inda aka tanadar mata tareda jama'arta kallon 'ya'yan nasu sukeyi full of love..they look so perfect together..they look takeaway kaman a daukesu a gudu..Lamido dai sake nutsuwa tayi na musamman sbd warning da Ammi ta kora mata wai idan ta kuskura tazo tayi mata rawar kai sai taci ubanta..wnn dalilin yasa ta sake nutsuwa tana takawa daidai har suka karasa inda aka tanada dominsu..bayan sun zauna bridesmaids dinta suma suka zauna a side din da aka tanadar musu likewise abokan ango..bayan sun zauna mc ya fara gabatar da surutanshi kmr dai yanda aka saba..aka bukaci bride and groom da su fito kan stage..tasowa sukayi a hankali Bobby na rike da hannunta suka fito stage din..maman amarya da ango aka bukaci da su fito su nunawa 'ya'yansu so..nan take Mummy da Ammi suka fito kowacce cikin shiganta na alfarma..yanda Ammi tayi kyau mutane da yawa sai sukayi mamakin wai ita ta haifi Aysha yayinda itama Mummy mutane da dama sunyi mamakin ganinta matsayin mahaifiyar Bobby sbd kyawun da tayi...Mummy tana zuwa batasan sanda ta rungume Aysha ba sbd farin ciki aikam wurin ya kaure da tafi da surutun mc..bayan nan sukayi musu watsin kudi snn suka koma..daya bayan daya ake Kiran mutane suna zuwa su watsa kudi su koma su Hajia Aunty Sumy da Aunty Munubiya dama sauran aunties dinshi na both familyn Mummy dana daddy duk sunyi ankonsu iri daya kuma sun taka rawar gani sosai...qawayen amarya su Billy suma ba'a barsu a baya ba sun taka rawar gani sosai sunsha liki suma tareda besty da bai dade da sauka ba...lokacin da aka fara rawa Aysha jikinta har rawa ya farayi sbd so take tayi amma idanun Ammi dake kanta sun hanata kata6us..ga kuma shi kanshi Bobbyn daya kama hannunta ya rike gam sbd gudun kada tace zata shiga tayi rawar don yasan halin kayanshi amma duk hakan bai yiwu ba don aunty Fiddausi da kanta tazo ta dauketa tace a ware musu fili zasuyi rawa aikam duk aka basu wuri dj ya saka musu waqa amma sbd kunya Aysha sai taji ta kasayin rawar kasancewar su biyu ne a wurin..kunyan su Mummy taji ya kamata don haka ta kasa zagewa tayi kaman yanda tayi jiya sai da su Billy suka shigo snn ta dan samu tayi tunda tasan ba ganinta za'ayi sosai ba..can su Aunty Sumy suma suka shigo sai kuma ga su Husna da Miemie da batasan yaushe suka zama qawaye ba..Yusra da Ilham suma duk inda sukayi suna tare don sosai suma suka rakashe a bikin Addah da Uncle Bobby..Ammi dai na zaune tana kallonsu tana daria wato ita dai Fiddausi har gobe bazata gane cewa ta girma ba knn...a fannin su Nur abokan ango suma ba'a barsu a baya ba dan sosai suka taka rawar gani a wurin mutane sai jinjina Kara irin nasu suke...lokacinda aka bukaci su fito suyi rawa Bobby yasha kallon rawa hadda na hauka wajen Friends din nashi especially Nur daya dage sosai yana dilliqar rawa shi ko kunyar students dinsu dake wurin ma baiyi..shi kuwa duk yanda akayi dashi kan yayi rawar kinyi yayi wai shi bai iya rawa ba saida aunty sumy tazo da kanta ta kama hannunshi ta shiga juyawa dashi kuma dukda hakan baiyi rawan da sukeso yayin ba...in summary dai taro yayi kyau Kuma yayi tsari sosai mutane sunci sunsha sun Kuma yi rawa yanda ya kamata..(kunsan dai duk bikin da ba'aci abinci anyi rawa ba bai amsa sunanshi biki ba). Sai kusan karfe karfe goma na dare aka tashi daga taron mutane kowa ya nemi motar da yazo ya shige ciki aka fara maidasu gida..su Mummy da ahalinta suma duk motocinsu suka shiga suka wuce gida yayinda Ilham da Miemie suka dage kan su saidai a barsu a nan tunda gobe daurin aure..Aunty Sumy batayi musu musu ba ta kyalesu tunda taga yanda jininsu ya hadu dasu Husna don haka ta wuce tareda alqawarin zata aiko Sab ya kawo musu kayansu na gobe. Nur na gama parking a kofar gidan uncle dinta ya juya yana kallon Bobby dake zaune baya yace"5 mins na baka kayi round up don na gaji so nake na huta"..harara Bobby ya watsa mashi kafin yace"ba dole ka gaji ba kaje ka dirki rawa kaman ba namiji ba"..banza Nur yayi dashi ya bude motar ya fita ya rage daga shi sai amaryarshi a ciki..a hankali ta dago tana kallonshi shima kallon nata yakeyi suna hada ido ya sakar mata smile dinshi mai kyau yace"I love you"..kai kawai take gyada mishi tana murmushi tama kasa cewa wani abu..kallonshi take kmr yanda yake kallonta..murya can kasa ta kira sunanshi"Partner"..ba tareda ya dauke idonshi a kanta ba yace"yes my partner"..hannu takai ta kama nashi hannayen tana kallon eyeballs dinshi tace"kayi kyau"..murmushi ya saki kafin yace"not as u baby..na tabbata ban kaiki kyau ba"..kallonshi kawai take ta kasa dena murmushi sbd farin ciki..Bobby ya lumshe Ido ya bude kafin ya sake matsawa kusada ita yana cewa"love gobe iyanxu kin zama matata na zama mijinki"..Kai ta sake gyadawa cikeda farin ciki..shi Kuma ya sake lumshe idonshi ya bude tareda daukan hands dinta ya dora chest dinshi har yanxun idanunshi a kanta yace"shknn daga gobe duk abunda naga dama zanyi maki and nobody will asked why?.."gyada kai ta sakeyi babu bakin mgn..shi kuma a hankali ya hada fuskanshi da nata before yacigaba da fadin"i can hold u to my arms..i can hug and kiss u baby..i can even..."bata bari ya karasa ba ta toshe bakin da hannayenta..kmr zatasa kuka tace"partner ba saika karasa ba plss..kunya nakeji"..murmushi ya saki yana girgiza kanshi yace"then kinada babban aiki a gabanki..a very huge one"..janye jikinta tayi daga nashi tana turo baki tace"kuma ni fasawa zanyi"..daria sosai Bobby ya saki tareda janyota ya rungume a jikinshi..soyayyarta yakeji na karuwa cikin heart dinshi fiye da yanda yakeji a baya..Allah kadai yasan yanda yakejin kmr ya janyo gobe sbd a daura mashi aure da ita ta zama property dinshi ko hankalinshi zai kwanta..itama lamo tayi a jikinshi ta lumshe tana shaqan daddadan qamshin da yake fitarwa..lokaci mai tsaho suka dauka a haka gaba daya sun manta da kowa da komai burinsu bai wuce su dawwama a haka ba har mahdi ya bayyana..gaba daya sabon son juna ke sake ratsa zukatansu abun kmr hadin baki..Nur da ya gaji da zaman jiransu a waje daddagewa yayi yayi knocking glass din window aikuwa firgigit suka dawo hayyacinsu Bobby ya raba jikinshi da nata a hankali yana kallon face dinta da tayi kasa dashi tana murmushi...bude kofa Nur yayi tareda lekowa tana kallonsu kmr zaisa musu kuka yace"Lamido a sakar mana shi haka mu wuce dan Allah..wlh na gaji so nake in samu in huta"..kai kawai ta iya gyada mishi tana kokarin kwace kanta a hannunshi amma yaki sakinta..daga Ido tayi tana kallonshi shi kuma ya lumshe Ido tareda pecking forehead dinta snn ya saketa yana cigaba da kallonta with a bright smile yace"good night wife"..juyawa tayi ta fita daga motar da sauri har tana hadawa da gudu. Wedding Fatiha... Tun safe both bangarori suka fara shirin daurin aure da za'ayi 11 na safe a nan cikin Lamido's Palace..Bobby har nafilah saida yayi na nuna godia wa Allah for witnessing wnn ranar in his life and for praying Allah ya basu zaman lafia da zuri'a nagari..ya roki Allah ya bashi ikon riketa Amana ya kuma bashi damar kulawa da ita iyakar karfinshi..addu'a yayi musu sosai yana idarwa kuma ya fada bathroom yayi wanka snn yazo ya fara shiryawa..some of abokanshi da suke tare dashi sai tsokanarshi wai ya cika zumudi shikam saidai yayi murmushi kawai sbd yasan bazasu ta6a ganewa ba..bazasu fahimci abunda yakeji gameda yarinyar ba shiyasa duk suke wnn surutan. A gidan Waziri ma sun gama shiryawa tsaf Waziri da kaf yayanshi maza da 'ya'yan 'yan uwanshi da abokanshi dana yaran nashi kai har ma da jikoki duk sun hallara a gidanshi lokaci kawai suke jira su tafi inda za'ayi daurin auren. Su Mummy ma suna gida suna nasu shirin don a yau zasu wuce da amarya kano zuwa da yamma suma zasuyi igbo day dinsu a can. A can gidansu Aysha ma shiri sukeyi sosai tun daga kan daddy da sauran 'yan uwa da abokan arziki har zuwa kan Lamido da nashi mutanen shima sai kuma Hajia Ammi da familynta..sosai suke shiri don tun yanxu Estate din nasu ya fara cika da mutane from different angles na Nigeria..manya manyan mutane suna nan da yawa wasu jama'ar daddy ne wasu kuma jama'ar Lamido. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 56 Karfe Sha daya da 'yan mintina dubban mutane suka shaida daurin auren Attahir Attahir Waziri(Bobby)da kuma Aysha Ahmad Lamido akan mafi karancin sadaki kaman yanda addinin musulunchi ya tanadar...jama'a sosai ta ko ina Estate din ya cika fal tun daga gidan Lamido har zuwa ciki wajen gidan su Aysha mutane ne keta 6ullowa ta ko ina...ango Bobby tunda yaji anyi sanarwar aure ya dauru tsakaninsu shaidu sun shaida kuma an shafa fatiha sai yaji wani irin nustuwa mai hade da kwanciyar hankali sun sauka a zuciarshi..wani irin feeling yakeji irin na wanda ya samu cikar burinshi bayan yasha wahala...mutane sai zuwa suke suna congratulating dinshi dukda hayaniya dake tashi a wurin ga masu algaita suma da suketa faman busa tun kafin a fara daurin auren...a nan cikin Estate din sukayi reception daga nan kuma suka shiga cikin gida don gaisawa da iyaye..har suka gama gaisuwan suka bar gidan Bobby baiga matarshi ba duk sai yaji hankalinshi ya tafi wurinta burinshi kawai ya sanyata a Idonshi..har sun shiga mota zasu koma can gidan dasu Mummy suke don suna can suna jiran dawowarsu wai za'ayi pictures kasa hakura yayi ya shiga Kiran wayanta amma bata dauka ba dan haka kai tsaye yace ma Nur ya kaishi gidan uncle dinta tunda yasan a can take kwana..kallonshi Nur yayi da mamaki yace"seriously..su Mummy na gida suna jiranmu fa snn ga abokanmu da suka fara wucewa can me kakeso muce musu idan suka rigamu zuwa?.."kama hannunshi Bobby yayi suka dan koma gefe ya wani marairaice kmr ba ango ba yace"Nur try and understand mana..zuwa fa kawai zamuyi mu ganta da gaske ba dadewa zamuyi ba"..ajiyar zucia Nur ya sauke tareda komawa ya sallami wasu daga friends dinsu dake jiransu snn ya dawo tareda wasu suka shishshiga mota zuwa gidan uncle din nata gaba dayansu...a kofar gida yayi parking snn ya sake kiran wayanta ganin bata dauka ba ya kira na Billy..sukayi sa'a kuma ta dauka nan yake fada mata sunzo suna kofar gida..wani irin ihu da yaji sun saki ya tabbatar mishi a hands free ta sakashi knn...walida ce ta fito tayi musu iso har cikin parlor..Lamido na zaune sun wani sanyata tsakiya fuskanta a rufe kmr wanda take yin kuka..hankalinshi yaji ya tashi badai yarinyar nan kuka take ba..ganin ya nufo inda take direct duk sauran mutanen da suka zagayeta suka mike daga wurin Bobby na isa ya mikar da ita tsaye kawai ya rungumeta tareda lumshe ido hawaye farin ciki na ciko idanunshi..he can't believe yau shi aka daurama aure da Lamido..rungumeshi tayi itama sosai tana hawaye sosai kmr Wanda akama auren dole..tunda taji an daura aure jikinta yayi wani irin sanyi data tuna shknn fa yanxu gidansu zata bari gaba daya..tafia zatayi ta bar su Ammi da daddy da Husna da Yusra?..oh Allah ashe haka auren yake?..dukda ta saba tafia ta barsu idan zataje makaranta amma wnn tafian yana da bambanci da Wanda ta sabayi a baya...tafi ta sowar da occupants din wurin suke shi ya dawo dasu hayyacinsu..a hankali ya dagota daga jikinshi yana share mata hawaye gamida girgiza mata kai alamar she should stop..sake 6are baki tayi zata dora daga inda ta tsaya kawai ya hade fuskanshi da nata yana mgn a hankali yace"baby stop..crying..mana"..lumshe ido tayi tana kokarin maida hawayen da suka kasa tsaiwa idanunta..hotuna da videos dai sun shasu a wurin jama'ar dake wurin kowa kokari takeyi ta samu na sawa a status..a takaice dai haka akayi pictures din da za'ayi musu Aysha bata dena kuka ba shi kuma angon nata bai dena aikin lallashi ba..kasa ma tafia yayi wai bata dena kuka ba saida Nur yayi da gaske snn ya samu ya wuce suka tafi..gidan Waziri suka fara zuwa nan ma sukasha hotuna tareda Waziri da uncles dinshi daga nan kuma sukayi can gida inda su Mummy suma suka dora daga inda suka tsaya..karfe biyu da wani abu suka fara shirin tafia kano Wanda zasu dauko amarya already dama sun tafi tun daxun don haka wucewa kawai zasuyi daga nan. Wata qanwar daddy ce tazo har gidan da suke ta shiga da ita bathroom bayan ta hada mata ruwan wanka full of turaruka tace tayi maza tayi wanka ta fito...tana kuka sosai ta shiga tayo wankan ta fito daidai lokacin kuma Aunty Fiddausi ta kawo mata kayan da zata saka suma bayan an gama turarasu..har zuwa lokacin bata bar kuka ba haka suka hada kai suka gama shiryawa tsaf qanwar daddy mai suna Aunty Amina ta nada mata farin laffaya daya amshi jikinta sosai..daga nan kuma suka kama hannunta suka fita tareda some of friends da cousins dinta da za'a tafi kai amaryan dasu...gidansu aka fara kaita daddy da Ammi sukayi mata nasiha sosai tareda yi mata fatan samun dawwamammen farin ciki a gidan aurenta..daga haka daddy yace su kaita wajen Lamido..Aysha dake kuka wiwi zuwa tayi ta rungume Ammi tana Kara sakin wani kukan kmr dai mutuwa zatayi ta barsu..duk karfin hali irin na Ammi saida ta zubda hawaye itama..ko Allah yasan ba karamin kewar 'yarta zatayi ba amma ya zasuyi?..haka gadonmu yake domin kowacce mace saita dandani wnn zafin na rabuwa da iyaye yayin da zata tafi dakin miji..har su Husna da Yusra kuka suke sosai Billy na tayasu..abun sai ya zama kmr a gidan mutuwa ba gidan biki ba..Saida daddy yayi da gaske snn suka iya 6an6areta daga jikin Ammi sukayi gidan Lamido da ita..ko cikin mota bata dena kuka ba har suka isa gidan Lamido..nan ma cike yake da uncles dinta haka suka dangana da ita har kusa da Lamido snn suma suka zauna..nasiha ya shiga mata shima sosai duk kan zaman aure da rayuwar gidan miji..bayan ya gama wasu daga cikin uncles dinta suma sukayi nasu daga nan kuma aka sake daukanta zuwa wajen wadanda sukazo daukanta suke..tana kuka sosai aka bude back seat ta shiga ciki tareda aunty Fiddausi da Aunty Amina da suka sanyata a tsakiya Billy kuma na front seat driver ya tada motar suka tafi..da akwai wasu motocin guda biyu daya na cousins dinta da wasu daga friends dinta dayan kuma duk yan uwan daddy da Ammi ne zasuje sbd event din da za'ayi a can Kano. Gidan Waziri aka fara kaita nan ma Waziri ya hadasu tareda Bobbyn yayi musu nasiha sosai daga nan kuma kai tsaye suka wuce Kano don su Mummy already sun dauki hanya tun daxun..shima Bobby daga nan gidan suka shiga motocinsu suka tafi tareda zugar abokai da coworkers dinshi..ko a hanya duk tunaninshi ya koma kanta ne..yanda yaga take kuka daxun abun ba karamin daga hankalinshi yayi ba..wai shi wnn kukan dole ne sai anyishi ko kuwa nata ne dai ya wuce gona da iri?..duk hankalinshi yaji ya koma gareta so yake kawai yaji dalilin wnn uban kukan da take. Karfe biyar da wasu minutes suka shigo garin Kano..har zuwa yanxun amarya Aysha bata dena kuka ba..face dinta har ya kumbura eyes dinta sunyi jajir sbd kukan da taci...direct gidan su Bobby aka wuce da ita inda su Mummy da suka rigasu sauka sun shirya tsaf domin welcoming amarya..ana shigo da ita wasu sisters din Mummy guda biyu suka mike tareda kama hannunta har zuwa parlon Mummy..nan ma yana cike da mutane wanda yawancinsu duk yan uwan Mummy ne da qawayenta..bedroom suka wuce da ita tareda sauran mutanen da sukazo tare...nan da nan sai bedroom din ta cika taf da mutane masu son ganin amarya..saida suka gama turereniyarsu snn aunty sumy ta kwashi su Aunty Fiddausi da sauran wanda sukazo tareda zuwa flat dinta da akayi musu masauki a can..ita kuma amarya sai aka barta tareda Billy da Walida a flat din Mummy..suna fita Billy ta matsa kusada ita tareda bude fuskanta dake rufe da lafayan jikinta..fuskan taga ya kumbura suntum likewise eyes dinta sbd tsabar kuka..dan langabewa tayi tana kallonta tace"yanxu Lamido bazaki dena wnn kukan ba?..haka kikeso kije wurin event din fuska a kumbure?.."banza Aysha tayi da ita tanajin kmr ta Kara sakin wani kukan..bazasu gane ba ita kadai tasan what she's going through right now..ji take kmr tace itadai ta fasa a maidata gaban iyayenta amma akace it's too late to cry when the head is cut off...matsowa walida tayi kusa dasu tace"ki rabu da ita Billy kilan so take mijin nata idan ya ganta yace batayi mishi kyau ba da kumburarren fuska"..wani harara ta maka mata kmr ba itace ke kuka a while ago ba nan take Billy da Walida suka hada ido tareda kwashewa da daria..ringing din wayar Billy ne ya dawo dasu hayyacinsu..tana ganin wanda ke kira tayi daurin dauka tana sakin wani murmushi tace"ango ango ango"..murmushi Bobby ya saki on the other side yana shafa gashin kanshi yace"pls are u together with her?..i have been calling her bata answering kuma i really want to know how she's doing..is she still crying?.."murmushi Billy ta Kara saki tana kallon Lamido data wani lafe kan gado tana sauke ajiyar zucia tace"Sir taki dena kukan nan har yanxu wlh..tun daga Gombe take abu daya gashi har munzo Kano bata dena ba..bakaga yanda face da eyes dinta suka kumbura ba"..lumshe Ido Bobby yayi yana sauraron abunda take cewa before yace"u mean har yanxu kuka takeyi?.."Billy tace"kuka takeyi wlh..gashi anjima kadan za'ayi wani event din kaga ai bai kamata aga face din amarya kumbure ba"..yace"ohk ki bata wayan idan kuna tare"..ba musu Billy ta mika mata wayan tana cewa"mijinki"..amsan wayan tayi ta Kara a kunnenta ba tareda tace komai ba..Bobby da yaji saukar breathe dinta cikin wayan yasan ta kar6a mgn ne kawai baza tayi mishi ba..murya can kasa yace mata"so kin dena kaunata right?.."girgiza kanta tayi tana wani turo baki tace"No"..yace"then why are u still crying?..bakiso hankalina ya kwanta ne?.."nan ma kai ta sake girgiza mishi hawayen na sake ciko idanunta tace"kawai am missing home..Ina missing Ammi da kowa da kowa"..a hankali ya sake cewa"I know baby..nasan da ciwo amma try not to cry again please!..for me"gyada kai ta shiga yi kmr yana ganinta tace"na dena"..ya dan saki murmushi before saying"to nagode love..i can't wait to..."bata bari ya karasa ba Kitt ta kashe wayar tareda mikawa Billy tana wani turo baki..tun kafin ya karasa dama tasan me zai fada so bazata tsaya ta saurareshi ba..shi baisan halinda take ciki bane da zai dinga damunta da irin wnn maganganun. Suna idar da sallahn isha'i aka shiryata cikin traditional Igbo attire daya matukar amsanta..shima Bobby shiryawa yayi cikin igbo attire sak irin nata..kyawunshi sai ya Kara fitowa sosai cikin kayan Aysha daketa kallonshi ta kasan idonta sai taga kaman bashi ba..ya koma mata inyamurin Proprietor dinsu sak masifaffen nan mai shegen takura mata...shima a nashi 6angaren yana dora idanunshi a kanta yaji komai nashi ya kwance..he was like Tabarakallah MashaAllah Alhamdulillah..gani yake duk dunia ba namijin daya kaishi dacewa da auran mace kyakykyawa kamarta..she is the real definition of beauty..yanxun kuma daya ganta cikin wnn dress sai yaji kaman yaje ya dauketa yayita juyi da ita sbd farin ciki..she looks so cute..so takeaway kmr yanda itama take ganin yama fita yin kyau...a nan compound din gidansu za'ayi dakeda haske sosai za'ayi event din don yanda wurin yakeda haske tamkar ba dare ba...anyi decorating wurin komai irin na inyamurai haka kuma duk jama'a dake wurin sanye suke cikin igbo wrapper da akayi ma dinkin boubou da zani kowa ta daura zanin kan riga bayan an dageshi can sama kmr dai yanda inyamuran na asali sukeyi..su Mummy Kalan nasu daban itada sauran manyan wajen dasu aunty sumy yayinda su kuma su Billy,Miemie,Husna,Yusra,Ilham,walida da duk sauran Yara da yammatan dake wurin suma nasu iri daya ne..a takaice duk wanda yazo Sai an bashi irin wnn dress yasaka snn zai shigo wurin..suma su Nur suna sanye da nasu kayan duk na inyamurai sun sanya ango a tsakiya...wata cousin din Mummy ce tazo ta kama hannun ango zuwa inda aka tsayar da Aysha don a tare akeso su shigo filin...tana zuwa ta kama hannunta ta saka cikin nashi snn tayi mishi rada a kunne taja baya tana kallonsu...zame hannunshi yayi daga cikin nata a hankali tareda zagayawa da hannun zuwa wait dinta ya tallafota a jikinshi sosai snn suka shiga takawa a hankali zuwa cikin filin...kida sosai aka sakar musu yayinda occupants din wurin keta tafa musu don abun ya burgesu ne sosai...Aysha da takejinta uncomfortable sbd kama waist dinta da yayi a hankali takai hannu zata cire hannun nashi daga jikinta shi kuma ya sake matse waist din nata yanda ba yanda zatayi ta zame hannun ba tareda mutane sun lura ba..dan bata rai tayi kanta a kasa tace mishi"partner let go mana.. people are watching"..murmushi ya saki mai kyau tareda Dan matsar da bakinshi saitin ears dinta yanda zata jishi sbd tsayi daya fita sosai yace"let the people watch mana ai it's not haraam..besides haka al'adan event din yake..dolene groom yayi holding bride dinshi to himself idan ba haka ba za'a ce he's not romantic ni kuma nasan am super romantic so bazan yadda mutane suyimin kallon am not romantic ba"..dan daga kai tayi ta kalleshi tana mishi puppy eyes shi kuma ya lumshe Ido tareda pecking eyes din nata aikuwa mutane suka kaure da ihu da tafi abun ya burgesu..su aunty Fiddausi da sauran yan uwan Aysha dai abun har kunya ma ya basu while yan uwan Ammi inyamurai abun ya kayatar dasu sosai..su a wurin su wnn ba wani abu bane groom yayi pecking bride dinshi ranar traditional event..infact ko kissing dinta zaiyi su bazasu ga wani abu ba tunda kusan al'ada ne hakan shiyasa duk musulman cikinsu basu cikayin traditional event din ba sai bayan daurin aure...bayan sun isa inda aka tanadar musu sun zauna ko hutawa basuy ba aka bukaci ganinsu a fili wai zasu taka rawa..haka nan suka sake fitowa suka tsaya a floor din yayinda aka saka musu traditional song shidai yana rike da hannayenta yana dan moving legs dinshi a hankali don bai wani iya rawa ba shikam..Mummy ce ta fara fitowa tazo tana musu watsin kudi daga nan kuma duk sauran yan uwanta suka fara tasowa suma..bayan sun gama Yan uwan amarya suma suka fito daga nan kuma sai abokai da kawaye..Bobby daga nan inda yake yana hango yanda Nur yaje yasa Miemie a kwana sai zuba mata rawar kai yake...murmushi kawai yayi yana girgiza kai cikin zuciarshi fadi yake"Allahumma yahdika Nur". A takaice taro yayi kyau kuma ya bada ma'ana matuka..amarya tasha gaisuwa da runguma a wajen sisters din Mummy dashi kanshi angon nata don ba ko kunya yake rungumeta gaban uban jama'ar dake wajen...karfe goma da kusan rabi suka tashi masu tafia gida suka tafi Wanda zasu kwana a gidan kuma kowa ya nemi makwanci...amarya tana flat din Mummy tareda su Billy yayinda su Aunty Fiddausi da sauran wanda suka rakota suke flat din aunty sumy zuwa da safe wasu zasu fara yin gaba saura kuma zasu bari har yamma su mika amarya dakinta snn su wuce...Bobby a ranar shima sai barin gidan yayi sbd yanda yake cike da jama'a Kai tsaye gidansu Nur suka wuce daga shi sai Nur din don sauran abokanshi duk a Kano suke so ana tashi kowa ya kama gabansa..suna hanya Nur time to time yake juyawa yana kallon yanda yayi relaxing jikin kujera ya wani lumshe ido yayi tsit kmr yana tunani...murmushin iskanci ya saki daidai lokacin da suka karaso cikin gidansu yace"gaskia su Mummy basu kyauta ba..taya zasu bar fresh ango kamarka ya kwana dakin tuzuru kaman ba yau aka daura maka aure ba"..banza Bobby yayi dashi dan a yanxu ba lokacin rigima ne dashi ba...sake murmusawa Nur yayi bayan ya gama parking motar yace"shawaran da zan baka kawai kayi sneaking kaje har inda take ka sameta don Allah ya gani ba abun farin ciki bane ango kamarka yayi spending first night dinshi ba tareda amarya ba"..wani kallo da Bobby ya watsa mashi baisan lokacinda ya kwashe da daria ba hadda dukan starring...Saida yayi me isarshi snn ya dan tsagaita yana cigaba da binshi da kallon da kana gani zakasan na tsokana ne yace"C'mon Bob wnn hararan fa?..am only trying to be of help don nidai Allah ya sani bazan iya kwana randa aka dauramin aure ba tareda amarya ba..hauka ma akeyi knn"..ya karasa mgn yana shafa kai gami da sakin murmushi...murmushi shima Bobbyn ya saki tareda dagowa yana kallonshi da kyau yace"don't worry badai ni kakema wnn iskancin ba?..bari muga wanda zai shige maka gaba a neman auren Miemie..wlh idan kayi wasa da kaina zan cema babanta kar ya kuskura ya baka aurenta tunda dan iska ne Kai"..ai tun bai rufe baki ba Nur ya koma kalar tausayi yana cewa"gaba Bob wnn ai mugunta ne..nidai kayi hakuri wasa nake maka wlh..idan ma so kake inje in dauko maka Lamido i can do that amma kar kace zakasa a hanani aurenta pls..inasonta sosai wlh"..daria shima Bobbyn ya kwashe da ita tareda bude motar ya fita..Nur ya bi bayanshi da sauri yana cewa"Bob please mana..plss I love her". Washegari tun safe su Aunty Fiddausi suka shiga gidan amarya dake nan kusada gidan nasu suka gyara mata shi tsaf..suka kumayi duk wani necessary abu da gidan ke bukata daga nan kuma da yawa daga cikin Wanda suka rakota suka wuce Gombe aka bar iyaka Aunty Fiddausi da Aunty Amina sai walida da Billy. Karfe hudu aka gama shiryata tsaf aka sake nadeta da wani lafayan snn aka kaita wajen su Mummy sukayi mata nasiha daga nan kuma aka bude kofar shiga gidan nata dake nan cikin gidan suka nufi can da ita...abun mamakin shine har yanxu Hajia indo bata bar kuka ba kmr dai yauma daga Gomben aka daukota aka sake zuwa Kano da ita...suna rike da hannunta har kofar gidan Aunty Amina tace tayi Bismillah snn ta shiga da kafar dama..ba musu tayi hakan snn suka shiga zuwa ciki.. compound din yanada girma sosai dukda baikai na asalim gidansu girma ba shima yanada girma ba laifi...a hankali suje tafia har sukazo entrance nan ma aka sake cewa tayi Bismillah da shiga da kafar dama snn suka shiga cikin parlor..basu ajiyeta ko ina ba sai one of bedrooms dinta dasu Billy ke ciki suka zaunar da ita kan gadon bayan sun sake mata nasiha sosai suka bar gidan sbd gudun kar ango yazo ya riskesu a dakin amaryarshi...daga ita sai Billy da Walida aka bari..Billy ta matsa kusada ita tareda bude face dinta tana kallonta with murmushi tace"har yanxu dai kukan kike Lamido?.."banza tayi mata tareda mikewa ta ware lafayan dake jikinta ta nufi wani kofa datake zargin bathroom ne..bayan few minutes ta fito sai kuma ta tsaya daga nan kofar bathroom din ta kama kugu ta shiga karema dakin kallo...walida da Billy suka hada ido kafin walida tace"zo muje kiga gidan naki da kyau"..girgiza Kai tayi still tana rikeda kugunta tace"mutane zasu iya shigowa"..da sauri Billy tace"aah ba wanda zai shigo wlh ai tun daxu sukazo suka gama ganin gidan..shi kuma angon ki nasan sai after magrib zai shigo so let's use this opportunity ki karema gidanki kallo sosai"...dan murmushi ta saki jin abunda Billy ta fada sai Kuma ta daga kafada tareda fadin"ohk"..daga haka suka fita daga bedroom din..sauran bedrooms dinta guda biyu suka fara shiga ta gama gani snn suka dawo parlor daga nan Kuma sukayi kitchen...sbd tsabar mamaki ma kasa cewa wani abu tayi don gidan yayi mata kyau ne fiyeda yanda take zato..hakika daddy da Ammi sunyi kokari sosai wajen zuba mata abun arziki a gidanta kaman yanda shima mijin nata yayi kokari matuka wajen tamfatsa mata gida mai kyau da tsaruwa kmr wnn..she just fell in love with the house har batasan lokacinda dan guntun damuwan da take ciki yayi disappearing ba..zagaya gidan sukayi sosai ko wane lungu da saqo Saida suka shiga ta kalli abunta snn suka wuce flat dinshi..walida ta kama handle din kofa zata bude Aysha tayi saurin tareta tana cewa"babu Wanda zai shigan min 6angaren miji"..wara ido Billy tayi tana dubanta tace"to mun rigaki ganin 6angaren mijin naki ma"..tace"eh ai lokacin bana nan amma yanxu da nake nan ba wanda zai sake bari ya shigar mata 6angarenshi..haka nan kowa ya gane mana sirrinmu"..daria Billy ta saki kafin tace"kinada gaskia Kam..wnn sirrin ai tsakaninki dashi ne and nan da anjima kadan sirrin zai fara aiki so bai kamata mu shiga ba"..daria ta Kara saki walida na tayata...ita Kuma Aysha sai jikinta yayi wani sanyi qalau tunawa da gagarumi aikin dake gabanta da tayi...yanxu fa mgnr Billy gaskia ne Koh..yanxu babu kunya sai mutumin nn yazo yace zaiyi mata wani abu Koh..kai amma ai da kunya..to ta Ina ma za'a fara ne Kam?..duk jikinta a sanyaye ta bar jikin kofar tareda komawa parlor ta zauna ta zuba uban tagumi kmr marainiya..ya zatayi da al'amarin nan ne wai?. Karfe takwas daidai motan Nur ya shigo gidan tareda Bobby daya kasa dena daria tun daxu..he is just smiling kmr mara hankali..gani yake no man is as happy as he is right now..he is super duper happy..he just can't believe yau shine zai kwana gida daya..daki daya kuma gado daya da love of his life..oh Allah what a blessing!..what a happy moment!..it's like a dream come true..the long awaited day has come. Yeeepeee💃🏻🥳💃🏻🥳💃🏻🥳 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 57 Da sallama suka shiga parlon daya cika da qamshi sbd turaren wuta dasu Billy suka saka..suna nan zaune cikin parlon Aysha da face dinta ke lullu6e da lafaya tana zaune tsakiyarsu..saida gabanta yayi wani irin faduwa sakamakon qamshin perfume dinshi da taji..dukda bataji voice dinshi ba don Nur kadai ne yayi sallama amma tasan tare suke sbd wnn qamshin nashi daya cika wurin...a nuste suka karasa ciki suka zauna Nur yana kallonta da fara'a sosai yace"amarya bakya laifi"..sunne kanta ta sakeyi ba bakin mgn..Billy dake kallonsu da murmushi itama tace"sannunku da zuwa sir..ina yini"..yace"lafia Lau..ya hidiman biki"..tace"Alhamdulillah"..walida ma ta gaisheshi ya amsa Bobby dai yana zaune sai kallonsu yakeyi kmr mutum mutumi..da zasu gane da barin wnn gaishe gaishen nasu sukayi suka fara gamawa dashi don Allah ya sani so yake su tafi su barshi da matarshi...Nur dake ankare dashi sarai yasan abunda yake saqawa cikin ranshi shiyasa duk ya sallami abokansu wai ba sai sun rakashi wajen amarya ba..shima Nur din dan ba yanda zaiyi dashi ne amma da shi kadanshi zai taho wlh...gyaran murya yayi tareda Bismillah kaman wani malami snn ya shiga musu nasiha kmr yanda aka saba idan an raka ango gidanshi ba'a tashi sai an dan yi musu nasiha ko yayane...kallonshi kawai Bobby yake yanda ya dage shi bai yadda ba fada yake musu abun sai ya bashi daria ma wlh..wai Nur ne yau da wa'azi kmr mutumin kwarai...Saida ya gama surutu da zolayarshi snn ya mike yana yima Bobby wani kallon kasan Ido yace"to ango mu zamu wuce..Allah ya baku zaman lafia da zuri'a na gari"..kai kawai Bobby ya gyada mishi yana murmushi..su Billy suma mikewa sukayi walida ta koma bedroom ta dauko musu bags dinsu Nur ya kama hanya zai fita Bobby na bayanshi..su Billy ma sun juya zasu tafi Lamido ta riko hannunta da sauri tana sakin kuka..da sauri Bobby ya dawo cikin parlon yana kallon yanda ta kwakwume hannun Billy yace"partner ki saketa mana..ai ba Bauchi zata wuce yanxu ba"..banza tayi mishi tacigaba da kukanta..Nur dake kallonsu ya fashe da daria yana cewa"wlh dole kiji tsoro Lamido..ni kaina zuwa yanxu tsoron mijin nan naki nake balle ke"..harara Bobby ya watsa mashi tareda karasawa inda take ya janye hannunta a hankali Billy dake daria tayi saurin kama hannun walida suka fita daga parlon suna daria..Nur dai na tsaye yana wani kallonsu yana murmushi Bobby yazo ya jashi shima suka fita kofar parlon yana binshi da wani kallo yace"oya go saida safe"..murmushi Nur ya Kara saki yace"dole kace saida safe mana.. anyways Allah ya baku zaman lafia mai dorewa..Allah kuma yasa kayi mata ciki a yau din nan"..tun kafin ya karasa Bobby ya tunkudashi tareda komawa cikin gidan ya rufe kofarshi..Nur ba karamin dan iska bane wlh..wai Allah yasa yayi mata ciki..yana dawowa parlon ya sameta zaune nan inda ya barta har yanxun kuma bata dena kuka ba..da sauri ya karasa ciki ya zauna kusada ita baice mata kala ba kawai sai ji tayi ya dauketa cak ya dora akan cinyarshi tareda rungumeta ga jikinshi sosai..tureshi ta farayi tana turo baki tace"ni ka saukeni banaso"..hannu yakai ya bude fuskanta da yake lullu6e ya tusrama face din nata ido yana kallo kmr ba gobe..wani irin nutsuwa da kwanciyar hankali suka saukar mashi..a hankali ya hade fuskanshi da nata tareda cupping fuskar nata da hannayenshi yana kallon eyeballs dinta yace"welcome..to your house..Mrs Bobby"..lumshe idanunta tayi tana sake turo baki ga gabanta sai faduwa yake..murmushi ya saki mai kyau tareda sunkuyawa a hankali yayi brushing lips dinshi akan nata for like 3 secs snn ya janye yana sake rungumeta sosai a jikinshi...Aysha dai tsuru tayi tana rarraba ido don Allah ya gani ba karamin tsorta tayi da yanayinshi ba..yanxu ya zatayi ta fitar da kanta daga wnn cakwakiyar ne?..wani tunani ne yazo mata kuma tayi na'am dashi dan haka bata sake yunkurin kwace kanta daga jikinshi saima Kara lafewa da tayi tana lumshe Ido..lokaci mai tsaho suka dauka a haka shima idanunshi na lumshe banda Hamdala da godia wa ubangiji ba abunda yakeyi a cikin zuciyarshi..a hankali yayi breaking hug din bayan yayi pecking forehead dinta ya sake daukanta cak zuwa flat dinshi..ita da idanunta na kulle ne har suka shigo parlonshi...dan bude idon tayi a sace ta shiga karema parlon nashi kallo shima yayi mata kyau sosai daga nan Kuma ya wuce bedroom dinshi..yana shiga ya direta a kasa tareda kama lafayan dake jikinta ya warwareshi ya ajiye akan gado sai kuma ya shiga karema jikinta kallo riga da skirt din jikinta sunyi mata kyau ne sosai kuma sun amshi jikin nata..sake karasawa yayi yayi hugging dinta yana dan rocking dinsu a hankali ya sake ce mata"Mrs Bobby"..nan ma dai shiru ta sakeyi ba bakin mgn shi kuma ya sake matseta jikinshi yakai bakinshi daidai kunnenta kafin yace"matar Bobby talk to me mana..what happened to ur mouth?.."makale shoulder dinta tayi alaman she won't say a thing shima bai sake takura mata ba ya ajiyeta nan gefen bed dinshi snn ya shiga bathroom..alwala yayi ya fito snn itama yace ta shiga tayi alwala zasuyi sallah..ba musu ta shiga bathroom din itama tayi alwala ta fito..ya dauko lafayanta daya ajiye kan bed ya yafa matashi kmr hijab snn ya shimfida musu praying carpet suka tada sallah...raka'ah biyu sukayi tareda addu'o'i sosai na samun zaman lafia da kwanciyar hankali mai dorewa da kuma zuri'a mai albarka..sun dauki almost ten minutes Bobby nata kwararo addu'a kafin ya idar..yana mikewa itama ta mike tana dan kallonshi kasa kasa tace"zan..je..dakina"..murmushi ya sakar mata bayan ya mayar da praying carpets din inda suke ya kama hannunta suka fita daga dakin..main parlor suka dawo ya dauki ledan da suka shigo dashi suka karasa zuwa dinning..da kanshi yaja mata seat ta zauna shima ya zauna kusada ita snn ya bude ledan..kaza ne a ciki da yaji kayan lambu sai qamshi yake sai Kuma fresh milk mai sanyi..mikewa yayi zuwa kitchen ya dauko plate da cup snn ya sake dawowa ya zauna yayi serving dinsu..itadai tana zaune tana kallonshi batada bakin mgn...bayan ya gama da kanshi ya shiga feeding dinta tana tun nokewa ita bazata ci ba har dai ta hakura ta danci Wanda zataci don tasan ba saurara mata zaiyi ba idan ba cin tayi ba..ya dauki fresh milk din shima ya bata a baki tasha dan kadan tace ya isheta snn ya daidaita saitin inda tasa bakinta shima yasa nashi bakin a wurin ya karasa shanye Wanda ta rage..suna hada ido ta wani dauke kai tana turo baki shi kuma ya kashe mata ido daya yana murmushi...Kazan yaci dan kadan shima snn yasa sauran a fridge ya maida plate da cup din kitchen snn ya sake kama hannunta suka bar dinning din..ganin hanyar bedrooms dinta suka nufa har wani ajiyar zucia ta sauke shidai baice mata komai ba har suka shiga dakinda aka ajiyeta daxu..direct closet dinta ya bude ya shiga yana duba kayan da zai dauka mata na bacci bai gani ba dan haka ya fito zuwa inda aka jere boxes din lefenta ya shiga budesu har yaci karo da wanda ke cike da undies da sleeping dress ya dauki box din gaba daya snn ya sake kama hannunta suka koma flat dinshi..ajiye box din yayi a kasa snn ya zauna zai fara bude box din yaga yanda tayi wani tsaye a gabanshi tana turo baki sai ya mike yana sakin smile ya karasa inda take..hannu yakai ya zame dankwalin dake kanta nan take black long hair dinta ya bayyana..lumshe ido yayi tareda kai hannu yana shafa gashin nata yana sauke numfashi..he just every single thing about this girl..he loves everything she have..saida ya gama shafa gashin nata to his satisfaction snn ya jata ya zaunar da ita gefen gado yana ce mata"sit right here"..murguda baki tayi kmr zatasa kuka tace mishi"kaina a bude fa"..dungure mata kai yayi yana dan hararanta yace"see you..sai kace ba kece mai son fitoda gashin naki waje ba"..daure fuska tayi tana sake turo baki shi kuma ya saki murmushi gamida girgiza yace"continue pouting those lips na kusa nayi maganinsu ai"..da sauri ta maida bakin nata tana sake daure fuska..shi Kuma bai sake bi ta kanta ba ya bude box din ya shiga neman mata kayan da zatasa..duk wanda ya dauko tana gani har wani dagashi yake yana kare musu kallo snn ya ajiye..saida ya daga almost ten duk baiga Wanda yayi mashi ba ita kuma tana zaune tana kallon ikon Allah..wani taga ya dauko red din riga mai hannun vest da bombshort mai net a jiki..wani murmushi ya saki yana sake jujjuya kayan ya kare musu kallo snn ya mika mata tun ma kafin yace wani abu cikin daure fuska tace"na rantse da girman Allah bazan sa wnn ba"..kallonta kawai ya tsaya yi kmr ta kwashe da daria amma ya dake..irin wnn shiga masallaci haka..wnn rantsuwa da wuri tunma kafin yace tasa din..baiyi mata musu ba ya maidasu ciki snn ya dauko wata purple din riga batada tsayi sosai itama kuma hannun vest ne da ita amma jikinta is very cotton unlike wancan da yake net..sake Mika mata rigan yayi shima bai jira tayi mgn ba yace"na rantse da girman Allah sai kin sa wnn rigan"..kallonshi kawai takeyi fuskan nan a kwabe da gani kiris take jira ta sakar masa kuka amma batayi ba..karban rigan tayi ta ajiye tana wani kawar da kai gefe shidai baice mata komai ba ya tattara sauran kayan ya maidasu cikin box din snn rufe ya daukeshi ya ajiye a gefe..tana ganin ya fara rage kayan jikinshi ta wani runtse ido wai bazata gani ba..murmushi kawai yake mata har ya gama cire kayanshi ya fada bathroom..brush kadai yayi ya fito don already yayi wanka kafin ya taho..yana fitowa itama yace taje tayi brush ta sako rigan nata ta fito..batayi musu ba ta mike ta fada bathroom shi kuma ya dauko wani three quarter fari yasa tareda singlet shima white snn ya hau gado ya kwanta yana jiran fitowarta yau ko pyjamas bazai sanya ba shi Kam..a hakanshi zai kwana yanda zaifi jin dadin baccin sosai...Aysha kuwa tunda ta gama brush din ta sanya rigar taga gaba daya tsayinta ko guiwarta bai kai ba sai ta nemi wuri ta zauna tana tunanin yanda za'ayi ta bari ya ganta da wnn rigan..idan ba iskanci ba dama taya zai wani bata wnn dan iskan rigan yace tasaka kuma a gabanshi..sai yanxu take sake tabbatar da mgnr da ake cewa gaba daya maza basuda kunya..Saida ta kwashi kusan minti goma a na ciki kmr daga sama kawai taga mutumi a gabanta ya dauketa cak ya fita bathroom din da ita..runtse Ido tayi tana karanta innalillahi a cikin ranta har taji ya kwantar da ita akan gado shima ya kwanta tareda switching off bedside lamp dakin yayi duhu don already ya kashe sauran bulbs din..hannunshi yakai tareda janyota ya hada da jikinshi tanajin yanda yake sauke ajiyar zucia a jere a jere itadai tayi mukus kmr mara lafia..cikin wata irin murya da bata sanshi dashi ba taji yana cewa"ki tayani addu'a rabbi ya bani ikon kulawa dake gwargwadon iyawata..Allah ya bani hakuri da juriar zama tare dake ba tareda cutarwa ba..Allah yasa na iya rike amanarki da iyayenki suka bani snn kada Allah ya kawo ranar da ni Attahiru zan juya maki baya ko in dena sonki ko inyi maki wani abu dazai sosa zuciarki..kada Allah ya nunamin wnn ranar har karshen rayuwata"..gaba daya shiru sukayi na dan lokaci kafin yacigaba da cewa"Ina sonki sosai Aysher kuma har dunia ya tashi nasan bazan ta6a son wata kmr yanda nake sonki ba..I love u so much and Ina godia wa Allah daya bani ke a matsayin mata..inshaAllah bazakiyi regretting aurena ba har abada"..hawaye taji sun wanke mata fuska har batasan lokacinda ta rungumeshi ba itama kawai sai sheshshekar kuka take tama kasa bude baki tayi mgn..son da yake mata da dadewa tasan mai girma ne and wnn maganganun da yayi sai taji tausayinshi ya kamata sosai..taji bazata iya aikata abunda ta shirya zata aikata don hanashi kasancewa da ita ba instead zata hakura ta kuma jure duk wani abu da zaizo mata dashi..she's going to be strong for him ko don sbd yanda yake azabtuwa da soyayyarta...lokaci mai tsaho ta dauka tana kuka a jikinshi Wanda har hakan ya fara ta6a zuciarshi..a hankali ya dago fuskanta yana kallo kafin daga bisani ya lumshe ido tareda hade bakinshi da nata..aikuwa diff ta hadiye kukan ta shiga rarraba idanu kmr shege a rabon gado...lokaci mai tsayi suka dauka a haka kafin ya zame bakinshi a hankali tareda sake hadeta da jikinshi yana shafa gashin kanta muryanshi can kasa yace mata"sleep"..da sauri da kulle idanuwanta tana sake lafewa a jikin nashi gabanta yana cigaba da faduwa har wani zazza6i taji yana neman kamata..addu'a kawai take Allah ya bata karfin halin da zata iya juran duk abunda zaizo mata dashi don sosai take a tsorace musamman da Billy ta sake tsoratar da ita daxu...shi kuma gani yayi bai kamata ya aikata wani abu a yau din ba sbd yasan gobe gidan zai cika taf da mutane sai kuma body temperature dinta da yaji yayi rising kmr fever zai rufeta..a hankali yaja duvet ya lullu6esu dashi snn yayi addu'a ya shafa mata shima ya shafa a jikinshi daga haka ya gyara mata kwanciya ya dora kanta a chest dinshi snn ya lumshe ido yanason bacci yazo yayi awon gaba dashi har baizo ba..har ita ta samu baccin shi nashi idanun a kekashe suke tamkar ba dare ne ba..kawai farin ciki kasancewa tareda ita ma kadai ta isa yasa bacci yayi kaura daga idanunshi..ganin da gaske ba baccin zaiyi ba sai ya kwantar da ita kan pillow a hankali ya sauka daga gadon ya shiga bathroom ya dauro alwala snn yazo ya tada sallah don ya sake nuna godia wa Allah daya cika mashi burinshi na samunta a matsayin mata. Koda ya tashi da asuba bai tada ta ba saida yayo alwala kafin ya wuce masjid ya zauna gefen gado yana kallon cute face dinta da ko kadan baya gajia da kallonshi..hannu yakai yana shafa gashin kanta snn ya lumshe ido yayi pecking forehead dinta followed by cheeks dinta sai tip of her nose..bude Ido tayi a hankali tana kallonshi yana murmushi yace mata"it's time for subhi"..mikewa tayi zaune tana murza idonta yayinda shi kuma ya kamata suka mike tsaye snn ya jata zuwa bathroom..tap ya kunna snn ya nuna mata shi da hannunshi yana cewa"ablution"..dan bata rai tayi kafin tace"ni fitsari zanyi"..yace"kiyi mana..i didn't stop u"..yanda ta zare idanu sai kayi zaton wani mummunan sa6on yayi..shi kuma kallonta kawai yakeyi yana kunshe daria..ganin da gaske ba fitsarin zatayi ba ya fita daga bathroom din yana girgiza kai..cikin ranshi fadi yake"duk ki gama guje gujenki ne ki dawo hanya yarinya"..yana fita ta tsuguna da sauri tayi fitsarin tayi tsarki duk cikin hanzari take yi wai kar ya dawo bata gama ba..tana gamawa tayi alwala snn ta fita..a cikin dakin ta sameshi ya shimfida mata carpet yana rikeda zundumemen hijab dinta da yaje bedroom dinta ya dauko..karasawa tayi ta tsaya kan carpet din tana mika hannu nufin ya bata hijab din amma sai yaki bata instead sai matsa kusada ita tareda zura mata hijabin..kallonta yayi a hankali yace"zanje masallaci"..ta gyada mishi kai alamar toh daga haka ya fice daga dakin ita kuma ta tada sallah zatayi raka'atainul fajr kafin lokacin sallah ya karasa. Lokacinda ya dawo already itama ta idar da nata tana addu'a dan haka ya zauna gefen gado har ta gama addu'an ta shafa snn ta mike tana ninke carpet din..mikewa yayi shima ya amsa carpet din ya karasa ninkewa ya ajiye inda yake snn ya zare mata hijabin jikinta shima ya ajiye daga haka kuma jata suka koma kan gado..idanunta a lumshe yaji tace mishi"Ina kwana"..ya saki murmushi yana kara sanyata a jikinshi yana shafa gashin kanta yace"lafia lau wife..how was ur night"..dan murmushi tayi ba tareda cewa komai ba shima kuma bai sake cewa ba ya lumshe Ido kafin bacci yazo yayi gaba dasu at once. 11:33 su Aunty Fiddausi suka shigo gidan don yi mata sallama sbd wucewa zasuyi Gombe yanxun nan..sunata kwada sallama a parlor amma tsit kmr dai ba mutane a gidan..Billy ce ta dauki waya zata kirata Aunty Amina tace ba saita kirata ba su wuce kawai idan yaso sai suyi sallama ta waya..hakan kuwa sukayi don komawa can gida sukayi nan ma sukayi sallama da Mummy da sauran yan uwanta snn suka tafi bayan an cikasu da abubuwan biki kala kala. 12 da wani abu kiran Nur ya tashesu daga baccin da suke..rai a 6ace Bobby yakai hannu ya dauko wayanshi ba tareda ko duba wanda yayi Kiran ba yayi picking tareda sakawa a kunne..on the other side Nur ya saki wani daria yana cewa"oh ni Nura..Bob i hope dai ba zuwa ka nakasta yarinyar mutane har zuwa wnn lokacin kuka kasa tashi a bacci ba"..wani tsaki da Bobby yaja ita kanta Aysha dake kwance abun saida ya bata mamaki..shi kuwa Nur bai damu da tsakin nashi ba yace"dama Mummy tace a kiraka kazo kayi sallama da masu wucewa Enugu amma idan baka gama..."Bobby bai bari ya karasa ba ya kashe wayarshi yana kara jan tsaki..wlh Nur ba karamin dan rainin hankali bane..he is freaking annoying..wall clock dake dakin ya kalla aikuwa ya wara ido ganin da gaske har 12 ya wuce yana bacci..lallai bacci kusada masoyi akwai dadi tunda gashi har hakan yasa yakai time dinda bai ta6a kaiwa yana bacci ba..ikon Allah knn...sauka yayi daga gadon da sauri ya fada bathroom shi duk a tunaninshi bacci takeyi baisan tun lokacinda ya tashi itama ta tashi ba likimo kawai tayi don batason yasan idonta biyu...wanka yayi sharp sharp ya fito zuwa closet dinshi ya saka qananun kaya ya dan shafa turarukanshi masu dadin qamshi snn ya dau key da phone dinshi ya fita zuwa gidan nasu...tana jin fitarshi ta diro daga kan gadon da sauri har zata fita sai kuma ta dawo ta gyara mishi gadon tsaf ta gyara ko ina snn ta dauko sweeper ta share dakin dukda ba wani datti yayi sosai ba...bayan ta gama ta zuba turaren wuta a burner tareda sauke duk curtains din dakin snn ta fita zuwa nata dakin..nan ma dan gyare gyaren tayi snn ta cire rigar jikinta ta fada bathroom..brush ta farayi snn tayi wanka tareda alwala ta fito daure towel data gani a bayin...saida ta karasa tayi locking kofarta da key snn ta iya zama nan gaban mirror ta shiga shafe shafenta..tana gamawa ta dauko fitted gown na wani lace silver da black ta saka snn ta kafa daurin dankwalinta ya zauna daram ko make up artist sai haka..gashin nan an fito dashi ta kasa sai daukan ido yake sbd kyallin da yake..powder ta shafa a fuska da eye pencil a ido sai farin wet lips lips dinta..nan take ta fito a amarya sak son kowa kin wanda ya rasa..ta dauki turare duk tabi jikinta dashi snn ta dauki waya ta zauna tana kiran Billy..tana dauka ne take sanar da ita cewa sunzo yi mata sallama bata tashi a bacci ba don haka sun wuce Gombe..ranta duk ya 6aci ta kira Aunty Fiddausi kmr zatasa kuka tace"yanxu Aunty shine kuka tafi ko sallama bamuyi ba?.."Aunty Fiddausi tace"to munzo baku tashi daga bacci ba Aysha ya kikeso ayi?..kiyi hakuri kiyi ai bada jimawa ba zan dawo..Allah ya baku zaman lafia da yara na gari"..turo baki tayi kmr tana ganinta tace"nidai Aunty da Kun kirani a waya ai zan tashi"..tsaki Aunty Fiddausi ta saki tana cewa"sbd mahaukata ne mu irinki kawai saimu hau kiranki ki baro wajen mijinki ki taho..kar ki nutsu kicigaba da wnn shashancin wlh dawowan da nace zanyi ma sai in fasa"..da sauri tace"aah Aunty dan Allah kiyi hakuri plss..na dena"..daga haka bata sake cewa komai ba ta kashe wayarta tana gunguni..kawai suka wani kama hanya suka wuce ba tareda ko ganin karshe sun bari tayi musu ba...tana kokarin dialing number Ammi kiran Husna ya shigo wayar..murmushi ta saki mai kyau tareda gyara zama kafin tayi picking call din..wani ihu da Husna ta sakar mata a kunne saida ta janye wayar daga kunnenta na wucin gadi..can sai taji voice din Yusra itama tazo suna ihun tare..saida suka gama duk tana sauraronsu snn suka shiga gaisheta Husna hadda cewa"Adda ya gidan naki dan Allah..ya Proprietor..how was the first night"..banza Aysha tayi mata bata amsa ba sukaci gaba da mgn da Yusra..Husna ta kwace wayarta wai sai suje suyi mgn da wayar Ammi amma ba nata ba tunda walakanci ma take mata...ba musu kuwa ta kira wayar Ammi nan ma suka gaisa Ammi nata sake jaddada mata tayi biyayya wa mijinta snn banda sakarci itadai tana amsa mata da toh..bayan sun gama Yusra ta sake kar6an wayan sukacigaba da hiransu..inshort dai ranar ba wanda batayi mgn dashi ba a gida don hatta Hamma da daddy duk saida ta kira ta gaishesu..bayan sun gama wayan kuma ta mike ta fita parlor don yunwan da taji tanaji. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07064800556. 58 Tana fita parlor taci karo da Nusaiba yarinyar aunty Munubiya da Miemie sun shigo dauke da basket din abinci...tana ganinsu ta saki murmushi tareda karasowa tana kallonsu tace"sannunku"..Miemie ce tace"yauwa aunty amarya..ga abinci Mummy tace mu kawo"..karasawa dinning sukayi suka ajiye abincin snn suka dawo parlon suna gaisheta ta amsa da fara'a sosai don da gaske taji dadin ganinsu at least dai bazata yini ita kadai ba...dinning din suka wuce gaba daya don cewa tayi su zauna suci abincin tare..ba musu Miemie tayi serving dinsu suka fara ci tunda suma basuci abincin ba kafin su fito...suna gamawa suka gyara wurin suka dawo parlor nan kuma baqi sukace salamu alaikum..mutanen Enugu ne da zasu wuce yau sukazo sallama da amarya..sosai ta tarbesu da kayan ciye ciye iri iri su Miemie na tayata..kayan gara tun daga kan su alkaki nakiya diblan da sauran kayan zaki...suna tafia wasu baqin suka sake zuwa a takaice dai har yamma basu dena fama da baqi ba shiyasa taqi bari su Miemie su tafi don sun taimaketa sosai ba kadan ba...duk Wanda sukazo haka zasuje su zubo kayan gara snn su hada da lemuka su kawo..Mummy ta sake aiko musu da wani abincin nan ma sukaci tareda baqi...sai dab da magrib suka samu saukin baqin nan Kuma suka hau gyaran gida tun daga parlor zuwa kitchen da dinning...Aysha da Nusaiba suna gyare gyare Miemie kuma na kitchen tana wanke wanke..in no time suka gyara gidan tsaf suka saka turaren wuta nan take qamshi ya cika ko ina...bedroom dinta suka shiga sukayi alwala sukayi sallahr magrib daga nan kuma Aysha ta dauki kayanda zatasa ta wuce flat dinshi don yin wanka..Saida ta tabbatar ko ina a gyare yake tsaf snn ta rage kayan jikinta ta fada bathroom...lokaci mai tayi ta dauka tana wanke jikinta sosai kafin ta fito daure da towel..bata damu da rufe kofa ba sbd a tunaninta ba yanxu xai dawo ba kilan har ta gama shiryawa ma bai shigo ba dan haka daga ita sai towel dinshi dake jikinta ta zauna gaban mirror ta hau shafa cream dinshi da sauri..tana gamawa ta dau comb ta taje gashinta ta gama tana kokarin parking kawai ta hangoshi ta jikin mirror ai batasan lokacinda ta mike a zabure zata koma bayi ba yayi saurin karasawa ya janyota jikinshi yana murmushi..murya can kasa yana shafa gashin data gama tajewa da Igbo yace mata"nwunye m"(my wife)..banza tayi mishi tana sauke numfashi da sauri sbd yanda gabanta ke faduwa..sake matso da bakinshi yayi dab da kunnenta kafin yacigaba da cewa"kedu?.."(what's up)..shiru ta sakeyi mishi as ba gane abunda yake cewa take ba..ita ina ta iya wani Igbo da zaizo yanayi mata mgn dashi...ganin ba mgn zatayi ba ya kama hannunta suka zauna gefen gado ya shiga kare mata kallo yana shafa gemu har wani lumlumshe ido yake sbd nishadi..sake lumshe idon yayi cikin sanyin murya yace mata"ahuru m gi n'anya"(I love you"..Lamido dai ta zama kurma as gaba daya ba gane wnn yaren nasu take ba..kanta na kasa tana son zamewa daga jikinshi tasa kayanta amma yaki bata daman hakan..ganin yanda take ta mutsu mutsu ya kara sakin smile yana rikeda hannunta yace"lee m anya mana"(look at me mana"..still dai ba response don haka tilas ya ajiye inyamurancin a gefe ya sake janta jikinshi still yana rikeda hannunta yace"ya kamata in koya maki igbon nan gaskia"itadai batace dashi kala ba shima bai damuba ya dagota yana kallon jikinta yace"so wanka kikayi?.."Kai ta gyada mishi da sauri tana wani karya wuya kafin tace"zansa kaya plss".. murmushi ya saki tareda mikewa ya dauko mata kayanda ta ajiye kan gadonshi ya mikar da ita tsaye wai zai saka mata aikuwa ta faki Idonshi ta kwace kayanta ta fada bathroom a guje saura kiris ta Fadi..daria sosai Bobby ya saki tareda mikewa zuwa kofar bathroom din yace"ok idan kin gama sa kayan ki fito Muna tareda Nur ne..and ban yadda ki fito without wearing hijab ba..i repeat kisa hijab kafin ki fito"..yana gama fadin haka ya juya ya fice daga dakin yana cigaba da murmushi..bata fito ba saida ta tabbata ya bar dakin snn ta fito ta duba sai bataga hijab dinta dake dakin ba don dazun ta maidashi dakinta dan haka ta gyara daurin dankwalinta tareda daukan mayafin data hado da kayanta ta yafa a kanta ta fita..Nur na zaune parlor yana kokarin powering tv ta shigo..da murmushi sosai a kan face dinta tace"sannu da zuwa sir"..shima yana murmusawa yace"lafia qalau amarya..ya zaman gida"..kanta a kasa tace"lfy Lau"..Bobby ya fito daga kitchen yana sipping ruwa dake hannunshi a hankali ya karaso cikin parlon ya zauna kusada matarshi ba tareda ya kalli inda Nur yake ba yace mata"ya kamata ki dena kiranshi da sir din nan mana..he is no more ur sir he is ur husband's friend so feel free to call him Nur ko kuma kice Dr Nuruddeen Ugochuku Dominic"..ya karasa mgn yana sakin wani dan iskan smile..murmushi Lamido tayi bata ce mishi komai ba shi kuma Nur girgiza kai ya shigayi yana cewa"ba laifinka bane Bob laifin auren daka rigani yi ne..ka jira nima kaga kalan walakancin da zanyi maka idan na auri pretty"..kmr hadin baki yana rufe baki sai ga Miemie da tray din drinks dasu alkaki ta kawo mishi...yana ganinta ya saki wani hadadden smile tareda juyawa yana facing dinta completely cikin excitement yace"oh my Goodness Pretty is this u?.."Miemie ta ajiye tray din kan table tareda zaunawa kusa dashi tana kallonshi with smile tace"nice mana uncle Nur..Ina yini"..da sauri yace"lafia..how are u?..ya hidiman biki"..tace"Alhamdulillah"..gyada kai ya shigayi yana kallonta banda murmushi ba abunda yake..ganinta ba karamin sanyaya zuciyarshi yayi ba sai yaji gwara da Allah yasa yazo nan din suka hadu da ita koba komai ya samu ganinta kuma yayi mgn da ita..Nusaiba ce ta shigo parlon ta gaishe da Nur snn ta juya tana kallon Bobby tace"uncle bobby sannu da zuwa"..yace"yauwa Nusaiba..Kun gama duk aikin naku?.."tace"eh mun gama"..yace"alright kuna iya tafia tunda na dawo"..hira suka dan ta6a kafin wucewan nasu Nur dai sai kallon Miemie yake yama kasa cinye abunda ke gabanshi...tare suka fita daga gidan leaving Lamido ita kadai a parlor..kofar da zata maidasu main house ya bude musu suka shiga shi kuma Nur yabi main gate ya fita tunda da mota yazo..yana ganin wucewarshi ya dawo ciki tareda kulle kofa..bai sameta nan parlor ba dan haka ya wuce flat dinshi ganin still bata nan sai yayi murmushi kawai ya shiga bathroom don yin wanka..har ya fito ya gama shiryawa cikin pyjamas dinshi bata shigo ba so yana gamawa sai ya fita zuwa dakin nata..tana kwance kan gado ta wani kudundune kanta cikin bargo ita bata yadda ba fever ne ya kamata..tsoron abunda ka iya zuwa ya dawo ya sanyata cooking wnn idea din wai a ganinta idan tayi haka shknn ta tsira..murmushi ya saki gamida girgiza kai yana karasawa cikin dakin..baice kala ba kawai yakai hannu ya dauketa cak ya fita daga dakin da ita zuwa nashi..idanunta a runtse sai karanta duk addu'an da yazo bakinta take..fatanta yau ma Allah ya kwaceta a hannunshi kmr yanda ya kwaceta jiya...bai ajiyeta ko ina ba sai kan gadonshi ya sunkuya sosai har breathe dinshi na sauka a fuskanta yace"kinyi sallah?.."kai ta gyada mishi da sauri dan tun daxun tayi sallahn isha'inta..a hankali ya sake cewa"abinci fa?.."nan ma kai ta gyada mishi alamar taci..bai sake cewa komai ba ya dauko box din sleeping dress dinta da har yanxu yake dakin yau ma ya shiga neman mata wanda zata sa..wata silk doguwar riga ya sake dauko mata peach color ya karasa gaban mirror ya fesheta da turare snn ya dawo kan gadon ya dagota ya shiga kokarin cire kayan jikinta..da sauri ya kama hannun nashi ta rike gam tana dubanshi hankali a tashe tace"partner zansa da kaina fa"..baice mata komai ba ya mika mata rigan ta kar6a da sauri snn ta mike ta shiga bathroom..tana sakawa ta fito kanta a kasa ta karasa gefen gadon ta zauna shi kuma ya mike yayi switching off lights leaving bedside lamp kawai..nan take hasken dakin ya ragu sosai sai dim light..komawa yayi inda take ya tsaya yana kallonta kafin yace wani abu ta marairaice tace"zazza6i nakeyi fa"..murmushi ya saki yana girgiza kai cikin ranshi yace"wai ni yarinyar nan zata rainawa hankali"..a fili kuma Mika mata hannunshi yayi yana cigaba da smiling yace mata"don't worry magani zan baki"..bata sake cewa komai ba ta kama hannunshi ya mikar da ita..ita ya fara kwantarwa kan gadon snn ya fara rage kayan jikinshi don zafi yaji yanaji aikam Idonta na ganin haka ta shiga yarfa hannu muryanta na rawa tace mishi"me..zaka..yi?.."baice mata komai ba Saida ya gama abunda yake snn ya kwanta nan kusada ita tareda janyo duvet ya rufesu dashi ya kashe bedside lamp..nan take jikin Hajia Ai ya dauki rawa sosai har wani zufa taji yana tsatsafo mata from no where..yana jin yanda jikinta ke trembling kawai sai yayi cupping fuskanta ya dora forehead dinshi kan nata murya can kasa yace"baby what is it?.."hawaye na gangrowa Idonta tace"tsoro..nakeji"..hannu yakai yana shafa bayanta a hankali ya sake ce mata"don't be plss..i am human just like u so don't be afraid okay?.."da sauri ta shiga gyada mishi kai har yanxu hawaye basu dena ciko idonta ba..voice dinta na sake breaking tace"nidai..dan..Allah..kayi.. hakuri"..girgiza mata kai yayi shima nashi voice din na breaking yace"am.sor..ry..i..cant"..ai yana rufe baki data rushe da wani irin kuka baisan lokacinda ya hade bakinshi da nata ba..lokaci daya kuma kukan ya dauke sai ta shiga kokarin kwatar kai tana wani zazzare idanu kmr wanda tayima sarki karya...Bobby dai eyes dinshi are still closed and zuwa yanxun yasan ko dunia zasu taru kanshi bazai iya fasa abunda yayi niyya ba...a takaice tun Aysha tana zazzare ido tana ganin abun kmr wasa har akazo limit din da zare idon ma bazata iya ba sbd bala'i..tun tana ganin kmr zai tausaya mata ya barta amma sai taga ma kmr baisan abunda ake kira tausayi ba..kuka takeyi tun karfinta tana kokarin kwatar kanta amma abun yafi karfin tunaninta don haka daga baya saita zubawa sarautar Allah ido tana cigaba da hawaye...after a very long journey Bobby ya samu hankali da nutsuwarshi suka dawo gareshi sai kuma ya fara tunanin danyen aikin da yayi..da kyar ya iya daga hannu ya sake rungumeta jikinshi yana sauke numfashi da sauri kmr wanda yayi tsere..duk systems din jikinshi feels empty baisan meyasa ba..yanajin yanda take rera mishi kuka kasa kasa amma ko bakin rarrashinta baya dashi tunda shine silar faruwar komai..lokaci mai tsaho suka dauka a haka yana rungume da ita yana shafa bayanta a hankali har wani baccin wahala ya lalla6o yayi masa gaba da ita..sai a nan ya iya mikewa yana takawa a hankali ya shiga bathroom..wanka ya farayi itama ya hada mata ruwan wankan kafin ya fito..ya dade nan tsaye yana kallonta yana recalling abubuwan da suka wakana yana murmushi..he can't believe it happened..he can't believe yau shi da Lamido sun zama one.."oh Allah Alhamdulillah"..zaunawa yayi a hankali yakai lips dinshi ya manna mata peck a goshi yana shafa gashin kanta mai dan Karen laushi yace"thank u so much wife..am proud of u..kuma i love u"..bata ma San me yake cewa ba as baccinta yayi nisa sosai..tunanin yanda zai tasheta kawai yakeyi don haka ya sureta gaba daya zuwa bathroom din da ita.. already dama ya hada ruwan zafi a ciki so yana shiga ya zaunar da ita yana dan murza hannunta wai ko zata tashi..bude ido tayi a hankali tana kallonshi sai kuma ta fasa wani ihu har tana kusan faduwa a kasa yayi saurin kamata ya hada da jikinshi ya shiga karanta mata addu'a a kunnenta..kuka ta farayi sosai tana tuttureshi amma kememe yaki ya saketa dan haka ta daddage ta gartsa mishi cizo a chest dinshi ai baisan lokacinda ya saketa yana shafa wurin ba..tana ganin ya saketa taja baya a hankali tana runtse ido sbd wani zafi takeji a ilahirin jikinta.. ruwan zafin daya hada ya nuna mata yana cewa"u need hot water baby..allow me to help u plss"..makale shoulder dinta tayi tana wani daure fuska tace"zanyi da kaina"..kallonta kawai yakeyi yana tunanin ta hanyar daya kamata ya bullo mata..for sure yasan idan ya barta ita kadai ya gasa jikinta zatayi yanda ya kamata ba amma ya zaiyi da ita?..ganin tsayuwar ma neman gagaranta yake yayi kundunbala ya sake kamota ya dannata cikin ruwan zafin..wani ihun data sakar mishi saura kiris don kunnenshi ya toshe amma bai biye ta kuka da uban duka da take kai mashi ba yayi mata duk necessary abu..saida ya tabbata ruwan zafin ya shiga jikinta sosai snn ya hada mata ruwan wanka ya barota a bathroom din tana aikin kuka kmr wanda akama operation..saida ta kwashi almost seven mins tana kuka kafin tayi wankan ta fito tana takawa da kyar sbd legs dinta da suka rike..kawai gani take dama can mugu ne shi ganewa ne batayi ba..idan ba mugunta ba why zai cutar da ita haka?..why zai kasa tausaya mata?..yana ganin fitowarta yazo da sauri ya kamata suka karasa ciki batayi yunkurin kwace kanta ba don tasan idan bada support din nashi ba tafiar gagaranta zaiyi..a gefen gado ya ajiyeta snn ya dauko mata wasu kayan ya sa mata da kanshi dukda yanda take tureshi bai saurara ba saida ya gama..analgesic ya bata da ruwa tasha snn ya sake sungumarta ya kwantar da ita kan gado ya rufeta da duvet..kallonta ya shigayi yanda take sauke ajiyar zucia akan kari sai ta bashi tausayi sosai..kuma har yanxu hawaye basu dena zarya fuskanta ba..a hankali ya kama hannunta ya rike yana dan marairaicewa yace"baby am sorry plss"..tun kafin ya rufe baki ta kwace hannunta daga nashi tana girgiza kai idonta a kulle tace"baka sona"..sake kama hannun yayi yana shgwa6e fuskanshi yace"baby why will u say that plss..i love u mana..i love u dearly"..sake kwace hannunta tayi tana cewa"it's a lie..u never loved me"..da sauri yace"wlh i do..i do love u alot..pardon my manners pls"..bude Idonta tayi tana kallonshi har yanxu tana hawaye tace"if da gaske u love me why ka ganamun azaba haka..i almost die of pain"..a hankali yace"baby it's the love..believe me bada son raina nayi maki haka ba..i just couldn't control or stop myself..the thing is u are kind of different baby..u are kind of sweet that when i.."kasa karasawa yayi kawai ya lumshe ido tareda pecking forehead da cheeks dinta yace"i just doesn't know how to put it love..nagode sosai for making me a happy man Allah ya baki aljannah"..banza tayi dashi tana sake lumshe ido don da gaske haushinshi taji tanaji..bai damu da cewarta ba shima ya haura gadon ya kwanta tareda matsawa kusada ita sosai yakai hannunshi yayi wrapping dinta dasu snn yakai bakinshi daidai kunnenta yace"i love u"..still bata ce komai ba shima bai sake cewa ba sai rungumeta da yayi a jikinshi..yanajin lokacinda bacci ya dauketa dan haka ya juyo da ita tana facing dinshi tareda gyara mata kwanciya a jikinshi ya dora kanta a chest dinshi shima ya gyara nashi kwanciya ya lumshe ido..lokaci lokaci yake sakin smile da baisan sanda yake escaping lips dinshi as a result tunawa da abubuwan da suka faru..shikam ya gode Allah daya bashi ita as a wife..ya tabbata ba kowane namiji Allah ke bama baiwan mace mai tarin ni'imomi kamarta ba..kusan komai tana dashi itakam babu inda Allah ya rageta saidai abunda baza'a rasa ba. Washegari ya rigata tashi don har yayi wanka ya gama shiryawa bata tashi ba.. breakfast aka kawo musu daga main house dan haka ya ajiye a dinning ya sake komawa dakin yaga ko ta tashi amma har lokacin bata tashi ba..stool ya janyo ya zauna nan kusada ita ya shiga yi mata pictures da wayarshi yana murmushi..yanda ta rungume pillow tana wani turo baki ga gashinta da yayi scattering all over ba karamin kyau tayi mishi ba..ya dauketa pictures da dama har shima saida ya hada fuskanshi da nata ya dauka a tare..ganin ta fara motsi yayi saurin ajiye wayar tareda kama hannunta ya rike..motsawa ta sakeyi ta dan juya mishi baya kafin ta sake juyowa sai kuma ta bude idonta tarwai a kanshi..ya saki murmushi bayan yayi pecking forehead dinta yace"good morning wife"..turo baki tayi tana harararshi ta gefen ido..yace"baby nace am sorry mana..abun bai wuce bane har yanxu?.."tale baki tayi kmr zatasa kuka tace"u almost kill me yesterday"..tana rufe baki yace"shiyasa nace am sorry kuma ya kamata ki hakura..son da nake maki ne duk ya janyo haka amma believe me ba laifi na bane"..harara ta sake Maka mashi ta fara kokarin sauka daga gadon ya rungumeta da sauri murya can kasa yace"baby please mana.. don't be upset with me plss"..rungumeshi back itama tayi tana cigaba da turo lips dinta tace"ai dai bazaka kara ba koh?..mutuwa zanyi Allah"..tana rufe baki yace"shush stop saying that bazaki mutu ki barni ba inshaAllah..yanxu ki tashi kiyi wanka ga breakfast can Mummy ta aiko"..batayi musu ba ta raba jikinta da nashi tareda sauke legs dinta kasa..mikewa yayi ya zagaya inda take yana cewa"can u walk?.."girgiza mishi kai tayi tace"i don't know"..Mika mata hannunshi yayi ta kama ya mikar da ita tsaye snn yace she should walk ya gani ko zata iya takawa..ba musu ta danyi taking steps forward saidai batayi nisa ba ta dakata tareda juyowa tana kallonshi fuska a kwa6e tace"partner har yanxu da zafi wlh"..karasawa yayi ya dauketa zuwa bathroom yace"don't worry yanxu zai dena"..daga haka ya shiga da ita bathroom duk wani noke nokenta saida ya sake repeating yanda yayi mata jia snn ya bar toilet din..tana gama wanka ta fito nan ma yayi saurin karasawa ya daukota ya dire a kan gado..da kanshi ya dauko cream ya shiga shafa mata..duk yanda taso ya bari ta shafa da kanta kin yadda yayi dan haka dole ta zuba mishi ido ya gama shafa mata cream din snn ya dauko mata undies da kayan da zata saka duk ya kawo mata dakin..tana ganin undies dinta a hannunshi ta wani marairaice tace"wa yace ka ta6amin undies dina?.."dungure kanta yayi yace"mai undies din ma na ta6ata balle su undies din?.."runtse ido tayi tana murmushi tace"partner bakada kunya wlh".. murmushin shima ya saki yana kokarin fara saka mata kayan yace"sonda nake maki ne ya maidani shameless..ai da ba haka nake ba ki tambayi Nur zai fada maki yanda nake da kunya a da"..murmushi kawai takeyi batace komai ba..tana jinshi yanata budurin saka mata kayan batace kala ba har ya gama snn yace ta mike ya zuge mata zip..ba musu ta mike yayi mata zipping rigar hadda su daurin dankwali shi yayi mata ya shafa mata turarukanshi snn ya sungumeta zuwa dinning..abincin ma da kanshi yayi feeding dinta saida ta koshi snn ya faraci..yana gamawa ya dauko magani ya bata tasha snn ya kuma daukanta suka koma parlor..zaunawa yayi itama ya zaunar da ita a jikinshi snn ya dauki remote ya shiga kokarin powering tv Aysha da har wani bacci taji na neman daukanta tace"partner yau bazaka fita ba?.."girgiza kanshi yayi yace"am not going anywhere yau ina tareda matata"..dan murmushi ta saki tareda zagayawa da hannayenta a jikinshi tana sake kwantar da kai a shoulder dinshi tace"nagode sosai..i love u"..hannu yakai yana shafa face dinta kafin ya amsa da"nima nagode sosai love..i love u so much"..daga haka ya manna mata peck a goshi snn ya shiga shafa kanta har bacci ya dauketa..gyara mata kwanciya yayi ya dora kanta akan laps dinshi ya shiga kallon fuskanta da baya gajia da kallo Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 59 Lokaci mai tsaho ta dauka tana bacci a jikinshi yayinda shi kuma ya ajiye duk abu da yakeyi ya maida gaba daya hankalinshi kanta yana kallonta kmr yau ya fara ganinta..soyayyarta yakeji na sake ninkuwa cikin zuciarshi fiyeda wanda yakejin yana mata a baya..har yanxu bai mance abubuwan da suka faru tsakaninsu a daren jiya ba..infact abu ne wanda yasan bazai taba iya mantawa dashi ba har abada..ya sameta ne kusan fiyema da duk yanda yake zaton samun nata..ta faranta ranshi fiyeda duk wani tunanin mai karatu..shiyasa baida wani abu da zai iya biyan wnn gagarumin kyauta da tayi mashi saidai kawai yacigaba da binta da addu'an Allah ya rabata da iyayenta da lafia snn ya bashi ikon kula da ita gwargwadon iyawarshi..wayarshi ya dauka daga gefenshi ya shiga daukanta hotuna kmr ba gobe..yanda take kwance a cinyanshi sai yaji wani sanyi da annashuwa suna zagaye ko ina a jikinshi..sunkuyawa yayi yayi pecking forehead dinta tareda kama hannun damanta ya rike a nashi ya bude baki da nufi cewa wani abu yaji ana ringing doorbell daga waje..lumshe Ido yayi yana ayyana waye yake neman katse mashi wnn jin dadin da yake ciki.. watching her sleep like this ba karamin farin ciki yake sanyashi ba amma yanxu ga wani nan da bai son ganin yana wnn farin cikin yana kokarin kusto musu gida at this time of the day..sake ringing bell din akayi daidai lokacin kuma da kiran Nur ya shigo wayarshi bai dauka ba sai mikewa da yayi daukeda ita a hannunshi ya nufi flat dinshi da ita don yasan da kyar idan ba Nur ne ke mashi wnn ringing bell din ba kmr dai wanda yakebi bashi..kan gadonshi ya kwantar da ita ya gyara mata kwanciya snn ya fita don ganin wanda ke ringing bell din..yana karasawa ya bude kofar fuska a wani daure yace"ni bansan dalilinda zaisa kazoma mutane gida da sassafen nan ba Nur..naci maka bashing wani ab..."mgnr nashi ya kamale ya throat dinshi sakamakon tozali da yayi da aunty sumy da Aunty Munubiya a bakin kofar...wani irin kunya yaji ya lull6eshi kmr ya tsaga kasa ya 6oye kanshi a ciki yayi kasa da kai yana sosa kanshi yace"am..sorry aunty..ashe kune?.."aunty Munubiya na murmushi tace"mune mara kunya..yanxu da Nur din ne yazo bazakaji kunyar fada mashi wnn mgnr ba?.."shafa kai yacigaba dayi yana murmusawa yace"Bismillah to ku shigo ciki"..da sauri aunty sumy tace"aah if we are not welcome gwara ka fada mana tun wuri mu san inda dare yayi mana tun kafin mu shiga ciki"..da sauri ya matsa daga jikin kofar yana cewa"haba come inside mana..kema dai kinsan ni ban isa in koreku ba koh?.."shiga cikin parlon sukayi Aunty sumy nacigaba da cewa"saka koremu mana Bobby..ka iya koran Nur da yake amininka ma balle kuma mu Karan kada Miya"..murmushi kawai ya saki gamida girgiza kai ba tareda yace komai ba..karasawa sukayi cikin parlor suka zauna aunty Munubiya ta shiga bin parlon da kallo tana gyada kai tace"MashaAllah gida yayi kyau Bobby..ina amaryar take zuwa nayi muyi sallama dan anjima kadan zan wuce Katsina"..dan bude idanu Bobby yayi kafin yace"Katsina kuma aunty?..me zakiyi a Katsina?.."tace"bikin qanwar babansu Taheer akeyi wlh..kaga dole zuwa ya kamani ba don ma wnn bikin naka ba ai da tuni ina can"..gyada kai yayi alamar ya fahimta yace"to Allah ya sa alkhairi"..da sauri aunty sumy tace"Ameen..yanxu Ina amaryar take?.."kallonta ya danyi yana hararanta yace"to bacci takeyi"..tace"to sai a taso mana ita mu gaisa ko aunty?.."aunty Munubiya dake murmushi tace"ba saika tasheta ba Bobby tunda bacci take ka kyaleta zamu hadu next time"..yana dan shafa kai yace"no aunty ki bari in tasota"..da sauri ta sake ce mishi"aah nace ka bari tayi baccinta..zamu hadu nan gaba ai..Allah ya baku zaman lafia"..a hankali yace"Ameen"..batasan shima cikin ranshi ba son tashinta a baccin yakeyi ba ya fada ne kawai don kar tace ya mata rashin kunya amma da gaske baccinta yakeso tayi to her satisfaction tunda yasan jiya ba wani baccin kirki ya barta tayi ba..mikewa aunty Munubiya tayi tana duban Aunty sumy tace"to Sumayya tashi mu wuce mana"..mikewa aunty sumy tayi tana dan hararan Bobby tace"aunty da kin bari ya taso mana ita wlh..maybe ma iskancinshi ne kawai zaice mana tana bacci..nasan da kyar idan ba wani abun yake 6oyewa bayason mu gani ba"..murmushi Aunty Munu ta kara saki tace"Allah ya nunamin ranar girmanki Sumayya"..da sauri Bobby yace"kema dai aunty kya fada yanxu har siriki gareta amma bata dena irin wnn tsokanan ba"..da sauri ta juya tana kallonshi ido a waje tace"siriki Kuma Bobby?.."yana daria yace"yes..har gida akazo aka sameni wai ana son Miemie da aure"..ya karasa mgnr yana sake fashewa da daria Aunty Munubiya na tayashi..aunty sumy kuwa tsilli tsilli tayi da Ido tana tunanin waye wnn a zaice yana son Miemie shi kuwa?..shin baisan ita din karamar yarinya bace ne?..kallonshi tayi da sauri in a serious tone tace"dan Allah waye?.."ya makale shoulder dinshi still yana daria yace mata"idan yayi wari zakiji"..bata sake cewa komai ba ta harareshi snn tabi bayan Aunty Munubiya da har ta kusa fita daga parlon..tare suka fita zuwa main house din dashi don dama baije ya gaisa da Mummy ba yau..suna shiga ya isketa zaune parlonta suna rarraba wasu souvenirs tareda Miemie..yana karasawa ya zauna kusada ita tareda yi mata side hug kanshi kan shoulder dinta yace"My Mummy"..murmushi ta saki tana shafa kanshi itama tace"My Bobby..how are u?.."yace"fine Mummy"..tace"ya amarya?.."saida ya saki wani kasaitaccen smile tunawa da yayi da ita kafin yace"she's also fine Mummy..tana bacci"..har yanxu Mummy bata bar shafa kanshi ba tace"ka barta tayi baccinta nasan rama wanda batayi a baya ba take"..da sauri ya dago yana kallonta yace"ban gane ba Mummy"..murmushi sosai Mummy ta Kara saki ganin tsarguwa yayi da mgnrta..ita bata kai nan wurin da tunaninshi ya kaishi ba..Ina ita ina shiga sabga irin wnn?..ganin yanda ta kasa dena smiling yace"Mummy me kike nufi plss?..i don't understand"..hannunshi ta kama ta rike tana dubanshi da kyau tace"bafa wani abu nake nufi duk ka tsargi kanka..na fada ne kawai sbd nasan tunda aka fara biki ba lallai tana samun bacci sosai ba"..ajiyar zucia ya saki a 6oye tareda sake maida head dinshi kan shoulder dinta yace"Mummy nayi missing dinki sosai"..sake shafa kanshi tayi before saying"ni kuma banyi missing dinka ba..farin ciki nakeyi sosai da Allah ya nunamin aurenka..Allah ya baku zaman lafia da kids masu albarka"..da sauri yace"Ameen Mummyna"..sai kuma ya 6ata rai yana wani tale baki kamar jariri yace"kikace bakiyi missing dina ba Mummy?.."a hankali tace"wasa nake nayi missing dinka sosai ma kuwa..i missed u like crazy"..rungumeta yayi yana sakin wani smile tareda fadin"that's my Mummy..Mummy i love u sosai wlh"..tace"nima i love u"..sake rungumeta yayi yana cigaba da smiling kmr wani sabon kamu. Lokacin da ya dawo gidan a kitchen yajiyo motsinta dan haka yana ajiye abincin da Mummy ta bashi ya taho musu dashi kan dinning snn ya shiga kitchen din..tana tsaye jikin gas tana dora tukunya akai ita bata yadda ba girki zata daura kmr daga sama kawai saiji tayi yayi sama da ita ya shiga juyawa da ita cikin kitchen din yana blowing mata kisses all over her body yace"baby am back..baby nayi missing dinki like hell..yaushe kika tashi a bacci?.."hannayenta takai tana shafa black sajenshi data dade tana burin ta ta6a yaudai gashi Allah ya kawo ranar ta6asu..murmushi ta saki har tana lumshe Ido sbd dan karen taushin da taji sajen kmr ba gashin namiji ba..lumshe Ido tayi tayi pecking dinshi a both cheeks dinshi snn tayi cupping fuskan nashi bayan ta hadeshi da nata exactly irin yanda ya kanyi mata sometimes kawai saita lumshe ido ta kasa cewa uffan..shi kuma yana rikeda ita har yanxu ko gajiya bayayi ya sake hade fuskokin nasu yana kallon cute lips dinta da yaji kmr yayi kissing dinsu yace"look up at me mana"..makale shoulder dinta tayi tace"i can't"..yace"oh har yanxu akwai kunya tsakaninmu knn?..well muje inyi feeding dinki yanxu sai mu sake zuwa in cire maki kunyan gaba da.."ai bata bari ya karasa ba da sauri tace"aah na dena dan Allah..am sorry pls"..murmushi ya saki yana kallonta yace"ki kalli idanuna toh"..kallon idanun nashi tayi for some mins sai kuma ta kulle nata a hankali tace"partner bazan iya kallo na plss..kadai san tun ba yanxu ba bana iya kallon eyes dinka kou?.."yace"shiyasa ai nakeso ki koya baby..bai yiwuwa ace ke da mijinki bazaki kallon eyeballs dinshi ba"..langabewa tayi tace"aidai zan saba amma ba yanxu ba"..kissing dinta yayi a goshi kafin yace"me kukeyi a kitchen?.."kokarin sauka ta shigayi daga hannunshi tana cewa"girki zan daura mana..yunwa nakeji sosai"..bai sauketa ba sai ma daukanta da yayi cak ya koma dinning da ita ya zaunar yana cewa"sorry na barki da yunwa..Ina tareda Mummy ne"..a hankali ta gyada mishi kai tana murmushi alamar ta fahimta..daga haka ya mike zaiyi serving dinsu tace ya barta ita zatayi komai yau..ba musu ya koma ya zauna yana kallonta ita kuma tayi serving dinsu a plate daya kmr yanda taga yayi musu snn ta dauki spoon ta mika mashi ba musu ya kar6a itama ta dauki nata suka fara cin abincin...suna gamawa ta gyara wurin tsaf tareda kai plate da spoons da suka bata kitchen ta wanke snn ta dawo tana kokarin dauke warmers daga kan dinning din kawai ya kama hannunta suka koma parlor suka zauna snn ya dan kashe mata ido yana murmushin da a kallon farko zaka gane na duniyanci ne yace"so ya jikinki?.."banza tayi dashi kmr bataji abunda ya fada ba..sake matsawa kusada ita yayi hadda su kama hannayenta yayi wani kasa da murya yace"partner talk mana..hope dai wurin ya warke?.."bazan ta sakeyi mishi kanta a kasa shi Kuma yayi saurin dagata ya dora a jikinshi yana cewa"ok let me check for myself tunda bazaki bude baki kimun bayani..."tun ma kafin ya karasa da sauri tace"ya warke fa"..cigaba da abunda yake yayi yace"no gwara in duba da kaina tunda naga kmr haka kikeso"..still bata bari ya karasa ba ta dan daga murya tace"partner please!..banasoo"..rungumeta yayi yana daria yace"to na dena wife..now fadamun ya wurin yake?..hope baya maki zafi yanxu?.."idonta a rufe tace"ya dena"..sake matseta yayi yace"MashaAllah kinga shknn we will..."toshe bakinshi tayi don bata shirya jin rashin kunyan nan nashi ba tace"banaso banaso manaaa"..daria yasa yana girgiza kai yace"to na dena wife..i love u"..shiru tayi kmr bataji me yace ba..ya sake cewa"I love u"..still taki cewa komai dan haka ya dan kwa6e fuska yana wani marairace mata yace"love say u love too mana"..ba musu tace"I love u too"..shi kuma ya sake kissing forehead da dimples dinta yana sake fadin"I love u more"..lumshe Ido tayi tanajin yanda baya gajia da furta mata wnn words din kmr yanda bata ta6a gajiya da sauraronta ba. Bai sake barin gidan ba saida aka kira sallahr la'asar yayi alwala snn ta tafi masallaci itama sai a lokacin ta samu sararin shiga yin sallahn don tun daxun ya ajiyeta gabanshi yana aikin kallonta ya hanata motsawa ko nan da can wai shi bai gaji da kallonta ba..ko dakinta bai bari ta koma ba daga parlor suka koma nashi dakin wai bai yadda ta dinga zama dakinta while he's around ba..bathroom ta shiga tayi alwala ta fito snn ta tayar da sallah a nan cikin dakin nashi..bayan ta idar tayi addu'o'inta sosai snn ta cire hijabin jikinta ta ajiye tareda hawa kan gadon ta kwanta bayan ta dauki wayarta data bari nan cikin dakin tun daxu..wanka takesonyi amma amma ta fara kunna data ta ta shiga Whatsapp tana duba messages dinta..duk tayi replying snn tayi updating status dinta tana kokarin kashe data saiga Billy ta kirata video call dan haka ta dauka da sauri tana kallon screen din taki cewa komai...Billy data shiga binta da kallo tana wani murmushi tace"Lamido amarya..how far?.."tsaki ta saki tana hararanta tace"ban saniba munafuka"..Billy ta kwashe da daria hadda tafa hannayenta tace"munafurcin me nayi Lamido?..ai ba wani abu nace ba kawai dai nasan yarinya taji maza..dan bani labari dan Allah inji how was it?..was he gentle?.."ajiyar zucia Aysha ta sauke tana kallon Billy kmr zatasa kuka tace"wlh he was not..don bakiga wahala da nasha ba da saikin tausayamun..kuma wai har yanxu nake cigaba da sonshi kmr bashine ya kusa halakar dani ba"..daria Billy ta kunshe tana jijjiga kanta tace"kice su Hajia Lamido an shiga kwaryan manya..to Allah ya kawo rabo mai albarka..in Allah ya yadda zamu dawo sunan baby in the next nine months"..wani tsaki Aysha ta saki tana binta da kallon banza tace"amma Billy bakya kaunata wlh..yanxu fatan haihuwan wata tara kikemun sbd bakya Sona?.."daria sosai Billy tasa tana cewa"meye abun rashin so anan dan Allah..haihuwa fa nace kiyi Lamido ba wani mugun abu ba"..tun bata rufe baki ba Aysha tace"to inshaAllah mugun fatanki a kanki zai tsaya don bazai karaso inda nake ba..kawai daga zuwa sai in fara daukan ciki kmr abunda nazoyi knn"..daria sosai Billy take hadda kyakyatawa..dama tun tuni tasan yanda Lamido ta tsani mutum yayi haihuwa da wuri don wani lokaci har mita take wai mutane kmr jira suke a kaisu gidan miji su dauki ciki su ko amarci basu bari sun gama ba..motsin shigowarshi tajiyo a parlor dan haka tayi saurin disconnecting call din tana cewa"malama sai anjima tunda bakida abun fada..my husband is back"..daga haka ta kashe wayarta tareda ajiye gefenta daidai lokacin kuma ya shigo dakin yana kokarin cire links din hannunshi...saukowa tayi daga gadon tana kallonshi da murmushi tace"sannu da dawowa"..yaja dogon hancinta shima yana mata murmushin yace"yauwa sannu love..Mummy na gaisheki"..dan marairaicewa tayi tace"ni bazanje gaisheta ba wai?.."kama hannunta yayi yana kallonta yace"zakije mana amma ba yanxu ba..daxun da bakinta tace in bari kiyi baccinki tunda da dare ba samun baccin kike ba"..ya karasa mgn yana wani kashe mata ido daya..nan take tsoro da firgici suka bayyana fuskanta tace"dan Allah haka tace da gaske?.."gyada kai yayi yana kunshe daria dake cinshi yace"yes mana..she even told me jiya taji ihunki da dare kina cewa azo a taimaka maki"..zare idanu ta sakeyi hadda su dafe kirji ga kuma hawaye da har ya ciko eyes dinta tace"shknn na shiga uku..yanxu bazan iya hada ido da itaba..wlh partner ka cuceni"..ta Karasa mgn tana wani rushewa da kuka kmr wanda akaima wani abun..Bobby dake dariar wnn rikicin nata ganin kuka takeyi da gaske sai yajata jikinshi ya shiga rarrashinta tareda ce mata shifa wasa yakeyi ba da gaske ba..har wani ajiyar zucia ta sauke data tabbatar da gaske wasan yake mata..yanxu idan da gaske ne ai ya gama cutarta wlh..ace sirika ta jiyoka kana ihu irin wnn ai abun ba kanta..saida yaga ta dawo nutsuwarta snn yake tambaya if da Billy yaji tana waya yanxu..da sauri tace"itace wlh..don mugunta wai fatan haihuwa takemun in the next nine months kmr abunda nazoyi knn"..murmushinshi ya fadada bayan ya gama cire links din ya zare rigar itama ya ajiyeta gefe ya rage daga shi sai singlet da dogon wando yayi pulling nata closer to him kafin yace"baby meye mugunta kuma a ciki?..fatan samun baby fa tayi maki ba wani abu"..girgiza kai ta shigayi tana wani ta6e baki tace"nidai inshaAllah bazan samu ciki anytime soon ba..ko amarci fa mutum bai gama ci sosai ba"..Bobby ya wara ido yana sake rike waist dinta fuskanshi daukeda wani shegen smile yace"really?.."shiru tayi tana kallonshi don sai yanxu ta fahimci 6arin zancen da tayi...shiko murmushinshi yacigaba dayi yana shafa fuskanta yace"kinada gaskia sosai love..ya kamata kici amarcinki yanda ya kamata".. marairaicewa tayi tana kallonshi kmr zatasa kuka tace"ni ba haka nake nufi bafa"..da sauri ya dagota sama yana kallon idanunta yace"cewa fa kikayi kinason kici amarcinki da yawa before conceiving"..da sauri ta hau girgiza kai tana cewa"ni bance haka ba wlh..kawai haihuwa ne banaso inyi da wuri fa"..yace"don't worry bazaki haihuba sai nan da wata tara..so we still have nine months to.."bai karasa ba ta rufe bakin da hannunta shi kuma ya saki murmushi tareda karasawa kan gado ya ajiyeta shima ya zauna yana wani yi mata kallon kasa kasa.. marairaicewa tayi tana rokonshi da idanunta amma ko gane me take nufi ma baiyi ba..right now ya shiga wani shaukin da ba komai zata fada ya iya ganewa ba..janyota jikinshi yayi a hankali snn yakai hannu ya zame dankwalinta ya Kuma hade fuskanshi da nata..lokaci daya ta rikice ta shiga yarfa hannu tana cewa"partner dan girman Allah kayi hakuri..wlh ban denajin ciwo ba"..finger dinshi ya dora akan lips dinta har yanxu kallonta yake eyes dinshi har sun canxa launi..nan ta sake rikicewa har ta fara hawaye tace"wayyo Allah Ammi..wayyo daddyna na shiga uku..dan Allah dan annabi kayi hakuri kaji?..banida lafia fa"..cupping fuskanta yayi da hannayenshi murya can kasa yace mata"please!.."tureshi ta shigayi tana kuka wiwi tace"baka Sona"..riketa yayi da kyau yanda bazata iya kwacewa ba yace"no it's the love..allow me to show yanda nake sonki plss"..tun bai rufe baki ba tace"aah wlh u don't love me..u always wants to suffer me"..bai sake cewa komai ba Saida yaja duvet ya rufesu dashi kafin a hankali yace"then let me show u exactly how much i love u..i..love..u..to the..moon"..ya karasa mgn voice dinshi na breaking sbd yanayin da yake ciki..ta bude baki zata kwarara masa ihu yayi grabbing bakin nata..daga haka nidai na tattaro kafafuna na baro musu dakin bayan na rufe musu kofa na koma parlor Ina duba agogo. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 60 Lokacin dana koma dakin kuka take mishi sosai wanda ko jiya batayi mashi irin wnn kukan ba..hankalinshi duk yabi ya tashi yama rasa taimakon daya kamata ya bata..da kyar ya samu ta bari ya taimaka mata wajen wanka shiga ruwan zafi snn ya fito da ita tana cigaba da rizgar kuka kmr dai yanka cikinta yayi ya fito mata da wani abun.. she's crying out loud kaman throat dinta zai toshe..drugs ya samu ya harhada mata tasha snn yasa mata dogon riga ta kwanta ba dadewa kuma bacci yayi gaba da ita..yaso ko dan tea ya hada mata tasha kafin tayi baccin amma yasan yana tashinta yanxu ya janyo ma kanshi tashin hankali..sai a lokacin shima ya samu nutsuwar shiga bathroom yayi wanka ya fito..jallabiya kawai ya dora akan singlet da shorts dake jikinshi snn ya tada sallahn magrib don already an riga an idar a masallaci..bayan ya idar yayi musu addu'a as usual snn ya mike ya maida carpet din inda yake ya koma ya zauna nan kusada ita yana kallonta..yanxu shi baisan ma yanda zai fara tashinta tayi sallah ba..yanda take wnn rikicin yana tashinta yasan rigima ne zai jama kanshi so gwara ya bari tayi baccinta duk lokacinda ta tashi sai tayi sallahn..hannu yakai ya gyara mata gashinta da bai samu damar daure mata shi ba daxun sbd kokawan da take...murmushi ya saki bayan yayi pecking lips dinta yana sake recalling abubuwada suka faru..she is super amazing domin kuwa duk wnn kuka da kokawan data ringayi bai hanashi jin dadinshi ba..yasan dole ne taji jiki tunda she's still new to the whole system amma ya zaiyi?.. it's not as if he can controls himself and he's 100% sure as time goes on zata dena..watarana ma da kanta zata nuna tanaso so ko kadan wnn rigiman nata bazai dameshi ba..hannu yakai forehand yaji akwai zafi kadan dan haka yaja duvet ya lullu6eta dashi snn ya dauki system dinshi ya fara aiki dashi..kawai tunanin yanda zasu kwashe da ita yake idan har ta tashi wnn zazza6in dake neman rufeta bai sauka ba..gashi kuma dole bazata iya shan magani ba saita tashi..haka ma bai isa yace zai fara mata allura yana bacci ba don wlh tlh yasna tara masa jama'a zatayi..yanda ta iya ihu dama ai tanajin saukan needle a jikinta bazata San sanda zata kwala ihun da duk mutanen dake cikin gidansu sai sun jiyo ba dan haka dole ya bari ta tashi a baccin idan fevern bai sauka ba sai yasan abunyi...ana Kiran sallahn isha ya fita da sauri zuwa masjid yayi sallahr ya dawo kuma har time din bata tashi a bacci ba..daya sake ta6a jikinta ma sai yaji zafin ya karu akan wanda yaji daxun..knn dai zazza6in kara gaba yakeyi ba baya ba..hankalinshi yaji ya tashi baisan taimakon daya kamata ya bata ba. Karfe takwas da yan mintuna ta tashi daga baccin..wurga ido ta shigayi yana son ganin ta inda zata ganshi ganin bata ganshi ba kuwa ta sake fashewa da kuka dama ga fever ya rufeta ruf..wato don rashin Imani kama gabanshi ma yayi ya tafi wani wurin sbd ya gama da ita..kuka takeyi sosai wanda sautinshi bai fita da karfi sbd zafin da jikinta yayi..shi kanshi kukan cikin karfin hali take yinshi don Allah kadai yasan yanda takeji..Bobby dake wanka a bathroom yana jiyo kukan nata ya zari towel dinshi ya fito da sauri ko karasa wankan baiyi ba sbd yanda hankalinshi ya tashi..karasawa yayi kusada ita ya zauna tareda dagota ya hadata da jikinshi yanajin yanda zafin temperature dinta har cikin jikinshi..a hankali ya ajiyeta tareda mikewa ya shiga closet dinshi ya jira jallabiya bayan ya zame towel din jikinshi ya fita da sauri zuwa main house don dauko drugs da injections daya kamata yayi mata..Saida yazo daidai kofan dazai maidashi gidan nasu ya tuna bai fito da key din kofar ba dan haka dole yabi ta gate ya fita snn ya zagaya zuwa gate din gidan nasu ya shiga ta nan..addu'a yake kada Allah ya hadashi da Mummy ko aunty sumy a parlor amma addu'anshi bai kar6u ba dan yana shiga yaci karo da gaba dayansu a dinning suna yin dinner..cikeda mamaki suka bishi da kallo Mummy tace"Kai lafia kuwa ka shigo a hargitse haka?..meya fito dakai ma a daren nan ka baro yarinyar mutane ita kadai"..juyawa yayi yana kallon inda suke yace"batada lafia ne Mummy shine nazo in sauki injection da zanyi mata"..hankali tashe tace"subhanallah meya sameta?.."a hankali yace"fever"..mikewa Mummy tayi daga inda take zaune ta shiga karasowa nan inda yake tana cewa"hope it's not that bad?..kodai asibiti zaka kaita?.."girgiza kai yayi yana kokarin kwantar da hankalinta yace"ai ba sosai bane Mummy nasan inayi mata alluran zata samu sauki"..ajiyar zucia Mummy ta sauke tace"to Allah yasa..yi maza ka dauka ka koma ka barota ita kadai"..da sauri yace"toh"..snn ya kama hanyar flat dinshi da sauri..aunty sumy dai na daga dinning tanayi musu daria daga shi har babar tashi..duk sun wani bi sun tashi hankalinsu kmr basu san abunda ke damunta ba..ita dai ko rantsuwa zata iyayi da kyar idan ba cin zali Bobby yayi mata take wnn fevern ba..dama a yanda taga take takenshi ai bazai yi sanya da yarinyar nan ba ko don sbd kaunar da yake mata..banda murmushi ba abunda take saki cikin ranta tana addu'a Allah yasa ma rabo aka samu shine ya haifar mata da fever..so kawai take taga ance yau ga Bobby da d'a ko 'ya sai taga wane irin kauna zai nunama 'ya ko 'dan..she just can't wait matarshi ta samu ciki ta haifa musu little Bobby. Yana daukan abunda zai dauka ya fito da sauri ya sake komawa can gidan..har lokacin kuma tana nan kwance yanda ya barta tana hawaye..karasawa yayi da sauri ya dagota zuwa a jikinshi ya shiga share mata tears din yace"kukan ya isa haka please"..kasa cewa komai tayi sai lamo da tayi a jikinshi..jin yanda har yanxu zafin jikinta bai ragu ba dole ya sake ajiyeta ya shiga bathroom ya debo lukewarm water a bowl ya hado da towel ya fito..wnn temperaturen nata yasan bazai ta6a sauka ba idan ba tepid sponging ya samu yayi mata ba..yana zama gefen gadon ya sake dagota zuwa jikinshi ya zare dan rigan dake jikinta snn ya jika towel cikin ruwan ya shiga shafa mata a jikinta a hankali..Aysha ta sake yin luf a jikinshi tanajin dadin yanda ruwan ke ratsa ilahirin jikinta..idanuwanta a kulle har ya gama shafa mata a ko ina snn ya dauko wani rigan yasa mata ya Kuma kwantar da ita kafin ya wuce zuwa kitchen..ruwa ya jona a kettle yana nan tsaye ruwan yayi zafi ya zuba ruwan a mug bayan yasa sugar,Milo da Madara yasa spoon a ciki yana juyawa ya fita daga kitchen din..yana shiga ciki ya dagota ta jingina da gado snn ya shiga bata tea din tanasha a hankali dukda ba wani dadinshi takeji ba don all of a sudden taji tayi loosing appetite dinta..Saida tasha sosai snn ya ajiye mug din ya dauki ruwan daya fito dashi daga fridge tun daxu ya 6alli magani ya bata tasha snn ya sake kwantar da ita yana tunanin yanda zaiyi mata allura..hannunta ya kama ta rike cikin nashi yana kallonta duk a rikice yace mata"baby anya ba injection zamuyi ba kuwa?.."girgiza kai tayi da sauri hawaye na fitowa daga idanunta tace"no plss..banaso".. marairaicewa yayi yana kallonta yace"amma fevern nan bazai sauka ba fa..indai ba alluran akayi ba i don't zai sauka da wuri"..kasa ce mishi komai tayi sai kai kawai ta iya girgiza mishi tana wani tale baki zata rushe mai da kuka yayi saurin rungumeta ga jikinshi yana shafa kanta yace"to yi hakuri na fasa..bazanyi maki ba Kuma"..shiru tayi tana sauke numfashi..sun dade sosai a haka yaji fevern nata ya sauka sai a snn ya samu ya taimaka mata zuwa bathroom ta dauro alwala ta fito ta gabatar da sallolinta duk a zaune don ko tsayuwa bata iyayi sbd azaba gashi sai wani bacci takeji don akwai maganin bacci cikin Wanda ya bata daxun..tana idarwa ya mikar da ita snn ya dauke carpet da hijabin da tayi sallahr dasu ya maida inda suke snn ya kwantar da ita na da nan kuma tayi bacci shi kuma yana nan zaune rike da hannunta sai kallonta yakeyi kmr abunda zai warkar da ita knn..jin ciwon nata yakeyi har cikin ranshi..gaba daya dana sanin abunda ya aikata ya shigeshi..da baiyi hakan ba yasan da kilan wnn zazza6in bai kama mashi ita ba..duk sai yaji inama ana iya transferring rashin lafia from one person to another shikam da yayi transfer nata zuwa jikinshi tunda yasan shi namiji ne zai fita dauriya and ciwon bazai wahalar dashi kaman yanda zai wahalar mashi da ita ba..ko abinci ranan kasa ci yayi tun Wanda sukaci da rana tareda ita..Mummy da aunty sumy sai kira sukeyi suna tambaya ya jikinta shi kuma yana ce musu taji sauki..har dare ya tsala sosai Bobby kasa runtsawa yayi..yana nan zaune yana gadinta kmr idan yayi bacci wani abun ne zaizo ya sameta..karfe daya ya shiga bathroom yayi alwala snn yazo yayi nafilah raka'ah hudu yayi addu'o'inshi snn ya hau kan gadon ya kwanta bayan ya sanyata a jikinshi yaji har zuwa lokacin zazza6in bai dawo ba dan haka shima bai jima da kwanciya ba baccin yayi gaba dashi..can dare ya sake dawowa sabo don har baccin ma kasa komawa tayi sbd zafin da jikinta ya dauka dole haka Bobby yayi mata alluran dai da bataso shima kuma bada son ranshi ba..dambe sosai sukayi da ita kafin ya samu yayi mata har mamaki ma ta bashi ganin ba lafia gareta ba amma ta iya kokawa dashi kawai sbd batason injection..shi duk randa akace ta samu ciki baisan yanda zai nayi da itaba tunda dai ko rashin lafia baisa anyi mata allura ba dole za'ayi mata tt idan taje antenatal..shi kanshi haihuwan ma idan yazo dole za'a mata allura so duk idan Allah ya kawosu baisan yanda za'ayi da ita wajen yin alluran ba..rigima ne yasan zai Sha daga wurinta kala kala amma zai dauki duk me zata mishi ko don son da yake mata..wani murmushi ya saki kawia sbd tunanin yanxu watarana haka zata samu ciki ta haifa mashi baby mai kama dashi ko mai kamada ita..baisan irin farin cikin da zaiyi ba idan Allah ya nuna mashi wnn rana..yanason gani sosai..yanaso yau ace ga d'a ko 'ya Lamido ta haifa mashi..yasan kilan duk wani so da kaunarshi zai tattara ya koma kan babyn sbd tsananin son da yakewa mamanshi. Washegari Alhamdulillah ta tashi da sauqi sosai don babu fever a jikinta snn duk wani wuri dake mata ciwo jiya yau bata tashi da ciwon ba saidai tunda ta tashi da shagwa6a ta tashi don banda kuka ba abunda take mishi wai ya tsaneta shi kuma ya rikice sai aikin rarrashi yake..ko wanka saida yayi da gaske snn ya samu tayi daga nan ya bata tea da magani tasha maimakon tayi bacci sai ta dora daga inda ta tsaya..kuma duk tana sane take wnn iskancin wai acewarta wahalar daya bata jiya ne take fanshewa sbd shima yaji a jikinshi kmr yanda taji..dama a dunia ba abunda take so kmr tayita zuba ta6ara ana biye mata yau kuma sai abun nema ya samu wai matar driver ta haifi mota..sosai ta rikitashi da wnn iskance iskancen ko breakfast bai samu yayi ba har yanxu don hanashi motsawa tayi ko na da can yana tashi zata fara kuka tana bubbuga kafa wai zaije ya barta..haka nan bawan Allah zai dawo yayi zaune yana rikeda ita yana bata baki amma duk a banza..kallonta kawai yake yanda take shagwaban yana lallashi sa abun ya burgesu matuka..bai taba sanin akwai ranar da zaiji irin wadan nan abubuwan na burgeshi ba saida ya hadu da ita..wato dai ita koma me zatayi yanaso kuma abun sha'awa ne a wurinshi..saida tayi bacci snn ya samu ya shiga bathroom don yin wanka..ita kuma yana shiga ta bude ido tana kyalkyala daria cikin duvet sbd kar yajiyota..draman nasu ba karamin kayatar da ita yake ba..ai wlh saita fanshe duk walakancin da yayi mata jiya shima sai yaji idan da dadi kasa mutum a gaba kayi masa abunda bayaso..tanajin fitowarshi tayi saurin maida idonta ta kulle shi Kuma ya karaso ciki dakin daure da towel a waist dinshi sai wani karami a hannunshi yana gashin kanshi..stool din gaban mirror ya janyo ya zauna snn ya shiga shafa cream ita kuma ta bude ido tana kallonshi daga kwncen da take yanda bazai gane tana kallonshi ba..broad shoulders dinshi ta tsaya kallo yanda suke nan fari tas don jikinshi har yaso yafi face dinshi haske..ga skin dinshi har wani glowing yakeyi sbd tsabar gyara kmr skin din mace..yana gama shafa cream ya shiga shafa mayukan gashinshi tana combin kanshi daga nan kuma ya dawo kan sajenshi da duk fuskanshi babu abunda take qauna kamarshi..tana kallon yanda ya shafeshi da mayuka masu kyau snn yayi using brush comb ya taje tun daga sajen har zuwa gemunshi..kallonshi kawai Lamido keyi tana murmushi ashe dai haka mijinta yake dan gayu bata sani ba..haba no wonder kullum wnn sajen nashi ke kara laushi da sheqi ashe kudi yake kashe mashi haka..yana gamawa da sajen ya shiga shafa turarukanshi masu masifar qamshi..tun tana kallonshi a kwance har batasan lokacinda ta mike zaune tareda tallabo cheeks dinta da hannayenta ta wani tsura mishi ido tana murmushi ba..duk yanda takai da son tayi fushi da mutumin nan bazata taba iyawa ba..she loves him to the extent that kome zai mata bazata iya dogon fushi dashi ba..yanxu dai gashi duk wahalan da tasha jiya a dalilinshi kallonshi kadai yasa ta manta da duk wahalan data sha sai more kallonshi takeyi kmr yau ta fara ganinshi..Bobby kuwa tunda ya fito bathroom dama yasan idonta biyu don ya lura da yawan motsin da take nuna mata ne kawai baiyi ba yayi pretending kmr baisan tana idon nata biyu..and koda ma baiyi noticing motsinta ba ya tabbata daga lokacinda ta kafa mashi wadan nan idanun nata dole zai fahimci kallonshi takeyi sbd tasirin da idanun nata ke dashi a tareda shi..kai tsaye suke piercing har cikin zuciyarshi so babu yanda za'ayi ta dauki tsahon minti guda tana kallonshi dasu ba tareda yaji a jikinshi cewa kallonshi takeyi ba..abun kuma ba karamin qayatar dashi yayi ba..gashi dai ita take kallonshi amma yasan ko ita bazata kaishi enjoying kallon nashi da take ba don kallo ne mai cikeda so da kauna ba ordinary kallo bane da ake iya samunshi wurin kowa da kowa..special kallo ne da sai mutumin da ake mutuwar so za'ayi ma irinshi and he's glad she does that don hakan ya sake tabbatar mashi da cewa matarshi Aisha na tsananin kaunarshi kmr yanda shima yake tsananin kaunarta dukda yasan nata son bai kama kafar wanda yakeyi mata ba..murmushi ya saki bayan ya kammala duk abunda zaiyi ya juya ya nufi closet dinshi bayan ya kashe mata ido daya..daria ta saki itama tana binshi da kallo sai kuma ta sauka daga gadon daga ita sai yar rigarta da baifi iya guiwarta ba ta nufi closet din nashi itama..ciki ta shiga ta ganshi yana neman kayan da zai sa..a hankali ta karasa ta tsaya a bayanshi tareda fadawa jikinshi tayi mashi kyakykywan hug ta baya..saida ya lumshe don dadi har baisan time din da rigar dake hannunshi ya zame ya fadi kasa ba..yana jinta a jikinshi yaji kmr komai nashi aka dakatar sbd tsabar shaukin da ta shiga..shi har yanxu mamakin wnn emotions din da kullum sake sabunta kansu suke..a tunaninshi tunda sunyi aure kuma har sun zama daya zai samu saukin wnn emotions din amma it's like abun ba haka yake ba sam..sai yakega ma kmr abun karuwa yakeyi akan na baya..lumshe Ido yayi yanajin yanda duk wani ga6a na jikinshi ke amsan sakonnin da take tura mashi in a breaking voice ya kira sunanta"Ay..sher"..kasa amsawa tayi ta kwantar da kanta a bayanshi tanata faman murmushi..a hankali ya juyo da ita suna facin juna yayi cupping fuskanta da hannayenshi full of excitement yace"I love u so so very much baby..duk dunia nasan idan aka dauke daddy da Ammi baza'a samu Wanda ke sonki kmr yanda nakeyi ba..i love u sosai"..ya karasa mgnr yana hada face dinshi da nata..Lamido da farin cikin dunian nan ya isheta sbd wnn kalaman nashi sai kace yau ta fara jinsu daga bakinshi kasa dena washe baki tayi kmr gonar audugu..dan dagen kafa tayi ta dafa shoulders dinshi da both hands dinta sbd yafita tsaho sosai ta samu ta manna mashi peck a tip of hancinshi don tsayinta kasa kaiwa forehead dinshi yayi sbd tsayinshi..tana gamawa Bobby ya rungumeta da kyau yana blowing mata kisses ta ko ina yana murmushi..wlh bai ta6a sanin haka aure yake ba..tabbas da yasan haka zama aure yake kilan da tun lokacinda ya fara sonta zaiyi duk yanda zaiyi yaga ya aureta tun kafin a kawo wnn lokacin..baisan ko nashi auren ne yazo a haka ba sbd sonda yake mata oho..bakinta yakai saitin kunnenta ya sake mata whispering"i love u"..murmushi take sosai ta dago tana kallon idanunshi tace"nima ina sonka sosai..i can't imagine my life without u..i love u so much"..pecking forehead da cheeks dinta yayi yana cigaba da smiling..a hankali ta janye daga jikinshi ta sunkuya ta dauko mashi rigan daya yar a kasa..Mika mashi tayi tana murmushi instead of ya kar6a sai ya makale mata shoulder dinshi yanayi mata nuni da finger dinshi wai tasa mashi da kanta..batayi musu ba ta balle botles din rigan shi kuma ya rage tsayinshi daidai yanda zata iya sa mashi ta zura mashi rigan snn ya mike yana gyara collarn rigan..ita tayi mashi buttoning rigan ta saka mashi links snn ya Miko mata trouser wai shima ta saka aikuwa ta fice daga wurin da gudu tana mishi daria..shima darian ya saki yana ayyana lallai ta wareke tunda har take iya gudu har haka..Sharp sharp ya karasa sa kayan ya sake gyara gashinshi jikin mirror dake nan ciki snn ya fita..bai sameta nan dakin ba harta gama gyara gado ta fita dan haka ya fice shima zuwa bedroom da yasan dole nan zai sameta..bai sameta a nan ba saida ya bude another one ya ganta a ciki tana kokarin saka skirt dinta..tayi wanka dama tun daxu so tana shigowa kaya ta dauka ta fara sawa don yau kome zaiyi sai taje gaida Mummy wlh..yana karasowa ciki ta gama veiling dinta dan haka ta shiga dubanshi tana dan daure fuska tace"nifa yau zuwa zanyi in gaida Mummy"..kallonta ya danyi kafin ya saki murmushi gamida girgiza kanshi yace"ba sai kinje ba tace da kanta zata shigo dubaki anjima"..ai tun bai rufe baki ba ta sake dinke fuska tana binshi da wani kallo tace"nidai wlh sai naje..ai ba daidai bane ace har sai itane zatazo inda nake ni banje na gaisheta ba"..murmushi yake cigaba dayi cikin ranshi yace"abubuwan sun motsa knn?.."a zahiri kuma matsawa yayi kusa da ita ya kama hannunta yace"to meye abun 6ata rai kuma baby..shknn kisa hijab dinki muje".. kallonshi da wani expression a fuskanta tace"ban gane hijab ba..daga nan zuwa gidan naku zakace insa hijab?.."hannu yakai zai sake kamo dayan hannunta tayi sauri kaucewa tana hararanshi..bai sake cewa komai ba ya karasa ya kama hannun nata suka fita daga dakin..wanda aka fara ajiyeta a ciki suka shiga ya saki hannun nata a nan shi kuma ya shiga closet ya dauko mata katoton hijab ya dawo ko mgn baiyi mata ba ya janyota ya zura mata shi ba tareda ko veiling dinta ya cire ba..ya kalleta from sama zuwa kasa then from kasa zuwa sama yaga komai na jikinta a rufe yake dan haka ya saki murmushi yana shafa gemunshi yace"perfect..now we are good to go"..banza tayi dashi ta dauke kai tana turo baki..shi kuma ya kama hannunta a haka suka fita daga gidan..bayan sun fito compound ya saki hannunta yayi locking kofa snn ya sake kama hannun nata suka nufi kofan da ake koma cikin gidan nasu ta nan..sai yanxu Lamido ta samu damar karema compound din gidan nata kallo don tunda aka kawota bata sake fitowa ba balle ta kalleshi da kyau..yanada girma sosai da akwai motocinshi guda biyu daga can gefe sai kofan da suka nufa shima yana daga gefe don ba kowa ma zai fahimci akwai kofa a wurin ba..tayi mamaki da taga ashe gidanta da main house din nasu kusa da kusa suke saidai kowanne gate dinshi daban sai dan kofa da akayi wanda zasu iya shiga main house din ba tareda sunbi ta gate ba..sosai yanayin tsarin wurin ya burgeta..suna karasawa Bobby ya bude kofar nan suka fada gidansu Mummy. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 61 Suna shiga aunty data fito daga kitchen ta rike baki baki tana kallonsu da mamaki sosai tace"yanxu Bobby mara lafiyan ka dauko ka fito da ita sbd rashin hankali?.."tana gama fadin haka kuma ta karasa inda suke tareda kama hannun Aysha ta rike cikin nata tana kallon with concern tace"kema kika yadda ya fito dake bakida lafia Aysha?.."sunne kai tayi tana murmushi tace"ai naji sauki aunty"..cikin ranta kuwa haushi taji da yazo ya tona mata asiri a wurinsu..yanxu shknn tasan da kyar idan basu san menene ma yayi coursing zazza6in nata ba..amma dai ya cuceta wlh..kamata aunty sumy tayi suka karasa parlor yayinda shi kuma yabisu da kallo yana murmushi..wnn son da suke nuna mata ba karamin faranta mishi rai yake ba..yana son yanda suke tayashi sonta sosai ba kadan ba..karasawa yayi ciki shima ya zauna yana kallon aunty sumy yace"ita fa da kanta tace sai na kawota shine zaki wani tsaremu da mgn ko welcoming dinmu bakiyi ba"..harara ta juya ta sakar mashi tana nuna Aysha tace"ita dai ya kamata inyi welcoming amma ba kai ba..dan rainin hankali kawai"..daria sosai yasa hadda girgiza kai yace"siriki ne dai dake kuma har yanxu baki dena wadan nn abubuwan ba"..shiru aunty sumy tayi tana kallonshi don dama ranar daya fada mata haka Saida taga alamun da gaske yake..ta bude baki zatayi mgn Mummy ta fito daga flat dinta tace"hayaniyar me nakeji ne haka?.."da sauri Bobby ya mike ya karasa gareta yana kokarin fadawa jikinta cikin igbo yace"Mummy nah"..Mummy dake murmushi tayi saurin kaucewa tana daria tace"let me welcome my daughter first"..daga haka ta wuce cikin parlon tana cigaba da mishi daria shi kuma ya wani tale baki kmr zaisa mata kuka yace"Mummy ni Koh..ni kikaima haka Koh..shknn nagode"..batace mishi komai ba tana isa inda Aysha take ta dagota tareda rungumeta a jikinta tana cewa"welcome to your Family daughter"..wani irin kunya ne ya kama Aysha tama rasa inda zata 6oye kanta sbd ita..gashi Mummy ta rungumeta har yanxun taki rabata da jikinta..aunty sumy na kallonsu with a very wide smile tace"Mummy bakiga kyan da kukayi a haka ba wlh..let me call Sab yazo da camera yayi muku hoto a haka a gaskia..kunyi kyau fa sosai kaman a daukeku a gudu"..Murmushi Mummy tayi tareda janye Aysha daga jikinta tana kallonta da fara'a tace"ya jikin naki?..hope bashi ya takura maki zuwa bayan bakida lafia ba"..girgiza kai Aysha tayi tana sunne kai duk kunya yabi ya isheta wlh..Bobby dake tsaye inda Mummy ta baroshi yana binsu da kallo tun daxu sai yanxu ya samu damar karasowa cikin parlon shima ya samu wuri ya zauna nan inda suke zaune yana fadada murmushin fuskanshi sbd farin cikin yanda suka tarban mishi ita..durkusawa tayi har kasa tana gaishesu yayinda Mummy ta dawo da ita zaune tana ce mata ta dena wnn durkuson ita dai ta yafe mata..aunty sumy da kanta ta shiga kitchen ta kawo mata lemo da ruwa dasu cupcakes tace ta fara ci kafin a karasa abinci..sai nan nan sukeyi da ita kmr zasu maidata ciki sbd soyayya ita sai kunya suke bata wlh..Mummy sai ce mata take duk Bobby yayi mata abunda ba daidai ba tazo direct ta fada mata ita kuma zatayi mata maganinshi itadai har yanxu babu bakin mgn sai na murmushi..mutanen nan ba karamin burgeta suke ba..dama tun ba yau ba tasan yanda suke gudanar da rayuwarsu cikin so da kaunar juna tasan Kuma inshaAllah bazata samu matsala dasu ba..ganin bata ta6a komai da aka kawo mata ba Bobby da kanshi ya zuba mata lemo a cup ya hada da cup cake din yana mika mata ita kuma tayi kmr bata gani ba don kunya yake bata..aunty sumy na hada Ido dashi ta sakar mashi harara shi kuma ya kashe mata ido daya yana cewa"to ko abinci bataci ba matsa saina kawota wurinku..yanxu kuma an kawo naga kunya ya hanata ci shine zan bata da kaina"..ba aunty sumy kawai ba har Mummy Saida tayi darian wnn rashin kunyan nashi.. Bobby da Aysha dama ai tasan zaiyi rashin kunya tunda tasan soyayyar da yake mata ba ordinary so bane..fatanta dai Allah ya dawwamar da wnn farin cikin da suke ciki har karshen rayuwarsu.. Allah kuma ya basu zuri'a masu albarka...suna nan zaune sunata janta da labari tun tana jin kunya har daga baya ta ware suka cigaba da labarin da ita..Kiran Nur ne ya shigo wayanshi ya dauka nan yake ce mashi photo albums dinsu ne na biki aka kawo mashi so yana kofar gida ya fito a amsa..Bobby yace ya shigo main house kawai don suna nan tareda Ayshan..babu wasting of time Nur ya shigo cikin gidan yana cin karo da aunty sumy sai yaji kunya ya lull6eshi musamman daya ga irin kallon da Bobby ke jifanshi dashi yana murmushi.. Allah dai yasa ba zuwa yayi ya tona mashi asiri yace musu yace yana sonta ba..yasan halin kayanshi tsaf zai iya aikata hakan amma dai daya gama dashi..har ya karaso cikin parlor ya zauna bai yadda ya hada ido da itaba yana zaunawa ya shiga gaida Mummy ita kuma ta amsa mashi with smile tana tambayanshi ya gajiyar biki yace gajia yabi lafia..a nutse ya juya yana gaida aunty sumy da hankalinta gaba ke ga albums data gani a hannunshi..bayan ta amsa gaisuwan nashi tace"wnn albums din biki ne a hannunka?.."kai a kasa Nur ya mika mata allbums din yana cewa"eh"..aunty sumy ta amsa ta fara dubawa yayinda shi kuma Nur suka shiga gaisawa da Aysha..sai tsokanarta yake wai har ta fara kumatu itadai sai murmushi don ba saba irin wnn wasan tayi dashi ba..har yanxu daukanshi take matsayin College Provost dinsu so bata iya sakewa tayi wasa dashi kmr yanda yake mata..aunty sumy dake kallon pictures din biki sai zuzuta kyan da sukayi take tana nunama Bobby dake zaune kusada ita wani picture da sukayi gaba dayansu tace"dan Allah wnn baiyi kyau ba Bobby..kallemu fa kmr wasu larabawa".. Bobby dai daria kawai yake yana kallon Nur da yake satar kallonshi yana Maka mashi harara..for the first time yau yakejinshi wani irin cikin familyn Bobby..wani sabon kunya ne ya shigo tsakaninsu sakamakon son nan da yakewa Miemie amma da shi ba haka yakeji idan yana cikinsu ba wlh..sakewa yake yayi abunda yaga dama don daukansu yakeyi daya da family dinshi amma yanxu wnn is gone sai jin kunya da sunkuyar da kai kawai..Saida ta gama kalle hotuna tsaf tana zuzutasu snn ta mikama Aysha tana ce mata"ungo wnn ki fara gani Aysha kafin Mummy ta gama da sauran".. Mummy tace"aah kuyi kallonku ni zan gani a nutse ba lallai sai yanxu ba"..Aysha batayi musu ba amsa album din tana kallon yanda cover dinshi yayi bala'in kyau tasan cikin ma dole yayi kyau shiyasa aunty sumy tayita exergerating..page din farko ta bude nan taci karo da wani beautiful picture dinsu ita dashi ya wani rike mata hannu yana kallonta itama tana kallonshi tana murmushi..a can saman page din kuma in italics aka rubuta The Waziri's Meets The Lamido's sai daga can kasa kuma aka rubuta Attahir Waziri Weds Aysha Lamido..sbd tsabar farin ciki batasan sanda ta lumshe ido takai hannu tana shafa ilahirin page din ba..yayi mata kyau ne nesa ba kusa ba..ya kuma kayatar da ita kwarai..a nuste tacigaba dabin pictures din tana kallonsu daya bayan daya tana murmushi daidai lokacin kuma Miemie da Sab suka shigo parlon..tun safe suka fita ya rakata tayi registration na jamb shine sai yanxun suke dawowa..Bobby najin sallamarsu ya juya da sauri yana kallon Nur sai kuma ya fashe da daria har yana tafa hannu..Mummy tace"kai bakada hankali ne?..wnn wane irin daria ne?."tsayar da dariar yayi yana kallon Nur yanxu yace"Mummy karki damu abokina nake yiwa"..juyawa Mummy tayi ga Nur tace"is he alright?.."da sauri Nur yace"wlh he is not Mummy..amma ki barni dashi nasan yanda zanyi maganinshi"..girgiza kai kawai Mummy tayi tana jinjina wnn iskancin na Bobby..daga yin aure kuma sai ka zama shashasha?..to Allah ya shirya..su Miemie na karasowa da taji sunyi komai normal ta mike zuwa flat dinta don bazata iyama wnn iya shegen na Bobby ba..cikin ranta kuwa farin ciki take sosai na ganin yanda walwalarshi ya dawo haka..bata ta6a tsammanin zuwan lokaci irin wnn da Bobby zai dawo rayuwa normal kmr kowa da kowa ba..ko a haka saidai tace Alhamdulillah don ubangiji yayi mata komai sai kuma fatan gamawa da dunia lafia..Nur da tun daxun kanshi ke kasa sai yanxu ya samu damar dagowa yana kallon Miemie don har yanxu aunty sumy bata gama kallon pictures ba..daidai lokacin itama ta kalli inda yake aikam suka hada ido Nur har cikin ranshi yaji wani abu amma ya danne ya shiga kallonta yana murmushi..murmushin itama ta saki tareda karasawa ta zauna kusa dashi tana kallonshi tace"uncle Nur ina yini"..da sauri yace"la..lafia..lau..ina kukaje..haka?.."Miemie tace"registration din jamb naje nayi kasan mun kusa graduation"..gyada kai ya shigayi yana dubanta da murmushi yace"MashaAllah ashe pretty ta kusa graduation..to Allah yasa albarka"..tana murmushi tace"Ameen..saura baifi 2 months ba mu fara waec"..yace"Allah ya bada sa'a"..tace"Ameen Uncle Nur"..daga haka kuma sai ta bar inda yake ta koma wurin Aysha ta wani rungumeta tana murmushi tace"aunty Aysha sannu da zuwa"..kafin Aysha tayi mgn Bobby yayi saurin janyeta daga jikinta yana mata wani kallo yace"are u mad?.."dan turo baki tayi tace"naji dadin ganinta ne fa"..Bobby ya matsar da ita daga wurin yace"oya San inda dare yayi maki kuma kar na sake ganin kinyi mata irin wnn abun dan ranki saiya 6aci"..zaunawa tayi kusada mamanta tace"to kayi hakuri"..Nur dake gaisawa da Sab duk yana sauraron wnn iskancin na Bobby yasan kuma da gayya yakeyi haka sbd ya kular dashi and he succeed..sbd presence na aunty sumy a wurin yasa bazai kulashi ba amma dole ma yayi maganinshi wlh don ya fuskanci walakancinshi karuwa yayi bayan auren nan nashi..bayan sun gama kallon albums din an gama lunch don haka duk sukaci abincin tare daga nan kuma Bobby yabi Nur suka fita zuwa hospital bayan yayi sallama da matarshi yace ta zauna nan tare dasu Miemie idan ya dawo sai ya biyo ta nan ya dauketa. Bayan sati biyu... Rayuwa suka gudanar mai cikeda soyayya cikin sati biyun nan..duk wanda ya zauna dasu yaga yanda suke concentrating akan junansu abun zaiyi matukar burgeshi don sai kayi tunanin a cikin gidansu aka halicci soyayya..they are the perfect couple da basa gajia da nunama juna love and affection..duk au biyun are meant for each other and each one of them can die for the other..hatta su Mummy da sauran yan gidan sun auren nasu aure ne irin na soyayya wanda ba ko ina ake samun irinshi ba..kusan kullum suna tare a gida don hutun one month ya dauka na zuwa aiki dan haka bai fita sai idan akwai emergency case da babu wanda zai iya handling sai shi..kullum yana nan tareda ita sai kuma main house da yake shiga gaida su Mummy amma ita ba kullum yake barinta zuwa ba..a halin yanxu batada problem din komai domin ko kewar su Ammi da takeyi yanxu ya ragu sosai sbd tsabar kulawan da yake bata wani lokaci har mantawa ma takeyi da kowa na dunia🤣..saidai kusan kullum zatayi waya dasu dan ko bata kira ba Ammi na kiranta ko su Husna sbd haka rayuwa is full of happiness a garesu baki daya sai dan abunda baza'a rasa ba na bahaushe da yake cewa zo mu zauna zo mu sa6a..masu aiki har biyu Mummy tasa aka kawo mata amma tace guda daya ma ta isa dan haka aka sallami dayar ita kuma daya ta zauna tana dan tayata su shara da mopping da sauran aiyukan gida..girki dai da kanta take abunta saidai ta dan taimaka mata haka gyaran 6angaren mijinta da bedrooms dinta shima da kanta takeyi ita mai aiki iyakarta gyaran parlor,dinning dasu kitchen sai kuma ta kama mata wasu abubuwan..dakinda take kwana yana daga can gefe so tana kammala aiyukanta dama can take komawa dan haka babu takura a tsakaninsu..abu daya dake dan damunta shine rashin fita da baya barinta..shi koda yaushe yafiso suyita zaune a gida kmr a nan aka halicce su musamman ita da ko compound bai cika son tana zuwa ba wai ko baki zata raka ta tsaya iya kofar parlor shi bai yadda ta fita compound masu gadi na kallonta ba..wnn shine kadai damuwarta sai kuma asibiti da takeso ya barta ta fara zuwa sbd mates dinta gaba daya suna asibiti waiting results amma banda ita hakan kuma ba karamin damunta yake ba..gani take kmr idan ta dauki lokaci mai tsaho bata aiki skills dinta na iya guduwa su barta and ko Allah yasan batason haka ita da takeson wucewa Cyprus ta cigaba da karatu ai bazata so tayi loosing skills dinta sbd rashin practicing ba dan haka ta kuduri niyyar sanar dashi ya barta ta fara zuwa ko Freedom ne don tasan ko rasuwa zatayi bazai bari taje wani asibiti apart from nashi ba..ita sai yanxu wnn kishin nashi ke damunta wlh..ta lura ba karamin kulle hakan zai haifar mata ba and Allah ya sani ita bazata juri kullum tayita zaune a gida kmr wata mara abunyi ba..yanxu ko aiki ta samu batasan da yaya zai barta tayi ba da wnn shegen kullen da yake mata..kullum kuma tana cikin hijabi kmr matar malam..ko Nur ne zaizo gidan haka zai zunduma mata jibgegen hijabi a jiki tayita fama dashi wani lokaci ma sai taji kmr tasa kuka..tun jiya take tunanin yanda zata fada mishi tana son komawa asbiti amma batasan ta yaya ba kawai addu'a take Allah yasa kai tsaye yace mata ya amince taje aiko da batasan farin cikin da zata tsinci kanta a ciki ba. Tun daxun da ya kirata yace gasu nan zuwa tareda Nur tayi saurin karasa girkin da take tareda taimakon mai aikinta mai suna saude suka jera komai kan dinning snn ta wuce dakinta don yin wanka ita kuma saude ta karasa gyara kitchen snn ta dauki abincinta ta wuce dakinta kmr yanda ta saba...Aysha na fitowa daga wanka ta dauko wani riga da skirt na atampa ta saka ta kafa daurin dankwalinta da yayi das a kan nata snn ta kawo veil daya shiga da atampar jikin nata ta yafa tunda dai tasan ko rasuwa zatayi bazai barta ta fita ba tareda wani abu a jikinta ba..mayafin ma tasan da kyar idan ba cewa zaiyi ta cire ba amma addu'a take Allah dai yasa ya barta dashi yau daya dai itama ta saka abunda takeso..bayan ta gama gyara fuskarta ta dauki turare daga kan madubi zata shiga fesawa a jikinta kawai taji an rike hannunta kmr daga sama ya kwace turaren daga hannun nata ya ajiyeshi nan inda yake snn ya juyo ta yana kallon fuskanta yace"wai bana hanaki sa turare idan Muna tareda baki ba?.."marairaicewa tayi tana kallonshi bata dai ce komai ba..shi kuma ya saki smile yana sake matsawa jikinta yaja cheeks dinta da hannayenshi yace"kinyi kyau sosai"..murmushi kawai ta saki tana gyada kai har yanxu bata ce komai ba shi kuma yace"tareda Nur muke dauko hijab dinki muje"..sake marairaicewa tayi tana dubanshi da puppy eyes tace"partner dan Allah inje a haka..kaga veil din dana yafa fa mai girma ne"..girgiza mata kai Bobby ya shigayi tun ma kafin ta rufe baki yace"bazan iya ba wlh..there is no way da zan bari ki fita bayan duk wnn kyan da kikayi"..kallonshi kawai take kmr tasa kuka..a fusace ta bar wurin ta koma kan gado ta zauna ta rungume hannaye tace"to kaje ka sallameshi da kanka ba sai nazo ba"..karasawa yayi shima ya zauna yana yin kasa da murya yace"yanxu baby sbd..."bai karasa ba ta mike ta bar mishi dakin duk rai a 6ace..da sauri shima ya mike yabi bayanta nan yaga ta bude kofa zata shiga daya bedroom dinta yayi saurin kamota yana cewa"ki tsaya muyi mgn plss..ya kamata ki fahimceni love..inada kishi sosai akan duk wani abu da nakeso..yanxu kina ganin.."still bai karasa ba ta katseshi da fadin"shine nace kaje ka sallami bakonka kai kadai ba tareda ni ba"..ganin juyawa tayi zata shiga dakin yasan kuma tana shiga kulle kofa zatayi yayi saurin rungumeta ta baya ya lumshe ido yace"to..kiyi hakuri..yanxu kije da veil din amma next time bazan yadda ba"..banza tayi dashi ta wani tureshi ta wuce parlon tana murguda masa baki shima yabi bayanta yana jijjiga kai..ita dai har abada bazata dena wnn rikicin nata ba..kan a very minor abu zata daga mashi hankali kuma idan baiyi yanda takeso basu ba zaman lafia..ya fuskanci ita din hukuma ce saida lallashi..zaune ya sameta a parlor suna gaisawa da Nur daga nan kuma tayi mishi introducing abinci dake dinning ba musu suka karasa dinning don dama tareda yunwar su suke..saida ta gama serving dinsu komai snn ta bar dinning din tanajin yanda Nur da har ya fara cin nashi abincin keta santi yana cewa abokinshi yayi sa'ar mata data iya sarrafa abinci..itadai murmushi tayi tareda komawa parlor..saita tuna a gida yanda sam bata son girki..shiyasa kusan kullum suke rigima da Ammi kan aiki ita kanta bata ta6a zaton akwai time da zaizo wai taji bazata iya bari wata tama mijinta bincin da zaici ba..duk kiyayyanta da shara dasu wankin toilet yanxu da kanta take na flat dinshi kuma ko kadan hakan baya damunta saima faranta mata da yakeyi..at least bata bama wata mace kofar da zata shigo rayuwar mijinta ba..hakan da takeyi kuma na burgeta..yanxu ta dauki full responsibility dinta na house wife duk wani aiki daya kama na mijinta ne da kanta take yinshi..tana nan zaune har suna gama cin abincin suka dawo parlor Nur har yanxu bai bar santin girkinta yana cewa ta ita abinci ba..ita kuma kallonshi tayi tana murmushi tace"Sir kar ka damu da kaina zan koyawa Miemie yanda nake girki sbd idan ta iya ta dinga yi maka a gidanka"..wani irin zare Ido Nur yayi yana mamakin abunda take..jmya juya yana kallon Bobby dake danne daria yace"amma kaci amanata..yanxu zuwa kayi duk ka fada musu nace ina sonta?.."da sauri Bobby yace"ni ba wanda na fadawa sai ita kuma itama believe me bani na fara fada mata ba da kanta ta gano sbd shegen rawar kanka dan haka stop blaming me..wnn rawar kan naka yasa ta gane ni kuma data tambayeni nace mata its the truth"..dafe goshi Nur yayi yana murmushi kmr bazai sake mgn ba can yace"amma dai baku bari ta sani ba koh?.."harara Bobby ya watsa mashi yace"kasan ko aikena kayi bazanyi such mgn da itaba balle baka aikeni ba..da bakinka zaka fara fada mata inshallah"..ajiyar zucia ya sauke yana murmushi ita kuma Aysha ta koma dinning din ta gayar inda suka bata snn ta koma daki don bata cika son zama if yana tareda baki ba musamman Nur da har yanxu ta kasa sakewa dashi as abokin mijinta. Da dare suka shiga main house sakamakon kiranshi da Mummy tayi tace yazo tareda Aysha tanason magana dasu. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 62 Tun daga compound da yaga bakuwar mota yasan lallai sunada baqi a gidan maybe ma shine dalilin kiran nasu da Mummy tayi saidai suna shiga parlor yaci karo da akasin haka..baban su Miemie ne zaune cikin parlon sai aunty sumy da yaran nasu gaba daya..duk yanda yaso kar ya tuna abun da suka faru a baya kasawa yayi dan yana ganinshi yaji komai ya shigo dawo mishi kmr yanxu abun ke faruwa..yana ganinsu ya taso da sauri yazo inda suke yana mika mai hannu da murmushi..Mika nashi hannun shima yayi yana kokarin ganin ya danne abunda yaji cikin ranshi suka shiga gaisawa a haka..bayan sun gama ya kalli Aysha itama suka gaisa duk yayi congratulating dinsu on their marriage..du Miemie ma suka gaidasu snn ya kama hannun matarshi suka nufi flat din Mummy..tana zaune parlor ita kadai suka shigo ciki..tana ganinsu ta saki murmushi har suka karaso ta kama hannun Aysha dake kokarin durkusawa a kasa ta zaunar da ita nan kusa da ita tace"har yanxu bazaki dena wnn ba koh"..murmushi kadai tayi kanta kasa..batasan meyasa har yanxu ta kasa sakewa da itaba..kunyarta takeji sosai ba kadan ba..bayan sun gaisa Mummy na dubanshi tace"Kun hadu da Isma'il a parlor?.."yace"na ganshi Mummy"tace"Waziri ne ya kira wai yazo su sake daidaitawa tunda auren bai yiwu tareda naku ba idan sun daidaita sai a maidashi nan da sati biyu"..gyada kai kawai yayi yace"to Allah tabbatar da alkhairi".. Mummy tace"Ameen ko har yanxu bakason mgnr ne?.."da sauri yace"aah indai taga zata koma ai inaga hakan zaifi ko dan sbd yaran ma".. Mummy tace"ko daxu da yazo bakaga murnan da yaran sukayi ba ni har tausayi suka bani wlh"..gyada kai Bobby yayi yace"to Allah ya za6a mafi alkhairi..dama shiyasa kikace muzo?.."tace"aah mgnr zuwa Enugu ne bikin Tauhid"..Bobby ya dan wara ido yana kallonta yace"wai bikin har yazo?.."tace"yazo mana jibi nakeso mu wuce shiyasa nace kuzo tare in fada muku don kuje ku fara shiri"..dan marairaicewa yayi yana kallonta yace"yanxu Mummy sati biyu.."ai bata bari ya karasa ba tace"nace kuje ku shirya Bobby banason mgn..itama Sumayya dasu Miemie duk tare zamu wuce shi Sab dai tunda yana makaranta banda shi"..kallonta kawai yake bai sake cewa komai ba sai kai daya daga mata..Mummy kuma ta juya tana kallon Aysha tace"ai kinason zuwa ko Aysha?.."da sauri ta gyada kai tana murmushi tace"sosai ma Mummy..i love travelling"..da fara'a Mummy tace"MashaAllah"..Bobby da yaji haushin reply din nata ya dungure mata kai yana dan hararanta yace"sarkin yawo kawai"..bai ajiye hannu ba shima Mummy ta dungure nashi kan tace"kai kuma sarkin kulle ba"..da sauri ya dafa kan yana kallonta kmr zaisa kuka..a tare Mummy da Aysha suka tuntsire mishi da daria..he look funny ne yanda yayi squeezing face dinshi..shima dan murmushi ya saki yana relaxing kan kujera shi bason tafian nan yakeyi ba wlh..yasan yanxu idan sukaje sai suyi sati a can shikuma takura zaiyi ya sani..dan ba yanda zaiyi da Mummy ne amma da bazai je ba wlh..yasan idan taso abu irin haka dole ne yayi hakuri yayi yanda takeso musamman idan abu ya shafi zumunchi don shi gani yakeyi duk dunia babu mace mai son yan uwan da zumunchi kmr ita..sun dan ta6a hira kadan har su aunty sumy suka shigo bayan baban su Miemie ya tafi suma aka cigaba da hiran dasu..farin ciki kawai suke na tafia Enugu amma banda Bobby da ba haka aka so ba wai qanin miji yafi miji kyau. Koda suka koma gida haka yayita kumbure kumbure wai shi bayaso ita kuma tana mishi daria..da kanta ta hada musu kayan tafia kowa akwatinshi daban amma yana gani ya fito da kayan ya hadesu cikin guda daya wai yanda ba wanda zai rabasu tunda kayansu na hade dole a bar masa matarsa..itadai daria yake bata dan tasan duk sbd me yake wnn abubuwan...washegari ma haka tayita shirye shirye tana bude jaka ta fito da wani kayan ko ta saka wani aikin knn tunda ta tashi daga bacci kmr wadda bata ta6a zuwa wani gari ba..murna kawai take ta samu saken fita don tun da akayi biki idan aka dauke gidan Mummy babu inda take zuwa.. she's always at home kmr matar malam..suna gama lunch ya dauketa zuwa daki wai zaiyi maganin dariar da take mashi aikam nan da nan ta shiga hankalinta ta fara bashi hakuri kmr zatayi kuka..shi kuma bai saurara mata ba saida yayi maganin bakin da take dariar dashi..bayan sunyi wanka ya sake janta suka koma gado wai duk yau ta jama kanta a haka zasu yini tunda take mishi daria itadai batace komai ba don tasan ko zata shekara cewa ya kyaleta ba kyaletan zaiyi ba shiyasa tayi shiru da bakinta..ganin kmr he is in a good mood tace bari tayi using wnn opportunity tayi mashi zancen komawa hospital..tana kwance a jikinshi tana wasa da gemunshi tace"partner"..hannu yakai ya sake matseta jikinshi yafin ya amsa da"yes partner"..murya can kasa tace"So nake in koma asibiti"..da sauri ya dago yana kallonta yace"are u sick?.."tace"No inaso in koma aiki ne..kaga duk yan class dinmu fa suna waiting results amma ni banda ni"..ta karasa mgn tana kwabe fuska kmr zatasa kuka..Jan cheeks dinta yayi yana murmushi yace"kema zaki koma ai amma ba yanxu ba"..da sauri tace"when"..yace"when the right time comes"..kallonshi ta tsaya yi kmr zatasa kuka..sai kuma tale baki ta shiga bubbuga legs dinta akan gadon tace"nidai inaso in koma plss..so kake skills dina ya gudu"..daria yakeyi sosai bayan yayi pecking lips dinta yace"ba wani skills dinki da zai gudu.. believe me very soon zaki koma"..banza tayi dashi tana cigaba da diddirza kafafunta..baiyi yunkurin hanata ba sai matsar da bakinshi da yayi saitin kunnenta yace"naga alama u want some more and believe me idan kika cigaba da abun nan kome ya biyo baya ke kika siya"..tun bai rufe baki ta shiga hankalinta don tasan kadan daga aikinshi yayi yanda yace wlh..ita wani lokaci har mamaki yake bata..shidai kullum ayita abu daya ko gajia bayayi. The next morning kmr yanda Mummy tace suka tafi Enugu gaba dayansu...basu sauka a can ba sai around 3 don haka bayan sun huta gajia Mummy da kanta ta kaisu gidan wani uncle dinta suka gaisheshi daga nan kuma sukaje bikin da ya kawosu.. traditional Igbo day sukayi suma exactly irin wanda akayi na bikinsu saidai Lamido gani take kmr wnn din yafi nasu batasan ko sbd su din gaba daya inyamuran bane amma abun ya burgeta matuka haka ta dinga daukan pictures da videos tana turama su Ammi da Billy wai su kalli bikin inyamurai..ranan basu dawo masaukinsu ba sai dare sosai..gida ne guda na Mummy da sauran 'yan uwanta suka sauka a ciki..daki daya aka basu da Miemie,aunty sumy da Ilham Mummy kuma ita kadai sai Bobby tareda wani cousin dinshi..yaji haushi sosai da aka rabashi da matarshi amma ba yanda ya iya da Mummy dan yanxu yana mgn ne zatace ya zama mara kunya snn ita kanta Ayshan ya fuskanci murna ma takeyi da hakan..bayan sun dawo duk sukayi shirin bacci kowa ya kwanta saidai tana kwanciya kiranshi ya shigo wayarta dan haka ta mike zaune bayan ta daga kiran tace"partner bakayi bacci ba"..tana rufe baki yace"how do u want me to sleep without u?..plss kizo parlor ina nan ina jiranki mu tafi..i can't sleep without u"..dan murmushi ta saki tana girgiza kai tace"yanxun partner kawai sai Mummy taga nazo dakinka?..no can't do that plss..besides naga ba kai kadai zaka kwana a dakin ba"..tun bata rufe baki ba yace"we're not sleeping here hotel zamuje..plss baby kiyi sauri kizo am waiting for u here"..dan langabewa tayi kmr yana ganinta tace"partner kayi hakuri i can't come out now..kaga Mummy fa bazata ji dadi ba idan na b..."tun bata karasa ba yace"then bari inzo in daukoki tunda cewa kikayi u can't come out now"..zare idanu tayi hadda su rufe baki jin abunda ya fada..ita fa bazai sata jin kunya ba wlh..sanin zai iya aikata abunda ya fada ta mike da sauri ta sama kofar key tareda dawowa cikin dakin ta zauna tanaji ya kashe kiran tasan nan din ya taho..yana zuwa kuwa ya murda kofa yaji a rufe ya kira bata dauka ba dan haka ya koma daki cikin ranshi yace yasan yanda zaiyi maganinta. Da safe bayan duk sunyi wanka suka fito yin breakfast a nan parlor..Aysha na lura da Bobby tunda ta shigo parlon ko gaisuwarta bai amsa ba ya maida hankali sosai yanacin abincinshi..jikinta taji yayi sanyi sosai tasan duk tsiya bai cancanci walakancin da tayi masa ba jiya amma ba laifinta bane ai da zaina wani daure mata fuska..bata sake bi ta kanshi ba itama ta fara cin abincin saidai loma daya tayi taji bazata iya ci ba don bata saba dacin irinshi ba..gashi dai abinci ne sosai amma bazata iya ci ba sam..bata bari sun fahimci bata ci ba tacigaba da jujjuya spoon dinta a ciki suma kuma da yake hankalinsu bai wurin basu gani ba..Bobby da gaba daya hankalinshi yake kanta ya lura sarai bacin abincin take ba and dama yasan hakan zai iya faruwa..ko gama cin nashi baiyi ba ya mike yana goge bakinshi da tissue yace"Mummy let me take out taci abinci nasan ba iya cin wnn zatayi ba"..da sauri Mummy ta juya tana kallonta tace"da gaske bazaki iya ci ba daughter?.."a hankali ta daga mata kai alamar eh dan haka Mummy tace"to tashi kuje ya sama maki wani abun kici zamu jira ku dawo sai mu fita gaba daya"..a hankali ta mike ta koma daki ta dauko mayafinta snn ta dawo parlon inda ta tarar shima har ya fita dan haka tabi bayanshi..a cikin mota ta sameshi ta karasa a hankali itama ta shiga snn ya tada ta suka bar gidan sai a lokacin ta dan juya tana kallonshi..taga fuskan nan a tamke dan haka ta dauke kanta gefe har suka isa eatery ba Wanda yayi mgn cikinsu..shi kadai ya fita ya siyo abunda zai siya ya dawo tareda zuba ledojin a baya shima ya shiga ya tada motar..a hanakli ta sake juyowa tana kallonshi still taga hankalinshi bai kanta kawai sai itama ta daure nata fuskan tana turo baki..suna isa gida ta bude motar kmr zata fita sai kuma tayi saurin dawowa ta fada jikinshi murya can kasa tace"partner kayi hakuri"..rungumeta yayi shima gami da lumshe ido yace"wahala kikeson bani don kinga ina sonki Koh?.."da sauri ta shiga girgiza kai tana cewa"me nayi?.."..yace"u refused me yesterday sbd kinga na damu dake"..dan murmushi ta saki tana sake kwantar da kanta a chest dinshi tace"to am sorry"..idanunshi lumshe yace"u have no idea how i missed u..i missed u so much"..murmushi takeyi ta dago tana kallonshi sai kuma ta lumshe ido ta shiga bashi the hottest kiss of his life..Bobby is just sitting there looking at her kaman wani statue..he is far far gone da wnn kiss din nata..he never thought she can do this..tunda yake da ita ko kallon eyes dinshi na tsahon lokaci bata iyawa balle ayi mgnr wnn..duk yanda zaiso tayi mashi bata ta6ayi ba sbd kunyanshi dake dawainiya da ita har yanxu..yanxun kuma da tayi sai yaji kaman an tsundumashi a aljannah don dadi..ko kwakwkwaran motsi kasayi yayi har saida ta janye bakinta a nashi snn ta sake kwantawa a chest dinshi tana sauke numfashi..hannu daya yakai ya dora a bayanta dayan kuma ya sake tada motar dashi kawai sai ji tayi yajata da gudu sun sake fita daga gidan aikuwa ta dago daga jikinshi da sauri tana kallonshi hankalinta har ya fara tashi tace"innalillahi partner where are u taking me to?..mu koma gida dan Allah"..bai iya ce mata komai ba sai hannu da ya kai ya sake janyota jikinshi gaba daya hankalinshi naga driving da yakeyi yace mata"relax"..tun bai rufe baki ta zame jikinta da sauri tareda komawa seat dinta ta zauna tana dubanshi kmr zata fashe da kuka tace"yanxu partner meye haka plss..me kakeso su Mummy suce..nidai take me back plss i beg u"..banza yayi mata baice komai ba don a halinda yake ciki gani yake mgnr ma 6ata mashi lokaci zaiyi..ita kuma ganin yanda yake sharara uban gudu ko a jikinshi kawai saita rufe fuska ta wani rushe da kuka kmr wanda akama dan banzan duka..daria ya saki sosai yana cigaba da driving dinshi don wlh ko me zatayi bazai hanashi abunda yayi niyya ba..haka nan mutum daga yin aurenshi an wani kawoshi nan an rabashi da amaryarshi ai kome ya aikata ma bai kamata aga laifinsa ba kmr yanda bai kamata a rabashi da amaryarshi ba at the first place..nearby hotel ya shiga yayi parking snn ya bude motar ya fito da ita tanata zabga ihu kmr karamar yarinya baice mata qala ba ya sunkuya zai dauketa tayi saurin matsawa baya tana kallonshi..sake matsawa yayi kusada ita ya janyota jikinshi murya kasa kasa yace"idan baki rufemun baki ba daukanki zanyi gaba daya wlh..kuma kinsan zan iya"..daga haka ya sake kama hannunta suka nufi cikin hotel din..daki yayi booking snn ya sake kama hannun nata suka nufi dakin..Saida ya family a tilasta mata cin abincin sa ya siyo snn ya sake janta jikinshi..duk wani kuka da kokawarta bai hanashi holewarshi ba har saida tayi dana sanin kissing dinshi don a ganinta shine ya janyo mata wnn abun kunya..kmr kullum yau ma har komai ya kammala bata dena kuka ba saidai wnn karon kukan na kunya da kuma tunanin yanda zata hada ido dasu Mummy ne don gani takeyi da kyar idan basu fahimci abunda ya faru ba..ita batasan wane irin mutum ne shi ba wlh..gaba daya baisan wani abu mai suna kunya ba..daukanta yayi da kanshi zuwa bathroom yayi wanka itama yayi mata da kanshi duk wani noke nokenta bai saurara ba saida ya gama snn ya sake daukota suka dawo dakin..shiryawa yayi itama ya shiryata snn ya sake janta suka kwanta wai bacci yakeji aikam data daddage ta kurma masa wani ihu ba shiri ya mike ya dauki car keys dinshi suka fita daga dakin..yana gama settling bills dinshi suka fita Lamido sai wani hade rai takeyi ita bata yadda ba ya 6ata mata rai shi kuma sai kunshe daria yake..har suka koma gida bata ce mishi komai ba yana gama parking ta bude motar ta fita kmr zata tashi sama shima budewa yayi ya fita yana sakin murmushi shi kanshi sai yanxu ya fara tunanin amsar da zai ba Mummy idan ta tambayi dalilin dadewarsu amma da Mummyn nashi ta musamman ce sai bata tambayi dalilin dadewan nasu ba saima shiri daya samu sunayi don tafia wajen biki..shima baiyi wasting time ba ya shiga daki don shiryawa..lokacinda ya fito itama ta gama shiryawa ta fito kuma yana sauke idanu kanta yaji wani abu ya taso tun daga brain dinshi har zuwa foots dinshi..hankalinshi yaji ya tashi ba dai a haka take tunanin zata fita ba?..anya kuwa tana ma da hankali yarinyar nan?..tana matar auren zatace zata fita da wnn veil din da shi a ganinshi dashi da babu duk daya..har sun kama hanya zasu fita itada Miemie yayi saurin kallon Mummy yace"Mummy kiyi mata mgn plss..ya zata fita a haka"..juyawa Mummy tayi ta kalleta snn ta dawo da kallon gareshi tace"ban ganeba"..yace"Mummy look at her mana da wnn dan mayafin zata fita"..tsaki Mummy ta saki ba tareda tace komai ba itama ta fita daga parlon..aunty sumy data fito yanxu tana ganinshi a tsaye tace"what again?.."da sauri yace"Mummy ce wlh..kawai ta bar yarinyar nan ta fita da wani dan karamin veil a jikinta..nasan kowa kallonta zai dinga yi wlh dan Allah kiyi mata mgn"..daria ta saki tana kama hannunshi tace"yanxu dai ka wuce mu tafi tun Mummy bata farajin haushinmu ba"..bai sake cewa komai ba ya bita suka fita amma shidai Allah ya gani ba haka yakeso ba..sam baiso ta fita a haka ba sbd yanda tayi kyau koshi da yake mijinta kasa dauke Idonshi yayi a kanta balle kuma wasu da ta6a ganinta ba kilan sai yau..duk ranshi yabi ya 6aci all of a sudden sai wani cin kunu yake yana daure fuska kmr wanda akama wani laifin. Har suka dawo daga wajen bikin nan ranshi a 6ace yake don gani yake kowa ma ya gama kalle masa ita yau din nan..itama da yake haushin abunda yayi mata daxun takeji sai batabi takan fushin da yake ba tacigaba da harkokin gabanta..the next day ma haka suka yini a wajen biki sai dare suka dawo gida daga nan kuma suka shiga zagaya wa gidajen yan uwan Mummy duk tana introducing Aysha wa Family dinta wanda basuje biki ba cewa itace matar Bobby..sosai suka samu tarba mai kyau daga yan uwan nata kowa sai nan nan yakeyi dasu kmr a maidasu ciki..Lamido taga kara iya kara a wajensu abun har mamaki ya bata yanda sukeda son yan uwa haka..sunada zumunchi sosai ba kadan ba sai yanxu taga inda Mummy ta dauko zumunchi don yan uwanta kaf zumunchi garesu da kuma son nasu..bayan sun gama ziyara sai suka shiga yawo da ita cikin garin suna nuna mata wurare da dama a matsayinta na wadda bata ta6a zuwa ba aikam tayi kallo iya kallo ta kuma ji dadin zuwanta garin don taci karo da abubuwa da dama wanda suka burgeta..shi kanshi yanayin tsarin garin ba karamin kyau yayi mata ba don da gani take duk states din nan na kudu idan aka dauke Lagos ba wani kyau na kuzo ku gani ne dasu ba amma yanxu tasan she was wrong don Enugu dai kam tanada kyau iya kyau saidai batasan ko iya wurare masu kyawun taje ba..yanda ta ware take harkanta a cikinsu abun har mamaki ya bata don yanxu ta rage jin kunyansu sosai tana kuma iya sakewa cikinsu ayi labari yanda ya kamata tunda ita din dama gwanar surutu ce..tsakaninta da mijinta ma sai abunda yayi gaba don soyayya ne ake zubashi yanda ya kamata..tun tanajin kunya idan yayi mata wani abun gabansu Mummy har tazo ta fara sabawa don ta fuskanci shifa haka yake kuma ba iya denawa zaiyi ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 63 Ana gobe zasu tafi Aysha zaune parlor tareda bobbyda aunty sumy dake bata labarin yanda ya shiga damuwa sbd ita kafin ta fara sonshi ita kuma banda daria ba abunda takeyi tana kallonshi..shidai yana zaune yana jinsu jira kawai ta wuce gona da iri ya taka mata burki don bazai yadda ta 6arar masa da mutunci ba..aunty sumy na kwaikwayon muryanshi tace"Ina fada maki da farko idan akace yana sonki har wani masifa yakeyi yana denying cewa shi ba sonki yake ba amma daga baya har zuwa yake yasa Mummy a gaba yana mata kuka yana cewa mutuwa zanyi..indai ban aureta ba Mummy mutuwa zanyi for sure..Mummy kuma sai ta daga hankali tayita lallashi tana bashi bakin cewa ai watarana zaki soshi"..aunty sumy ta karasa mgn tana kallonshi tana cigaba da daria..Lamido ma daria takeyi iya karfinta tana kuma mamakin wai shine yake kuka akanta kmr dai bashine wnn mutumin daya takurawa rayuwarta ba..da sauri ta juya tana kallonshi da murmushi tace"do u really cry because of me partner?..i can't believe this?.."daure fuska yayi ya mike yana wani cin magani shi bai yadda ba kar a rainashi yace mata"hiran ya isa haka tashi mu tafi"..dan langabewa tayi still tana danne daria tace"please mana"..kamata yayi ya mikar da ita tsaye ya sake cewa"let's go"..kmr zatasa kuka tace"to where?.."yace"to my friends house"..aunty sumy tace"yaushe kakeda aboki a Enugu bamuda labari"..yace"gidan Mi'iraj zamuje"..gyada kai aunty sumy tayi tace"kaidai kawai bakason matarka tasan how much u love her"..tana rufe baki yace"ai ko yanxun tasan Ina sonta sosai..baby ai kinsan dai inasonki da yawa Koh?.."girgiza kai tayi tana makale shoulder dinta tace"nidai ban saniba"..wara ido yayi yana kallonta sai kuma ya shiga janta yana daria yace"to bazaki sani ba..now ki wuce muje idan ba so kike in daukeki da kaina ba"..juyawa tayi tana kallon aunty sumy kmr zatasa kuka tace"aunty kiyi mishi mgn plss"..aunty sumy na murmushi tace"karki damu idan kun dawo zamu cigaba daga inda tsaya"..da sauri ta saki wani murmushi tana cewa"yauwa aunty godia nake"..shi kuma ya juya yana kallonta ya saki wani murmushi yace"idan kika cigaba nima zuwa zanyi in samu saurayin Miemie in bashi labarin duk abubuwan da kikeyi ince masa to yayi a hankali 'yar gidan yarinya zai aura"..ai tun kafin ya karasa ta jefo mashi throw pillow dake kusada ita tana daria tace"sai nayi maganinka wlh..dan rainin hankali"..daria sosai shima ya saki tareda kama hannun matarshi suka fita daga gidan.. already dama Mummy ta fita tun safe tare dasu Miemie so su kadai suka rage a ciki. Tunda suka shiga mota take juyawa tana kallonshi akai akai tana sakin murmushinda ya kasa tantance na menene..ganin yanda take kallonshi sai shima ya dan juya ya kalleta for like 2 secs snn ya dauke kanshi yanacigaba da driving..Lamido da ta matsu taji karshen labarin nan tace"dan Allah da gaske partner ka ta6a yin kuka sbd ni?.."kai ya gyada mata ba tareda kallon inda take ba yace"of course..ba sau daya ba ba sai biyu ba"..yana rufe baki tayi wani irin zaro ido kmr wanda taji abun tsoro hadda su rufe baki da hannunta cikin so much excitement tace"ikon Allah..i can't believe this"..juyowa yayi ya kalleta kafin ya maida kanshi ga titi yace"u have to believe..ba karamin wahala nasha kanki ba"..sake gyara zama tayi tana facing dinshi tace"tell me more plss..i want to know"..murmushi ya saki tareda gangarawa gefen titi yayi parking snn ya juyo yana kallonta..kallonshi itama takeyi with a smile don da gaske abun really get to her jin cewa mijinta har kuka yayi sbd ita..it's kind of romantic..kamo hannayenta yayi ya rike yana kallon cikin idanunta babu alamar wasa tattare dashi yace"i have suffered alot..na wahala sosai..duk wani taurin kai da zafi irin nawa saida na nemesu na rasa because of u..at first nayi tunanin tsanarki nayi sai daga baya na gane it was not hatred but love..duk wnn abubuwan that i have been doing to u inayinsu ne with the out of pain and anger..gani nake kmr zuciata batamun adalci data bari na fara sonki ba..wnn dalilin yasa koda yaushe nake maki masifa duk a kokarina na ganin nayi denying the fact that ina sonki amma the love was very powerful..it was more powerful than my heart shiyasa all my effort go in vain sbd na kasa cireki a raina"..dakatawa yayi yana kallonta eyes dinshi har wani ja sukayi sbd tunawa da mawuyacin halin daya shiga a wancan lokacin..itama kallonshi takeyi ko kifta ido batayi sbd yanda takeso lallai taji karshen wnn labarin nashi..ta lura har yanxun abun na ta6ashi don gashi nan ta gani a idanunshi..bata ta6a sanin ya wahala haka a kanta ba..hannunta ya saki tareda kai hannu ya kara karfin ac sbd zafi da yaji yanaji from no where snn ya dawo da idanunshi gareta kafin yacigaba"a lokacin Allah kadai yasan yanda nakeji idan na ganki da wani..ji nake tamkar zuciata zata tarwatse ta dalilin abunda nakeji..wnn dalilin yasa zakiga duk wani abu da zakiyi idona yana kanki musamman daya kasance kedin fitinanniya ce bakijin mgn"..tun kafin ya rufe baki takai mishi duka a chest dinshi tana wani narkewa tace"nine fitinanniya koh?.."janyota yayi jikinshi yana shafa bayanta yace"eh mana..kin bani wahala sosai amma yanxu duk ya wuce tunda na aureki"..dagowa tayi tana kallonshi da murmushi tace"ni kuma da gaske a lokacin na tsaneka..ko ganinka banason yi sbd masifan nan naka kuma tsoronka fa nakeji sosai nunawa ne kawai banayi"..murmushi shima yakeyi yace"na sani wlh..nasan maybe duk dunia ba wanda kika tsana irina a lokacin sbd takurawan da nake maki"..kanta ta gyada tareda kama hannayenshi tana dubanshi sosai tace"sosai ma kuwa..kawai gani nake u are against my happiness but i was wrong"..tsura mata ido yayi yana kallonta for some minutes kafin yace"kinsan tun yaushe nasan ina sonki?.."girgiza kai tayi da sauri alamar bata sani ba..yace"ranan wata Monday 11th of July around 8:15 am"..shiru tayi tana kallonshi ido a wajen jin har su date da time ya rike na tsahon wnn lokacin..kallon yanda ta bude idon yayi sai ya saki murmushi bayan yayi pecking dinsu yace mata"yes ranan da kuka fara clinic posting dinku na first semester year two..ranan kunzo zakuyi reporting a Freedom kawai naga kinshiga motar wnn tsohon mutumin"..kamo hannunta yayi ya rike sosai yace"wlh Aysha kasa fitowa daga cikin motata nayi..i was just sitting inside looking at direction na motar nashi inajin kaman inzo in fito dake daga ciki..yanda naji zuciata ta buga a wnn lokacin na tabbatar da cewa am in love amma naki admitting..kuma fa nike Shan wahala ba wani ba amma still naki amincewa sonki nake..ban kara shiga damuwa ba sai ranan da daddy da bakinshi yace ya bani amanarki..tun daga wnn lokacin abubuwa suka fara kwa6emun amma still ban yadda ina sonki bafa"..ya karasa mgn da murmushi a fuskanshi dan shi kanshi sai yanxu yake ganin wautan da yayi a wancan lokacin..Kiri kiri wai yana feeling abu kuma yana denying sbd wani dalili nashi mara tushe..rungumeshi sosai Aysha tayi tana tunawa da yanda yayita cin zalinta a wancan lokacin kuma wai duk a snn ma yana sonta...murmushi ya saki har yanxu tana rikeda hannunta yace"and kinsan the funny part of all these?.."girgiza mishi kai tayi alamar no..yace"farkon tsanar da nayi maki sbd kin kasance Fulani ne Kuma from Gombe..a wancan lokacin na tsani yan Gombe sosai especially Fulani sbd wani abu daya ta6a shiga tsakaninmu da su waziri..amma when i met u..komai ya lalace kmr dama turoki akayi don kizo ki rusa wnn hatred dake tsakanina da Fulani dama Gombe gaba daya..daga lokacin dana fara sonki da yawa daga halayena canxa ba tareda ni kaina nasan lokacinda suke canxawan ba..wayar gari kawai nakeyi in ganni kmr ba Bobby ba"..a akaice labari sukasha sosai kowa Saida ya bama dan uwanshi labarin yanda sukeji game da juna a baya sun ma manta da ba gida suke ba cikin mota suke kuma a kan titi..after a very long conversation ya sake tada motar suka tafi gidan Mi'iraj din da yace zasuje. Washegari bayan sunyi sallama da kowa suka dawo Kanon Dabo..around 2 something suka isa gida dan haka kowa matsuguninshi ya wuce don huta gajia. Kwanakin da suka biyo baya kuma shirye shiryen daurin auren aunty sumy suke da za'ayi this coming Saturday..dukda ba wani biki zatayi sosai ba sudai sunata shirinsu wai a cewarsu yanda ta dade batayi aure ba ya kamata tayi biki sosai ita Kuma tace baza tayi ba..maza ne kadai zasuje Gombe daurin aure mata kuma suyi yininsu a nan gidan nasu zuwa dare kuma akai amarya don Waziri yace bai yadda da a daura aure kuma amarya tacigaba da zama a gida ba gwara a hada komai ayishi lokaci daya a wuce wajen...tunda Aysha taji mgnr zuwa Gombe duk ta daga hankalinta wai dan Allah yaje da ita amma yace sam ba inda zataje tunda bada mata za'ayi tafiyar ba..haka ta karaci fushinta ta gama daga karshe ya lalla6o ya lalla6a kayarsa suka shirya kmr dai yanda aka saba. Ranar Saturday kmr yanda aka tsara su Bobby sukaje har Gombe inda Waziri ya sake maida aurenta da Isma'il akan sadaki mafi kankanta...Kai tsaye daga wajen daurin aure wurin reception suka wuce inda Bobby keta tsokanar Nur wai 'yar yara zai aura tunda gashi bikin uwa da ubanta yazo kuma wai hadda reception..daria yakeyi sosai ya dauka aunty sumy ce kadai mai dabi'un yara ashe shima mijin nata haka yake idan ba haka ba meye wani reception kmr auren fari..gashi kuma sai wani farin ciki yake yana gaisawa da mutane yanda kasan bai ta6a aure ba shidai Nur sauraron iskancinshi kawai yakeyi babu bakin mgn don shi kanshi dai yaji abun wani banbarakwai wai namiji da suna hajara..gaba daya sirikar tashi baya tunanin ta bashi sama da four years amma ya zaiyi tunda yana son 'yarta?..shi kanshi dai zuwa yanxu ya tabbatar da 'yar yara din zai aura kaman yanda Bobby yace amma who cares?..shidai fatanshi bai wuce ya auri Miemie ba kuma yasan da yardan Allah zai samu so bashida wani matsala da yarintar iyayenta...kafin a tashi daga reception suka bar wurin zuwa Lamido's Palace don zuwa ya gaida daddy da kuma Lamido kmr yanda Waziri yace lallai kada ya bar Gombe ba tareda yaje ya gaishesu ba..suna daukan hanya shima Nur ya fara nashi iskancin shidai yanajinshi baice komai ba don tareda driver suke..gidan Lamido suka fara zuwa suka gaisheshi daga nan kuma suka karasa gidansu dama daddy da bai dade da shigowa gari ba..a parlonshi suka sauka bayan sun gaisa ya tambayesu aiki da sauransu suka amsa da lafia..daddy ya dora da tambayan ko Aysha tanayi mashi wani abun don a cewarta yasan har yanxu wauta bai saketa ba..shidai Bobby ya amsa da ba komai don harga Allah idan yace yarinyar nan tayi mashi wani abu daga aurensu zuwa yanxu to tabbas ya zalunceta..Ammi tasa Husna ta kawo musu abinci dasu ruwa duk suka kasa sakewa suci wai akan hanya suke..ko suna nan cikin parlon Aysha ta kirashi kusan say uku bai dauka ba sbd daddy and yasan duk Kiran bazai wuce akan yaushe zasu dawo ba?..Ammi ma tazo suka gaisa itama ta tambayi ko tana mishi wani abu da ha daidai ba yace shidai ba abunda take mishi lafia Lau suke zaune hakan kuma ya mara dadi matuka tace ashe dai 'yar tata ta fara hankali yanxu..nan dai sukayi sallama dasu suka wuce kai tsaye daga nan kuma suka dauki hanyan Kano..tun a hanya Bobby ya kira aunty sumy yana tsokanarta wai an daura itadai tayi mashi banza daga karshe ma kashe wayarta tayi tana ayyana kalar walakancin da zatayi mashi duk ya shigo hannunta...karfe biyar da wani abu suka sauka Kano inda kai tsaye gidan Bobby suka sauka don main house dai sunsan bazai shigu yanxu ba sbd jama'a don haka suka fara branching a nan kafin mutane su ragu...bayan sallahn magrib few mutane da Mummy tayi selecting suka raka amarya aunty sumy gidanta. Wnn knn Bayan sati biyu... Tsahon 5 weeks knn da bikin Bobby da Lamido..cikin 5 weeks din nn Aysha ta sake tabbatar da ba wata mace a zuciar mijinta sama da ita..ta kuma tabbata tafi duk wata mace sa'a da kuma dacewa da samun miji kmr nata..he is such a loving and caring hubby..he is super romantic..he is handsome and rich..he is so so down to earth infact he is all in a man and she is so very lucky to have found him..yanda yake nuna mata tsantsan so da caring abun har mamaki yake bata..kawai sai takega kaman duk dunia ba namijin dake nunawa matarshi so haka..kullum bai gajiya da nuna mata how much he loves and care for her..wnn dalilin yasa itama ta sake kware mishi..zuwa yanxu duk wani abu da yakeso ta sani ta kumayi registering dinshi cikin brain dinta tana mishi baja kolin irin nata caring din..tasan a daidai lokacin da yake da bukatan wani abu a wurinta likewise she knows exactly how to handle him..ita kanta yanxu har mamakin kanta take yanda ta dawo fitsararriya sbd shi..sam ta dena wnn kunyan don gani tayi idan fa ta tsaya kallon ruwa tsaf kwado zaizo ya mata kafa shiyasa ta tattara dan ragowan kunyan ta ajiye a gefe ta kuma shiga nunawa mijinta shi kadai ne namijin da zataso har karshen rayuwarta..rayuwarsu is so full of soyayya,farin ciki da kuma girmama juna kmr ba Lamido da Bobby da basa ta6a jituwa a baya ba..bayan four weeks da biki Bobby yayi resuming office ranan har kuka saida tayi masa wai bazaije ya barta ita kadai ba batasan shima idan na son ranshi ne bazaije ya barta ba amma it's his work dole ba yanda ya iya haka zai koma tunda bazai taba dawwama zaune a gida ba..ranan yini tayi kuka saida ya dawo ya fara aikin lallashi ta hanyar da yasan iya taurin kanta sai ta saduda kuma hakan ne ya faru don tuni ta mance da wani kuka ta bada kai bori ya hau. Yau Thursday karfe hudu da 35 mins ya dawo daga office..ya shigo ciki rikeda briefcase dinshi as usual ya kama hanyar flat dinshi sai Kuma yajiyo kmr motsinta a kitchen dan haka ya ajiye briefcase din nashi a nan parlor ya nufi kitchen din..tsaye ya ganta jikin gas tana kokarin juye ruwan zafin data tafasa a wani bowl daga ita dai jean da Jessy dinta na Man u red..kallonta ya tsayi from head to toe yanda shape dinta ya fito sosai a cikin kayan..ya hanata da Jessy din nan amma har yanxu taki denawa wai ita tafi sabawa dasu dole haka nan ya bari take sawa a gida bada son ranshi ba ..a hankali yana karasawa ciki ya dagata sama ya shiga juyi da ita cikin kitchen din yana kissing duk inda yaci karo dashi a jikinta full of excitement yake cewa"baby am back..i missed u so much..muahh"ya karasa yana sake manna mata peck a forehead dinta ita kuma ta zagaya hands dinta a wuyanshi tana kallonshi da murmushi tace"welcome back love"..makale mata shoulder yayi tareda nuna mata lips dinshi da hannu daya yana wani kashe ido yace"here"..makale nata shoulder itama tayi tana dungure kanshi tace"No"..fuska ya kwabe kmr zaisa kuka ya shiga bubbuga legs dinshi a kasa still Kuma yana daukeda ita a hannunshi kmr ba abu mai nauyi ya dauka ba yace"Allah sai kinyi"..daria ta saki tareda matsar da head dinta tayi pecking forehead dinshi snn ta dago tana murmushi tace"now saukeni"..shoulder ya sake makale mata alamar he won't..kallonshi tayi for some secs sai kuma ta lumshe ido ta dora finger dinta akan lips din nashi kafin ta bude idon tace"promise it won't pass that"..da sauri yace"i promise..only kiss"..lumshe Ido tayi bayan tace"ohk"..snn ta sake matsawa a hankali ta hade bakinshi da nata shima yayi grabbing da sauri kmr abunda yake jira knn..after like 5 minutes ta samu ta kwace bakinta da kyar tana kokarin sauka kasa tace"wnn shine promise din?.."ajiyeta yayi tareda sake janyota ya hadata da jikinshi yana sauke numfashi yace"sorry i couldn't stop myself"murmushi ta saki bayan ta janye hands dinshi daga jikinta ta shiga nuna mishi kofa tace"oya muje kayi wanka sai kazo kaci abinci"..shoulder ya sake makalewa yana kallonta kasa kasa yace"No..me kikeyi a kitchen?.."kama hannunshi tayi suka fita daga kitchen din tace"custard zan dama"..da sauri yace"nima ina shan custard din plss"..girgiza kai tayi tana murmushi tace"naji..amma muje ka farayin wanka first"..bai sake yi mata musu ba yabita har zuwa flat dinshi..suna shiga bedroom ta saki hannunshi snn ta zaunar dashi gefen bed ta shiga unbottoning shirt din jikinshi..kallonta kawai yakeyi yanda ta cire shirt din nashi ta ajiyeshi gefe ta zare singlet shima ta ajiye gefe sai kuma ta mikar dashi tsaye ta zame trouser leaving only shorts a jikinshi snn ta sake jan hannunshi har cikin bathroom shi kuma sai binta yake kaman wani rakumi da akala..tana gama hada mishi komai ta fita da sauri don tasan tsaf zai iya riketa ya hanata fitowa ita kuma bata shiryama wnn fitinan nashi ba shiyasa tayi saurin fitowa tun kafin ya rutsa ta...closet dinshi ta shiga ta fiddo mai kayan da zai saka snn ta fita don karasa dama custard dinta tunda already tayi setting dinning tun kafin ya dawo..saida ta sake kunna gas ruwan ya tafasa snn ta dama custard din ta fito dashi a hannu tana juyawa da spoon..a dinning taja kujera ta zauna tana cigaba da juyashi don so take ya danyi sanyi kafin tasha..tana sane taki komawa dakin sbd gudun kada ma ya ganta ya hanata fitowa..komawa tayi kitchen ta zuba milk da sugar cikin custard din nata snn ta sake dawowa dinning din ta zauna ta fara shan abunta hankali kwance..Bobby ko yana fitowa daga bathroom sharp sharp ya shirya cikin kayan da ta fito mashi dasu snn ya fita don cin abinci..yana hangota zaune tana shan custard dinta yace"baby rowa koh?.."dan dagowa tayi tana kallonshi daidai lokacinda ya karaso dinning din ya ja kujera ya zauna kusada ita ta mika mashi bowl din tace"to Bismillah"..makale shoulder dinshi yayi yana hararanta yace"banaso ai saida na roka kika bani"..da sauri tace"to zan dama maka wani"..tabe baki yayi yana girgiza kai yace"No"..nan da nan ta tale baki ta shiga mishi kukan karya tana bubbuga legs dinta kasa tace"Allah nidai sai kasha"..murmushi yayi sosai gamida dan matsawa saitin kunnenta yana shafa gemunshi yace"baby da kiyi saving wnn strength din for later..naga kaman zaifi maki amfani a can"..da sauri ta hadiye kukan nata tana hararanshi tace"ni saloon zaka kaini ai"..plate ya dauka ya fara serving kanshi tayi saurin mikewa ta karba tacigaba dayi shi kuma ya relaxing ya rungume hannu yana kallonta da murmushi yace"saloon da yamman nan baby?.."da sauri tace"eh ai Kaine kace yau zamuje kuma nidai bazan sake kwana kaina ba kitso ba"..kama hannunta yayi bayan ta gama serving dinshi yace"baby da ki bari sai gobe"..tun bai rufe baki ba tace"ni yau nakeson zuwa"..bai sake cewa komai ba ya shiga cin abincinshi itama tacigaba da Shan custard dinta..yana cin abinci yana santi dan da gaske tana maida hankali tayi mashi girki yanda ya kamata shiyasa a kullum yakejin abincin nata so delicious kaman abunda ta karanta knn a school..tana gama Shan custard din ta mike zuwa flat dinshi ta dauko car keys dinshi tun ma kafin ya gama yace mata ba yanxu ba snn ta wuce bedroom dinta ta zumbula zumbulelen hijab dinta ta fito rikeda phone dinta a hannu alamar she's ready to go..yana gama cin abincin yayi clearing dinning din da kanshi snn ya koma parlor yana sipping drink..kokarin kunna tv yake kawai sai ganinta yayi tsaye a gabanshi tana mika mashi key din mota..daria ya saki yana kallon yanda ta wani hade rai yace"yanxu baby ko hutawa bazanyi ba?.."kai tsaye tace mishi"idan mun dawo sai ka huta..nasan da hutawa wlh cewa zakayi sai gobe ni kuma am tired of zama da gashina a haka so kawai ka tashi muje ko kuma wlh in kira Mummy"..ajiyar zucia ya sauke tareda mikewa ya amsa key din suka fita daga gidan..tunda tasama ranta sai taje yasan idan ma baije ba ba barinshi zatayi ya sarara ba and tana hadashi da Mummy yasan nashi ya kare. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 64 Kai tsaye suna barin gidan saloon din da yasan su Miemie na zuwa ya kaita..tare suka shiga ciki ya zauna a reception yayinda ita kuma aka shiga da ita inda ake gyaran gashin..wash and set aka yi mata hade da kitso duka..lokaci mai tsaho suka dauka suna kitson sbd tsayin da gashinta ke dashi ga kuma kitson kananu ne..Bobby dai na nan zaune yana jiranta har zaman wurin ya fara gundurarshi sai gata ta fito bakin nan a washe kmr gonar auduga...tun a nan wurin ta bude mishi kitson ya gani aikam yayita santi yana yaba irin kyawun da yayi har matar dake wurin ta zauna kallonsu..kudi sosai ya debo ya bata snn ya kama hannun matarsa suka wuce bayan sun mata sallama..suna shiga mota ta dan juya tana kallonshi tana marairaicewa tace"partner i have a request plss"..tada motar yayi suka fita daga harabar saloon din yana cewa"just say what u want love"..da sauri tace"cinema zaka kaimu muyi kallo dan Allah"..da sauri ya girgiza mata kai yace"No"..sake marairaicewa tayi tana hada hannayenta wuri daya cikin sanyin murya tace"partner dan girman Allah muje..Manchester ne suke wasa kuma nasan ana haskawa a can plss don't say no please!.."juyawa yayi ya dan kalleta kafin ya dauke idon yana dan furzar da wani iska a bakinshi yace"bana sonki da kallon ball din nan bakiji koh?.."a hankali tace"only this once plss..daga yau bazan sake cewa ka kaini cinema ba wlh i promise"..banza yayi mata yacigaba da driving dinshi as baiga dalilinda zaisa ya dauki matarshi ta Sunna ya wani kaita cinema da yasan almost wayanda ke ciki maza ne ba..ganin yanda yayi banza da ita sai ta kawar da kanta gefe tana matsar kwalla ganin still yaki ce mata komai kawai sai ta hade kai da guiwarta ta shiga rera masa kuka kmr wanda yayi ma dukan tsiya..still Bobby bai tanka ta ba duk kuwa da yanda kukan ke ta6ashi amma ya daure bai ce mata kala ba..ganin abun nata bana kare bane kawai ya dauki hanyar Cinemar da yasan dole ana haska wasan a can..dalili daya zaisa ya kaita wlh amma ba don wani abu ba..har suka isa Cinema bata dago kanta ba shima baice mata kala ba..yana gama parking ya mika hannu ya dagota ya dora a cinyanshi yana nuna mata wurin da hannayenshi ai kam tana ganin Platinum Cinema rubuce a wajen ta saki wani ihun farin ciki tareda kwakwumeshi ta manna mashi peck a cheeks dinshi snn tace"nagode partner"..dungure mata kai yayi yana murmushi at least dai yaga darianta yanxu..hannunta na cikin nashi suka shiga cikin cineman bayan sun fito daga mota..a bakin kofar ya tsaya ya siya musu tickets snn ya sake rike hannunta zasu shiga tayi saurin dakatar dashi tana nuna mashi popcorn daga dan gefen inda suke tana wani kwabe fuska tace"baka siya mana popcorn ba"..kallonta kawai yayi gamida girgiza kai snn ya juya zuwa inda popcorn din yake..ita kuma ta samu wuri ta zauna tareda rungume hannunta daga nan inda take tana kallonshi tana murmushi..ita bataki su dauwama a haka ba wlh..ace mutum da matarshi wai bazai na kaita cinema kallo ba saida 'yan dabaru..mikewa tayi da sauri ganin yana dawowa nan wurin garin saurin da take ta take hijab dinta ta kasa aikuwa ta zame da tiles din wurin ta tafi luu zata fadi wani guy da yazo wucewa yayi saurin tareta ta fada jikinshi akan idanun Bobby da har ya kusa karasowa inda take..wani irin abu yaji ya daki chest dinshi kmr an harbeshi da kibia..Lamido kuwa runtse idanunta tayi tasan tunda tajita a jikin mutum to tabbas shi ya tareta shiyasa ko bude Ido batayi ba don ta riga ta gama sadakarwa zata jita zube a kasa sai kuma yazo ya tareta har wani sake matseshi tayi ta hannunta tana cigaba da sauke numfashi..mutumin daya riketa da sauri yakai hannu ya janyeta daga jikinshi yana kallonta daidai lokacin itama ta bude idanunta sbd qamshin perfume dinshi da taji ba irin na Bobby bane..gabanta ya bada wani irin sauri rass ganin wani mutumi ne daban tsaye a gabanta and bisa ga dukkam alamu shine wanda ya riketa ba Bobby da tayi tunani ba.. innalillahi wainna ilaihi rajiun..yanxu hakan na nufin ta rungumi kato knn..duba takai da sauri izuwa inda ta hango tahowarshi aikuwa ta ganshi yayi tsaye a wurin kikam yana kallonta kmr wani statue ga popcorn din da ya siyo gaba daya sun tarwatse a kasa..wani irin dummm taji wuta ta dauke mata gaba daya har wani juwa taji yana daukanta ta sake tafia da baya zata fadi the same man daya tareta daxu ya sake matsawa zai rikota Bobby da baisan lokacinda kafafunshi suka karaso dashi wurin ba yayi wani irin kukan kura ya gaura ma mutumin mari a fuska..da sauri ya safe cheeks dinshi yana kallon yanda take huci kmr wani tsohon zaki yace"how dare u..how dare u touch my wife with those filthy hands of yours..how dare u"..ya karasa mgn da wani irin karfi da hatta sauran mutane dake wajen saida suka tsorata..eyes dinshi sunyi wani jajir sun kankance sbd tsabar bala'i..da sauri guy din yaja baya har yanxu yana dafe da cheeks dinshi yace"am sorry gani nayi zata fadi kuma bansan matar aure bace"..hannu Bobby ya sake kaiwa zai kwada masa another mari mutane sukayi saurin shiga tsakani suna bashi hakuri..Lamido dai tunda tayi zaman 'yan bori a kasa a kasa tabuka komai sai kallonsu da take ga gabanta na tsnanta faduwa kuma ko digon hawaye babu a idanunta..wato idan masifa yayi masifa shi kanshi kuka bazai zo inda kake ba..ashe duk abunda akewa kuka ba wani babban abu bane..da wani irin force Bobby ya juya zuwa inda take kawai saiji tayi ya dauketa cak sun fita daga wurin sai a snn taji cikinta yayi wani irin murdawa kaman zataje toilet sbd tashin hankali..yanda taga face dinshi cunkus dama tasan yau mai rabata dashi sai Allah..ya dawo mata Proprietor sak data sani a FCNM mai shegen masifa da takurawa mutane...shiko Bobby tafia kawai yake yana yin karo da duk wani dake gabanshi don gaba daya hankali da nutsuwarshi basa tare dashi..he can't still believe what just happened..he can't believe a gabanshi kuma a kan Idonshi wani Wawa can ya samu damar ta6a masa mata kuma wai har da kanta take sake hugging dinshi.. innalillahi wainna ilaihi rajiun..da kyar ya iya isa inda motarshi yake ya bude baya ya sakata a ciki snn shima ya zagaya ya shiga ya tada motar ya figeta da wani irin gudu kaman zasu tashi sama..gudu kawai yake shararawa baya ko la'akari da yanayin hanya da kuma motoci dake wucewa a wurin burinshi kawai su isa gida yaji dalilin ta na cewa sai sunzo Cinema at the first place..su Lamido dai ana baya sai wuwwurga idanu akeyi kmr munafuka..ga wani zufa da takeyi duk kuwa da sanyin acn dake motar sbd tsabar rudani..duk wani addu'a da yazo bakinta yinshi kawai takeyi don bata ma San wanda ya kamata tayi ba a halin yanxu..suna isa gida bayan yayi parking ta runste ido tana jira taji yazo ya fito da ita daga motar ya fara kwallo da ita tun daga nan wurin amma sai taji shiru kmr ma baya cikin motar..bude ido tayi da sauri tana kallon driver seat sai taga wayam ya bude motar ya fita..da sauri itama ta fita tabi bayanshi taga har yakai entrance door dinsu ya bude ya shiga ciki itama da gudu gudu ta karasa ta bude kofar ganin baya parlor direct ta kama hanyar flat dinshi amma sai tajishi a kulle alamar rufewa yayi daga ciki..zaro ido tayi tareda jingina bayanta da bango ta dora hannu a ka sai yanxu hawaye suka kawo idanunta tace"na shiga uku na lalace..mena janyoma kaina haka ni Aysha?..wane masifa ne wnn na janyoma kaina..wayyo Allah na shiga uku"..daga haka ta durkushe a wurin tana sakin wani marayan kuka..kuka sosai irin na wanda uwa da uba suka mutu suka barshi shi daya tak a doron dunia ba tareda wani shaqiqi ko masharci ba..kmr an tsokareta ta mike ta fara buga kofar da karfi tana cewa"partner dan Allah ka bude kaji..i can explain everything plss open door plss"..ta karasa mgn cikin kuka sosai amma bataga alamar zai bude kofar nan ba..shima ya a ciki yana jinta kawai takaici yakeji na duk wani abu daya faru.. gani yake dama on purpose tace suje cinema din kilan dama tasan hakan might happen shine zata raina mashi wayo..wai ace agaban idonshi..akan idonshi wani ya rungume masa mata kuma kiri kiri ya kasa yin komai akai?.. innalillahi wainna ilaihi rajiun..gaba daya wani irin zafi yakeji all over his body..ga zuciarshi da yakeji kaman fashewa zatayi sbd takaicin da yake ciki..gani yake kmr bai ladabtar da yaron yanda ya kamata ba..ita kuma baima san hukuncin dazai dauka a kanta ba dan a halin da yake ciki yasan tsaf zai iya Marin nata itama shiyasa bazai ma bari ta doso inda yake ba don zai aikata mata abunda he might end up regretting..kawai dai ta riga taci amanarshi kuma ta gama dashi data bari wani tsinanne can ya rungumeta..har yanxu ganin hug din yake a cikin idanunshi tamkar yanxu abun ke faruwa..wnn wace irin rayuwa ce ne?..wane irin masifa ne wnn ya kutso kai cikin rayuwarshi Kuma?..wane irin bala'i ne wnn?..gani yake duk dunia a yanxu da kyar za'a samu wanda zai kaishi baqin ciki da tashin hankali..he feel like doing something stupid amma bazaiyi ba sbd gudun dana sani...haka nan yayita zaune cikin dakinshi sai kaiwa da kawowa yake ko zama ya kasayi sbd tashin hankali..Aysha dai har yanxu na bakin kofa tana faman kuka tana bashi hakuri amma to no avail tunda gashi har anyi sallahn magrib bai bude kofar ba..mikewa tayi da kyar ta shiga dafa bango sbd jirin da takeji ta koma zuwa dakinta ta zame hijab dinta a hankali tareda kwanciya kan gado ta rufe face dinta da pillow tana sake rushewa da kuka..Bobby na dena jin sheshshekar kukanta yayi saurin shiga bayi yayi alwala snn ya fito ya bude kofar ya tabbatar bata wajen snn ya wuce masallaci..koda yayi sallahn magrib bai dawo gidan ba har akayi Isha..daga masallacin kai tsaye eatery ya wuce yayi mata takeaway din abinci don shidai yasan bazai iya sa komai a bakinshi ba..koda ya shigo gidan bai ganta a parlor ba dan haka ya ajiye mata abincin a dinning hoping Allah yasa taci snn ya wuce flat dinshi..kayan jikinshi ya rage snn ya kwanta kan gado yayi pillow da hannayenshi ya lumshe ido scene din daxu na sake dawowa kwanyarshi..har yanxu hango abunda ya faru yake kaman a mafarki..ciwo yakeji sosai cikin heart dinshi wanda yasan if care is not taken yana iya samun gagarumin problem..dauriya kawai yakeyi amma Allah kadai yasan halin da yake ciki..gyara kwanciya yayi ya rungumi pillow wai yanxu after duk abunda ya faru ji yayi yana missing dinta..he missed her warmth body a jikinshi and yasan yau bacci barawo ne kadai zai iya zuwa daukanshi don a yanda yakejin eyes dinshi dai babu alaman bacci a tare dasu..bai tana tunanin zuwan rana irin wnn da zai kasance suna gida daya amma bazasu kwana the same room ba..sam bai taba kawo irin wnn thought din ba a zuciarshi..gani yake ko nawa za'a bashi bazai iya bari hakan ya faru ba amma now gashi. A nata 6angaren itama tayi kuka tayi kuka har wani bacci ya lalla6o ya dauketa a nan inda take zaune ba tareda ta shirya ba..ba ita ta tashi a baccin ba sai after nine ta shiga bathroom tayo alwala snn tazo ta gabatar da sallah tareda da addu'an Allah ya daidaita tsakaninta da mijinta don bazata iya jure wnn fushin nashi ba..tana idar da sallah ko hijab din jikinta bata cire ba ta sake komawa flat dinshi wai ko Allah zaisa ya bude mata kofa amma iya tsaiwanda tayi a wurin ko motsinshi bata ji ba balle tasa ran ya bude mata kofar..tana kuka sosai ta sake komawa bedroom dinta ta wurga kanta kan sofa tareda kudundunewa cikin hijab dinta nan take kuma zazza6i mai zafin gaske ya rufe mata jikinta..dama tun safe takejin alamun zazza6in amma bai sauka ba sai yanxun tasan kuma bazai rasa nasaba da zullumi da kuma uban kukan da taci bane..ko baccin ma kasayi tayi don basu taba kwana separate room ba tunda sukayi aure sai yau..kuma ita tsoro takeji don ko a gida bata saba kwana ita kadai ba suna tareda Husna a school kuma tareda Billy so zata iya rantsewa ma ita bata taba kwana ita kadai a daki ba ko gidan aunty Fiddausi taje tareda Mufida suke kwana..tun kukan nata na fita tareda sound har ya koma zallar hawaye takeyi babu saurin komai sbd disashewa da muryanta yayi...har dare yayi nisa sosai bata samu bacci ba sbd zazzabin dake jikinta sai gabannin asuba ta samu baccin yayi gaba da ita shima kuma cikeda mafarkai marasu dadi. Shima Bobby sbd rashin samun enough bacci har ya makara sallahn asubah dan lokacin da ya tashi an idar da sallah a masallaci..alwala ya shiga yayi snn ya gabatar da sallah yacigaba da zama nan yayi su azkhar da addu'o'i har saida gari yayi haske snn ya mike daga wurin ya fita direct to her bedroom dan tashinta tayi sallah..a nan kan sofa ya sameta kwance ta kudundune da hijab dinta..ya karasa a hankali ya zauna kusa da ita yana kallon yanda face dinta yayi jaa sbd kukan da kwana tanayi..lumshe ido yayi ya bude tareda kai hannu da nufin ya zare hijabin dake jikin nata sai yaji jikin ya dauki wani irin zafi kaman ana hura mata wuta..da sauri ya daga hijab din nata yana sake dora hannu jikinta yaji still temperature yayi rising baisan lokacinda ya dagata gaba daya ya cire mata hijabin ba..a firgice ta tashi taga baccin tana hada ido dashi ta mike zaune da sauri tana kwabe fuska tace"par..tner"..daure fuska yayi yana kallonta yace"what's wrong with u?.."kuka ta farayi tana cewa"partner dan Allah let me explain"..bai bari ta karasa ba ya dora finger dinshi akan bakin nata still fuskanshi daure yace"i said me yake damunki?.."kasa tayi da idanunta hawaye na sake cikowa cikinsu tace"fever.."yace"only fever?.."kai girgiza tana share hawayen tace"da ciwon kai"..dauke idonshi yayi daga kallonta dan yanda yaji kukan nata na neman karya mishi da zucia yace"kinyi sallah?.."Kai ta girgiza mashi alamar no yace"then shiga bathroom kiyo alwala"..kallonshi ta tsaya yi zatayi mgn ya dan daga murya yace"just go don't waste my time"..mikewa tayi da sauri ta shige bathroom tana shiga ta durkushe nan kasa ta fashe da matsanancin kuka..gaba daya gani tayi ya dawo mata asalin Dr Bobby data sani..gabanta har wani faduwa yakeyi duk ta kalleshi taga fuskan nan nashi a cunkushe..da kyar ta iya mikewa tayi easing kanta tayi brush snn ta daura alwalan ta fito tana takawa a hankali sbd zazza6i dake sake rufe mata jikinta..tana karasowa ya nuna mata inda ya shimfida mata praying carpet ya mika mata hijab dinta without looking at her yace"kiyi sallah"..ba musu ta amsa hijab din ta saka snn ta tsaya kan carpet ta tayar da sallah shi kuma ya mike zuwa kitchen don nema mata abunda zataci kafin ya bata drugs..hankalinshi ya tashi sosai da jin yanda temperature dinta yayi high hakan Sam bazai hanashi nuna mata girman laifinda ta aikata ba..takeaway din daya ajiye mata jiya a dinning yaga yana nan untouched meaning bataci abinci ba ta kwanta knn..duk sai ya sake jin jikinshi yayi sanyi kawai ya shiga kitchen yana tunanin abunda ya kamata yayi mata yanxu taci kafin ya bar gidan.. custard dinta ya gani inda ta ajiyeshi jiya dan haka ya dora ruwa a gas da sauri ya dama mata custard din ya zuba Madara da sugar snn ya koma dakin nata..a kwance ya sameta inda ta idar da sallah ta sake lullu6e kanta da hijab ya karasa ya ajiye custard din akan table snn ya mikar da ita tsaye bayan ya cire mata hijabin ya nuna mata custard din da hannunshi fuskan nan ba sarari yace"dauka Kisha"..kallon custard din tayi kafin ta dawo da kallon gareshi kmr zatasa wani kukan tace"na..koshi"..saida gabanta ya fadi da ganin yanda ya sake hade rai yana kallonta..murya a cunkushe yace mata"ina wasa dake ne?.."da sauri ta hau girgiza kai tana goge hawayen dake zubowa face dinta tace"ah..ah"..yace"then ki dauki custard din nan kisha idan baso kike kiga other side of me ba"..wani yawu ta hadiye mai daci snn takai hannu ta dauka custard din ta fara sha a hankali tana yatsine fuska kmr mai Shan magani..baifi spoon biyar tasha ba zata ajiye cup din yace"don't u dare..shanye shi zakiyi gaba daya"..haka tacigaba da danna custard din cikinta tana hawaye tana komai har Allah ya nufa ta gama shanyewa..dauka cup din yayi ya fita daga dakin can sai gashi ya dawo da drugs da goran ruwa a hannunshi..daga nan inda take ya tsaya ya 6alli drugs din ya mika mata tareda ruwan dake hannunshi yace"amsa Kisha"..nan ma ba musu ta amsa drugs din daga hannunshi ta fara zuba ruwan a bakinta snn ta watsa drugs din ta hadiyesu aikam tana hadiyewan taji wani irin amai ya taso mata tayi saurin mikewa tana toshe da bakin zata wuce bathroom saidai kafin ta karasa bathroom din ta durkushe nan kasa ta shiga kwarara aman a nan..Bobby na tsaye rungume da hannu yana kallonta..tausayinta yakeji sosai amma taurin kai da kuma zafin abunda tayi bazai bari ya nuna hakan ba..karasawa yayi shima ya durkusa nan inda take ya dagota jikinshi bayan ya fuskanci ta gama aman ya dauketa cak ya shiga bathroom da ita..ruwan zafi ya hada ya mata wanka da kanshi yanata wani daure dauren fuska shi a dole baiji wani abu ba har ya gama ya daura mata towel ya fito da ita..da kanshi ya shiryata yasa mata simple doguwan riga mara nauyi snn ya kwantar da ita kan gado ya fita daga dakin..tea ya sake hada mata da Milo kadai sai sugar snn ya hada da injection ya dawo dakin nata..wnn karon da kanshi ya bata tea din tasha snn ya shiga withdrawing alluran da zaiyi mata..tana ganin allura duk ta rikice tana kuka tana rokon yayi hakuri shidai baice mata komai ba har ya gama hada alluran sai kawai ya tsaya yana kallonta..duk wnn abun da yake Allah ya sani karfin hali ne kawai amma shi kadai yasan yanda yakeji a cikin ranshi..yasan halinta ne indai ba wuta wuta yayi mata ba bazata shiga hankalinta ba shiyasa zaiyi iya bakin kokarinshi yaga bai bar tausayinta da yakeji yayi tasiri a yanxun ba har saita fahimci kuskuren data aikata..zaunawa yayi kan gadon ya dagota yayi mata alluran tanata faman ihu amma bai saurara ba saida ya gama snn ya rungumeta a jikinshi yana patting bayanta a hankali..wnn zafin na jikinta har tsoro yake bata wlh..ji yake kaman yayi transferring ciwon daga jikinta zuwa nashi da kilan bazai dingajin yanda yakeji yanxu da ciwon yake a jikinta ba..karfin hali kawai yakeyi amma yana cikin damuwa sosai..bai ajiyeta ba saida bacci ya dauketa snnya kwantar da ita ya rufeta da duvet ya fita daga dakin..wanka yayi shima ya shirya snn ya sake komawa dakin nata ganin baccinta yayi nisa sosai yayi deciding ya dan leka hospital kona few hours ne ya dawo tunda yanada aiyuka a can..ko abincin shi baici ba ya karasa shiryawa ya bar gidan tareda driver dinshi..yau ko main house bai shiga ya gaida Mummy ba sbd baison ta tambayi abunda ke damunshi. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 65 Har wajen 1 yana Hospital yanata duba patients ga kuma hankalinshi gaba daya yana kanta..so yake yaji halinda take ciki kuma yanata Kiran wayanta bata dauka dan haka yayi deciding ya kira Mummy tasa aje a duba mashi ita..bayan ya sallami patient din gabanshi bai sake Kiran wata ba yayi relaxing kan seat dinshi yana dialing number Mummy..tana dauka ko gaisawa bai bari sunyi ba yace"Mummy aje a dubamun Aysher plss..batada lafia and inata kiran wayanta bata picking"..da dan damuwa Mummy tace"subhanallah what's wrong with her?.."murya can kasa yace"fever da headache"..Mummy tace"amma kasan batada lafia shine baka zauna tareda ita ba Bobby?..yanxun idan wani abun ya sameta fa?.."a hankali yace"Mummy nothing will happen to her inshaAllah..ya kama dole ne fitan nima da bazan fito ba..yanxun dai ko Miemie ki tura taje ta ganomun halinda take ciki plss..i still have lots of patients ne da zuwa zanyi da kaina in ganta"..ajiyar zucia Mummy ta sauke kafin tace"don't worry yanxu zataje ta ganota..i will get back to u"..yace"alright Mummy.. nagode"..Mummy bata sake cewa komai ba tayi hanging Kiran..fitowa tayi da kanta tacema Miemie dake karatu sbd sun kusa fara waec taje ta duba mata Aysha wai bata da lafia..da sauri ta warware veil dinta data daura a kai ta yafashi snn ta fita daga gidan..ta main gate ta fita sbd taga kofan cikin kaman a kulle ne..tana zuwa ta kwankwasa mai gadi ya bude mata ta shiga cikin gidan kai tsaye..a bedroom dinta ta sameta tashinta daga bacci knn sai kuka take har lokacin kuma akwai fever sosai jikinta..hankali tashe ta kira Mummy ta fada mata halinda ta sameta a ciki don haka Mummy ta turo driver dinta tace ya daukesu kawai su wuce asibiti tunda Bobby yana can sai ya dubata..Miemie ta dauki hijab dinta tasa mata snn ta kamata suka fita compound inda driver je jiransu..suna shiga motar ya tadata suka fita daga gidan. Suna shigowa hospital din Miemie ta fita da sauri zuwa office dinshi ta banka ta shiga ko sallama batayi ba ta fada mashi halinda ake ciki..yanda ya fito a rude har mutane saida sukayi mamaki dan lokaci daya yaji komai nashi yayi tsaye cak..da sauri ya karasa inda motar yake ya bude back seat nan ya ganta jingine jikin seat din idonta na fitar da hawaye..hannu yakai ya ta6a forehead dinta yaji still da zafi a jikin kawai sai ya dauketa a hannunshi ya fito da ita daga motar zuwa cikin asibitin..sauri kawai yakeyi ya karasa office dinshi bai ko damu da kallon da jama'a ke binshi dashi ba..yana shiga ya kwantar da ita kan gado snn ya cire mata hijabin jikinta kawai sai ya tsaya yana kallonta without saying anything..Miemie data shigo office din da sauri yace ta shiga bayi ta kawo mashi warm water da towel..ba musu tayi yanda yace ta kawo mashi yace taje driver ya maidata gida..shi kuma ya fara jika towel din yana shafa mata ruwan a jiki sbd temperature nata ya sauka..bayan ya gama ya fita zuwa pharmacy da kanshi ya kar6o drip da allurai snn ya koma office din nashi..tana ganin drip da allurai hannunshi ta fara kuka shidai bai iya ce mata komai ba ya samu ya lalla6a yasa mata drip din don yasan ba wani abinci zata iyaci ba..yana gamawa ya mata alluran da zaiyi saurin saukar mata da fever din snn yaja seat dinshi ya zauna nan kusada ita yana kallonta..Aysha na kuka sosai tace"partner am so sorry plss"..hannunta ya kama ya rike cikin nashi baidai ce mata komai ba..mikewa ta shiga kokarin yi shi kuma yayi saurin maidata yana nuna mata cannular dake hannunta yace"careful mana"..komawa tayi ta kwanta tanacigaba da kallonshi tana hawaye..shima kallonta yakeyi yanajin wnn abun da yazo ya tsaya mashi a throat dinshi tun jiya yasan indai ba mgn ya samu yayi da itaba wnn abun bazai fada ba dan haka ya dan runste eyes dinshi kafin a budesu a kanta voice dinshi kasa kasa yace"so da gangan kikayi hakan koh?.."da sauri ta hau girgiza kai tace"wlh coincidence ne..i never knew such thing will happen am sorry"..yace"but u even hugged him..why did u do that?.."tace"i thought it was u sbd eyes dina a kulle suke saida naji perfume dinshi ba irin naka ba nasan u are not the one..kayi hakuri ka yafemun dan Allah"..ta karasa mgnr tana kuka sosai..shiru kawai yayi yana kallonta yasan shima yayi over reacting jiyan nn amma it wasn’t his fault..sake matsawa yayi yuana rikeda hands dinta yace"nima am sorry for reacting the way i did..i shouldn’t have done that so kiyi hakuri"..kai kawai take gyada mishi..ganin yanda har jikinta na rawa sbd kukan da takeyi yace she should stop talking zasuyi mgn anjima..sosai ya sake bata hakuri yana cewa yasan bai kyauta ba..itama tace mishi ko dan gaba if wani abu irin wnn ya faru saurin fushi bayada amfani gwara su zauna suyi communicating that communication is a solution to any problem..shiru kawai Bobby yayi yana kallonta dan kunya yaji sosai wai itace take fada mashi what is right..sauka ajiyar zucia yayi yana ayyana idan fa bai dena wnn saurin fushi da zafin ran ba watarana zaiyi dana sani duk sai yaji jikinshi yayi sanyi yace inshaAllah zaiyi kokarin gyarawa kuwa..ita kuma tayi shirun bata sake mgn ba har drip din ya kare zuwa lokacin kuma fevern dake jikinta ya dan sauka shima sai a lokacin ya dan samu peace of mind..a hankali ya mike zuwa inda wayanshi keta ringing ya dauka snn ya samu wuri ya zauna bayan yayi picking call din..a daya bangaren Nur yace"hey are u at the office?.."kmr bazaice wani abu ba sai can yace"what?.."Nur yace"just answer me dan rainin wayo"..lumshe ido yayi yana kallon inda take kwance kafin a hankali yace"ina nan".. Nur yace"ohk gani nan zuwa"..daga haka ya ajiye wayar tareda mikewa zuwa inda take ya maida mata hijab dinta yana cewa"do u need anything?.."a hankali ta girgiza mashi kai alamar no..yace"bazaki ci komai ba?.."nan ma kan ta sake girgiza mashi yace"bari Nur yazo idan ya tafi sai in maidaki gida tunda zazza6in ya sauka"..kai kawai ta iya gyada mashi shi kuma ya fita daga office din..can parking space yaje ya tsaya tana jiran isowar Nur bai dade da tsaiwa ba kuma sai ga Nur din ya karaso..bai bari ya karaso nan inda yake ba ya nufi wurin motar shi..yana zuwa ya bude ya shiga tareda relaxing yana kallon Nur din a hankali yace"daga ina kake haka?.."maimakon ya bashi amsa sai cewa yayi"wai what's wrong with ne?..u look disturbed..ina Lamido?.."a hankali Bobby yace"she's inside"..Nur ya dan wara idanu yace"inside kuma?..yanxu wurin aikin ma saika taho da ita Bobby sbd gajen hakuri"..harara ya watsa mashi mai kyau tareda sakin wani tsaki yace"u are annoying wlh..to batada lafia kuma ni bana gidan shine aka kawota na dubata"..wani murmushi Nur ya saki yana shafa gemu yace"so meke damunta?.."Bobby yace"fever..amma nasa mata drip yanxu fevern ma ya sauka"..Nur na gyada kai yace"Allah bata lafia..amma why ba'a yi mata test ba?.."juyawa yayi ya kalleshi rai a dan 6ace ganin kmr neman zance kawai yakeyi yace"ban saniba".. Nur ya kwashe da daria yana kallon abokin nashi yace"kaga malam ka maida wukar ka ni bani na kar zomon ba..am only trying to be of help"..a dan fusace Bobby yace"to hell with u and ur help"..kallonshi kawai Nur yake har yanxu bai bar murmushi ba yace"ohk let me keep quiet tunda bakaso..dama cewa zanyi kasa ayi mata pt kilan she's pregnant"..da sauri Bobby ya juya yana kallonshi idanu a waje yace"what do u mean?.."Nur yace"Ina nufin kilan ciki ne da ita mana..kai ina ka taba ganin anyi haka kawai matarka ba lafia kazo ka wani farayi mata blind treatment baka tunanin ko karuwa ka samu"..wani irin diff Bobby yayi yana bin Nur da kallo kmr bai gane abunda yace ba..tunani ya tafi yi tabbas tunda akayi bikinsu bata ta6a period ba and idan ba wai manta lissafin yayi ba bikinsu saura 2 weeks tayi period and idan akayi adding two weeks to that shine ovulation period dinta kuma a daidai wnn time din akayi bikinsu so there is 90% possibility na zata iya samun cikin within wnn kwanakin sbd time din ovulation dinta ne..nan take fuskanshi ya washe da wani irin murmushi yana sake wara idanu akan Nur hannunshi dafe da bakinshi cikin tsananin farin ciki da kuma mamaki yace"oh my Goddess..why didn't i think of this?.."harara Nur ya watsa mashi yace"oho banza"..sake juyawa yayi yana kallon Nur da kyau yace"Nur ina kyauta zaton wnn mgnr naka gaskia ne..she might be pregnant oh Allah"..ya karasa mgnr full of excitement kaman an tabbatar mishi tana dauke da cikin already..shi gaba daya tunaninshi baizo nan wurin ba all he was thinking was incident daya faru jiya har ya kulle mashi kai ya kasa zargin cewa cikin ne da ita.."ikon Allah"..ya sake fada out of excitement Nur dai na zaune yana kallon ikon Allah at the same time yana mishi daria..shi kanshi zai so ace yau Lamido tanada ciki ko dan yayi kallon uban rawan kan da Bobby zaiyi akan cikin...bude motar yayi ya fita shima Bobby ya fito da sauri ya kama hanyan cikin asibitin yana fadin"we need to conduct this test now..i pray it turn out to be truth"..Nur dake bin bayanshi ya amsa da"Ameen"..har suka shiga cikin building din..direct office dinshi suka shiga lokacin tana kokarin mikewa tsaye Bobby yayi saurin karasawa inda take yana kallonta full of love and excitement yace"baby where are u going?.."a hankali tace"ruwa zansha"..ruwan ya dauko da sauri ya kawo mata yana cewa"here u go"..ta saki dan murmushi snn ta amsa ruwan tasha cikeda mamakin sudden change din nan nashi?.. it's like ya gama saukowa completely..saida ta gama Shan ruwan snn ta lura da Nur dake zaune kan sofa yana kallonsu..ta danyi kasa da kanta tace"sir Ina yini"..yace"lafia ya jikinki?.."tace"naji sauki"..yace"to Alhamdulillah".. Bobby dai drawer ya bude ya dauko duk wani abu da zaiyi amfani dashi snn ya koma wurinta ya shiga lallabata wai zai dauki blood sample..itadai batace komai ba ya dauki sample din snn yaba messenger bayan ya rubuta test din da za'ayi a paper yace ya kai lab yace yana jiran result yanxun nan. Ana kawo result din Bobby yayi saurin karba daga hannun messenger daya kawo har ya fara budewa sai kuma yayi saurin maidata yanda take tareda juyawa yana kallon Aysha da har yanxu ke zaune tana kallonsu..juyawa yayi suka hada ido da Nur sai kuma ya sake juyowa gareta ya sakar mata murmushi.. Lamido data kasa gane what they are up to kawai sai ta sauka daga gadon a hankali tana kallonshi ta nuna bathroom dinshi tace"zanyi alwala"..da sauri kmr jira yake yace"ok babe"..ta saki murmushi snn ta juya ta shiga bathroom din...tana shiga Bobby yayi saurin bude papern ya wara ido sosai yana karanta content din dake ciki idanunshi na sauka inda yaga an rubuta positive yayi saurin yar da papern tareda juyawa ya kankame Nur sosai kmr zai maidashi ciki..cikin so much excitement ya juya language zuwa Igbo yanda bazata fahimta ba yake cewa"Nur it's positive.. it's positive wlh.. Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah"..ya karasa mgn still yana rungume dashi kaman shine mai cikin..shima Nur farin ciki sosai ya taya abokin nashi dan haka yayi hugging nashi back tareda daka tsalle yana wani iri ihu shima da Igbo yace"ekele bro..ekele"(congratulations bro.. congratulations)..shima Bobby tsallen yayi exactly irin yanda Nur din yayi kawai sai Hamdala yake yama rasa inda zaisa kanshi sbd excitement..haka suka rungume juna suna ta faman tsalle a dakin kmr kananun yara..Aysha dake la6e bakin kofa tana kallonsu batasan lokacinda ta fashe da daria ba..yanda suka rungumi juna suna tsalle tsalle sai suka koma mata kaman small kids..wato dai su biyun nan are so something else..dama tunda taga yanda suke kallon kallon tasan kilan space sukeso ta basu and gashi nan ta gani saidai Allah kadai yasan dalilinda yasa suka wnn farin cikin because ba gane language da suke speaking take ba..daria takeyi sosai wanda rabonta da irinshi tun kafin faruwar incident din jiya...Saida suka gama tsalle tsallensu Nur yayi saurin daukan paper da Bobby ya yarda a kasa shima ya karanta..nan take ya wara ido yana sake duban abokin nashi da wani killer smile ya danyi kasa da voice dinshi yanda bazata jiyoshi ba yace"oh my Goodness yanxun five weeks knn da aurenku and the pregnancy is four weeks..what a sharp shooter"..ya karasa mgn yana kashe mashi ido shidai Bobby bai iya cewa komai ba tsabar farin ciki kawai sai ya durkusa ya fara sujood shukur shi kuma Nur ya kama kugu da hannunshi daya..dayan hannun kuma ya dafe forehead dinshi dashi snn ya danyi bending kaman zaiyi ruku'u ya shiga juya waits dinshi yana taka rawa a hankali yana cewa"aga m abu nna..aga m abu nna"..(am going to be a father..am going to be a father)..cikin excitement sosai yake rawa yana waka Kai kace shine za'ayi ma haihuwan..Bobby daya gama sujood dinshi tun daxu dagowa yayi kawai yana kallonshi with a very wide smile..yanda yake rawan ba karamin daria ya bashi ba..da dadewa dama yasan Nur yafi karfin aboki a wurinshi saidai ya kirashi da brother so ko kusa baiyi mamakin wnn farin cikin da yake tayashi ba..shi din mai sonshi ne kuma tsakani da Allah..ya tabbata wnn excitement da yake ciki da za'a bincika zuciarshi za'a ga har cikin ranshi yake tayashi farin cikin..he is one in billion..samun aboki irinshi yana da wahala sosai and shiyasa yake godia wa Allah for having him..soyayyan da suke ma juna genuine ne ba fake ba...Lamido dake bathroom tana kallonsu tayi daria kaman cikinta zai kulle..dukda batasan me sukema wnn farin cikin ba ta tabbata it's something huge don tunda take bata taba ganinsu cikin such excitement ba..Saida ta gama kallon snn tayi alwalan ta fito daga bathroom din kanta a kasa tana kokarin boye darian dake son sake kufce mata.. Nur daya dage yana dirkar rawa yana ganinta yayi saurin mazewa yana wani shafa kai shi a dole ba kamashi tayi ba...Bobby dake kokarin danne dariar dake cinshi juyawa yayi ya isa gareta kafin ta zauna kan bed ya janyota jikinshi kawai sai ya rungumeta so tight yana sauke numfashi..ta kwalo ido waje tana kokarin kwace kanta sbd presence na Nur amma sam yaki sassauta rikon da yayi mata balle ta samu daman kwacewa din..wani irin farin ciki ya tsinci kanshi a ciki.. right now gani yake dunia babu Wanda ya kaishi farin ciki kaman dai ba shine yake ganin babu wanda ya kaishi shiga kunchi da damuwa a while a go ba..wato Allah ba yanda bayayi da bayinshi a duk lokacin da yaso..idan yaso ya saukar Maka da farin ciki haka idan yaso ya saukar maka baqin ciki.. that's how life is shiyasa masu iya mgn sukace ba kullum ake kwana a gado ba and it's true..ba koda yaushe mutum ke dawwama cikin farin ciki ko akasin haka ba..dole watarana za'a jarrabaka da either happiness or sadness saidai Allah ya bamu ikon yadda da qaddara mai kyau da mara kyau...yayinda yake rungume da ita Nur sai ya zaro phone dinshi daga aljihu ya shiga camera ya fara musu video yanajin yanda shi kanshi suka burgeshi sai yaji inama shi da pretty ne haka..at this point sai yaji wani shaukin sonta ya kamashi..yaji inama a bashi ita ya aura koda bata gama secondary din ba amma yasan that can never be possible..Saida Bobby ya dauki lokaci mai tsaho yana rungume da ita yana kuma sake ma Allah godia cikin zuciarshi snn ya raba jikinshi da nata tareda hade goshinshi da nata ya lumshe ido yana sakejin wani extraordinary feeling yana sake bijiro mishi..he missed her like crazy sai kuma abun ya hadu da farin cikin samu karuwa tsakaninsu..he just can't thank Allah enough for such a blessing..hannu ya sake mikawa ya zagayo waist dinta dashi pulling her more closer to himself snn ya lumshe ido ya manna mata peck a goshinta followed by cheeks da tip of her nose..yana bude ido yaci karo da Nur da har zagayowa yayi ta saitin da faces dinsu zaifi fitowa sosai yana cigaba da recording video din yana sakin murmushi hadda su gyada kai..suna hada Ido yayi saurin saving video din ya wani kashe mashi ido daya yana cewa"ahuru m ihunanya"..(I see love)..murmushi Bobby ya saki tareda gyara mata hijab dinta snn yayi mata side hug yana kallon beautiful face dinta yace"i think we should go home now"..batayi musu ba ta gyada mishi kai alamar ok shi kuma ya sake pecking forehead dinta snn ya kama hannunta suka bar office din Nur na binsu a baya..sallamar driver dinshi yayi yace ya wuce da motar gida su kuma suka shiga motar Nur suka nufi gidan a cikinta..duk yanda Aysha taso ya zauna front seat kin yadda yayi wai saidai ya zauna kusada ita gashi kuma ya kasa dauke ido a kanta daidai da one second..gani yake kaman idan ya rufe idanun za'a tasheshi daga bacci ace dreaming yake..ita dai mamakin wnn sudden change din nashi take don batasan meya sauko dashi daga dokin zuciar da ya hau all of a sudden ba..amma koma menene she's happy tunda ta dalilinshi ya dena fushi da ita..sai satar kallonshi take tanajin yanda tayi missing dinshi itama..ba dan presence na Nur ba da babu abunda zai hanata mannewa a jikinshi kafin su karasa gida amma bazata iya ba sbd tanajin nauyinshi sosai..gashi kuma suna hada ido dashi sai yayi pecking forehead dinta dan haka tilas ta dena kallon nashi sbd batason wnn abubuwa da yake mata gaban provost wlh..idan shi yana ganin friend dinshi ita fa har yanxun tana mishi kallon gentle provost dinsu mai bala'in kirki da mutunta students dinshi. Suna isa gida dama direct main house Nur ya shiga yayi parking snn ya bude kofa ya fita..shima Bobby fitowa yayi snn ya zagaya ya fito da ita sai wani hadata da jikinshi yake ita kuma tana kaucewa amma still bai bari bar har suka shiga gidan..Nur dai a baya yake binsu yana murmushi har yanxu kasa dena smiling sbd excitement..he is so happy for the both of them..suna zuwa daidai entrance Lamido ta dakata tareda zare hands din Bobby daga jikinta tana kallonshi da dan marairaicewa tace"partner just stop it mana..Mummy fa tana ciki"..murmushi ya saki tareda bending ya danyi pecking lips dinta snn ya kama hannunta ya rike yana kallon eyeballs dinta yace"is this ohk?.."girgiza mishi kai tayi da sauri tana kwabe fuska tace"Noo"..sai kuma ta shiga bubbuga kafa zata fara mishi kukan karya yayi saurin sakin hannun nata yana cewa"No no don't do that plss..gashi na saki hannun naki is that ok?.."kai ta gyada mashi tana sakin murmushi sai kuma ta shige cikin parlon..da kallo ya bita har ta 6ace ma ganinshi snn ya sauke wani ajiyar zucia mai karfi daidai lokacinda Nur ya karaso inda yake dan haka suka shiga ciki a tare..Lamido na shiga Miemie dake zaune dinning tana karatu tayi saurin mikewa tazo gareta tana wara idanu cikeda mamaki tace"Goodness!..aunty Aysha me yayi maki haka naga kin samu sauki?.."Bobby da yaji duk abunda ta fada ya dan watsa mata harara yana cewa"gidanku nayi mata"..da sauri ta kama bakinta tana yin kasa da kanta tace"ohh yi hakuri Uncle Bobby"..bai sake ce mata komai ba ya wuce flat din Mummy shi kuma Nur ya karaso nan cikin parlon ya zauna yana kallon Miemie da yakejin kmr ya maidata ciki yace mata"hey pretty"..kama hannun Aysha tayi suma suka karasa ciki suka zauna snn ta dawo da kallonta gareshi tana murmushi tace"Uncle Nur ina yini"..yace"fine pretty..ya exams?.."tace"Monday zamu fara"..yace"MaashaAllah..Allah bada sa'a..yasu aunty da Ilham?.."..tace"Ameen Ameen Uncle Nur nagode..su Aunty suna gidansu muma gobe zamuje ko aunty Aysha?.."ta karasa mgn referring to Lamido dake zaune tana sauraran conversation dinsu tana daria kasa kasa..da sauri tace"yeah indai naji sauki sosai gobe zamuje inshaAllah"..sai kuma ta mike tunawa da batayi sallah ba tace ma Miemie"rakani daki inyi sallah plss"..ba musu Miemie ta mike suka nufi dakinta dake nan cikin parlon don ta baro flat din aunty sumy tun baya barinta gidan..suna shiga Aysha tace mata ta koma kar su bar Nur shi kadai a parlor dan haka Miemie ta koma parlor yayinda ita kuma ta tayar da sallahrta..har yanxu kuma ba wani karfi takeji a jikin nata sosai ba. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 66 Bobby na shiga ya iske Mummy a parlor suna waya da aunty sumy..bai damu ko ta gama wayan ko bata gama ba kawai yana zuwa ya zauna kusada ita tareda mata side hug ya kwantar da kanshi a shoulder dinta cikin so much farin ciki yace"nwunye m di ime Mummy"..(my wife is pregnant Mummy)..da sauri Mummy ta dago kanshi tana kallonshi cikin tsananin farin ciki tace"are u for real?.."da sauri yace"yes i am Mummy..she is four weeks pregnant"..wani irin zare idanu Mummy tayi cikin so much excitement kafin tace wani abu aunty sumy data gama sauraran duk abunda ya fada sbd call dinsu is still connected ta saki wani irin guda tana cewa"My Bobby is becoming a Father.. Alhamdulillah"..da sauri Bobby ya dauki wayan daga jikin Mummy ya manna ta kunnenshi yace"yes aunty am becoming a father..am becoming a father"..wani murmushi ta karasa saki before tace"congratulations qanina..Allah kawo mana babyn nan lafia and extend my regards to Aysha kace mata nace she should take care of our baby sosai"..ajiyar zucia ya sauke yana cewa"aunty ai har yanxu bata sani ba..i didn't tell her"..da sauri aunty sumy tace"why?.."yace"rigima zataimun ne..i have to wait for the right time..yanxun allow me to talk to my Mummy plss..my regards to Ilham..kice mata her Uncle Bobby yayi missing dinta da yawa"..yana gama fadin haka bai jira jin me zata ce ba yayi disconnecting call din don yasan aunty sumy da zance sake dauko wani dogon surutun zatayi..yana ajiye wayar Mummy dake kallonshi full of surprise tace"meyasa baka fada mata ba Bobby?.. what's the meaning of this?.."kama hannunta yayi yana dan marairaicewa yace"Mummy nasan halinta rigima zataimun wlh..kullum cewa take ita batason ta samu ciki da wuri and tunda Allah baisa ta gane ba we shouldn't tell her plss"..a hankali Mummy tace"amma kasan zata iya ganewa ko ba'a fada ba Bobby..she is a health worker too..zata iya noticing some changes a jikinta da zaisa ta fahimci ciki ne da ita"..yace"na sani Mummy amma we shouldn't tell her now..gwara mu bari har zuwa lokacinda zata fahimci tana dashi din da kanta maybe by then bazata dagamun hankali ba"..ajiyar zucia Mummy ta sauke sai Kuma ta rungumeshi cikin so much happiness tace"am so happy for u son..Allah ya basu lafia ita da abunda ke cikinta snn Allah ya sauketa lafia"..rungumeta back shima yayi yana wani lumshe ido sbd dadi yace"Ameen Ameen Mummyna..i can't love u less". Da dare bayan sun dawo gida ya tilasta mata taci abinci snn ya bata paracetamol sbd fevern da yaji kaman zai dawo mata..suna zaune parlor suna kallo tanata faman cin apple daya yanyanka mata a plate daga ita sai dan sweet pants dinta blue da crop top baby pink..kanta da akayima kitso a bude sai daukan ido yake sbd kyan da yayi..yayinda ta maida hankali wajen cin apple dinta Bobby kuma yana zaune yana kallonta kmr yau ya fara ganinta..she looks do adorable right now..so looks cute that har baison ya dauke idanunshi daga kanta..kallonta kawai yake yana imagining yanxun da akwai da ko 'yarshi inside her tummy..banda smile ba abunda yake saki yana shafa saje zuwa gemunshi cikin so much happiness..kawai he's eager to see tummy dinta ya zama qato..he can't wait for the baby to come..he wants to hold the baby's hands snn yayi kissing forehead dinshi yace he loves him or her..he just can't wait for the baby's arrival..he's so desperate..yayi nisa sosai cikin tunaninshi sai sakin smile yake kuma har yanxun yana shafa beard dinshi kmr wani sabon kamu..kamar daga sama yaga ta mike da sauri ta kama hanyar bedroom dinta har tana hadawa da gudu sbd ringing din wayanta data jiyo..nan da nan ya dawo hayyacinshi tareda mikewa shima yabita da sauri yanajin wnn gudun da take har cikin zuciarshi wlh..yayi zaton wani gagarumin abun zatayi a dakin but to his biggest surprise yana shiga yaga ta dauki wayanta da bai dena ringing ba tayi saurin picking call din ganin Hammanta ke kira ta zauna gefen gado tareda Kara wayan a kunnenta tana wani cunno baki tace"ba ruwan ni dakai"..daga daya bangaren Hamman nata ya saki daria yana cewa"C'mon mana Maama..ba'a jin tsakanina dake fa?.."sake turo bakin tayi tace"ba wani Maama ni ka dena kirana Maama tunda baka damu dani ba"..jingina Bobby yayi jikin kofar dakin tareda rungume hannu yana kallon ikon Allah..yanxun Najeeb din takema wnn shagwaban sai kace muharraminta?..Najeeb dake dariar wnn rikicin nata yace"ohk wait kiji abunda zan fada maki..gobe zamuzo Kano"..batasan lokacin da ta saki wani irin ihu ba sbd farin ciki tace"dan Allah da gaske Hamma?.."yace"of course mana..tareda su Husna da Bilkisu"..nan take ta Kara sakin wani ihun tana cewa"Hamma amma dai kwana zakuyi koh?.."da sauri yace"Ammi tace banda kwana so a goben zamu dawo"..dan marairaicewa tayi kmr yana ganinta tace"haba mana plss..ya kamata ku kwana ai"..yace"idan kinaso su kwana saidai ki kira Ammi da kanki"..yana gama fadin haka tace"alright let me call her yanxu"..daga haka ta kashe kiran sai kuma ta shiga neman number Ammi zatayi dialing..a hankali Bobby ya karasa inda take ya wani daure fuska ya fizge wayar daga hannunta yace"are u mad?..bakida hankali zakizo kina gudu haka?..and waya fada maki ana yima cousin irin wnn shagwaban?.."murmushi ta saki tana kallon yanda ya hade girar sama dana kasa..batace dashi komai ba sai mikewa da tayi tareda matsawa inda yake ta shige jikinshi..a tare suka saki ajiyar zucia Bobby ya zagayeta da hands dinshi murya can kasa yace"how many times do i have to tell u this?..na fada maki cewa duk wani cousin dinki ba muharraminki bane amma bakiji..ko so kike na fara kishi dashi?.."a hankali ta girgiza mashi kai alamar no..yace"then meyasa kike mashi abubuwan da ni kadai ya kamata kiyima a matsayina na mijinki?..kina tunanin bana jin haushi ne?.."a hankali ta dago kanta tana kallonshi shi kuma yayi cupping fuskanta yana cigaba da kallonta yace"if u think bana jin haushi u are very mistaken baby..kishi nakeji sosai duk naga kina mishi wnn shagwaban..banaso"..hannunta ta mika itama tayi cupping nashi fuskan tareda dan dage ta manna mishi peck a forehead snn tace"to na dena partner..am sorry".. pecking nata back shima yayi yana cewa"na hakura love..yanxun yaushe ne zasuzo?.."da sauri ya dago taga jikinshi tana cewa"gobe..inaso in kira Ammi ince ta barsu su kwana yace saidai inyi mgn da ita"..ba musu ya kama hannunta suka zauna snn ya mika mata wayarta dake hannunshi yace"ohk call her"..da sauri ta karba tayi dialing number din Ammi..tana dagawa Aysha ta wani marairaice tana langabar da wuya kmr Ammin na ganinta tace"Ammi banida lafia"..daga daya bangaren Ammi tace"Amin wa'alaiki salaam"..da sauri ta gyara mgnrta da cewa"sorry salamu alaykum Ammi"..Ammi tace"wa alaiki salaam..ya gidan"..tace"lafia lau amma banida lafia"..ta karasa mgn kmr zatasa mata kuka ta wayar..Ammi tace"rashin lafiar kikema wnn abun sbd har yanxu bakida hankali"..turo baki tayi tace"Ammi zazza6i nakeyi sosai fa..kuma hadda amai"..Ammi tace"to Allah ya sawake..laifin Bobbyn ne da bai danqara maki allura ba"..daria sosai mgnr Ammi ya bata aikam ta shiga yinta kmr ba gobe..Saida tayi me isarta snn tace"Ammi wai su Husna zasuzo gobe?.."Ammi tace"eh zasuzo inshaAllah..tareda Bilkisu da Najeeb"..Aysha tace"Ammi dan Allah dan annabi su kwana"..Ammi tace"aah Aysha su da zasuzo da yawa banason suzo su takurama mijinki ne gwara suzo a goben su dawo ai yafi babu"..da sauri tace"Ammi dan girman Allah su kwana shida bama a dakina yake kwana b.."bata karasa ba Ammi tace"zakici ubanki wlh..wa kikaji ya tambayi inda yake kwana..wato har yanxu wnn shashancin yana nan kanki koh?.."shiru tayi tana danne dariarta tace"to Ammi kiyi hakuri..amma dan Allah su kwana ai munada dakuna da yawa"..Ammi tace"shknn sai suyi kwana biyu..dama shi Najeeb yace akwai aikin da zaiyi a garin na kwana biyu so idan ya gama sai su dawo tare"..cikeda farin ciki tace"yauwa Ammi nagode sosai Allah ya kara girma..Ammi kema dai ya kamata kizo wlh"..Ammi tace"zanzo amma ba yanxu ba..saiki daure ki dinga shan magani ba sai ama tilastaki ba..Allah ya baki lafia ya maku albarka gaba daya"..cikin tsananin jin dadin addu'an na Ammi tace"Ameen Ameen Ammina..nagode"..Ammi tace"shknn sai anjima..ki gaida Bobbyn dasu mamanshi"..da sauri tace"zasuji inshaAllah..sai da safe"..daga haka sukayi sallama..Bobby kmr jira yakeyi ta ajiye wayar ya shiga kyalkyala mata daira sosai..dama da dadewa ya fuskanci there is a little drama between the mother and the daughter..hakan kuma its the sign of love they have for each other..yanda ta dauko zancen ba'a dakinta yake kwana ba ita kuma Ammin ta katseta was so very funny to him..kallonshi tayi yanda yake mata daria tana dukan chest dinshi tace"what?.."ya kama hannunta ya rike yana kokarin dakatar da darian nashi yace"nothing baby..kawai dai am happy gobe su Husna zasuzo"..lokaci daya ta washe bakinta itama tace"nima am happy sosai sbd nayi missing dinsu..i can't wait to see them"..tana rufe baki ya dauketa suka fita daga dakin yana cewa"yanxun muje ki karasa cinye apple dinki sai muje mu kwanta sbd mu tashi da wuri koh?.."kai ta gyada tana sake lafewa a jikinshi..daga haka suka fita daga dakin..parlor ya koma ya dauki sauran apples dinta snn ya wuce flat dinshi..zaunar da ita yayi kan sofa tareda dora mata plate din apples din akan laps dinta yace he's coming..parlor ya koma ya kashe su tv da bulbs snn ya rufe gidan da key ya koma flat din nashi..kwanciya yaga tayi bayan ta ture apple din nata gefe..ya karasa da sauri ya dagota yana cewa"baby what?..why baki cigaba da cin apple dinki ba?.."hannunshi ta kama ta dora a forehead dinta idonta har ya ciko da hawaye tace"kaji fevern nefa zai dawo"..da sauri ya zauna tareda dorata a jikinshi yana girgiza mata kanshi yace"no don't cry plss..bazai dawo ba inshaAllah"..kuka ta fara mishi sosai tace"Allah zai dawo..yanxu haka su Husna zasuzo gobe ni banida lafia"..rungumeta yayi sosai yana shafa bayanta cikin sanyin murya yace"baby dan Allah stop crying..idan kina kuka zakiyi ciwon kai fa"..shiru tayi mishi tana cigaba da hawayenta as Allah kadai abunda takeji..nan take hankalinshi ya tashi ya shiga aikin rarrashi..gani yake kmr wnn kukan zaiyi affecting babyn cikinta..yasan yanda baason pregnant woman da damuwa shiyasa yake tsoron wnn halin nata.. yanxu idan wani abu ya samu babynshi ya zaiyi?..lalla6ata ya dingayi sosai har tayi bacci a jikinshi ya samu ya kwantar da ita..har zuwa lokacin kuma jikinta akwai zafi sosai dan zafin ma yafi wanda yaji a jikin nata daxun..lumshe ido kawai yayi yana tunanin taimakon daya kamata ya bata..yasan babu treatment din da zai dauke mata wnn zazza6in indai ba lokacin daukewan shi ne yayi ba..gashi kuma yanxu tunda yasan tanada ciki dole bazai dinga bata drugs anyhow tana sha ba tunda yafi kowa sanin illar hakan..addu'a kawai yake kada Allah ya dora mata laulayi mai wahala dan baisan yanda zaiyi da ranshi ba..shi kanshi yasan daga mashi hankali zata dingayi da wnn koke koken nata shiyasa yake fatan Allah ya bata mai sauki yanda bazasu sha wahala sosai ba..ya dade nan zaune yana kallonta saida dare yayi nisa snn ya samu ya gabatar da sallah shima ya kwanta nan kusada ita tareda sanyata a jikinshi. Washegari har wajen goma bata tashi ba sbd baccin da bata samu tayi sosai ba jiya..Bobby na nan zaune yana kallonta ko nan da can ya kasa matsawa sbd gudun kada ta tashi baya kusa..saida yaga rana ta farayi gashi kuma yau Friday snn ya samu yayi wanka ya shirya kanshi cikin farin shadda da akama dinkin kaftan..yasa hula white sai takalmin kafarshi shima white..bayan ya gama feshe jikinshi da turaruka ya dauki wayarshi ya fita sbd kiran da Nur keta mishi tun daxun..yana fita parlor yayi picking call din yana cewa"yane"..a daya bangaren Nur yace"normal..ya jikinta?.."a hankali yace"gata nan dai wlh..har yanxu tana kwance".. Nur yace"subhanallah zazza6in dai?.."zaunawa Bobby yayi kan one of kujerun parlon before yace"shine fa..amma dai yanxu naji da sauki sosai..bata samu bacci bane jiya shine yanxun take ramawa"..Nur yace"ohk Allah ya kara sauki..gashi kuma kace yau zatayi baqi koh?.."Bobby na shafa kanshi yace"sun kusa zuwa ma yanxu haka..kana ina yanxu?.."Nur yace"ina shiryawa kafin sallahr jumu'a".. Bobby yace"alright mu hadu a masallacin nima yanxu zan fito"..yace"alright sai ajima"..shima yace"sai anjima"..daga haka suka aiye waya..Bobby ya sake komawa dakin har lokacin bacci takeyi..ya taba forehead dinta yaji babu zafi sosai sai ya gyara mata kwanciya tareda pecking forehead dinta snn ya dau keys dinshi ya fita zuwa main house..bayan sun gaisa da Mummy yace mata zaije masallaci daga nan zai biya eatery ya siyo ma su Husna abinci tace he shouldn't buy anything tasa ayi musu girki sbd tasan dama Ayshan ba lafia..godia yayi mata sosai snn ya mata sallama ya fita bayan yace Miemie ta dinga shiga tana duba mashi ita time to time idan ta tashi ta kira ta sanar dashi. Around 2:17 su Billy suka shigo Kanon Dabo.. Husna ce ta kira Bobby ta sanar dashi karasowarsu yace su karasa gida shima yanxun zasu wuce..kusan a tare motocinsu suka yi parking a compound din gidan..nashi da na Nur sai kuma na Hamma Najeeb da sukazo a ciki..shi ya fara fita ya nufi inda suke sukayi musabiha da Najeeb snn yace su shigo su fara gaisawa da Mummy sai suje inda Aysha..Mummy ta tarbesu da farin ciki sosai suka gaisa tana tambayarsu ya Ammi da daddy suka amsa da suna lafia..bayan Miemie ta gama setting dinning tace suje su fara cin abinci kafin Aysha ta tashi daga bacci sai suje itama su gaisa. Bayan sun kammala suka nufi gidan nasu gaba daya tareda Najeeb dake sauri ya wuce aikinda ya kawoshi...suna shiga compound Yusra tayi saurin kwace hannunta cikin na Billy ta shiga cikin gidan da gudu tana kiran"Addah..Addah"..da sauri Bobby yabi bayanta gudun kar ta tasheta a bacci..suna shiga parlor yace they should make themselves comfortable shi zaije ta fito musu da ita..Husna ta bishi da kallo tana kunshe daria tace"Allah sarki Uncle Bobby..da gani Adda ba karamin wahalar dashi takeyi ba"..Miemie dake kusa da ita ta dan matsar da kunnenta kusa da nata tace"ke batada lafia"..da sauri Husna ta juya tana kallonta tace"da gaske?..ko ciki ne da ita?.."gyada kai Miemie tayi tana sake yin kasa da murya tace"but don't tell anybody oo.. Uncle Bobby might slaughter me"..hada ido sukayi suka tafa Billy dai kallonsu kawai take tana mamakin yaushe suka zama kawaye...Bobby na shiga dakin yaga kan gadon wayam dan haka ya bude bathroom da sauri ya shiga sai ya ganta tsaye jikin sink ta zubama mirror idanu tana hawaye..da sauri ya karasa tareda janyota jikinshi hankalinshi har ya fara tashi tace"what?.."goge tears dinta tayi tana girgiza masa kai..rikota yayi ya fito da ita snn ya zaunar da ita gefen bed shima ya zauna yana rikeda hannunta yace"baby menene plss?..akwai inda ke maki ciwo ne?.."girgiza kai ta sakeyi tana cewa"No"..hannu yakai ya karasa goge mata tears din snn yace"kinga su Husna sunzo dan Allah ki bar kukan nan indai baso kike suyi tunanin wani abu ke damunki ba"..kai ta sake gyada mishi without saying anything..shi kuma yayi pecking cheeks dinta snn ya mike yana cewa"let me get u something to wear sai muje parlor ku gaisa dasu"..kallonshi kawai tayi batace komai ba shi kuma ya fita da sauri zuwa bedroom dinta don dauko mata kayan da zatasa..tagumi tayi da both hands dinta tana tunanin abunda ya dameta..lissafi tayi yau kusan 2 weeks knn ya kamata period dinta yazo amma baizo ba sai kuma ga fever ta farayi da amai..dukda ba test tayi ba tanada tabbacin morning sickness take..tasan ciki ne da ita wlh.. musamman data tuna yanda suka rungumi juna suna farin ciki jiya a hospital sai ta sake tabbatar da zarginta..kawai gani takeyi baici ace ta samu ciki yanxu ba..Ina ma laifin tayi ko 6 months ne idan batayi 1 year ba amma wai ciki tun yanxu knn dai haihuwan 9 months din da bataso shi zatayi and Allah kadai yasan what will people say about her..kilan haka za'a zauna ayita gulmarta kaman yanda take zama tayi na mutane itama..ita bawai haihuwan ne bataso ba kawai bataso mutane suce daga yin bikinta ta samu ciki sai kace dama jira take..tayi nisa cikin tunani har batasan time din da ta fara hawaye ba..she knows for sure yasan da mgnr cikin yana sane ya boye mata..bayan few minutes ya dawo da kayan nata a hannunshi..ya taimaka mata tasa snn ya dan gyara mata fuska yanda bazasu gane tayi kuka ba ya kama hannunta suka fita zuwa parlon. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 67 Hannunta na cikin nashi har suka shigo cikin parlon..tana hada ido dasu Husna batasan sanda ta kwace hannunta daga nashi tayi saurin karasawa inda suke kawai sai ta shiga kokarin daukan Yusra da itama tana ganin nata ta taso cikin farin ciki sosai take cewa"Habibty"..itama Yusra rungumeta tayi tana daria tana kuma jin yanda har yanxu take kokarin dagata amma ta kasa..ta dago tana kallonta tana daria tace"Addah bazaki iya daukana ba yanxu"..da sauri Bobby daya karaso ya zauna kusada Nur yace"tell her"..Aysha tayi pecking forehead dinta snn taja hannunta suka zauna tana cewa"I missed u guys sosai wlh"..itama Yusra zaunawa tayi kusada ita tace"muma munyi missing dinki Addah"..daga haka ta juya tana kallon Billy data wani kura mata ido tana kallonta tace"what?."Billy tace"aah me kikaji nace?.."dan murmushi ta saki tareda matsawa tayi hugging dinta itama tana cewa"nayi missing dinki"..Husna da tun daxun bakinta ke kaikayi ganin hug din nasu bana kare bane tace"Adda kinga yanda kikayi kyau kuwa..kinyi wani fresh kin canxa"..juyawa Aysha tayi tana kallonta sai kuma ta dungure mata kai tana murmushi tace"idan bakiyi haka ba ai ba sunanki Asma'u Lamido ba"..Husna da har yanxu ke murmushi itama tayi hugging dinta tana cewa tayi missing dinta..Hamma dai na zaune yana kallon wariyar launin fata..saida ta gama da kowa snn ta dawo da kallonta gareshi tana wani murguda baki tace"ba ruwana ni dakai"..daria ya saki tareda juyawa yana kallon Bobby yace"inaga saika lamarin nan Dr..wnn matar taka rikicinta yawa ne dashi wlh"..dan murmushi Bobby ya saki yana kallonta yace"baby C'mon mana..ko me yayi ai yakamata ya wuce tunda har ya taso yazo inda kike"..da sauri Najeeb yace"exactly..kuma bayan zuwa ma har matata na kawo mata da qannena amma still take cewa ba ruwanta dani"..ya karasa mgn yana kashe ma Billy dake kallonshi idanu..tayi saurin kawar da kan nata tana daria..ita bazata iya wnn abun nashi ba..Lamido kuwa tasowa tayi daga inda take ta dawo nan kusa dashi ta zauna tana kallonshi da smile din nan nata dake sa both dimples dinta fitowa tace"to Hamma sannu da zuwa..Ina yini"..juyawa yayi yana kallonta da kyau shima yace"lafia lau my Maama..hope kina lafia"..tace"am fine..ya aiki".. yace"Alhamdulillah"..juyawa tayi ta kalli Billy da wani dan iskan murmushi snn ta sake dawo kallonta gareshi tace"Ya Billy?.."kallon Billy shima yayi kafin ya dawo da dubanshi gareta yace"aminiyarki ce ai..so Kunfi kusa"..da sauri tace"aah wlh ni Kunfi kusa yanxu"..daria ya saki yana girgiza kanshi yace"yanxun dai tunda na kawo maki su i have to take my leave"..da sauri ta mike tana marairaicewa tace"ko ruwa fa baku sha ba..kuma ni banyi girki ba"..Najeeb yayi relaxing yana cigaba da kallonta yace"kuma gaskia yunwa mukeji"..sake marairaicewa tayi tana kallonshi sai kuma ta juya gasu Billy suma duk tana sunyi wani kalar tausayi Husna hadda cewa"yanxu Adda mu taso gari ya garara tun daga Gombe muzo gidanki amma ko abinci bakiy mana ba..gaskai saina fadawa Ammi"..hankalinta ya sake tashi jin tace zata hadata da Ammi tayi rau rau da ido kmr zatasa kuka tace"ai dai banida lafia"..daga haka ta juya zata nufi kitchen Bobby yayi saurin mikewa ya kamota yana fadin"baby wasa fa suke maki sunci abinci"..dagowa tayi tana kallonshi a hankali tace"da gaske?.."hannu yakai yana goge mata dan guntun hawayen daya gani a Idonta tace"da gaske nake mana..Mummy tasa anyi musu abinci"..rungumeshi tayi da karfi tana sakin murmushi tace"Allah ya sakama Mummy da aljannah"..ya dagota yana jan dogon hancinta yace"Ameen Ameen love"..daga haka ya dawo da ita parlon sai taga duk suna mata daria..samun wuri tayi ta zauna tanata daure dauren fuska shidai Najeeb ya mike yace zai wuce don ana can ana jiranshi..sukayi sallama da Bobby da Nur snn ya fita su kuma suka bishi a baya..har mota suka rakashi suka sakeyi sallama snn suka dawo ciki shi Kuma yaja motar yayi gaba...suna dawowa Nur da gaba daya hankalinshi ke gare Miemie yace"pretty yau ba zuwa gidan aunty knn?.."da sauri Miemie ta dubi Aysha tace"zamuje mana..ko aunty Aysha?.."Lamido da taga yanda Bobby ya wani tsareta da ido yanason yaji amsar da zata bada ta hade ranta itama tareda fadin"eh mana"..tana gama fadan haka ta jasu suka wuce bedroom dinta Bobby yabisu da Ido..suna shiga ciki Nur ya kwashe da wani daria yana cewa"tofa kai saidai kayi hakuri na yan kwanakin nan dan naga alama Lamido tunda ta samu mutanen nan mantawa zatayi dakai"..harara mai kyau Bobby ya watsa mashi yana cewa"do u know ur problem?.."Nur yace"nope"..Bobby yace"dan iska ne kai wlh..kuma a haka kake tunanin zan dauki 'yata in baka..u better wake up dan idan ba canxa hali kayi ba tsakaninka da Miemie saidai kallo daga nesa"..ya karasa mgn yana wani daure fuska kai kace da gaske yake..shi kuma Nur nan take ya shiga hankalinshi sai ya hau bashi hakuri yana cewa"kaifa matsala na dakai bakasan wasa ba"..kallonshi Bobby yayi yana kokarin sakin dariar dake cinshi yace"inyamurin banza"..yana rufe baki shima Nur yace"Kai kuma bafulatanin banza ba"..gaba daya suka hada baki suka sheke da daria kaman wasu kananun yara..bayan sun gama Nur yayi saurin cewa"yauwa ya mgnr cikin?..did she knows?.."a hankali Bobby yace"anya kuwa?..i don't think so..kawai nidai addu'a nake koda ta gane kar ta daga hankalinta da yawa"..dafashi Nur yayi ganin kmr abun na damunshi yace"don't worry bazata damuba inshaAllah..mutum nawa ne ke neman haihuwan basu samu ba so ita da Allah ya bata am sure bazata kasa nuna farin ciki ba"..gyada kai kawai Bobby ya iyayi yana cewa"i hope so". Suna shiga daki Aysha da Billy suka baje kan gado suna hirar yaushe gamo yayinda su Miemie,Husna da Yusra suka bar musu dakin suka shiga dayan bedroom dinta suma suka dasa nasu labarin..yanda Husna da Miemie suka sake da juna zakayi tunanin tun tasowarsu dama suie qawance while ba haka bane..kawai hali ne yazo daya shiyasa qawancen nasu yayi daidai..har yamma yayi suna nan suna abu daya dan sallah kadai ya tada su shima suna idarwa suka sake dorawa daga inda suka tsaya..magrib na kawo kai jikinta ya fara rufewa da zazza6i wanda a daidai lokacin shima Bobby da suka fita da Nur tun daxun duk hankalinshi ya dawo gareta dan yasan daidai wnn lokacin zazza6in yake rufeta..sallama sukayi da Nur ya dawo gidan da sauri don yanaso yaga halinda take ciki..gashi yinin yau dama duk bataci wani abincin kirki ba..yana shiga ya iske Miemie da Husna sun wani baje a parlor suna labari suna kallo..suna ganinshi kowa ta shiga taitayinta har hada baki sukayi wajen fadin"Uncle Bobby sannu da zuwa"..yana dan murmushi yace"yauwa..Ina Bilkisu da Aysha?.."Husna tace"suna daki.. should i call them?.."yace"eh kice musu suzo"..da sauri ta mike zuwa bedroom din da suke ba'a dauk lokaci ba sai gashi sun dawo tareda su..tun daga nesa yake kallonta yana ganin yanda fuskan nan nata ke a daure yasan abunda ake gudu ya afku..suna karasowa ciki Billy na dan murmushi tace"Sir sannu da zuwa"..yace"yauwa Bilkisu..dama ce muku zanyi u should go get ready we are going out for dinner"..da sauri Miemie tace"Uncle Bobby Mummy tace an gama abinci fa"..kallonta yayi kmr bai gane me tace ba ita kuma ta sake cewa"tun daxu ta kirani tace zata aiko suwaiba ta kawo abincin nan..that ba sai Aunty Aysha tayi girki ba"..ajiyar zucia ya sauke yana gyada kai kafin yayi mgn Billy tace"Sir basai an kawo ba zamuje can muci"..tana rufe baki Husna ma tace"eh zamuje can Uncle Bobby"..kai kawai ya gyada tareda cewa"ohk"..yana kallon Lamido da har yanxu batasa baki cikin mgnr nasu ba..karasawa yayi inda take tsaye ya kama hannunta suka nufi flat dinshi..Husna tabisu da kallo tana murmushi Saida suka shige snn ta dawo da kallonta ga Miemie tana cewa"gaskia kuna ganin love a gidan nan..anya kuwa nima ba inyamurin zan samu in aura ba..naga kaman sunfi hausawa iya soyayya"..tana rufe baki Miemie ta sheke da daria tace"kamar a kunnen Uncle Bobby kika Fadi mgnr nan"..Husna ta wara ido da sauri tana cewa"ki rufamun asiri dan Allah in mutu maza su kaini ba yammata ba"..Billy dai daria ta saki tareda juyawa ta koma bedroom. Suna shiga ya zauna nan parlor tareda zaunar da ita kusa dashi yana kallonta kmr zaisa mata kuka yace"zazza6in ne koh?.."Kai ta dora a shoulder dinshi tareda gyada mishi kai..a hankali yakai hannu yana shafa kanta yace"kiyi hakuri kinji..zai dena inshaAllah"..lumshe ido kawai tayi hawaye na cikowa cikinsu ta kira sunanshi"partner"..yace"na'am baby"..runtse idon ta sakeyi nan hawayen dake ciki suka silalo ka fuskanta tace"ciki ne dani koh?.."yayi shiru yana kallon spot daya kmr bazai ce komai ba sai can yace"who told u that?.."da sauri tace"i don't have to wait sai wani ya fadamun..i noticed some changes a tareda ni and koda banyi test ba na tabbata am pregnant..morning sickness nakeyi"..ta karasa mgn tana rushewa da kuka..da sauri ya juya tareda rungume gaba daya a jikinshi yana patting bayanta yace"stop crying plss"..batace mishi komai ba saida ta gama kuka iya son ranta snn ta sake dagowa tana goge tears dinta tace"kasan ciki ne dani koh?.."yayi mata shiru kawai dan baisan me zaice ba..ta shiga gyada kai tana cewa"ko baka fada ba nasan u knew it all along..ai jiya Ina kallon yanda kuke murna kai da Provost bayan an kawo result"..kallonta yakeyi har yanxu ya kasa cewa komai..saida ya bari ta gama mitarta tsaf snn ya mikar da ita tsaye yana cewa"now u need to stop talking..muje kici abinci sai kisha magani before fevern naki yayi yawa"..batace mishi komai ba itama tabishi suka fita daga dakin..gaba daya suka fita tareda su Billy zuwa main house tunda sunce a can zasuyi dinner...Mummy na ganinsu ta tarbesu da fara'a snn tace su karasa dinning ga abincin can..duk suka isa suka zazzauna Miemie na kokarin serving Husna tace a barta tayi..ba musu kuwa suka barta duk tayi serving din nasu suka fara ci shidai Bobby na tsaye kusada Aysha yana kallon yanda take ta faman jujjuya abincin ta kasa kaiwa bakinta..kujera dake kusada ita ya janyo ya zauna yana kallonta kmr zaisa kuka yace"eat mana baby"..kallonshi tayi a hankali sai kuma ta girgiza kai tace"bashi nakeso ba"..matsawa yayi kusada ita sosai tareda kama hannunta yace"then me kikeso?.."ta juya ta kalli su Billy taga duk hankalinsu naga abincin da sukeci snn ta dawo da idanunta gareshi tana wani hade rai tace"Custard zansha"..ya dan marairaice mata yace"amma baby custard kadai bazai rikeki ba tunda duk yau bakici abinci sosai ba"..kallonshi ta danyi yanda taga duk ya tashi hankalinshi sai ya bata tausayi dan haka ta sake janyo plate din abincin tana jujjuyawa tace"to zan faracin wnn idan mun koma sai insha custard din".. kanshi ya shiga gyada mata yana murmushi sosai yace mata"yauwa partner"..ta saki dan smile snn ta shiga cin abincin a hankali shi kuma yana aikin kallonta..ganin shi baida niyyar cin abincin ta juya tana dubanshi tace"kai bazaka ci ba?.."hannunta ya kama ya rike idanunshi a kanta yace"ni ke nakeso kici..banso kina zama da yunwa"..murmushi ta Kara saki snn ta maida plate din nan tsakiyarsu tasa mashi spoon tana cewa"to muci wnn din tare"..murmushin shima ya saki bayan yayi pecking hannunta snn ya dauki spoon ya shiga cin abincin shima..daurewa kawai take tana turawa amma ko kadan batajin dadinshi a bakinta..bayan sun kammala suka dawo parlor inda Mummy ke zaune tana jiransu suka dan taba hira bayan sunyi sallahn isha yace su mike su koma gida..Husna dai tace"Uncle Bobby nidai zan kwana a nan tareda Miemie"..Bobby na murmushi yace"to Mummy kinada baqi knn"..Mummy tace"aikam kin kyauta Asma'u dan da baki Fadi haka ba nasan ita kanta Miemien cewa zatayi a can zata kwana"..Aysha dai kunyarta takeji yasa ta kasa cewa komai..bayan sun mata sallama suka koma gidan tareda Billy da Yusra..duk yanda taso ya bari taje inda su Billy hanata yayi sbd fever dake sake sauko mata..dole tayi sallama dasu ta dawo dakinshi inda yake nan zaune yana jiranta...custard din da tace tanaso yaje ya dama ya kawo mata tasha sosai snn ya rage mata kayan jikinta suka kwanta..can dare ta tashi tana ta kwarara amai don kaf abincin da taci saida ta amayar dashi..duk hankalinshi ya tashi haka ya gyara wurin tsaf snn yayi mata wanka ya dawo da ita ya kwantar a kan gadon tanata faman kuka kmr karamar yarinya..hankalinshi yakai kololuwar tashi gaba daya ya rasa inda zaisa kanshi yaji dadi..da dadewa dama yasan zaisha fama da ita musamman daya fuskanci dan banzan raki ne da ita..dan ciwo karami da bai taka Kara ya karya bama langwai take mashi balle laulayi da kowa yasan yanda yake da cin rai musamman daya kasance shi ba wani specific magani yake dashi ba dole saidai mutum yayi hakuri har lokacin tafiarshi yayi..duk yanda yaso ko black tea ne tasha kasa Sha tayi wai idan tasha zatayi amai haka nan ya hakura ya kyaleta bayan ta gama kukan bacci yayi gaba da ita. Wahsegari ta tashi normal babu fever as usual dama kullum kalau take tashi da safe sai dare yake sake dawowa..da kanshi ya mata wanka ya bata one of three quarters dinshi ta saka da wata shirt dinta dake dakin nashi snn ta fito zuwa wurin su Billy..da mamakinta sai taga suma sun tashi itada Yusra har ma sunyi wanka sun shirya..zama tayi suka fara labari kafin Kuma daga baya tace su shiga kitchen su fara girki don yau dai ba bazata bar Mummy da sawa ayi musu girki ba tunda ta samu sauki.. tare suka shiga kitchen din da Billy Yusra kuma suka barta a nan parlor tana kallon cartoon..Billy ce ta shiga peeling Irish yayinda ita kuma Aysha ta dauko chicken a freezer ta shiga gyarawa zatayi musu pepper soup..karnin Kazan na bugun hancinta taji wani irin amai ya taso mata aikuwa ta matsa jikin sink da sauri ta shiga kwarara aman..Billy ta bar peeling Irish da takeyi ta karasa nan kusada ita tana mata sannu..bayan ta gama ta bata ruwa da kuskure bakinta snn taja stool ta zauna tana maida numfashi..Billy dake murmushi tun daxun ta karasa ta dauki Kazan ta shiga wankewa tunda ta gama gyaran tace"ohh Allah da iko yake"..a kule Lamido ta juya tana kallonta tana daure fuska tace"ban gane ba"..Billy ta gama wanke kazar tasa ruwa snn ta dora a kan gas ta zuba duk abunda ake buqata snn ta rufe tukunyar ta koma kan Irish tacigaba da ferewa ta kuma kasa dena murmushi..ganin yanda taki kulata tace"Billy wai meye haka?.."Billy tace"kici gaba da 6oyemun kinada ciki nima ramawa zanyi wlh"..shiru tayi kmr bazata ce komai ba sai kuma can tace"shi ya fada maki koh?.."Billy tace"wlh ba wanda ya fadamun..bayan duk wnn fever da amai da kikeyi still sai inyi zaune sai wani ya fadamun kinada ciki kmr dai ba health personell ba..have u forgotten am a registered midwife?.."Aysha ta dan saki murmushi tana cewa"to registered midwife munafuka"..Billy ta shiga wanke Irish data gama peeling tace"ba wani munafurci fa.. addu'a na ya karbu knn"..tana rufe baki Aysha tace"wlh ke kimamun baki muguwa.. inshaAllah kema yanda bakinki ya kamani sai nawa ya kamaki..ke preterm ma zaki haifa inshallah 7 months da biki kawai saidai Muji ance kin haihu"..Billy ta kwashe daria tana cewa"aikam bakinki saidai ya tsaya kanki inshaAllah"..Lamido tace"idan na fara labour zan roka maki tunda kinsan ance adduar mace mai labour karbabbiya ce"..Billy tasa daria..haka dau suka cigaba da aikinsu suna hira kmr wanda sukayi jiya bai ishesu ba..Bobby dai ko da ya fito yana jiyo sautin dariarta a kitchen tayi Hamdala dan yasan tunda yaji haka sauki ya samu knn. Karfe 11 suka gama shiryawa bayan sunyi sallama da Mummy suka shiga mota zuwa gidan aunty sumy kmr yanda Aysha ta dage ma Bobby kan sai ya kaisu sun gaisheta..ita da Billy da Yusra suna motarshi yayinda Husna da Miemie suke motar Nur da sai wani giggiwa yake yau gashi ga pretty a mota daya..sai kuma abun ya hadu da Husna mai shegen rawar kai itama aikam baka sukaita zuba masa iyayi yana kallonsu da murmushi yana kuma mamakin wnn iyayin da suke dashi a shekarun nan nasu...aunty sumy ta karbesu hannu bibbiyu ta dinga nan nan dasu kmr ta maidasu ciki don so..sosai suma suka ware suka saki jiki da ita suka kwashi labari don itama ba daga baya ba wajen surutu..Nur ne kadai ya kasa sakewa duk yajishi a takure sbd nauyinta da yakeji yayinda ita kuma ko a jikinta don batasan ma yanayi ba..Bobby banda tsokanarshi ba abunda yake yana masa daria amma bai kulashi ba sbd baida lokaci tanka mashi tunda a gidan surkai yake..sun jima sosai a gidan don a nan sukayi lunch daga nan kuma suka mata sallama suka wuce bayan ta cika su Billy da gifts iri iri..basu zame ko inaba daga gidan nata sai wani park mai kyau..sunyi enjoying wajen sosai don sai after four suka bar wajen..daga nan kuma ya kaisu shopping yace kowa ta dauki abunda takeso..su Husna an samu abunda akeso nan aka shigo kwasan kaya kmr wanda zatayi changing wardrobe..Billy dai kasa daukan komai tayi sai Lamido ce ta daukan mata snn ta dauka ma Yusra..har su Ammi saida yace ayi musu tsaraba dan haka sukayi spending lokaci mai tsayi a nan cikin mall din basu gama ba..bayan sun bar wurin yanaso ya biya eatery suyi takeaway na abinci Mummy ta kira tace he shouldn't buy food that already an gama preparing musu dinner..haka suka koma gida sukayi dinner din a nan zuwa lokacin Aysha dauriya kawai take don abokin daren nata ya fara dawowa wato fever amma bata bari sun gane ba har suka gama hiransu snn suka wuce tareda Yusra da Billy kmr dai jiya Husna da Miemie Kuma suna gidan Mummy. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank State...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 68 Washegari around 2 Hamma Najeeb yazo ya daukesu suka wuce bayan sunyi sallama da Mummy da kuma Aysha da taci kuka ta koshi kmr idan sun tafi bazata sake haduwa dasu ba..sosai takejin zatayi kewarsu..Mummy da Bobby sun cikasu da tsaraba sosai na abun arziki haka suka tafi suma sunajij kewarta kaman yanda itama takejin nasu..Yusra har kuka saida tayi wai zata zauna tareda Adda amma haka nan ba yanda suka iya suka rabu suna kewar juna. Laulayi sosai Aysha ke fama dashi dan tun zazzabin yana tashi da dare har saida abun ya dawo kusan ko yaushe akwai fever jikinta ga kuma ba dama taci abinci sai ya dawo kmr zata fitar da kayan cikinta..sosai take shan wahala cikin lokaci karami ta rame tayi wani irin haske fau wanda kana gani dama zakasan ciki ne daita..Bobby kullum yana tareda ita dan zuwa yanxu ko hospital bai fiye zuwa ya dade ba sbd yanda hankalinshi bai kwanciya idan baya tareda da ita..ko abinci bata iyaci saidai taita kame Kamen kwadayi amma abincin kirki dai bazata tsaya taci ba sai idan jan ido yayi mata..sosai shima take bashi wahala dan gani yake ko ita da cikin ke jikinta bazata kaishi shan wahala ba..kullum fatanshi shida Allah ya rabata da cikin lafia don sosai ya matsu yaga ya rike da ko 'yarshi..wani lokaci sai ya zauna yayita surutu shi kadai wai babynshi yake mgn..ko Kuma yakai kunnenshi cikin nata wai yanaso ya jiyo heartbeat din babyn..sosai yake kulawa da ita da kuma cikin dake jikinta don duk wani abu da mai ciki ke buqata yana mata likewise wanda ba'a buqata ya nesanta ta dashi..lokacin da cikin ya isa antenatal da kanshi yake zuwa hospital da ita yayi mata duk wani necessary abu snn suje ayi mata duk tests daya kamata..scanning ma da kanshi yake mata don haka nan ma wani lokaci zaice suje yayi mata scanning yanason yaga ya kwanciyar babynshi yake..haushi yake bata sosai idan taga yana wnn abubuwan don gani take duk ranan da ta haihu kilan dena ma kulata zaiyi ya koma kan babynshi..tana ganin abubuwa iri iri dai akan wnn cikin ba daga Bobby ba ba kuma daga Mummy dasu Hajia Aunty Sumy ba..har kunya suke bata idan sukayi wani abu akan cikin amma su ta fuskanci ko a jikinsu..koda yake zuwa yanxu ta riga ta gama gane cewa jinin igbo dake running a jikinsu shike haifar musu da wnn rashin kunyan dan abubuwa da yawa idan sukayi saidai ta tsaya tana kallonsu tunda hausawa dai da Fulani tasan bazasu iya rabin rabin abunda sukeyi ba..tun cikin nada 3 months suka fara siyan kayan baby suna ajiyewa daga shi Bobbyn har zuwa kan su Mummy ta kasa gane Wanda zafi zakuwa da haihuwarta..yanda suke tulan kayan suna ajiyewa kai kace a kanta za'a fara haihuwa duk dunia..kulum cikin browsing unisex kayan yara suke designers masu kyau wai they don't want the baby to lack wani abu a dunia..kulawa sosai take samu ta kowane bangare amma hakan bai hanata wani lokaci ta sanyashi gaba tana kuka wai itadai ya cuceta musamman yanxu da cikin ya fara girma sai yasa mata wani irin qiba kusan duk kayanta sunyi mata kadan saidai taita fama da dagayen riguna...gashi mugun kunyar cikin takeji shiyasa ko Ammi ta kasa fadawa saida wasu sisters din daddy sukazo suka ganta da cikin shine da suka koma suka cema Ammi sai ta fara shirin tarban jika..sosai Ammi tayi mamakin wai Aysha nada ciki amma ta kasa fada mata dan dai ta Santa da rashin kunya kilan dai hankali ta farayi shiyasa ta kasa fada ma kowa kuma wai har uwar tata Fiddausi bata fadama ba lallai Aysha ta fara hankali kam..cikinta nada wata shidda aka sanya bikin Hamma da Billy four months masu zuwa aikam tasha takaici sosai wai ba'a tashi sa ranar ba saida aka daidaici lokacin haihuwarta sbd baaso taje biki..Billy taita mata daria tana tsokanarta wai Kilan lokacinda za'a fara bikin ita tana cikin labour room tana fama da kanta hakan kuma ba karamin bata ranta yakeyi ba dan har kuka saida tayi da akace four months aka saka. Wnn knn... Zaune take cikin parlonshi ta tasa katon warmer dake cike taf da awara a gabanta tanaci tana hadawa da uban yaji data ajiye kusada warmer din..daga ita sai wani qaton rigarshi blue daya tsaya mata iya guiwa..cikinta yana nan yayi zaune kmr yanda itama take zaune..a gefe guda kuma tv na aiki tana kallon wani series..yanda ta dukufa tanacin awaran dama kana gani zakasan ba lafia take ba dan mai lafia dai bazaiyi wnn abun ba saidai irinsu masu juna biyu..after like 7 mins Bobby ya shigo parlon hannunshi rikeda katon jug da aka zuba tamarind juice a ciki..yana zuwa ya ajiye matashi gabanta yana kallon uban yajin data ajiye gabanta yace"yanxu sake dauko yajin nan kikayi baby?.."dan marairaicewa tayi tana kallonshi tace"nifa bazan iyaci a haka ba partner"..tun kafin ta rufe baki ya dauke yajin daga gabanta yana hararanta yace"to bazaki karaci ba wlh"..kallonshi tayi da sauri tana kwabe fuska tace"dan Allah partner ka bani dan kadan zan zuba wlh"..girgiza mata kai yayi yace"No kici haka..ga tamarind din nan Mummy tayi maki"..turo baki tayi ta wani daddage ta ture warmern daga gabanta snn ta mike da tulelen cikinta a gaba ta wuce bedroom dinshi..da kallo kawai ya bita yana jinjina kokarin da maza suke da matansu masu ciki..gaba daya yanxu ta zama masifaffiya dan dan abu karami zaiyi ta haushi da fada Kai kace itace Hajia Nadia data durkusa ta haifeshi..hakan kuma bai taba damunshi ba dan yasan ba yin kanta bane condition din da take ciki ne ya haifar mata da haka..mikewa yayi shima ya dauki tamarind da sauran awaran nata ya bita dakin dashi..saida ya ajiyesu bisa table snn ya karasa kan gadon tareda dagosu gaba daya itada cikin nata ya dorasu kan laps dinshi..hawaye sosai ya gani a fuskanta nan take kuma hankalinshi ya tashi dan dunia idan akwai abunda ya tsana yanxu bai wuce wnn kukan nata ba..sam bayason gani sai yaga kmr yana affecting da ko yarshi dake cikinta..rungumeta yayi batareda damuwa da cikinta dake zungurinshi ba yace"yanxu baby sbd yajin kikemun kuka haka?..bakiso hankalina ya kwanta koh?.."hannu takai tana share hawayen tace"to ai bazan iyaci a haka ba kuma ni ban koshi ba"..nashi hannun ya mika ya karasa goge mata tears din yana cewa"banason yajin yayi affecting babyna ne ke kuma naga baki iyacin kadan ba"..kallonshi tayi hawaye na sake ciko idonta tace"ai dama baka damu daniba ni..wlh tunda na samu ciki ka dena sona"..cupping fuskanta yayi tareda manna mata peck a forehead dinta yana kallonta da murmushi yace"i love u both baby..ku biyun are my family so i love u equally"..tun bai rufe baki ba ta kwace fuskanta daga hannunshi tana sake rushewa da kuka tace"wato u love us equal..tun babyn baizo dunia ba kana cewa u love us equal then idan yazo kilan watarana cewa ma zakayi baka san wace ni ba".. Bobby couldn't help it but laugh da jin wnn mgnr nata..rungumeta yayi yana daria sosai yace"don't tell me kishi kikeyi da abunda ko dunia baizo ba"..sake daure fuska tayi tana turo baki tace"kaima ba gashi kana nuna bambanci ba"..dagota yayi ya sake cupping fuskanta yace"u don't have to be jealous baby..i love u more..my every little happiness depends on u love so i love u more..i promise i love u more"..sake turo baki tayi tareda raba jikinta da nashi tace"indai da gaske u love me more ka bani yajina in karasa cin awarata"..ba musu ya dauko yajin ya zuba mata dan kadan snn ya daukota ya ajiye kan sofa ya fara massaging legs dinta yace"to gashi nan yi sauri ki karasa ci sai ayi wanka"..bata sake cewa komai ba tacigaba da cin awaranta shi kuma yana massaging legs dinta da suke dan kumbura time to time..dan kadan ta rage cikin tulin awaran dake gabanta snn ta kora da tamarind da Mummy keyi mata kullum sbd shi kadai take iya sha..shi kuma ya dauketa suka shige bathroom. Washegari kafin ta tashi ya fita sbd kiran da Nur keta Maka mashi wai there's emergency a college clinic kuma shi bai cikin makarantan..kafin ya fita saida ya tabbata ya ajiye mata duk wani abu da take buqata tareda dan short note snn yayi pecking forehead dinta da katon cikinta ya fita..lokacinda ta tashi was around 11 ta shiga bathroom dinshi tayi wanka snn ta fito ta shafa cream da turare ta zura jallabiyarshi ta fita..these days gaba daya kayanshi take sawa dan nata kusan duk sunyi mata kadan..riguna ya ware mata manya da jallabiyas marasu tsayi sosai ya bata yace ta dinga sawa tunda duk maternity gowns da yasa aka dinka mata bata sawa wai nauyi suke mata..tana fita parlonshi taga ya ajiye mata goruba da tsamiyar biri da shansu zame mata kullum kmr ka'ida..ta saki murmushi tareda karasawa zata dauka sai taga ya ajiye mata note a kusa dasu dan haka ta zauna snn ta dauki note din ta fara karantawa kmr haka"hey love..sorry zaki tashi baki ganni ba naje clinic ne wai there's emergency but bazan dade ba zan dawo..take care of urself and my baby for me..love u"..da murmushi sosai ta karasa karantawa snn ta dauki gorubarta ta fita main parlor tanaci..bangaren mai aikinta ta nufa tayo mata mgn snn ta dawo cikin parlon ta zauna..mai aiki na zuwa bayan ta gaisheta tace"dan Allah saude kin iya wainar flour?.."da sauri mai aikin tace"na iya Hajia"..tace"yauwa to shi nakeso kimin yanxu..akwai flour a store kar kisa kwai amma kisa attaruhu sosai yanda yajin zai fito and kisa maggi ma da yawa"..yarinyar ta amsa mata da"toh"snn ta juya zuwa kitchen ita kuma ta shiga cin goruba tana kokarin kunna tv..Kiran daddy ne ya shigo wayarta ta dauka da sauri tana cewa"daddy ina kwana"..yace"lafia lau Aysha ya jikinki?.."tace"Alhamdulillah"..yace"to Allah kara lafia ga mamanki zakuyi mgn"..daga haka daddy ya bawa Ammi wayar itama Aysha ta gaisheta ta amsa da tambayarta ya jiki..duk kunya suke bata idan suna tambayar ta ya jikin nn wlh..kawai saita dinga imagining shknn sun san yanda akayi ta samu cikin..Ammi tace"maganin nan da aka kawo kinasha yanda akace maki dai koh?.."tace"Ina sha"..Ammi tace"to kicigaba da Sha dan Allah yanda aka fada maki..amfani ne dashi sosai karkiyi wasa dashi"..kanta a kasa tace"toh Ammi..yanxu Ammi dan Allah bazaki sa baki ya barni inzo in ganku ba?.."Ammi tace"keda kike da tsohon ciki Aysha Ina ke ina zuwa Gombe a yanxu?..ki bari idan kika haihu lafia sai kizo amma dai yanxu bazai yiwu kizo har Gombe da tsohon ciki ba"..kmr zatasa kuka tace"Ammi ba tsoho bane it's just 6 months ai zan iya zuwa"..dan murmushi Ammi ta saki tana girgiza kai tace"6 months din ne bai tsufa ba?..kinfiso kizo kiyita yawo da ciki knn kowa yana kallonki".. tayi shiru batace komai ba Ammi ta sake cewa"idan ma kinzo yanxu nasan bazai fi kiyi one week ba amma idan kika bari kika haihu saiki dawo gida gaba daya idan kinyi 40 sai ki koma"..nan da nan ta washe baki jin abunda Ammi ta fada tace"to Ammi na bari"..Ammi da yanxu sosai suke shiri da yar tata dan a ganinta tayi hankali tace"yauwa ko kefa..Allah dai ya saukeki lafia"..tayi murmushi cikin ranta tace"Ameen"..daga haka sukayi sallama da Ammi ta ajiye wayar. Ana kawo mata wainar flour ta tasa a gaba ta faraci tana hadawa da yaji kaman yanda ta saba..ga kuma sauran tamarind dinta na jiya da tasa a fridge shima tana korawa dashi..ita yanxu har ta mance yaushe rabonta da shan tea dan koda safe ko rana ko dare batada abunsha daya wuce tamarind..ko ruwa bata cika sha ba yanxu sbd batajin dadinshi a baki amma tamarind Kam yana mata dadi sbd wnn tsamin da yakeyi..saida taci tayi nak snn ta ture plate din tacigaba da kallonta time to time tana duba agogo ganin har rana ya farayi bai dawo ba..har ta gaji da kallon dayi bacci a nan cikin parlon kawai taji ana shafa cikinta ta bude ido da sauri tana ture hannunshi tace"meye haka?.."zaunawa yayi nan kusada ita yana kallonta da murmushi yace"ina mgn da babyna ne fa"..murguda baki tayi tana hararanshi shi kuma yayi pecking goshinta yana cewa"to am sorry"..banza tayi mishi batace komai ba shima bai sake mgn ba sbd kiran Nur daya shigo wayarshi..dauka yayi suka gama mgn snn ya janyota jikinshi yana gyara gashinta da bata gyarashi ba yace"what is it baby?..waya ta6amun ke?.."tale baki tayi kmr zatasa kuka tace"shine ka dade baka dawo ba"..yace"sorry naje hospital ne sai kuma Nur ya kirani wai da akwai emergency a college clinic so shine naje na dubata"..da sauri ta dago tana kallonshi jin ya ambaci college clinic tace"u mean college clinic kaje?.."gyada kai yayi yace"yes"..tace"kuma mara lafiyan da ka duba mace ce?.."yace"mace ce mana baby akwai wani problem ne?.."tun bai rufe baki ta hau girgiza kai tana hawaye tace"amma ka cuceni"..mikewa take kokarinyi yayi saurin dawo da ita jikinshi yana patting bayanta yace"subhanallah me nayi?.."tace"amma tun yaushe nake fada Maka banson kana zuwa clinic din nan..ni college din ma da inada dama wlh bazaka sake zuwa ba dan bakasan yanda mata suke kallonka bane"..wara ido yayi yana kallonta da murmushi yace"so kema kina kallona knn lokacin da kike makarantan?.."harara ta watsa mashi jin zai canxa mgn tace"don't change the topic"..kissing gashinta yayi yace"am not changing the topic baby i just want to know..kinsan dai dunia ya nade bazan so wata mace apart from u ba so ki kwantar da hankalinki"..sake turo baki tayi tace"how will ever kwantar da hankali bayan nasan yanda halin maza yake especially now that my body is Chang..."bai bari ta karasa ba yace"kome zaki zama ni ina sonki haka and ba abunda zai canxa hakan..i love u for who you are bawai dan kyawunki kadai nake sonki ba so stop saying your body is changing indai baso kike muyi fada ba..i love u and only you".. kallonshi tayi yanajin wani irin sanyi na mamaye zuciarta..wato she is so lucky to have found this guy..he is so amazing and she loves him so much..rungumeshi ta sakeyi tana sakin murmushi tace"to na dena..amma da gaske tsoron yammata nakeji"..hannu yakai yana shafa kanta yace"u don't have to baby..duk macen da zata kalleni saidai kallon kawai amma bazata iya dauke heart dina wajenki ba for i love u unconditionally"..smile ta Kara saki tana shakan kamshin perfume dinshi tace"nima i love u more partner..u are my world"..dago face dinta yayi yayi pecking forehead dinta yana cewa"now tell me are u among wayanda suke kallona lokacinda kina school?.."murmushi ta saki tana gyada kai tace"sosai ma amma kasan irin kallon da nake maka?.."girgiza kai yayi yana smiling yace"no"..tace"irin masifaffun inyamuran nan masu shegen taurin kai..har cewafa nake da kyar in baka cikin masu assasa yaki Biafra"..wara idanu Bobby yayi yana kallonta yana daria yace"so yanxu baby kallon mai son a raba Nigeria kikemun?.."kama hannunshi tayi tayi pecking tana cewa"it was then ai..amma yanxu i know better..nasan duk dunia za'a dade ba'a samu namiji kaman kai ba shiyasa nakesonka sosai"..murmushi shima ya saki yana rike da hannun nata yace"amma gaskia baby baki kyautamun ba..koda yake ba laifinki bane laifina ne dana sa maki ido ma takura maki"..murmushi take tana kallonshi as abubuwan da suka faru rush back to her tace"ai gaskia partner ba karamin wahala ka bani ba..ka takuramun a lokacin nan kullum saika mun masifa"..murmushin shima yakeyi yace"and believe baki kaini shan wahala ba..duk wnn abun da nake maki qi fadi ne kawai amma Allah kadai yasan halinda nake ciki a lokacin"..daria ta saki sosai ta rungumeshi yace"shiyasa idan kika haifamun babygirl kaman ki bazan yadda in kaita irin colleges din nan karatu ba sbd kar taje tarwatsa rayuwar proprietor kmr yanda kika tarwatsa nawa"..dukan chest dinshi tayi cikin shagwaba tace"tarwatsa rayuwarka ma nayi koh?.."ya sake rungumeta da hannunshi daya dayan hannun kuma ya dauko wani abu cikin pocket dinshi snn ya dagota yana cewa"now close ur eyes in nuna maki wani abu"..ba musu ta rufe eyes dinta shi kuma ya bude hannun nashi snn yace ta bude idon..tana budewa taci karo da zabunanta na gold guda biyu daya ta6a kwace mata a college aikam ta wara idanu sosai tana kallon rings din tace"oh my Godd..kasan gaba daya na mance dasu wlh"..kama hannunta yayi ya shiga kokarin zura mata su a fingers dinta yace"ai ni ban manta dasu ba"..tana daria tace"ai ranan haushinka naji bafa daka kwacemun su"..shima yana dariar yace"ni kaina a lokacin saida naji haushin kaina ta yanda har idanuna suka gano abunda ko Nur da yake mgn dake bai gani ba..a duk lokacin da muka hadu kokari nakeyi sosai na ganin ban kalleki ba amma bansan ya akeyi ba kawai saidai in tsinci kaina Ina kallonki kuma ba tareda na gaji ba especially idan kikasa wnn glasses din naki".. kallonshi kawai takeyi tana murmushi har ya gama saka mata rings din snn yakai hannun bakinshi yayi kissing yana cigaba da murmushi yace"ya kamata dai acigaba da samun glasses din nan a gida ina gani dan da gaske ji nake kaman in daukeki duk lokacinda na ganki dasu"..har yanxu murmushi take tace"da wnn tulelen cikin ne zan wani dinga da glasses?.."kissing cikin yayi yana cewa"itama zan siyo mata irin naki yanda idan kin haihu sai ku dinga sakamun Ina gani"..daria kawai ta saki tana girgiza kai shi Kuma ya sake janyota jikinshi ya dan rage muryanshi yace"kinsan fa ni mace nakeso ki haifa"..gyada kai tayi tace"i know..ni kuma nafison namiji"..kallonta kawai yake yana murmushi lokaci daya kuma ta fara ganin wasu abubuwa cikin idanunshi..a hankali yakai hannu yayi cupping fuskanta fasu snn ya dora forehead dinshi akan nata..kallon eyeballs dinshi takeyi kmr yanda shima yake kallon nata dan zuwa yanxu tana iya daukan lokaci tana kallon idonshi amma dukda ba kmr yanda shi yakeso ba..a hankali ya lumshe ido tareda dora lips dinshi akan nata murya can kasa yace"baby please..i missed us"..hannunta ta zagaya wuyanshi dashi snn tayi grabbing bakinshi shima nan da nan ya kama kaman magnet..daga haka kuma na baro musu parlon and ban sake dawowa ba sai bayan wata uku...lol😂 Bayan wata uku... Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 69 Bayan wata uku... Cikin Aysha ya shiga wata na tara knn cif and edd dinta baifi saura 3 days..gaba daya ta canxa daga Lamido da kuka sani a baya ta dawo wata irin salaha kmr dai ba itane ke ba iyayenta ciwon kai ba..sosai ta zama kalar tausayi dama ga cikin nata da girma sosai musamman yanxu da haihuwan ta kusa sai girman ya sake fitowa..ga kuma nauyinshi da takeji wani lokaci har cewa take kilan twins zata haifa maybe scanning machine dinsu ne baida kyau shiyasa bai nuna haka ba..duk ta Fadi haka saidai Bobby yayi daria dan yasan baby daya ne cikinta saidai girman kawai..ga masifa data koya da rashin hakuri Dan abu karami zata hau fada tana cewa ai dama dole ya dena sonta sbd yanxu tayi Muni shidai banda daria ba abunda yake mata..wani lokaci har video yake mata bata sani ba idan tana wnn sababin yasan idan ya nuna mata nan gaba daria zatayi..sai kuma fever da take yawan kwana dashi da ciwon baya wanda har yasa take cewa kilan mutuwa zatayi..sosai take daga hankalinshi duk tayi wnn mgnr amma bai taba nuna mata ba.. addu'a kawai yake mata tareda fatan Allah ya sauketa lafia..a bangaren mummy ma tana kulawa da ita sosai dan da dadewa itace ta dauki nauyin dafa mata duk abunda takeso tunda ba komai take ciba..yanda take lalla6ata ita har kunya ma takeji amma sai taga su ko ajikinsu..siyayya kuwa zuwa yanxu ba abunda basu gama siya ba tun daga kan kayan baby har zuwa ita kanta nata kayan..bedroom guda ya ware cikin nata yasa akayi renovating dinshi zuwa baby room mai kyau aka kuma cikashi da kayan yara iri iri tun daga kan furnitures har zuwa su toys da sauran kayan wasa na yara..tsakaninta da Amminta ma yanxu mutunci sukeyi sosai dan yanxu tayi hankali ta dena rashin kunya a cewar Ammi shiyasa suke dasawa abunsu..kusan kullum sai sunyi waya da ita dan ko ita Ayshan bata kira ba Ammi zata kirata taji ya jikinta..tana kuma turo mata addu'o'i tace taitayinsu daga nan har lokacin da Allah zai kawo haihuwar wai sai yazo mata da sauki..sosai itama take tausayawa 'yar tata sbd halin da take ciki shiyasa Husna na gama ssce daddy yace tazo ta zauna tareda ita ko ba sbd aiki ba at least zata dan dauke mata kewar gida da take fama dashi..zuwan Husnan kuma ya yayi mata dadi sosai dan kusan kullum suna tareda ita da Miemie a gidan su suke mata komai saidai mai aiki ta tayasu kawai..shima Bobby yana bakin kokarinshi kwarai wajen ganin batayi lacking wani abu daga gareshi ba including time dinshi da kuma caring..sosai yake tsayawa ya kulada ita don ko wurin aiki ma sai ya tabbatar ya gama mata komai snn yake wucewa hakan da yakeyi kuma ba karamin faranta mata rai yake ba..tana jin dadi sosai idan taga yanda daga shi har Mummy da siblings dinshi ke nuna tsantsar so da kula wa cikin nata har watarana takejin ta matsu ta haihu sbd taga irin kaunar da zasu nunama babyn..gani take kmr Mummy da Bobby sunfi ita kanta da babyn ke jikinta kaunarshi amma batasan ko dan riga yazo dunia bane..a halin yanxu dai duk wani fatanta bai wuce Allah ya sauketa lafia ba. Yau Friday suna zaune parlor ita da Miemie da Husna suna kallon wani film Sab ya shigo gidan da sallama yana hararar Miemie da gaba daya hankalinta ke ga film da suke kallo..bayan ya karaso ciki ya zauna sai ya dan saki fuska yana duban Aysha da murmushi yace"sannu Aunty Aysha"..murmushi itama ta saki tana girgiza kai tace"bazaka dena cemun sannun nan ba koh?.."yana cigaba da daria yace"ai dole ace maki sannu matar Uncle Bobby..wnn babyn namu nasan da kyar idan baya baki wahala don da gani nasan fitina zaiyi wlh"..daria gaba daya suka saki har su Husna da hankalinsu ya dawo kan hiran nasu..Husna tace"wlh uncle Sab kmr kasan nima tunanin da nakeyi knn..na tabbata indai ya dauko halin Adda to wlh ba karamin fitinanne za'ayi ba"..ta karasa mgn tana daria Aysha Kuma tace mata"zanyi maganinki wlh..ki bari insamu time dinki"..Sab yace"ai idan ya dauko halin babanshi bayan fitina ma sai ya hada da masifa da rashin mutunchi..ta6 Uncle Bobby ai ba baya bane wajen wadan nn dabi'un"..da sauri Miemie tace"wlh kuwa uncle Sab..ni kaina gani nak..."bata karasa ba ya katseta ta cewa"C'mon keep quiet wayasa dake a wurin nan?.."turo baki tayi tana rungume hannunta tace"ai nima ba da kai nakeba"..kwafa yayi yace"kicigaba da murguda min bakin nn watarana saina karyashi wlh..badai ni kikaje kikama munafurci a wurin Mummy ba..zan kamaki ne"..sake daure fuska tayi tace"nidai gaskia na fada mata ai..kuma ba ruwanka dani Uncle Bobby yace ka dena shiga harkata"..ya bude baki zaiyi mgn Lamido tace"ya isa haka dan Allah..na rasa meyasa ku kullum cikin fada kuke kmr tom and Jerry".. Sab yace"yarinyar nan batada kunya bakisan halinta bane..wai har ni zataje tayima gulma a wajen Mummy"..Husna tace"ASP Uncle Sab da gaske ba gulma tayi Maka ba..a gabana Mummy ta tambayeta"..wani irin daria Sab yayi yana cewa"bazaki dena Asp Uncle Sab din nan ba koh?.."dariar itama takeyi tace"to ai Asp ne naga"..murmushi kawai yayi ya gyada kai kafin wani cikinsu ya sake mgn Bobby da Nur sun shigayi parlon a tare..da sauri Sab ya mike yana kallonsu da murmushi yace"sannunku da zuwa"..Bobby yace"kai baka zuwa sallahn jumu'a knn?.."Sab yace"yanxun na dawo ai..ask Aunty Zata fada maka ban jima da shigowa ba"..Bobby bai sake cewa komai ba suka karasa parlon suma suka zauna..Miemie da Husna suna gaishesu suka bar parlon shima Sab yana gama gaisawa dasu ya fita dan dama akwai inda zaije...kallon Aysha da har yanxu take zaune yayi kafin a hankali ya mike ya koma kusada ita ya zauna yayi mata side hug yana fadin"how is my baby doing?.."a dan kufule tace"ban sani ba"..yayi murmushi yana nuna cikin nata yace"bafa wnn babyn nake nufi ba wnn"..hannunshi ta ture daga jikinta tana duban inda Nur yake zaune tace"Sir Ina yini"..murmushi ya saki yana kallonta shima yace"lafia lau Lamido..ya jikinki?.."kanta a kasa tace"Alhamdulillah"..Bobby yace"baby bana hanaki kiranshi da Sir din nan ba..call him Nur mana ai sunanshi ne"..girgiza kai tayi tana dan murmushi tace"bazan iyaba"..tana rufe baki Nur yace"kinji mutumiyar kwarai..duk iskancinka dai haka zaka hakura ka barta tace bazata iyaba"..Bobby yayi daria kawai tareda dan rage murya yana kallonta yace"kinsan mene?.."kai ta girgiza mashi alamar bata sani ba..yace"zuwa mukayi dai yau mu fadawa Miemie cewa muna sonta"..dan wara ido tayi tana kallonshi tace"da gaske?.."yace"eh mana..nine ma zanyi masa zancen sbd a abokin Nur nazo yau ba Uncle Bobby ba"..murmushi kawai Aysha tayi tana girgiza kai tasan wnn mgnr wasa yake mata..mikewa zatayi yayi saurin kamata ya mikar da ita snn yace ta turo musu Miemie idan ta shiga..tana murmushi itadai ta wuce zuwa bedroom dinta ta tura musu Miemie kmr yanda suka bukata...tana zuwa ta nemi wuri ta zauna kasa Bobby yace ta koma kan kujera ta zauna..ba musu tayi hakan sai kuma duk sukayi dif aka rasa wanda zai fara mgn cikinsu..can Bobby ya nisa tareda Kiran sunanta..ta amsa kanta kasa dan har wani faduwar gaba taji tanayi ba gaira ba dalili..a nutse sosai ya fara mata bayani ta sigar da yasan zata fahimce shi sosai.. already dama Saida ya fara mgn da Mummy da parents din Miemie snn yazo gareta so ba tareda wani shakku yake mata bayani ba..itadai tsit tayi tana sauraran yanda yake koda mata abokinshi sai daga karshe kuma yace zai barta dashi ya karasa Mata sauran bayanin..bayan ya bar parlon Nur ya dora daga inda ya tsaya itadai kusan mutuwar zaune ma tayi jin wai da gaske Uncle Nur ne ke sonta..sosai ya kakkashe mata jiki da salon soyayyarshi wanda ita halin yanxu dai bazata iya gane shin tana sonshi ne ko kuma bata sonshi ba..shima baiyi gaggawa ba yace she should go and think about it idan ma tanada Wanda zatayi shawara dashi tayi idan ta gama yana jiran feedback dinshi..haka ta mike ta bar parlon jiki a sanyaye kmr kazar da kwai ya fashewa a ciki. Wnn knn... Washegari bayan ta idar da sallahr asuba ta dade sosai zaune inda tayi sallahr tana ta addu'o'i bayan ta kammala azkhar dinta..Bobby kuma na masjid bai dawo ba..sosai take addu'a tana rokon Allah ya sauketa lafia ya kuma raya mata abunda zata haifa cikin tafarki madaidaici..saida gari ya fara haske snn ta shafa addu'an snn ta shiga kokarin mikewa amma sai me?..kugunta taji ya rike gam ta kasa ko kwakwkwaran motsi a wurin..ta kai hannayenta biyu ta dafe waist din dasu snn ta sake yunkurawa zata tashi sai kuma taji bayanta shima ya rike da sauri ta sake komawa ta zauna ta rintse ido tana maimaita innalillahi a cikin ranta..Saida taji ciwon ya dan lafa snn ta sake kokarin mikewa a karo na uku still taji bazata iyaba dan haka ta koma tacigaba da zama tana salatin annabi..Bobby daya dawo daga masjid direct kitchen ya shiga ya hado mata tea da shanshi ya zama mata constant duk ya dawo daga sallahn asubah dama saiya fara hada mata yake shiga daki..yana shiga ya ganta zaune nan inda tayi sallah ya ajiye mug din hannunshi kan table da sauri ya nufi inda take yana dagota yace"baby are u alright?.."a hankali ta dago ido tana kallonshi yaga eyes din are so red nan take hankalinshi ya tashi baisan sanda ya durkusa nan kusada ita ya kamo hannnuwanta yana tambayanta what's wrong ba..dan murmushi ta saki ganin har hankalinshi ya tashi tace"ba komai fa partner..kawai tashi zanyi naji bayana ya rike amma believe me yanxu banajin komai"..kamata yayi ya mikar da ita tsaye snn ya shiga kare mata kallo wai ko zaiga wani canji tattare da ita still yaga ba komai dan haka ya rike hannunta ya zaunar da ita kan sofa bayan ya zare hijabin dake jikinta..tea dinta ya dauka ya mika mata yace"to ga tea dinki Kisha"..murmushi tayi ta karba shi Kuma ya dauke carpet da tayi sallah dashi ya ajiyeshi inda ya dace snn ya sake dawowa ya zauna nan kusada ita yana kallonta tana shan tea din...bayan ta gama ya sake kamata suka kwanta kan gado ya rufesu da duvet cikin lokaci kankani kuma bacci yayi gaba da ita shi kuma ya kasa baccin sbd har yanxu bai gama yadda she's alright ba..gani yake kmr idan ya rufe ido ya fara baccin wani abu na iya faruwa da ita har saida ya ga baccinta yayi nisa snn shima ya lumshe ido baccin yayi awon gaba dashi...can cikin bacci Lamido taji kaman ana yi mata suka a maranta nan take ta bude ido baccin ma gaba daya yayi kaura daga idonta..dan motsawa tayi da nufin ta gyara kwanciya sai kawai taji wani irin ciwon mara ya sake kamata har batasan lokacinda ta wani irin salati cikin tsananin tashin hankali ba..da sauri Bobby ya bude ido jin kmr kuka take aikam yana ganinta ya mike zaune da sauri yana janyota jikinshi yace"baby what's wrong"..hannayenta na rike da mararta tace"ba..ya..na..mara..ta..way..yo"..sauka yayi daga gadon da sauri ya dora t shirt akan singlet da three dake jikinshi snn ya dauketa cak ya fita daga dakin da ita..sbd tsabar bala'i ko kuka ta kasayi sai faman salati take dan da gaske tayi zaton karshenta ne yazo..Bobby ma duk a gigice ya fita daga gidan kai tsaye mota ya bude ya sakata ciki snn ya shiga ya tayar da ita suka fita daga gidan..direct hanyar clinic dinshi ya nufa ita kuma tana baya sai faman murkususu take tana maimaita innalillahi..har wani zufa ke keto mata despite air condition dake aiki cikin motar..Bobby gaba daya gigicewa yayi ko driving din yaji kaman bazai iya ba amma dole yacigaba dayi dan kafin ma yace ya kira driver dinshi yazo wani bata lokaci ne haihuwa Kuma ba zaman jiransu zaiyi ba ya sani.. addu'arshi dai bai wuce Allah ya sauketa lafia ba..yana shiga hospital ko parking space bai karasa ba yayi parking daga nan bakin gate tareda bude motar ya fita itama ya fito da ita da sauri yayi cikin asibitin..da yake safiya ne babu mutane sosai asibitin sai few daga cikin staff da masu jinya da suka kwana a nan..labour room ya nufa da ita kai tsaye yaci sa'a kuma ya tarar da matron salamatu on duty dan haka yayi saurin shigar da ita ciki yace tazo ta duba mishi ita..babu wasting of time matron tayi mata ve nan kuma taga cervix dinta is 4 cm dilated koda ta sanar dashi hankalinshi sake tashi yayi don yasan zaiyi taking nata so many hours before ya gama fully dilation tunda primi ce..ga kuma ciwo da take fama dashi tun yanxun dan yanda takejin maranta kamar zai rabe gida biyu ne dan azaba..waya ya zaro daga aljihunshi ya kira aunty sumy yace ta samesu asibiti that bazai iya fadama Mummy ba don tashin hankalinta zatayi sosai so gwara ya bari idan ta haihu sai a fada mata..suna gama waya da ita ya kira Nur shima ya sanar dashi suna asibiti daga nan kuma ya ajiye wayar tashi ya shiga taimaka mata da kanshi..hannunshi ta rike gam cikin azabar da takejin kmr shi zaiyi ajalinta tace"par..tner..zan..mutu..mutuwa..zanyi".. girgiza mata kanshi yakeyi duk a rikice yace"bazaki mutu ba inshaAllah baby..lafia zaki haihu"..girgiza kai kawai Lamido take tana karanta innalillahi wainna ilaihi rajiun..har yanxun bata dena zufa ba ga kuma ciwon yakici yaki cinyewa..tun tana ganin abun kmr wasa har tazo ta fara gaskata tunaninta da gaske mutuwarta ne yazo..sosai take shan wahala amma wai ace har yanxu 4 cm take?..anya kuwa zata iya haifan babyn nan da kanta?..Bobby dai na tareda ita duk ya rikice dan kmr ma bazai iya cigaba da aikin ba amma da taimakon matron ya samu yayi gripping kanshi snn yacigaba da bata duk wani taimako da yasan tana bukata at this stage of labour..bayan lokaci kada n aunty sumy ta karaso asibitin nan Kuma yace taje gida ta taho musu da kayan haihuwa Dan shi bai samu ya dauko komai ba sbd rudu daya shiga..ba musu kuwa ta koma gidan ta dauko kayan da taimakon su Husna da suke gidan ta kuma ce kar su bari Mummy taji labari har sai idan ta haihu..lokacinda ta dawo asibtin suka hadu da Nur a kofar shiga labour room din yanata kiran Bobby amma baya dauka..a karo na farko da taji wani irin nauyin Nur ya kamata kasancewar yanxu tasan shine yake son Miemie..gaba daya sai tajita wani uncomfortable dashi unlike before da har wasa da daria sukeyi a tsakaninsu..shima kanshi Nur din rasa abunda zai ce mata yayi sai yayi kasa da kanshi kawai yana gaisheta cikeda respect kmr yanda ya saba..aunty sumy ta amsa snn tayi excusing kanta ta shiga ciki ward din ta bada kayan aka Mika masu..waiting room aka bude mata ta shiga yayinda shi kuma yaketa sintiri yana kai kawo a wurin yanda kasan matarshi ce nan ciki zata haihu. After a long suffering Allah ya taimaketa da kuma taimakon perfect hubby dinta ta haifi santalelen yaronta namiji..yana zuwa dunia dama daya tsala wani irin kuka hatta Nur dake waje saida ya jiyo sautin kukan..sosai Bobby ke farin ciki da kanshi yayi mata komai ya gyarata matron kuma ta gyara baby snn sukayi moving nata to postnatal matron na rikeda jaririn dake lullube da shawl..har lokacin Bobby bai amsa yaron ba duk kuwa da yanda yakejin kmr ya ajiye duk wani abu da yakeyi yaje ya karbeshi amma baiyi hakan ba saida suka kaita postnatal snn matron ta mika mashi babyn ya karba da Bismillah yana kallon cute face din babyn da at once yaji wani iri so da kaunarshi na sake mamaye ko wane lungu da saqo na heart dinshi..lumshe Ido yayi tareda matsar da bakinshi ya Karanta addu'a sosai ya shafama babyn sai kuma yayi kissing forehead dinshi tareda mannashi da chest dinshi a fili ya shiga furta"Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah..Allah ya rayaka cikin tafarkin islam"..ya jima sosai rungume da yaron kafin ya kwantar dashi a cradle tareda karasawa kusada ita ya zauna ya kama hannunta ya rike bayan yayi pecking forehead dinta cikin tsananin happiness yace"Rabbi ya saka maki da aljannah..i love u so much"..itadai bata ma San yanayi as tunda ta samu ta haihu wani baccin wahala yayi gaba da ita..sai a lokacin ya tunada su aunty sumy dake waje nan yace matron ta turosu ciki shi kuma yayi saurin daukan wayanshi ya dannawa Mummy kira...tana dagawa cikin excitement yace"Mummy guess what?.."Mummy tace"just go straight to the point which one is guess what?.."murmushi ya karasa saki yana sake godema ubangiji cikin zuciarshi yace"Mummy Aysher ta haihu..u need to see my son Mummy he is so so very cute..he is more than handsome Mummy ina sonshi sosai wlh"..shiru Mummy tayi kmr bata fahimci me yace ba har saida ya sake kiran sunanta snn tace"u mean Aysha ta haihu?.."yace"yes Mummy tun asuba muke asibti and bata dade da haihuwa ba"..wani Hamdala yaji Mummy ta saki kawai sai yaji tayi disconnecting call din ya maida wayarshi aljihu dan yasan yanxun nan za'a ganta ta iso asibtin..aunty sumy na shigowa ta rungumeshi cikij farin ciki take cewa"Oh Allah mungode Maka..Alhamdulillah"..shima rungumeta back yayi har yanxu ya kasa dena murmushi yace"am now a father aunty Sumayya..i can't believe this"..rabashi da jikinta tayi cikin tsananin murna ta karasa inda babyn ke kwance ta daukoshi tana kallonshi with so much love tace"Allah ya Maka albarka"..daga haka ta ajiyeshi tareda komawa inda Aysha ke bacci itama ta rike hannunta tana kallonta with smile tace"sannu da kokari Aysha..Allah maki albarka kema ya baki lafiar breastfeeding"..Bobby dake tsaye yana kallonsu yace"Ameen Ameen"..daidai lokacin Nur ya shigo Bobby na ganinshi yayi saurin isa inda yake yayi hugging dinshi so tight yana ce mishi"u have become a father man.. congratulations to u"..rungumeshi back Nur yayi cikin so much excitement yace"Congratulations to u too bro..am so happy for u..Allah ya raya mana boy"..da sauri Bobby yace"Ameen..Ameen Ameen"..har yanxun sai suna rungume da juna sun kasa rabuwa musamman Nur da yakejin kaman ya taka rawa dan farin ciki amma ba halin yin haka sbd aunty sumy dake cikin dakin..duk sai yaji kaman baby expressing farin cikinshi yanda ya kamata ba..a hankali ya zame jikinshi shima ya nufi cradle din yaron..ya dagoshi yana washe baki kmr gonar auduga yace"Allahumma barikh ya Habibi..barakhallahu lakha"..ya karasa tareda yima yaron addu'a ya shafa mashi shima snn yayi saurin ajiyeshi ya fita daga dakin yana cewa"i will be back soon"..daga haka ya fita waje shi Kuma Bobby ya karasa inda babyn yake yanata kallonshi yanajin kmr zai maidashi ciki sbd son da yake mashi..ko 30 mins baiyi da zuwa dunia ba amma jin sonshi yake ta ko ina a cikin zuciyarshi wnn baisan ya zaiji ba idan yaron yafi haka girma Kuma. Finally dai yau an haifi dan soyayya😂 welcome to parenthood Uncle Bobby and Aunty Lamido❤️🥰 Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 70 Nur ne ya dawo dakin dauke da zamzam da dabino kai tsaye inda babyn ke kwance ya nufa ya daukoshi snn ya mikama Bobby ruwan zamzam din yace"come and give it to him"..ba musu Bobby daya kasa dena smiling ya matso yana bude zamzam din shi kuma Nur yana rikeda babyn haka sukayi bashi zamzam din yasha tareda dabinon da Bobby ya danyi chewing snn ya matsa mashi ruwan a bakinshi..aunty sumy dai na zaune tana kallonsu tana smiling..wnn friendship nasu ba karamin burgeta yakeyi ba tuntuni..they treat each other like brothers..Saida ta bari sun gama bashi snn tana dan murmushi tace"so doctors basa ma kids dinsu exclusive breastfeeding knn?.."kallonta sukayi gaba dayansu ba dai Wanda yace mata wani abun ita kuma ta sake cewa"naga dai kune kullum kuke counselling mutane kan su dinga ma yaransu ebf amma ku gaku nan Medical doctors daku kunzo Kuna bama yaronku ruwa ko one hour baiyi a dunia ba"..Nur dai kanshi na kasa ya kasa cewa uffan sai Bobby ne yace"aunty wnn ai ba normal water bane..zamzam ne fa"..daria kawai tayi bata sake cewa komai ba. Mummy na shigowa dakin direct dama inda ta hango cradle ta nufa Bobby yayi saurin mikewa zakiyi hugging dinta tayi saurin kaucewa tana cewa"abeg let me pass..ana ta sabon jini wa yake ta kai"..daga haka ta karasa inda cradle din yake ta dauko babyn ta shiga kare mashi kallo..Bobby ya wani kwabe fuska yace"Mummy amma nine danki fa bashi ba"..harara ta sakar mashi tace"to daga yanxun shine yarona not u"..sake kwabe fuska yayi yana kallonta sai ta bude mashi hannu tana daria sosai tace"come here my son..the latest dad"..da sauri ya karasa ya shige jikinta Mummy ta hadasu shi da yaron mashi tayi hugging nasu so tight tana yima Allah godia cikin ranta..saida suka gama expressing farin cikinsu snn ya janye jikinshi Mummy kuma ta maida babyn cradle snn ta nufi inda Aysha..kallonta tayi yanda take bacci peacefully ta sauke ajiyar zucia tareda furta"Alhamdulillah Alhamdulillah..Allah shine abun godia". Karfe 12 saura driver ya kawo Husna da Miemie tareda abinci da Mummy tace suzo dashi..zuwa lokacin Aysha ta tashi daga baccin har ma ta dan ware tana responding to mgnr da Aunty sumy ke mata har yanxun ko babyn bata dauka ba wai kunyar mummy takeji..ganin da gaske ba daukan nashi zatayi ba gashi ya fara rigima dole ta tashi suka bar dakin itada aunty sumy da Miemie ya rage daga ita sai Husna..cikeda farin ciki Husna ta karasa ta dauko mata babyn ta kawo mata shi tana cewa"take a look at him Addah..he is more than cute..har na kira Ammi na fada mata"..kallon nashi Lamido tayi tanajin wani irin sanyi na ratsa zuciarta..soyayya mai girma taji tanayima yaron just by looking at him..nan take taji she's so attached to him kaman dai ba yau yazo dunia ba..tana dan murmushi ta dagoshi ta mannashi da chest dinta snn ta sauke wani ajiyar cuzia tana godema Allah cikin zuciarta Husna Kuma na zauna tana kallonsu with adoration..shigowar Bobby yasa ta mikewa ta fita daga dakin bayan ta gaisheshi..a nutse ya karaso cikin dakin ya zauna nan kusada ita tareda yi mata side hug yana lumshe eyes dinshi yace"na gode sosai partner..May Allah reward u abundantly"..dan murmushi ta saki tana Kara rike babyn a jikinta shi kuma ya dagota daga jikinshi tareda durkusawa nan kasa ya kama hannunta yana kallon eyeballs dinta yace"i don't have enough words to thank u baby..i just want u to know that ina sonki and zan cigaba da sonki till my very last breathe..thank u for making a father today..Allah ya raya mana shi yayi mashi albarka"..kai kawai Lamido take gyada mishi tama kasa cewa komai.. shi kuma sosai ya rikice mata yanata faman godia hade da expressing mata how much he loves her..banda blushing ba abunda takeyi sbd dadi..itama tana sonsu fiyeda komai nata. A ranar akayi discharging dinta suka koma gida bayan an tabbatar da itada babyn suna cikin koshin lafia..suna komawa gida ta samu kira daga daddy da Ammi duk sai murna suke sun samu grandson ita har ta kasa tantance wanda yafi wani murna da haihuwar nata..a ranar wata Goggonta tazo daga Gombe sbd ta zauna da ita ta kuma kula da ita da babyn gaba daya..Billy ma dake can tana ta faman shirin biki without her best friend tana samun labarin haihuwar ta kirata vid call tanata ihun murna wai a nuna mata danta ta gani..sosai suka bata lokaci suna video call Billy sai santin babyn take wai kmr tayi tsuntsu tazo Kano. Bayan kwana hudu... Cikin kwanakin nan Lamido taga asalin so da kauna daga wajen family da friends..ba family dinta ba ba kuma familyn Bobby ba..sosai suke samun kula itada baby abun har mamaki yake bata..mutanen Gombe zai zuwa suke ganin baby wasu kuma suna nan bazasu tafi ba sai bayan suna ciki hadda aunty Fiddausi..Besty ma yana samun labarin haihuwar a bakin Husna ya kirata ya mata barka tareda alqawarin zaizo ganin baby..haka zalika yan school dinsu ma da yawa sunzo abun dai ba'a cewa komai..Bobby kuwa bai cika zama ba yanxun as yanata shirye shiryen raka Waziri India ganin doctor dan Waziri da kanshi yace lallai saidai suje tare dashi..shima da kanshi yazo ganin baby har Kano tareda uncles din Bobby da kuma some of their family members..family din Mummy ma sunzo sosai kasancewar ita din mace ce mai zumunchi so kusan kowa yana kokarin yazo duk wani sha'ani daya shafeta...ahalin Lamido ma sunzo sosai tun daga kan uncles dinta da aunties dinta dama sauran family da friends..wasu sun wuce a ranar wasu kuma sunan nan sai anyi suna. Yau ma kmr kullum tun safe suke fama da baki yan barka gashi babyn sai kuka yake an rasa abunda ke damunshi..har kuka itama saida tayi wai batasan me yakeso tayi mashi ba kuma..da kyar ta samu yayi bacci da taimakon Goggonta dake tareda ita..tana zaune gefen gado tana kallon yanda yake bacci peacefully sai taga ya koma mata kmr babanshi..he looks exactly like Bobby dan ko abu guda nata bai dakko ba..haskenshi eyes dinshi nose dinshi bakinshi and even fingers dinshi irin na Bobby ne sak..komai da komai irin nashi ga kuma dan banzan rigima da yake dashi shima ta tabbata na baban nashi ya dauko..hannu takai tana shafa soft hair dinshi tana cigaba da kallonshi tana murmushi Goggonta ta shigo dakin da ruwan zafi a flask tace"au yanxu Aisha har yanxu kina nan zaune kina kallon danki sbd rashin kunya so kike ruwan wankan ya gama wucewa ne kome?.."dan daure fuska tayi tana duban Goggon nata tace"yanxu dan Allah Goggo baza'a hakura da wankan yamman nan ba..shima fa da kanshi yace a denamun wanka sau biyu nidai dan Allah kiyi hakuri tunda anyi da safe sai a bari gobe Kuma"..wani tsaki Goggo ta saki tareda shiga bathroom ta juye ruwan flask din cikin wanda ta sirka tun daxun snn ta dawo dakin ta kama hannunta suka shiga bathroom din tare..duk yanda batason wankan dai saida Goggonta tayi mata wai shine zaiyi saurin dafa mata jikinta tunda yanxun ya dawo danye sbd haihuwan da tayi..suna gamawa ta dawo dakin tanata wani bace bacen rai itada Goggo bata kulata ba tayi wucewarta as tun daxun ta riga tayima babyn wanka..shiryawa tayi cikin dogon riga bayan ta gama shafa cream da perfume dinta snn ta koma kan gadon ta zauna tana cigaba kallon yaronta..a haka Bobby ya shigo dakin ya sameta..har ya karasa ya zauna kusada ita bataki shigowarshi ba Saida yayi mata side hug snn ta dawo hayyacinta sai kuma itama ta zagaya hands dinta around waist dinshi tana pecking shoulder dinshi tace"so u are back?."yace"yes baby how is my baby and u"..tace"as u can see we are all fine..just missing u"..juyoda ita yayi hugging dinta sosai snn yayi breaking hug din yana rikeda hands dinta yace"believe me i missed u more"..murmushi kawai ta saki tana cigaba da kallonshi..a hankali ya saki hands dinta tareda dauko baby dake bacci abunshi shima yayi pecking goshinshi yana kallon yanda he looks just like him ya dan bata face dinshi"i told him to look like u but he didn't"..daria Aysha ta saki tana kallon babyn itama tace"and i told him to look like u so mgn na yaji ba naka ba".. murmushi shima yakeyi yace"don't worry nasan next ones bazasuyi kama dani ba..inshaAllah next baby girl dake zatayi kama ba dani ba..now do u have any name in mind da kikeson asa mashi?.."girgiza kai tayi tana dora kanta a shoulder dinshi tace"No..duk sunan daka sa mashi is ok by me".. pecking forehead dinta yayi yana cewa"that's why i love my baby so much..u are one in zillion"..daria kawai ta saki jin wai ya ambaci zillion.. hankalinshi ya maida kan babyn yana tuna conversation dinsu da Mummy a while ago..he asked if da akwai name da takeso a saka mashi and her reply was duk sunan daka saka mashi daidai ne Bobby.. already dama yanada sunan da yakeson sa mashi amma sbd ya basu right dinsu yasa ya tambaya and he's glad sun bar mashi zabi..a hankali ya daga babyn yayi mashi huduba cikin ears dinshi snn ya maidashi kan shoulder dinshi yana patting bayanshi murya can kasa yace"he's named Noor.. Nuruddeen"..wara ido Aysha tayi out so much excitement tace"sunan provost right?.."a hankali Bobby ya daga mata kanshi yana cigaba da patting bayan babyn yace"yes..he's more than a friend to me u know..we became brothers"..tayi hugging dinshi tana cigaba da smiling tace"i knew that already..Allah ya raya little Noor Allah kuma yasa ya dauko halin mai sunanshi"..dan tabe baki Bobby yayi yace"ba kowanne ba gaskia..bakisan yanda Nur yakeda sa ido bane and i don't want my baby to be like him"..daria ta saki shima yana dariar ya hadasu yayi hugging da ita da babyn yana sake jin kaunarsu har can cikin zuciarshi. Lokacinda labarin sunan ya iske Nur Saida yayi kaman zai zauce sbd excitement..he can't believe wai sunanshi Bobby yasama boy din..Allah ya sani dama tuntuni yakeda burin ya haifi danshi yasa mashi Bobby amma he never thought Bobby zai iya sama babynshi sunanshi..yaji dadi sosai and duk Wanda ke tareda shi Saida ya fahimci hakan..uban kayan daya siyo ma babyn ko shine babanshi sai haka..gaba daya ya rasa inda zaisa kanshi sbd farin ciki..har su raguna ya kawo manya guda biyu wai a yankama namesake dinshi..Bobby dai saidai ya bishi da kallo kawai dan baima san me ya kamata yace ba...ana gobe suna Bobby suka wuce India shi da Waziri da wani small uncle dinshi. Ranar suna mutanen Gombe da yawa sunzo tun daga familyn Ammi zuwa na daddy da kuma familyn babansu Bobby..sosai gidan nasu ya cika da yan uwa da abokan arziki..da yake ha gida sukayi sunan ba wani hall sukayi booking sukaje sukasha shagalinsu a can..Billy da baifi saura 9 days aurenta ba Saida tazo itama Dan cewa tayi baza'a barta a baya ba..sosai yan class dinsu ma sukazo haka sukayi taro lafia suka tashi lafia mai jego da babyn sunsha gifts sosai kmr dai a kansu aka fara haihuwa a dunia. Bayan suna da two days suka wuce Bauchi ita da Billy da Husna da kuma su Aunty Fiddausi da basu koma ba sbd bikin Billy daya gabato..Lamido a nan Bauchi ta sauka gidansu Billy dan ko Gombe tace bazata je ba sai bayan biki duk kuwa da kasancewar angon Hammanta ne to amma tunda a Bauchi duk zatayi events din tasan ko taje Gomben ma kullum suna hanyan zuwa Bauchi ne so gwara tayi zamanta inda aminiyarta itama ta taimaka mata da shirye shiryen kaman yanda tayi mata. Ranar Thursday suka yi kamu a wani hall dake nan cikin Bauchi Friday akayi daurin aure da yamma kuma akayi dinner ranan Saturday kuma suka dunguma kai amarya gidanta dake Lamido's Palace..sosai Lamido tayita tsokanar Billy ranar har faduwar mata da gaba saida tayi dan yanda take zuzuta mata first night abun har saida ya kusa sanya Billy kuka..bayan ango yazo kafin ta tafi saida ta sake matsawa dab da kunnen Billy tana wani shegen daria tace mata"hope baki manta addu'an da nayi maki ba.. inshaAllah nan da 7 months zaki haifo mana preterm baby cox i just can't wait in ganki da baby wlh.. besides baby Noor ma yace i should tell u that sister yakeso ki haifo mashi ba brother ba..so take note plss..da safe zan dawo inyi maki sit bath don nasan dai bazaki taba moruwa ba"..tana gama fadin haka ta fita tana mata daria Billy dai da ido kawai ta bita as batada abun fada..duk ta gama tsoratar da ita wlh..gabanta banda lugude ba abunda yakeyi. An gama biki da sati daya Bobby ya dawo Nigeria and ko gida bai fara zuwa ba suka taho nan Gombe tareda Waziri sbd yasan suna nan and duk dunia yanxu ba abunda yayi missing sama da boy dinshi da matarshi..tunda ta samu labarin zaizo dama ta sanar ma Ammi tasa aka shiga kitchen akaita faman girke girke da za'a tarbeshi dashi..itama taje tayi wanka ta shirya kanta cikin wani purple lace riga da skirt daya fito ainihin shape dinta ta kafa daurin dankwalin nan as always snn tabi duk jikinta da perfume da tasan yanaso..shima little Noor Ammi da kanta ta shiryashi sosai yayi kyau abunshi dama gashi da saurin girma dan yanda yayi 6ulele mutane da yawa thinks he's 3 months or above..sosai Ammi ke kulawa da dan jikan nata dan komai nashi ita keyi abun har mamaki yake ba Aysha..infact duk gidan ma kowa sonshi yakeyi dan daddy shima idan ya daukeshi watarana har bacci yakeyi a wurinshi sai idan yana kuka ne za'a kawoshi tayi feeding dinshi..soyayya da kulawan da take samu a gidan yasa sukayi adding weight daga ita har babyn sukayi wani kyau dasu kusan duk wanda ya kallesu sai yaji kaman ya suresu ya gudu dasu sbd tsabar kyau da sukai. Bayan ya iso Ammi tasa aka bude mashi parlon daddy ya shiga ciki snn su Husna suka cika gabanshi da kayan ci iri iri shi kuma duk ba wnn ne gabanshi yanxun burinshi kawai yayi tozali da matarshi da yaronshi dan yayi missing dinsu like hell..tana shigowa parlon daukeda babyn nata a kafada Bobby ko jira ta karaso baiyi ba kawai ya mike ya isa gareta yayi wrapping dinsu gaba daya da hannayenshi yana sauke wani wawan ajiyar zucia..Noor ne ya fara mutsu mutsu alamar zaiyi kuka Bobby yayi saurin amsarshi daga hannunta yana dan dungure kanshi yace"abeg allow me to hug my wife mana..don't u know that i missed her"..yaron kmr yaji abunda yake fada sai ya shiga babbaka mashi daria and Bobby couldn't take his eyes off the boy..he looks so cute and adorable right now and he can't thank Allah enough for blessing him with such a lovely boy..a hankali yayi kissing forehead din babyn snn ya mannashi da chest dinshi yana saki murmushi sosai yace"i missed u too aboki..i missed u like crazy"..Karan camera da yaji yasashi dagowa yana kallonta sai yaga pictures takeyi musu a haka..suna hada ido dashi tace"you two looks so so cute..i can't love u less"..dayan hannunshi yayi using itama tayi hugging dinta yana kissing head dinta yace"nima i can't love u less baby..i love u two so so much..you are my whole world"..janyewa tayi daga jikinshi tareda kama hannunshi suka koma cikin parlon suka zauna..tayi serving dinshi abinci snn ta amsa Noor daga hannunshi tana cewa"now kaci abinci dan nasan idan ba daukeshi nayi be he won't let u eat sbd mutsu mutsunshi..duk zanci abinci saidai Ammi ta goyashi dan bai iya zama wuri daya ba nan da kake ganinshi"..murmushi sosai Bobby ya saki yace"bazanyi mamaki ba ai tunda namesake din Nur ne".. daga haka ya shiga cin abincinshi ita kuma tana kallonshi bayan ya gama ya sauke daukan danshi yana mishi wasa Lamido nata musu hotuna da videos dan da gaske kyau sukayi mata fiyeda tunanin mai karatu..ranar kusan gaba daya time din akan babynshi ya karar dashi saida yazo tafia ne yayi hugging nata so tight giving her the hottest kiss of her life snn ya tafi cikin so much so da kuma missing dinsu..the next day ma before ya wuce Kano saida ya sake zuwa and this time around tareda Nur da yazo all the way from Kano don yayi picking dinshi..if u see yanda Nur ya zage yana wasa da namesake dinshi abun zai baka daria sosai dan he behaves kaman yana wasa da babban mutum shi kuma yaron yanata mishi daria..Bobby da Aysha dai sai kallonsu sukeyi with so much love..ganin yanda yake cillashi sama yaron yanata daria Bobby ya girgiza kai yana murmushi yace"duk ka 6ata yaron nan da habits dinka wlh..look at how he's laughing kaman ba new born ba..u two are annoying"..harara Nur ya watsa mashi yana cigaba da wasa da little Noor yace"Kuma a haka baza'a iya rayuwa batareda mu ba..we are some kind of light da bazaka ta6a iya rayuwa without us ba shiyasa sunanmu ya kasance Noor..koba haka ba Namesake?.."ya karasa mgn referring to small Nur da har yanxu bai dena daria ba..Aysha da Bobby a tare suka fashe da daria ganin da gaske fa Nur neman zaucewa yake sbd wasa da karamin Noor. Rano✨ Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556. 71 Bayan sunyi 40 Ammi ta gama gyarata tsaf sai kuma ta shiga zaga dangi duk gidan bata samu zuwa ba taje kafin ta koma Kano..suna nan sun Kara kyau da kiba abunsu itada little Nur..Saida suka gama ziyara kaf snn yazo da kanshi ya daukesu bayan sunsha kukansu itada Billy kmr bazasu Kara ganin juna ba dan kusan koda yaushe tana gidanta tunda anan cikin estate din nasu take..su Ammi sunsha godia sosai wajen Bobby ita har kunya ma ya fara bata kaman wanda sukayi ma wani gagarumin abun..bayan komawarsu gida kuma suka shiga bajema juna kolin love kowa yana nuna ma dan uwanshi yanda yayi missing dayan abun dai ba'a cewa komai..zuwa yanxu soyayya mai karfi ya shiga tsakanin Nur da Miemie dan har an fara mgnr aure sbd Nur da gaske he's desperate shima yayi auren nan ya shige daga ciki ko don as ya huta da walakancin da Bobby keyi mashi..bayan anyi mgn da familyn baban Miemie aka tsayar da biki next five months aikuwa farin ciki da rawar kai a wurin Nur abun sai wanda ya gani kawai. Biki ya rage saura 2 months Bobby da Aysha suka tafi aikin Hajj hade da honeymoon dinsu wanda Mummy tace itakam bazata je ba sbd shirye shiryen bikin Miemie..wnn dalilin yasa suka tafi su biyu tareda little Nur da yayi girma ya Kara wayo sosai kuma kamanninshi da babanshi na sake fitowa...Malaysia suka fara zuwa for their honeymoon aikam anyi kara'in honeymoon sosa dan ba wanda zai gansu yace ba latest couple bane saidai idan little Noor aka gani..sosai suke enjoying honeymoon dinsu Aysha mai cewa zata koma karatu duk ta mance da wnn tana enjoying life dinta to the fullest..satinsu hudu suka wuce Saudi inda daga nan kuma zasu dawo gida dan immediately bayan sallah za'a fara bikin Miemie..sun gabatar ibadar su yanda ya kamata sun kumayi addu'a sosai na neman zaman lafia mai dorewa da zuri'a masu albarka da kuma fatan gamawa da dunia lafia..nan ma 4 weeks sukayi kafin su dawo daidai lokacin kuma an fara shagalin bikin Miemie so basu samu zama ba dan suna dawowa suka shiga harkan biki kuma. Kusan sati guda akayi ana shagulgulan biki dan events sukayi sosai kmr dai bazasu kare ba inji Bobby yace shi har ya gaji da attending events din ma..yan uwan Aysha da yawa sunzo bikin daga Gombe ciki harda Ammi da bata zuwa gidanta ba sai Yusra da Husna da kuma Aunty Fiddausi da Billy dake dauke da katon cikinta itama da alama dai bakin Aysha ne ya kamata don da kyar idan ba haihuwar 9 months din zatayi ba..a lokacin ne Aysha ta samu labarin wai ashe soyayya ne tsakanin Husna da Bestynta abun kuma ba karamin dadi yayi mata ba dan tafi kowa sanin waye Sa'eed haka zalika tasan Husna ba karamin dacewa tayi da damunshi a matsayin miji ba..ranar da aka kai amarya gidanta su Aysha sune gaba gaba itada Billy da sauran familyn Mummy sai kuma yan uwan babanta..su Hajia Husna kuma sune qawayen amarya..sosai su Aysha sukayi mata nasiha sosai kafin su bar gidan ita kuma banda kuka ba abunda take wai tama fasa auren su maida wajen Mummy haka dai suka samu suka lalla6ata suka bar gidan. Bobby da kanshi ya rako Nur har compound din gidanshi amma kememe yace shi bazai shiga ciki ba tunda amaryar tashi matsayin 'ya take a wurinshi that shi bazai iya wnn rashin kunyan ba..haka Nur yanaji yana gani Bobby yaki rakashi ga kuma wani iskanci da yake ta mashi tunda aka fara bikin wai yabi mashi yarinyarshi a hankali if not da kanshi zaizo ya dauketa if yaga yana neman hallakata..Nur bai samu bakin cewa komai as haushinshi yakeji for not rakashi cikin gidan amma ba yanda zaiyi dashi haka yana gani ya tada motarshi ya bar gidan ya gama masa iskanci iri iri daga karshe dai shi kadai ya shiga wajen amaryarshi as dama idan aka cire Bobbyn ba wasu abokai yake dashi ba. Allah sarki Miemie Saida ta bani tausayi dan da gaske Nur bai saurara mata sbd tsabar azaba gari na wayewa ta dokowa Aysha kira wai dan Allah dan annabi tace ma uncle Bobby azo a dauketa daga gidan that bazata iya zama ba wai kasheta zakiyi..hakuri sosai Aysha ta bata tareda tura mata Billy gidan taje tayi mata duk abunda ya kamata don hanashi zuwa inda yake tayi balle ya taimaka mata..Bobby Kam yana samun labarin ya dinga 6a66aka daria kmr mahaukaci sabon kamu dan takanas yaje har inda Nur din yake yayita mashi daria yana tsokanarshi wai tsabar shi novice ne shine yaje yayima yarinya fata fata har take cewa bazata iya zama dashi ba..Nur dai baice dashi komai as yasan duk wnn abun ramuwa ne yakeyi tunda shima ba kalan tsokanar da bai masa ba lokacin nashi bikin. Haka rayuwa yacigaba da tafia musu cikin zaman lafia da kwanciyar hankali..ga kuma uwa uba tsantsar soyayya da kulawa da juna..lokacinda ta mashi zancen komawa asibti yace ta bari idan Nur ya bude asibtinshi sai ta fara aiki a can that idan asibti daya suke bazasu maida hankali suyi aiki ba..hakan kuwa akayi don ana fara aiki asibitin na Nur mai suna Annur specialist hospital ta fara aiki a can as a staff midwife..little Noor da yayi wayo ya zama Kato dashi take barinshi wajen Mummy da ko kusa yanxu bata kaunar rabuwa dashi dan ganinshi takeyi kmr Bobbynta...yanada wata 10 a dunia Aysha ta sake samun wani cikin aikuwa zo Kuga tashin hankali a wajenta kmr wanda tayi cikin shege..wai a matsayina na midwife bai kamata ace tayi haihuwa irin wnn ba ya kamata ace saita yaye Little Noor kafin ta samu wani cikin..Bobby dai baida bakin cewa komai sai na bata hakuri gashi laulayi takeyi sosai kusan fiye ma da wanda tayi a cikin small Noor hakan yasa har aikin ma ajiyeshi tayi tacigaba da rainon cikin a gida..shi kuma small Noor kusan koda yaushe yana wajen Mummy gashi ya hanata yayeshi wai sai yakai 17 months...haka dai ta hakura take fama da ciki da kuma shayar dashi don dai ba yanda zatayi ne amma da tuni ta yayeshi ta huta. Cikinta nada 5 months Billy ta haifi yarta mace aikam sunje Gombe sunsha suna yarinya taci sunan Maman Hamma Aysha suke kiranta da Maama..Saida sukayi sati biyu itada small Noor daya kara girma da wayo kuma yana yawonshi ko ina snn suka dawo Kano..nan kuma tacigaba da zaman jiran nata haihuwan itama. Kamar yanda yace yana shiga 17 months ta yayeshi ya koma wajen Mummy gaba daya..cikinta na shiga wata tara ta haifi twins dinta mata masu kama da ita sak kmr an tsaga Kara an karya gasu kuma kamarsu daya da juna dan ko Bobby Saida yayi da gaske snn ya iya ganesu...farin ciki a wajen wnn ahalin ba'a mgn dan duk wani Maison Aysha da Bobby Saida yayi musu farin cikin samun wnn karuwar..Yara masu mugun kyau da shiga rai kuma identical twins..ranar suna Yara sukaci sunan Mummy da Ammi wato Maimunatu da Nadia anci ansha anyi shagali sosai wajen sunan kmr sunan fari. Bayan wata daya Miemie itama ta haifi baby boy dinta mai sunan Bobby..fadan farin cikin da sukayi is a watse of time amma sunyi murna sosai musamman daya kasance anyima Bobby takwara dan hatta nickname din iri daya ne..Attahir ne sunanshi na gaskia amma za'a dinga kiranshi da Bobby...rana suna shima Bobby ya taka rawa gani sosai fiyeda tunanin mai tunani..haka Mummy da aunty sumy sunyi farin ciki sosai da wnn takwara na Bobby kuma takwara daddy tunda sunan daddy shima yaci. Twins din Aysha nada one and half year akayi bikin Husna da Sa'eed..su amara Lamido sati biyu taje tayi a Gombe dan har aka gama biki aka Mika Husna gidanta dake Kaduna bata dawo ba saida ta sake komawa Gombe..kowa ya kalleta ita da yaranta sai sun burgeshi dan yanda suke kyawawa dasu kuma masu wayo da shiga ran mutane..kwana hudu suka karayi suka dawo gida Kanon Dabo inda Kuma suka dora daga inda suka tsaya..tuni dama tacigaba da zuwa aikinta so no more zaman banza a gida..daga little Noor har twins din wajen Mummy take barinsu da nanny dinsu taje aikinta ta dawo. Yau ma kmr kullum tana zaune dakin yaran nata da sukayi bacci ta sanyasu a tsakiya sai addu'a take musu tana bin dukkaninsu tana shafa musu a jikinsu..Bobby dake tsaye bakin kofa yana kallonta a hankali ya karaso ciki yana kallonta da murmushi hannayenshi rungume a chest dinshi yace"this is not fair baby"..kallonshi tayi itama tana murmushin tace"me Kuma nayi again partner?.."yace"kaga daya hankalinki yanxu ya koma kan twins dinki mana..tunda kika samesu ni da aboki kika dena kulawa damu Kuma"..murmushin dai take cigaba dayi snn ta mike daga inda take ta tsaya nan kusa dashi tareda mishi side hug ta dora kan akan shoulder dinshi tana kallon yaran nata dake baccinsu peacefully tace"ni ban wani dena kulawa daku ba partner..kishi kawai kukeyi dasu"..hannu yakai shima ya zagaye waist dinta dashi yana kallon kids din nashi yace"no kinfi damuwa dasu a kaina"..daria ta saki before tace"oh yanxu ka dawo kai kadai banda little Noor knn?.."yace"yes mana duk kinfi basu time dinki akaina..kuma dai kinsan ni nafisu bukatarki a kusa dani"..har yanxu bata dena murmushi ta danyi dagen kafa ta manna mashi kiss a right cheek dinshi snn tace"yi hakuri ai from now zuwa safiya duk time dinka ne and babu yaron da zai cinye Maka shi believe me"..murmushi ya saki yana kallon kids din kafin ya dawo da kallon nashi gareta yana cewa"bazan taba gajiya da godia wa Allah daya mallaki mun such a lovely family kaman ku ba..u guys are my everything and i love u so much"..sake rungumeshi tayi itama tana kallonshi eyeballs dinshi tace"we also love u so much papa..u mean the entire world to us..we are so proud of u"..rungume juna sukayi suna kallon yaransu cikeda so da kauna.. little Noor na kan gadonshi yana bacci likewise twins suma suna kan nasu bed din suna bacci rungume da juna..matsawa yai yayi kissing yaran duk snn ya rufesu da duvet snn ya jata suka fita dakin bayan sun kashe masu haske yana rungume da ita yake cewa"ina sonki kwatankwacin son da Umar Faruk ke yiwa Amal(INA ZAN GANTA)..snn ina kishinki kaman yanda Dr.Taheer ke kishin Layla(Dr.TAHEER)"..murmushi sosai takeyi ta kasa dena blushing sbd words din nan nashi means the entire world to her..Saida suka shiga bedroom dinshi ta hade goshinshi da nata snn tace"nima inasonka sosai partner..u are my hubby,my love,my soul partner,my darling..my very own husband and the father to my beautiful kids..i love u unconditionally"..lumshe Ido Bobby yayi ya hade bakinshi da nata itama tayi grabbing nashi da sauri nan kuma wasan ya sauya tsakaninsu. Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! Anan na kawo karshen novel dina 🤍Dr.BOBBY🤍..kurakuran da mukayi ciki Allah ya yafe mana. Dubun godia ga each and everyone of u out there that patronize..May Allah reward u abundantly..Allah ya biyama kowa bukatunshi na alkhairi🙏🏻 Thank u! Thank u!and Thank u! Masu buqatan document should contact me through 07063800556. Thank you once again and love u all❤️ Am going to miss you guys😭💔 Rano✨