: DUNIYA TA BISMILLAH INA MATUKAR GODIYA GA ALLAH DA YA BANI RAI DA LAFIYA DA KUMA IKON RUBUTA SABON NOVEL DIN NAN DUNIYATA. MAKARANTA NOVELS DINA DA BIBIYATA INA MUKU GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI,ALLAH YASA WANNAN NOVEL YA FADAKAR YA KUMA NISHADANTAR,KAMAR YANDA MUKA FARA LAFIYA ALLAH YASA MU GAMA LAFIYA AMEEN. KAMAR YANDA KUKA SANI NOVELS DINA NISHADI YAFI YAWA CIKI,INA KUMA GODIYA DA KUKE KARANTAWA HAR MUTUM YA SA KUDI YA SIYA WANNAN YAFI KOMAI DADI,INA GODIYA ALLAH YA BAR KAUNA. 1-5 FREE PAGE LITTAFAN DANA RUBUTA GASKIYA CE MARAICIN RAHMA MAAIKACIYAR GOMNATI CIRANIN AMANA DUK INDA TA FADI KAMARSU CE DAYA KASUWANCI NA JIN DADI SABO HADIN KAI ME MAGANI TUBABBIYA NA KUDI DANA RUBUTA RASHIN SA'A TA GYARU YAR KWANGILA ADDUAR KAWA GIDAN GWAURO/DAN NAZIA DANGIN RABI DUNIYA TA....... GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN DUNIYATA DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD, GTBANK. MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER TA 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page din farko naku ne Fans Dina duk wacce ke cikin groups Dina. Zaune suke a wani katafaren Palo na Alfarma,Palo Wanda yaji furniture Dan gaske,duk Wanda ya Shiga wannan Palo bazai so Fitowa ba,wani uban kamshi da sanyi ne ke tashi,Family Guda su Shida rakacal sai ta bakwan Yar karamar yarinya tana Wasa a kasa,Kidan Bob merly ne ka tashi a wata katuwar plasma tv kamar ka dakko mutum,gaba Daya sunyi Shuru duk Basu cikin nishadi,Ahmad Dake narke cikin luntsumemeyar kujera shine yake kada Kai cikin maye da kwaya da gani kasan Kansa ba kalau ba,sai bin wakar yakeyi da bakinsa,gashi babu Wanda ya Isa yace ya kashe ko ya daina,baya Jin Maganar kowa,Mummy dattijuya itace ta nisa fuskarta dauke da damuwa Tace Haba Ahmad Kaine fa babban Danmu Amma ka duba yanda ka maida kanka Completely Useless har mun gaji da Dake Hanya tun daga Lagos muna zuwa Nan Kaduna wajenka akan magana Daya kaki ji,tunda hakane yau da Yamma zamu koma,Wani farinciki ne ya bayyana a kyakyawar Fuskarsa,ya Mike tsaye yace wow Mama the Mama,Allah yau zaku tafi?yawwa Haka nake so sabo da na samu freedom,yau kwananku biyu Kun dameni dama,Shut up Daddy ya Furta banzan yaro marar tarbiyya,ai Kai dama Daddy nasan baka so na,Zama ya sake Yi Yana bin wakar Bob merly,sai Chanel din Suka cire wakar aka Sako tallan Wani body lotion. Wata Uwar Tsawa Ahmad ya saki tare da nuna Tv da yatsa cikin mayensa na giya da kwaya ya kalli dalleliyar Budurwar da aka Nuno tana tallan Body lotion a tv yace Kai...dalla ku matsa can Kar ku kawo Mana Harkar Daudu anan,mu ba Daudu Muka zo gani ba Ana Harkar arziki zaku zo Mana da Mata Yan Daudu,ke dalla ja can, Dan uwarki a Nan Nigeria muna da man shafawar mu Habiba yawwa,Muna da Habiba Muna shafawa Muna Kara Baki wuluk abin mu yafi Mana,Dariya ya Bawa duka Yan palon har Daddy ya kalle shi yace Ahmad Kai da kake fari Kal jinin Larabawa Kuma a gidan uban wa kake shafa wannan Man,sannan ce maka aka Yi Habiba karamin company ne? Mummy Tace Allah ya shirya min kai,Baki ya turo tare da gyara Ass down dinsa da yayi da wani Creazy jean. Wata Yar kyakyawar jar mota ce Honda tayi parking a bakin wani Restaurant,Yar kyakyawar Budurwar ta fito Hannunta dauke da Handkerchief tana goge zufa, Hannayenta ta Shiga tafawa tana Waka Sannu da Zuwa.....Sannu....da zuwa kekashashe na,Oyoyo Dan Kedararre na.....Oyoyo Karmashashe na,Barka da dawowa Dan tsomalalle na,My Karmash I miss you,Wani saurayi ne matashi mugun siriri wuyansa kamar murkin laima,Kugunsa Kamar zai tsinke,Baki ne wuluk Kamar Iska zata dauke shi Haka ya fito daga jar motarsa Yana wani basarwa a dole babban yaro,Bakinsa ya Bude da Niyyar magana Yan hakoransa manya na gaba Guda hudu Suka yo waje,Yana kallon Budurwar yace naga Alama Baki da tarbiyya,Kamar Ni saurayinki Ina sonki kina so na Amma kina ci min Fuska,glass dinsa ya zare a Fuskarsa ya kalle ta sama da kasa yace Yar talakawa Dake matsiyaciya ki kalle Ni kina wani ce min Oyoyo Karmashashenki? Baki da Manner? An fada Miki badan so ba Zan iya tsayawa da Yar matsiyata irinki? Ki kalle Ni nafi karfinki ta ko Ina,Yar budurwar kyakyawar gaske fara Tace Kayi Hakuri Wasa nake maka wallahi badan naci fuskarka na fada ba,Tsawa ya daka Mata yace dalla ja can dama iyayenki Basu Miki tarbiyya ba,Baki da hankali dai,Ran Budurwar ya baci tace kaga Malam na maka tauna na maka hadiya baka gani ba,to naji bani da tarbiyyar sai kace Iyayenka suzo su Yi min,daga na maka Wasa Kai baka San wasan masoya ba,wannan ne wasan a gidan uban wa ya Zama Wasa? Nan take Budurwar ta bashi amsa a gidan Ubanka Kamalu,Baki Bude ya kalle ta yace Aamna a gidan wa kika ce? Wacce aka Kira da Aamna ta sake cewa a gidan Ubanka nace Kamalu,Kamalu ransa ya dugunzuma yace it's over between me and you,bani ba ke,Aamna Tace ae naji Nima bani ba Kai tsotsatsen banza,me zanci da Kai dama idan anyi auren ma Banda kashinka ya dinga suka na me zanyi,Dana kwanta a jikinka gwara na hau katifar fasasun kwalaba,Kuma da na aureka ka min kiss da bakinka me hakora Kamar kacar Keke gwara na tsotsi Kusa me tsatsa,Yace irin na Ubanki ne ai hakoran,naji ta furta tare da koma cikin Restaurant taci gaba da aikinta. Wajen masu girkin taje ta faki idonsu ta saci yankan nama Uku ta watsa a Jakarta ta fito ta baya can ta cinye Naman sannan ta dawo ciki ta Iske Fried rice an Gama an kaiwa wani yaci ya bar Rabi kadan ma ya ci,Aamna da sauri tazo Wajensa Tace Alhaji ka Gama Zan gyara wajen 2pm yanzu resturant zai cika,kafin yayi magana ta sunkuce abincin ta dauke Masa lemon da ko budewa baiyi ba ta Sha kwana tayi ciki,Alhaji ya saki Baki Yana cewa ke ke ke ban Gama ba Amma Ina Aamna tuni Taki ma kula shi,tana zuwa Tace Alhaji ya koshi ta zauna ta lashe abincin ta Balle lemon ta shanye sannan ta fito fes da ita da mamakinta sai taga Alhajin Bai tafi ba,da sauri ta koma Wajensa Tace Alhaji wani abincin Za'a kawo maka ne? Alhaji ya kalleta yace ke Amma wacce iri ce bance na koshi ba kin dauke abinci lemon ma Dan wulakanci ko Bude shi banyi ba kin dauke Ina ta kiranka bakya ji? Aamna Tace eyya Allah sarki kayi Hakuri matsalar kunne gareni banji ba Kuma gashi na zuba komai cikin shara bare na dawo maka da shi,Harara ya balla Mata tare da zube wani kudin yace kawo min wani abincin,da murna ta dauka dama Bata koshi ba,taje ta hadowa Alhaji duk abinda ya bukata,wata white rice with salat ga kwai da kaza,ga lemo,Aamna tunda taga Haka take ta faman zaga wajen da mopper a Hannunta Wai a dole gyara takeyi,tana ta faman goge goge a saitin Alhaji,Alhaji yace ke kin dameni da goge goge ga customers can sunzo kije Mana Haba wannan wacce irin Maaikaciya aka dauka Haka idan bakya so sai na daina zuwa cin abinci a wajenku aikin banza,Aamna tayi murmushi tare da gyara pcap dinta Tace afwan Alhaji ta juya ta tafi Amma sai ta labe a bayan wani lungu daga ciki tana ta kallon Alhaji tana so yayi ya Gama ta samu rabonta,Siyama ce kawarta taje ta sallami wasu customers din Aamna tana labe tana zalama wajen Alhaji,Siyama tayi Dariya tare da kallon Aamna tana labe labe Tace Allah ya shirye ki,Alhaji kadan yaci ya bar komai ya tafi kafin ya Gama fita tuni Aamna ta kwashe komai tayi ciki,Nan ma ta zauna ta cinye ta koshi sannan Tace saura na dare kafin na tafi gida,dole na dinga kiba Ina yin kyau,Aiki a restaurant ai Dadi gare shi ko ba komai Zan cika tumbi na. Dattijo ne fari me gemu sosai Wanda shi kanshi gemun ka kalla kasan Dattijon ya tsufa domin yayi fari,da gudu gudu sauri sauri ya shigo gidansa inda yake wani mugun Rubabben gida,Gida ne na Haya Kuma gidan Talauci,da gani ba sai an fada maka ba Dattijon Talauci ya Gama da shi,cikin Gida ya Fado Yana masifa tare da furta me zangani Aishatu?me zangani yau,wacce ya Kira da Aishatu ta kalle shi shekeke tare da balla Masa Harara Tace mene? Gashi can kina karar min da kudi,kina min asarar Duniya da Almubanzanranta,yanzu ki duba sabo da Allah tunda na taho Ina kallon kwalabati kumfar Omo tana ta bin ruwa tana ficewa Ful...ful,Yanzu a zamanin Nan kumfa ka gani a kwata kasan kudinka ake kashewa,kina ta kashe min kudi kina abinda kika ga dama,Ga jarabar karar da Ashana kiyi ta kyastata sai ta Kare,Takaici na yanda kike wanki ko wanke wanke sai asarar Omon bala'i,to wallahi da sake baza ta yuwu ba,kullum Ina fama a hanyar sakateriya wajen Dan aiki na Wanda masinja ne ni nayi retired Ina nemowa Ana wulakantawa bazai yuwu ba,Daga yau ko mangyada ne za a zuba a abinci to kowa cokali Daya Daya babu kari aikin banza,Wata buta yasa kafa tare da yin fatali da ita Yana zare Ido yace Ina Aamna sakarai da Sweety Zuhra?Aishatu banza tayi Masa ta ci gaba da aikinta,yace Aamna har yau ba labarin Mijin Aure? Aishatu tayi Shuru,Dattijon yace na gaji da yahudanci wallahi da nasan Haka ne Aamna ko secondary baza tayi ba,Dan fa Kawai Ina tunawa Amana ce a wajen mu, Nima ban San ya akayi basirata ta toshe na biya Mata har tayi wani HND sabo da asara,ai karatun mace Bai da amfani,amfanin mace aure da girki tayi ta zazzago Haihuwa,yarinya ta Zama bayahudiya abinda taga Dama shi takeyi,Nima jarabata ce tasa Rana tsaka Ina Kauye tare daku cikin sutura na dawo damu Birni na Kama haya,da Muna Kauye da tuni hankalinmu kwance,da duk wannan karyar Bamu shige ta ba,Aishatu Tace ai sai Dana fada maka kaki ji Aamna tana secondary a Kauye Ss3 ka kwaso mu Muka dawo birni gashi yanzu ta waye Taki aure muna ta ciyar da ita a banza ,wallahi baza ta Sabu ba,gidana ya koma na yahudu bazai yuwu ba,ai Birni na dawo ne Kawai Dan na samu sana'a me kyau to gashi hakan Bata samu ba,Dan pension Nawa ma baya Isa Nawa yake Ina abin,kullum sai talauci ne ke karuwa,birni kwai masifa Ni tunda nazo banga wayewar ba,ban wani waye ba,Aishatu Tace yo shekarar mu Nawa a Birnin kwata kwata shekara hudu fa rak Ina wani wayewa Aamna da Zuhra ne Kawai Suka Dan waye Dake su Yara ne,Dattijon yace ke tafi can Aamna Ina ta waye ai gwara Zuhra,Amma Aamna kina gani magana ma Bata iya ba ta Kauye takeyi duk abinda yazo bakinta dankarawa mutum takeyi Dan tayi makaranta ne ma take Dan canjawa,ni dai na fada Miki a kiyaye asarar Omo yawwa ya furta tare da ficewa falau falau da rigarsa doguwa ta wani tsohon yadi dinkin wani falkeke komai ta Masa yawa Kuka Aamna ta saki Wiwi tana Hawaye tare da nuna Budurwar da Hannu tana masifa tare da Furta In Allah yayarda Shedan sai ya sumbace ki,Shedan sai yayi kissing dinki,muguwa,Azzaluma, maciya Amana,Baza kiga dai dai a rayuwarki ba Saratu,Saratu anyi asarar Duniya,An Sarai asarar duniya,Shegiya wacce Shedan yayi Mata fitsari a Kai, Wacce ake Kira da Saratu murmushi ta saki tare da karkada key din motarta Tace nafi karfinki Kina talaka kucaka me Deeni zaiyi dake duk kudinsu,ke wawiya ce Baki da hankali da har kina me siyar da Abinci a Restaurant kike tunanin Dangidan Dan Majalisar jaha Deeni zai so ki,ai ko kansila Aamna bazai tayaki ba,ganinki kyakyawa Fara Wai zai sa samari su soki? Kinyi kuskure Aamna,ai yanzu samari sai masu kudi suke Nema gidan da Suka gaji arziki,ai yanzu sai kana da kudi ake rayuwa da kai,ke Dan Dakikiya ce tunaninki kyau Yana sawa a so mutum? Dan kina da kyau har Shishigi kike Yi to ki sani samari sai dai su yaudare ki Amma yanzu duk munin masu kudi Haka ake aure su,Talaka ma Bai son Auren talaka bare irin su Deeni masu kudi,Ina Baki shawara ki fita Harkar Deeni ba ajinki bane. Aamna tana tsaye sanye da Jean skert Blue da rigarta T-shirt fara tas me Rubutu Red a Gaban Rigar An saka A&G Food Joint,ta Sanya pcap Red takalminta ma Red,ba karya Aamna karshe ce a kyau,haskenta me kyau ba fari Kal Kal ba Amma fara Ce dai ba Wanda ya Isa yace wankan tarwada ce,dole dai farar ce,Gashinta har gadon baya Baki wuluk,Ga Zararan gashin Ido tare da kwantaccen Gashinta dake goshinta,Girarta wuluk me yawa,Hancinta me kyau bai cika tsayi ba,Fuskarta ba doguwa ba baza Kuma ace Round face ba,Dan Bakinta gwanin Sha'awa Karami with pink lips,Gata doguwa Amma ba can ba,ga Uban Hips kamar ita tayi kanta komai nata me kyau,hakoranta kanana farare tas,Idonta dara dara, Mashaallah,Aamna baza ta wuce 24years ba,Haka kanwarta ma Zuhra kyakyawa ce Amma ita chocolate ce kamarsu Daya da Baba. Murmushin takaici Aamna tayi Tace ai gaki Nan da Muni yayi Miki yawa Deeni zai kwasa ki cinye Deeni please ta juya tare da komawa Kan bakin aikinta wurin masu siyen abinci,ita kuwa Saratu Tsaki ta ja tare da Bude dalelleliyar motarta baka ta Shiga sannan ta fisgeta a Tamanin. Sai 11pm ta tashi a Aiki ta saka After dress dinta me Dan kyau tare da rataya handbag dinta tayiwa abokan aikinta Sallama ta wuce gida,Napep ta Shiga zuwa gida,can cikin wata Unguwa ta masu rangwamen gata aka sauke ta a Kofar gidansu na Bulon siminti Amma ka rantse kango ne baiyi Kalar gida bane,da Sallama ta Shiga da kyar aka samu aka amsa mata,Mama Wato Aishatu ta Iske tana Daura Net a dakin babansu Tace Mama na dawo,Tsaki dattijuwar ta ja Tace to sai me,idan da sabo ta Riga da ta Saba,Baba ta kalla Yana daki Tace Sannu Baba,da kyar ya amsa,Kai Kawai ta girgiza ta wuce kitchen Nan ta Iske abincinta an zuba Mata Amma an barshi a Bude baza a iya rufe Mata ba,ta Saba Kawai ta dauka tare da Fitowa sai ga Daya matar gidan tunda dama gidan Haya ne,mutum Uku ne a ciki ko wacce mata da dakinta biyu da kitchen Amma toilet Guda Daya ce du,Gaisawa Suka Yi Tace Maman Zeenat ya gida,Tace lfy Alhmdllh da fara'a, dakinsu ta wuce ta Iske kanwarta Zuhra tana kwance a saman katifarsu tana chatting da saurayinta Wanda zata aura Nan da wata daya. Murmushi Aamna tayi Tace Zuhra Ana Shan love, Murmushi Zuhra tayi tana juyi Tace Aunty Aamna an barki a baya wallahi,Soyayya tayi a rayuwa,Adam ne ke kashe Ni da zafafan kalamansa masu sweet,Dariya Aamna tayi Tace na tayaki murna kanwata ke kin samu Miji Ni kuwa kin barni nice Kuma yayarki gashi Mama da Baba sun tsaneni akan ban kawo musu Wanda Zan Aura ba,Hawaye ne ya silalowa Aamna Tace why me naaa?why Me Zuhra? What have I done wrong? Tausayin Yayarta ya Kama Zuhra Tace kiyi hakuri Aunty Inshaallah kema Zaki samu miji very soon,Kuma Inshaallah su Mama zasu hakura su daina fushi da ke. Kai Aamna ta girgiza Tace Zuhra Ni bazan iya auren Wanda bana so ba,da Zan Iya Dana fitar da ko ma waye Dan na farantawa Iyayena Rai Amma idan nayi bazan iya yiwa Wanda bana so Biyayya ba,Illar Hausawa kenan Allah Bai kawo maka Miji ba a takura maka karshe har sai ka auri Wanda baka so,baza ka Dade ba za a sakeka,ko Kuma kullum ku Kare a fada da sasanci,bana fata inyi aure na fito Zuhra,Nafi so ko wa Zan Aura ace Ina sonsa sosai sabo da shine kadai Zan iya Masa Biyayya,kin San halina Ina da taurin Kai,Kuma Ni ba a iya tankwara ni,So shi kadai ne zai sa nayi Biyayya,Kin San idan bana son mutum wallahi zanci ubansa ne,Amma su Mama sun kasa fahimtata,Zuhra Tace ai ke matsalarki kenan Aunty akwai saurin fushi ga rashin barin ko ta kwana,aure Kuma sai Hakuri,Hakuri na Kawai na auri Wanda nake so ko jibga ta zai nayi kullum Zan zauna Kuma bazan ji Haushin kowa ba. Mama ce ta fado dakin Tace Ina Jin duk abinda kuke cewa,ke Zuhra ki daina saurarar marar hankali,ai yanzu ba auren kauna akeyi ba dubawa akeyi aikin mutum ake dubawa me yake samu,zai Iya rike ki, ci da Sha shi ake kallo ayi aure,ke soyayya Zaki aura Zaki ci ubanki kuwa a hannun maza,kika sake sai Namiji ya sa Miki ciwon zuciya,Aamna tace kinji ko Mama bakwa duba Iliminsa da Addininsa Kawai kudi kuke dubawa ayi aure,Baba Yana ji ya tsomo Baki daga dakinsa yace Ni ki tambaya Sanda na auri Uwarku ban taba ganinta ba Haka itama Bata taba ganina ba Kuma gashi Muna tare har mun haife ku,wallahi Aamna kika sake Watarana sai na koreki daga gidana,badan ma kece kike rage min nauyin gida ba da tuni nayi Miki auren Sadaka Kuma wallah Matukar Naga dama auren Sadaka Zan bada ke. To Baba kuyi Addua Allah ya kawo min na gari,Kuma da kuke cewa Baku ga juna ba aka muku aure ai ku a zamanin da ne Kuma asiri akeyi Ana kafe matar ta zauna dole,Salati Baba ya saki yace Ni Zaki hada da shirka Ina Dan Izala? Shuru Aamna tayi,Mama Tace mayaudariyar banza,kin Yaudari Affan kin Kore shi kince kin Kama shi da cin Amanarki Yana kula Mata,Hassan Kuma kince Dan karya ne,Deeni ma yaro me kudi yanzu kince ya yaudareki ya koma wajen Saratu kawarki Yar gidan Alhaji Sani Likita, yanzu ga Kamalu kin ci Masa mutunci ya gudu shima,Jollof din shinkafata wacce ta rigada tayi sanyi ta bushe ita Aamna ke ci su Mama suna ta mata fada har ta Gama,ta cire kayan jikinta gaba Daya ta wanke tare da shanya su a daren,Wanka tayi da ruwan zafi tare da Shirin bacci ta kwanta ta bar Zuhra tana chatting da masoyinta . Dalleliyar mota ce ta gaske wacce a kalla ta miliyoyi ce,ta danno cikin wani katafaren gida na Gagara,Gida ne Wanda ya amsa sunansa,Babu abinda babu a ciki,motoci ne zasu Kai takwas a gidan Wanda suka gaji da haduwa ga tsada,farare Guda hudu a jere bangare daban Haka ga wasu kaloli daban,Machine ne Guda Uku kala daban daban masu tsada harda Keke na masu kudi su biyu,Gidan Ya gaji da tsaruwa ga flowers ko ina,idan ka Shiga gidan baza ka so Fitowa ba,Kalar gate din ma na daban ne,ba ko Ina ake ganin Irinsa ba a kasar Haka furniture sai dai ko gidajen Gomnoni, Wani Matashi ne ya Bude motar baka Daya shigo da ita,Fitowa yayi da kyar Wow wani Fari ne tas kamar Balarabe har wani ja yake kamar ka taba shi jini ya fito,dogo ne Amma ba can ba,gashi shi ba Mai kiba ba baza ace Kuma siriri ba,Fuskarsa me dauke da hancinsa zarkadede ba irin me tsayi da yawa ba,Sumar Kansa baka wuluk dauke da wani mayen Aski irin na Yan duniya,an kwashe gefe da gefe an yanki wani waje siriri an Kona shi tare da maida shi Fari tas,Sajensa me kyau luf luf me dauke da Dan gemunsa cas,idanunsa Dara Dara farare tas suna wani lumshewa,kowa ya kalli wannan matashi yasan ya Gama gajiya da haduwa,Naira da Hutu sun zauna a jikinsa,Jikinsa na maza Wanda suka amsa sunansu maza,sanye yake cikin wani Crazy Jean me tsada gaba Daya wandon a farfashe yake ruwan toka,da wata T-shirt me Rabinta Fari Rabi Kuma Blue,Takalminsa da agogonsa masu tsada,Yatsansa sanye da zoben Azurfa,da kyar yake takawa ga takama ga aji Amma Kuma Yana tangadi da Alama yayi shaye shaye ya gaji,Yana dafa bango Yana tangadi AHMAD kenan a Haka har ya Isa katafaren palonsa tare da fadawa saman kujera ko Takalminsa Bai cire ba ya kwanta Haka Yana sambatun maye shi kadai har bacci ya kwashe shi. Tunda ya fara bacci gab da Magriba Bai tashi ba sai da gari ya waye sannan Rana da hasken gari yasa ya Bude lumsassun idanuwansa a hankali,Kara ya saki kadan Jin jikinsa a gajiye,da kyar ya iya tashi a hankali ya haura samansa Direct toilet ya shige ya Dade Yana wanka dake akwai tsafta,Bayan ya fito daure da Towel jikin mudubinsa ya nufa turaruka ne da mayuka na maza masu tsadar gaske,Lotion me kamshi ya shafa tare da fesa Body Spray a jikinsa sannan ya dakko sabuwar jallabiya me tsadar gaske fara sal Amma ta Dan tsangale Masa baya sa wacce zata Kai Masa har kafa sabo da Damunsa takeyi,Turaruka ya fesa sannan ya dauki wayarsa me tsada Yana latsawa,a hankali cikin tafiyarsa ta Isa da takama ya sakko kasa ya Bude kofa ya fito sanye da wani flat shoe fari sal shima Yana tafiya a hankali ya bi ta wani corido gaskiya gidan Nan ya Gama haduwa tiles din kasan gidan na tsakar gida fari da Baki ne ko Ina sheki yake Yi da walwali,Me Gadinsa ya hango Yana karasa gyara gidan Yana kida da bakinsa Yana rawa Yana aikinsa,Ya Dade a tsaye Yana kallonsa,Abin Dariya ya bashi mutum shi kadai Yana kida Yana Waka Kuma Yana rawa duk shi Daya, murmushi ya saki kadan tare da girgiza Kansa ya juya ya koma inda ya fito. Har yayi nisa sai ya dawo ya Kira me Gadi Musa,da sauri Musa ya dago yace Oga tare da takowa da gudu yazo gabansa yace Ina Peter banga ya gyara ciki ba Sannan ba Abinci,Oga ai Peter ya tafi kasuwa yace abincinka Yana kitchen yace sauri yake yi,Ni gaskiya Oga Ina tunanin yafi a dakko mace yar Aiki wacce zata na maka girki da gyara maka ciki tunda Ni Ina kula da Campun,Ogan yace ba Campun ake cewa ba Musa Compound,Kuma Ni bana bukatar mace yar aiki,Ni bana son mace ta rabe ni,duk abinda zai sa na hadu da mace bana kauna,Musa ya zaro Ido yace Oga Mata sune Jin dadin duniya duk wata nutsuwa da Namiji zai samu tana jikin mace,Baki Ogan ya tabe yace Allah ko? A wajen wawaye ba,gwara naci abincin Gardi akan naci na mace,Karka sake furta kalmar Nan mace a gaba na,idan ba Haka ba Kora ce tukucinka,Musa yace an Gama,Kayi Hakuri Ranka ya Dade Namiji gwara nace Namiji,macen banza Banda Mum dinka Oga,Baki ya tabe ya juya da Gadara ya wuce,Abincin Peter ya Bude yaga Bai Masa ba,da Kansa ya shirya Girkinsa da lafiyayyen tea dinsa ya karya sannan ya dauki key din mota yayi waje,Yau da wata mota Ruwan toka ya fita kirar Benz. Washe gari Aamna wanka tayi tare da Shiryawa tsaf cikin kayanta Riga da wando sunsha wanki da guga,After Dress ta Dora a Kai tare da yafa Mayafi,ba Wanda ya kalle ta a cikin Iyayenta Balle Tace Za'a Bata wani abinci dama yanzu basa kulata,ko ta gaishe su basa amsawa,Sallama ta musu ta tafi,Mama Tace yarinyar banza ace tasan Burin mu Bai wuce mu Aurar da su ba Amma Taki fitar da Miji abin kunya kanwa zata Riga Yaya aure duk ta tsufa a gida Allah wadaran Dan Riko,shekara ashirin da Hudu ai ba Wasa bane,mu duk da a cikin birni muke muna Nan da akidar mu ta Iyaye da kakanni na auren wuri Amma kash Yaran namu musamman Aamna ta Gama watsa Mana kasa a Ido,marikinta Bai da Buri sai na Aurar da su,ai mutuncin ya mace gidan Miji Amma ba komai Aamna wahala da azaba ma Sai ta sa kin fito Mana da Miji,kin daina Jin dadin gidan Nan kwata kwata,yanzu Zan canja Taku wajen gana Miki azaba duk da Kamar mahaifiyarki ce Ni dole wahala tasa ki fitar da Miji,Zuhra kuwa Shiryawa tayi tuni tayi Kari me kyau Ana ta nuna Mata gata da kauna ta tafi makarantar Boko Wato Secondary school sabo da sun kusa yin candy. Ahmad Bai tsaya ko Ina ba sai gidan Mashkoor inda Suka Fi Zama suna shaye shaye a gidan,can ya Iske abokansu su Biyar Mashkoor, Abdul Tawaga,Jibril Jibson,Bashir Bash, Mubarak Brown sai shi Oga Mai gayya me Aiki Ahmad King,Yana zuwa ya Iske su a zaune a Garden suna zaune a kujeru ga karamin Table an zube kayan maye na shaye shaye kwayoyi da giya iri iri ga Sigari taba da Wiwi,Kirari suke Masa Suna The King...Our King,shi Kuma Yana uban Gadara Abdul Tawaga ya Daga Masa kujerarsa ta tsakiya Kuma kujerarsa ta mulki ya zauna tare da Balle kwalabar Giya ya Shiga tiltila Kamar ya samu ruwa,Bash ya kunna Wiwi Yana zuka ga wasu kwayoyi Daya hada a cikin wani ruwan giya Yana korawa Yana tiltilo hayaki ta Hanci ta Baki cikin kwarewa,Tawaga Yana Aswaki Yana cijewa Yana karkace Baki yace Our King....Sweet Boy,The Handsome King,Fresh Boy, shi kuwa King ya kalli Kansa yace Na me....Na me My Guy,Look at my skin color.... Mubaraq Brown yace Handsome King,Mashkoor Yana wani tangadi a zaune yace Our King ka huta baka hura hayaki sai ruwa Kawai kake bulbula sai kwaya,King ya wani girgiza Kai alamar ya fara daukan chaji shima yace,Hayaki sai dai na shaki na Titi My Guy, Mashkoor yace Look King akwai wata yarinya tayi Fuck Up,the Girl done Mess up man, Wai Ni Ina sonta Tace Banda hankali wani yaro Rabiu Yana Nan malamin makarantar Islamiyya ya kwace min ita,King Yana lumshe Ido duk ya fita a hayyacinsa ya karkace bakinsa gefe Daya irin na Yan shaye shaye cikin kakkausar da mayen muryarsa yace She must Collect,Dole ta karbi Certificate na abinda ta aikata,Na yarje muku kuci mamanta,shi Kuma Yaron za a tare shi dole mu bashi Sample,Sumarsa me laushi ya yamutsa,yace guys gobe Mommy da Dad zasu shugo garin Nan Karku zo gida na sai bayan sun tafi,Abdul yace Confirm,No wahala,Jibril Jibson ya Mike Yana tangal tangal yace ya za ayi ace baza mu zo gidan King ba,The sweet Boy,Cikin zafi da daga Murya King Ahmad yace hey What's up man Ina magana kana magana kana hauka ne? I'm sorry cewar Jibson ya Fadi a kasa Yana mayensa,da ganinsu kasan talakawa ne Ahmad shine me kudin shike musu komai,Haka Mashkoor Yana da kudi shima Amma ba Wani da yawa ba,Sai Abinda Ahmad yace shine King dinsu,duk wani rashin mutunci da sukeyi a gari shine yake daure musu gindi sai da sa hannunsa akeyi,Ba Wanda ya Isa ya nuna su da yatsa,Dai Dai ne Basu San da zamansu ba musamman Ahmad King din Wanda ya fita daban sabo da Naira da hutu,suturarsa Kawai abin kallo ce,Dukkansu baza su wuce 30years ba zuwa 34years,Ahmad 34yrs yake cif. Washe gari da Yamma su Mashkoor da abokansa gaba dayansu har King din nasu Ahmad machine sababbi suka hau kowa da nasa Kuma duk King ne ya Siya musu kowa da nasa King shine a gaba suna binsa a baya sun kure Masa gudu sun biyo Hanya duk Wanda Bai matsa ba sai dai su bige shi ba ruwansu,sabo da an sansu Ana ganinsu ake kaucewa,Can layin da Islamiyayyar take suka tsaya Suka Parker machinansu,King shine kadai ya zauna a saman nasa suna ta Masa Kirari suna Our King,Fresh Boy,Sweet Boy,shi Kuma Yana ji da Kansa,Suna Haka sai ga malamin Islamiyya ya taho zai wuce matashi da shi Yana tafiya cikin nutsuwa Baki da shi,Tare shi Mashkoor yayi tare da cewa Yawwa ga dan Iska ya Furta tare da tallafe Masa keya,King ya Mike cikin maye yace kana gaba na kana tsaye,Robar Lemo Wanda ciki hadin kwaya ne a ciki Yana Sha ya daga ya tsiyaya wa malamin Islamiyya a kansa,Nan suka rufe shi da duka Wai yayiwa Sarkinsu magana a tsaye,Wata Mahaukaciyar mota ce me kyau da tsada ta taho a hankali,Mommy da Yar Autarta Humaira sai Daddy Mijinta a baya gaba Kuma Kanin Ahmad ne Saddiq da matarsa Mufida a Gaban mota suna tafiya, Saddeeq shi ke tuka motar,Daddy yace ai Kinga Ahmad din ma gashi Nan da Yan Iskan abokansa,na gaji da zuwa Kaduna akan Yaron Nan wallahi,Na rasa wannan masifa data sameni,Kinga Ni yanda suke dukan wani,Kanwar su Humaira Tace ga Yaya can da kayan maye a hannunsa, Saddiq ya tabe Baki tare da cewa kalli Askinsa Ana ganinsa anga Dan Iska,Mufida matar yayan Tace kuyi Masa Addua Kawai. A wajen Suka Yi parking sai tsawar Daddy dinsa yaji a Kansa Ahmad Mene Haka? Baka da hankali ne,duk suna mota ba Wanda ya fito sai Mummy da Daddy,Daddy ya tashi malamin makaranta Wanda ya ci duka da gudu ya arce Yaron,Su Mashkoor suka kame a Gaban Daddy tare da Sara Masa kamar suna Gaban wani Soja,Zaga Daddy da Mummy suka shiga Yi suna musu Sannu da zuwa Wai Nan murna ce da girmama Iyayen Ogansu,Bash kuzo mu Basu kariya Guys ba Wanda ya Isa ya daga Musu yatsa a Birnin Kaduna kaf. Tsaki Daddy ya ja Yana Jin yanda suke wa Ahmad Kirari,Wandonsa ya kalla wani shegen crazy an Masa daga daga,Askinsa ya kalla yace kalli yanda ka maida kanka Ahmad, Dariya ya Shiga Yi ta mahaukatan Yan maye,Mommy Tace Ahmad Dina meke damunka muje gidan da kake,Daddy yace shiga mota mu tafi,Wani fareti ya shiga Yi a Gaban Daddy Yana dariya cike da maye Yana karkace Baki yace No...no Ni a bike Dina zanzo kasan Ina Jin dadin bike Dina Kawai kuje zanzo daga baya,Tsawa Daddy ya daka Masa shiga muje,Amma ko a jikinsa sai ma Dariya da ya Shiga kyakyatawa irin ta basawa Yana kallon Daddy din da Mommy,Dole Haka Suka shiga mota Suka tafi shi Kuma shi da Abokansa suka take musu baya a machine suna tukin ganganci Dan Ahmad harda dage kafa Daya ya daura ta can sama Yana tuki da kafa Daya,Har katafaren gidansa Suka shiga sannan abokan daga bakin Gate Suka tafi gida abinsu shi Kuma yayi Horn me Gadi ya Bude Musu Gate,Bayan sun Shiga Suka firfito da akwatunansu,Wani handkerchief ya daura a wuyansa ya tsaya a Gaban Mommy Dinsa Yana zagata cike da maye Yana cewa Mummy...Mummy....Momma....You are looking Good ya furta tare da rungumeta yace Ina sonki Mummy,rokonsa ta fara Tace Dan Allah ka nutsu Ahmad,Da karaji Daddy yace Mene ne kike rokonsa, why are you Begging him,Dan ubansa tunda bashi da hankali sai yayi ai,Why...why...Daddy Ni dama fa ba tun yau ba nasan baka kaunata,musamman idan ka saka wannan farin Glass din naka sai ka dinga kwana idan anyi Nan sai kayi can,Ido Daddy ya zaro Yana kallon rashin kunyar Ahmad,Kaninsa Sadeeq ne yace ka canja wallahi Yaya,Cikin karaji ya tasowa Saddeeq Yana ce Masa Kai dalla gafara Ina yayanka zaka min fada,ko Dan kaga munyi Kai Daya Ina da gemu kana da gemu shine zaka rainani Kai wuyanka ya Isa yanka ko,Ka dai gyara halinka,Tafiya yayi zai Mari Saddeeq Mummy ta rike shi tana rokarsa yayi Hakuri, Humaira ya riko tare da Rungume ta yace kanwata kin girma,ya school? Tana Dariya Tace nayi Candy Yaya,Wow ya Furta tare da dagata sama ya ajiyeta suna Dariya,Matar Kaninsa ya kalla Mufida nutsatsiya kyakyawa yace matar mu ya gida fatan wannan shashashan yana kula Dake? Dariya Mufida tayi Tace sosai ma,yace Good muje ciki matar mu ke kadai ce tawa a gidan Nan,kishi ya Kama Saddeeq ganin Ahmad Yana shaye shaye tunaninsa har Mata yake bi sai kishi ya kamashi yace kaje kayi aure wannan matata ce Ni Daya ka daina cewa matarmu yawwa,Stupid Boy Kawai Ahmad ya furta Suka jera da Mufida suna Hira duk da a maye yake Amma Yama Saba Bai fiye buguwa da yawa ba, Sadeeq da Sauri yazo ya shiga tsakiyarsu ya rike Hannun matarsa ya janye ta da karfi,Baki Ahmad ya tabe ya Rungume Humaira Suka Yi ciki. Bayan sun huta sunci abinci Daddy yace da dare Yana neman kowa za ayi Meeting zasu fadawa Ahmad dalilin zuwansu yanzu ma again, Har dare yayi Ana jiran Ahmad Amma tuni ya bar gidan Yana can suna shaye shaye har 1am Bai dawo ba sai kowa ya hakura yayi bacci,Da safe ma Ana ta jiransa har sun karya Shuru Bai dawo ba,can sai gashi a bige ya Fado palon ya tafi taga taga zai Fadi sai ya cije ya Dage Yana bude Ido da kyar Yana Rufewa ya fada saman kujera shirim kusa da Daddy yace An tashi lfy? Ina....Ji...ji..jinku.....m....me.....yaaaaaa....ya...kawo ku Kuma yanzu Kun wani sake dawo min gida...na tuna ance jiya za ayi meeting yanzu gani Ina da abin Yi ku Fadi meke tafe daku har zuwa gidana? Daddy ya zaro Ido yace au gidan ka ne ma? Gidana kace gidanka? Yace gida nane Mana Kai ai Temporary Owner ne Nan gaba mutuwa zakayi naci gado,Ran Daddy ya baci yace gidan Nawa? ni da gidan gida ka gaje min gida?aikin uban me kake Yi? Kaki nutsuwa,Mummy Tace Ahmad Dan Allah ka tsaya ka nutsu kaji abinda ya kawo mu,Ina jinku Mana ku fada,Kaninsa Sadeeq ya tabe Baki,Humaira Tace Addua zaku Masa please,Ita Mufida ita tunda auro ta akayi Bata cikin wacce zata Shiga matsalar Family tana bedroom. Daddy yace kana ji na Ahmad? Yace Yeah,yace so nake ka bar Nan ka dawo Lagos kazo mu koma inda nake da Zama can Lagos Ina so Zan maka Visa mu tafi London gaba Dayan mu,akwai Company na Dake can kayi Handling dinsa kayi Aiki a can ka dogara da kanka,kullum sai dai na cika maka account da kudi kana kashewa a banza,ya kace?Ahmad yayi Dariya yace kasan amsata Mana Daddy Ni bazan je ba wata kasa da zanje Kuma Ni bana son Lagos a Nan gidana Zan zauna a Nan Zan mutu,Daddy yace to gidanka ne? Ni da gida na,Mummy Tace Dan Allah Ahmad ka bimu mu tafi kaga London ko Turkysh ko Kuma a Nan kasar Nigeria sai kayi Aiki an baka company kyauta ka dogara da kanka Kaine fa babban Danmu Kai ya kamata ace ka nutsu,kalli kaninka ya rike nasa a Lagos Yana aikinsa gashi da Degree da Masters Kai kuwa Degree daya ma da kyar muka samu ka karasa a Russia,Ahmad yace kunga fa Ni ba inda zanje Kawai ku daina Bata bakinku mutanen da basa son bakar fata ku Kun damu da su kuje kuyi harkarku,kuyi rayuwarku nima nayi tawa,yawwa kunji ba inda zanje ya tashi Yana tangadi ya haura sama,ya barsu a Nan cike da Alajabi yafi karfinsu.Daddy bakin ciki ya Kama shi ya juya kalli Mommy tare da galla Mata Harara yace Kinga danki ko kin ga abinda kika haifa ko? Mummy Tace au da nane ma Ni Daya? Daga Nan suka fara cacar Baki. Aamna ce ta fito tsakar gida sanye da wani gajeren wando ko gwiwa Bai ba Milk color,da Yar rigarta t-shirt dark Blue,Hannu biyu ta zuba a cikin aljihunta tana tafiya tana yan ga,Cinyoyi da kafafunta lukutaye,Mama ce ta Bude Baki Tace Yau me Zan gani? Aamna kece yau kika Yi wannan shigar ke da bakya so aga jikinki yau me Zan gani na Shiga Uku Kamar Namiji, Malam fito ka gani,Kuma wandon ma na Yan Ball ta saka wani katon buje,Aamna saman bakin rijiyar tsakar Gidan ta zauna daram tare da Harde kafafu,Baba ne ya fito da sauri shima ya Bude baki,yace kwaya kika Sha? Nan fa gidan haya ne ga maza Wanda da matansu,Aamna Fuska ta bata tare da Furta naga Alama a gidan Nan magauta sun min yawa,Magauta sun sani a gaba Ana so aga baya na,to Zan dauki mataki Mama kirji ta dafe Tace Aljanu ne da ke Aamna? Tace Ni yawwa da ace akwai Sigari a kusa ma yau Zan fara zukawa sai anayi ana feso da hayaki ta Hanci da baki sabo da Naga an tsaneni a gidan Nan so ake na lalace to wallahi Zan bi duniya kowa ya huta Matukar ba a daina uzura min ba. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK. MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 6-10 Official By AsmaBaffa. PAGE NAKU NE SAMEERAN GAYA FLOWER AUTA AIDA MAMAN TASNIM CHOICE Aamna ce a Resturant dinsu tana hadowa customers abinci tana bin wakar Dake tashi a ciki da manyan speakers sabo da Jin dadin masu cin abinci a wajen,idan kaji uban kida kamar kana club,ai Aamna Bata San Sanda take kada Kai ba tana bin wakar da Baki tana bi layi layi inda masu jiran order suke zaune tana ajiyewa kowa nasa,duk Wanda ya kalleta sai yayi Dariya yanda Bata ji bata gani bilhakki aikinta takeyi tana rawa da kanta,wani babban mutum Bai San Sanda ya saki Dariya ba Amma Aamna ko a jikinta sai ma data soke Wayarta a jikin aljihun skert dinta,wani kida ya dado ta tayi tafi tare da daura Hannayenta biyu a kanta tare da Furta wayyo Baba.... Ai kuwa wasu duk sunyi tunanin kwaya take Sha Kawai sai Dariya akeyi tana Basu nishadi gata kyakyawa ta karshe. Wata Budurwar da saurayinta Tace wannan Yarinyar ba karamar Yar Iska bace ko a jikinta duk mutanen Nan ko kunya babu,Matashin Yana zuba Dariya yace ai shi yasa nake zuwa resturant din Nan,sabo da ita nake zuwa wlh abin Dariya Zaki gani iri iri tana yi,Budurwar kishi ya turnuketa ta kalle shi ta watsa Masa Harara Tace Ni Kuma fa? Allah ya tona maka asiri ka Fadi gaskiya,shi yasa ko yaushe kace muzo Nan munafuki Ashe Dan ita kake zuwa,sai lokacin matashin ya tuna tabargazar da yayi a Gaban Babynsa. Aamna kuwa wani sufa tayi da takalminta a tiles din tana tafiya a Haka Kamar wacce ta hau takalmin Taya Wai duk cikin saurin Aiki ne,Siyama kawarta itama Haka ta shararo da sufarta Hannunta dauke da tire da kayan Abinci Washe gari da Ahmad ya fita Wata hanya Suka samu tare da tare hanyar mota kowa idan yazo sai dai ya juya Inda ya fito,sai da aka kawo Yan Sanda wajen suka dinga fada da Yan Sanda,Bincike Dpo yayi Dan waye? Ai Yana ji an Fadi waye Baban Ahmad a kasar sai ya tsorata yaje har gidan ya samu Babansa tunda ance yazo Yana Kd ma,Bayan sun gaisa Dpo ya Kai karar Ahmad yace mun kyale shi ne sabo da Kai da irin taimako da kake Yi a kasar nan sabo da Haka Dan Allah Ka Jawa danka kunne,Daddy ya Basu Hakuri tare da sanar musu duk irin kangarewar Dansa,Dpo yace sai dai ku dage da Addua Amma a tsawatar Masa Kar mu dauki mataki aga Bamu kyauta ba,Bayan sun tafi Shuru Ahmad Bai dawo ba sai cikin dare Daddy,Mummy da Saddeeq duk suna jiransa sai kuwa gashi ya dawo a make,Daddy ya lullube shi da fada ba ji ba gani,Kaninsa Sadeeq yasa Baki Nan take Ahmad ya shaki kwalar Sadeeq zai Duke shi,Mommy ta rirrike shi tana kuka tana cewa ka Bari Mana Ahmad wayyo na Shiga Uku Ni,Daddy kuwa Mari ya kwadawa Ahmad,Nan take ya dafe kuncinsa Daya da mamaki sai Kuma ya sheke da Mahaukaciyar Dariya Yana Nuna Daddy da yatsa Yana ka mareni akan wannan kanina shi zai ce zai min fada,Daddy yace banza shashasha sai na sake marinka wallahi,Juyawa Ahmad yayi ya haura samansa a fusace,Humaira kanwarsa da Mommy suka bi bayansa suna ta bashi Hakuri suna lallaba shi,Ahmad yace kina gani Mommy marina fa yayi Akan kanina,Ni dama nasan Daddy Baya kauna ta,Bai so aka haife Ni ba gaba daya,Ba Haka bane Ahmad Yana sonka Nima Ina sonka,Yace ai nasan ke kina so na Amma Daddy Baya kauna ta Ni ku tafi ku bani waje Kawai ya dakko kwalabar barasarsa ya shiga korawa,Mummy suka fita sun San halinsa idan yayi Fushi. Ranar da su Mymmy suka kwana Uku da Yamma Ahmad,Mufida matar Saddeeq da Humaira Autarsu suna Garden suna Hira Ahmad Yana ta musu magana irin ta Niggogi irin ta Yan kwaya suna ta dariya, Sadeeq ta sama ya hango su ta window kishin matarsa ya kamashi ya sakko tare da Fitowa Haka ya dinga zaga garden Yana kunci,ya Shiga ya fita ya dawo ya wuce ya sake dawowa,Mufida ta fuskanci wani Abu Tace lafiya dai Baby? Cike da bala'i yace ba lafiya ba ki taso ki kula da mijinki kin zauna kina wani dariyar banza da wofi,Ahmad yace ya zaka dauke ta muna Hira,Hira mukeyi Kai wanne irin yaro ne? Tsaki Saddeeq Yaja ya Fisgi matarsa Suka tafi,Juyawa yayi Suka ci gaba da Hira da Mufida kanwarsa suna ta dariya abinsu,Wayar Humaira ya karba ya juya yace irin wannan waya Haka sis idan kika hadu da irinmu Yan duniya ai sai mu tare Miki Hanya muyi Miki fashin ta,Dariya Suka sake yi Yana ta Dariya ba ji ba gani irin ta Yan kwaya,yace sis yanzu ma Dan na sanki ce ke kanwata ce da su Jibson Zan turo su kwace ta,Dariya Suka sake Yi a tare Humaira ta daki kafadarsa tare da furta Kai Yaya,Kallon Kanwar tasa yayi sosai yace sis you are cute wooo...see your Nose fine nose,kina sa Nikaf fa Kar ki hadu da irin su Brown abokina I swear Kamaki zasu Yi su Sha harka kina kula fa tam,hope Baki kula samari Kar wani yazo ya taba min kanwa Naga kin fara girma abubuwa sun fito Haka, zanzo har Lagos nayi yaki ne idan wani ya Bata min ke, Humaira harda rike ciki sabo da dariya ga kunyar abinda yace,shi kuwa ko a jikinsa Kwanan su Mummy biyar suka fito cikin Shirin tafiya Ahmad Yana binsu a baya Yana ta murna zasu tafi yanzu ma su barshi ya sakata ya Wala,Mummy ta Rungume shi Tace ka Zama mutumin kirki Dana tunda baza ka bimu ba ka kula da kanka,yace to Mummy na, Saddeeq yace wannan ba Wani shiryuwa da zaiyi Nan take Ahmad yayi Kansa da bala'i,Mufida tazo Tace Yi Hakuri kyale shi Yaya King,yace yawwa matar mu ki kula da kanki,Da sauri Saddeeq ya janye matarsa cike da kishi,Ahmad yace wannan wanne irin Dan Uwa ne Haka? Daddy ne ya Kira Driver su wurin Tara yace ya kwace Motocin Dake Hannun Ahmad kaf,Dama Bai damu ba yace tunda Yana da kudin machine ya ishe shi,Daddy kuwa yace tunda baza ka nutsu ba ai Motocin da kudi na ka siya na karbe,Ko a jikin Ahmad yace kuje da ita,Daddy yace dole ma ko baka fada ba,kudi dai Zan na tura maka na kula da kanka sabo da hakki na ne,gida ma kayi ta Zama Amma ka sani ba gidanka bane Nawa ne. Mummy Tace please Ahmad ka daure nasan kana Sallah Amma baka Yi sai Sanda kaga dama ka gyara Sallah ita ce komai awajen musulmi,Ahmad yace sured Mum Zan gyara ki yarda Dani,Nafa sanka Ahmad tun yaushe kake cewa zaka gyara Amma kaki,Ki yarda Mum Inshaallah,nine fa Ahmad dinki,Sunana fa aka kalla aka yo Guarantee trust Bank,Dariya sukayi har Daddy,Yawwa ehem Dad karka manta na tura maka new accnt number Dina Ina bukatar kudi kudina sunyi low,Daddy yace Zan tura ai Ina sane sakaran banza. Ahmad Yana ji suka shiga mota Gate man ya Bude Musu suka tafi Basu bar mota ko Daya a Hannun Ahmad ba aka su Suka kwashe su,Suna tafiya ya dauki waya tare da Kiran Abokansa su zo Iyayensa sun tafi sai murna sukeyi yau suna gidan King. Me Gadi ya kalle shi kawai ya jinjina Kai Amma Ogansa Yana da Hali me kyau Kawai matsalarsa shaye shaye da Rashin Ibada sosai. Aamna tana cikin Restaurant dinsu tana ta Kai abinci wajen masu ci,sannan Kuma suna Hira da Babbar kawarta Siyama wacce aikinsu Daya,tare suka Yi HND a Poly,Rashin samun Aiki yasa suka nemi Aiki a sabon Restaurant da Maman kawarsu Saratu ta bude sabo da Talaucin da suke fama da shi, Siyama Tace kawata Nima fa Allah ya kusa daga Ni,na manta ban fada Miki ba Nafa fada cikin kogin son Faisal,kwanan nan ma nake so na bashi dama ya turo magabata,Murmushi Aamna tayi Tace wow I'm Happy for you Kawa But Ina ganin Kamar kinyi gaggawa ya kamata ki Bari ku fahimci juna sosai Bai Yi ko 1month da fara zuwa wajenki ba,Karki je garin sauri da matsuwar Aure a samu matsala,Siyama ce ta dakatar da Aamna ta hanyar daga Mata Hannu tare da Bata rai,Tace Ni fa Aamna ban Gane Miki ba,ai sai kisa nayi zargin ko bakya kauna ta kina bakin ciki na samu Miji ke Baki samu, Subhannallahi Siyama Allah ya kiyaye ko wani da musulmi bazan Masa bakin ciki ba bare ke da kike kawata wacce muke kashewa mu rufe tare Allah ya kiyaye min,sabo da Haka Dan Allah gobe a daura aurenki da Faisal ma Bai Dame Ni ba Bai shafe Ni ba,babu abinda Zan tsinta ciki,idan wahala ce ma ke Zaki Sha abarki mu Yan jaje ne. Siyama Tace ai ke dama bakya kaunar Aure bakya so kiyi Kuma bakya kauna wani yayi,gaba kike da Sunnar ma'aiki sabo da ke Kinga Baki da samari idan ma kin samu guduwa suke yi,idan Zaki hakura ki auri kowa kika samu ki hakura yanzu an daina auren Soyayya wa zai Iya rike ka Kawai ake Nema ya zaka ci ka Sha ka rayu inda zaka huta da iyayenka,Faisal Doctor ne matarsa mutuwa tayi wajen haihuwar fari,yaro matashi ga kudi me nake jira ai yanzu ba a jira Yan Secondary ma idan suka samu Miji aure suke Yi,kiwa kanki fada,shekaru tafiya suke Yi mu matane,ko ba komai kar tsufa ba aure har mu zo lokacin Haihuwar mu ya wuce,Aamna Tace Allah Baki Hakuri ayi aure lafiya mu muna Nan daram za muci gaba da Addua Allah Bai manta damu ba Yana sane da mu,Siyama Tace ae aci gaba da Zama lafiya Ana gantali, wanne gantali mu da muka yo rako duniya,gamu an halicce mu a Nigeria babbar jarabawa,ga talauci,wannan duniyar Ina Dadi cikinta, aikinsu Suka ci gaba Yi suna Hira kamar ba sune Suka Yi fada ba,dama sun Saba fada da junansu. Washe gari Bayan ta tafi wajen Aiki Sai ta Iske Siyama Bata karaso ba sai Aamna da sauran ma'aikatan,Siyama kuwa Direct gidan Su Aamna ta wuce,Mama ta tarbe ta,Tayi sa'a Baba ma Yana gida,Bayan sun gaisa Tace Baba wata magana ce ke tafe Dani da Kuma shawara,Baba yace Muna jinki Siyama,Siyama ta Basu labarin yanda sukayi da Aamna Akan Maganar Aurenta da Faisal,Baba yace na rasa dalilin Yarinyar Nan da Bata kaunar Aure,Siyama Tace Ni abinda na fahimta Baba Aljani ne ya auri Aamna Kawai shawara ku kaita gidan malamai a Nema Mata magani shine Kawai,Mama Tace tabbas yarinya kinyi nisan hankali,shi yasa ake son kawa irinku ta gari,Haba biri yayi Kama da mutum cewar Baba,yace Inshaallah gobe zamu dauketa mu tafi da ita kauyenmu can Sokoto mu Nema Mata magani,dama jiya anyi Mana Albashi sai a fasa siyan komai mu tafi neman magani Allah yasa a Dace kafin ayi Auren Zuhra itama ta samu nata Mijin mu hada a Sha rikitiba sosai,Haka Siyama ta fito ta zo wajen Aiki a makare ranar Aamna Bata San dalili ba tana komawa gida taga Baba da fara'a ya amsa Sallamarta,ta Gaida shi Kuma ya amsa,Mama ma Haka,Aamna dai hankalinta Bai kwanta ba tayi mamaki,Zuhra kuwa tana ta karasa miyar Taushe,Mama Tace Aamna Sannu da Aiki zauna na kawo Miki abinci,Aamna mamaki ya kamata sai binsu take da kallo har taga an kawo Mata abincin a flask Wanda a baya ko rufe Mata ba ayi bare wani Flask,ta kalli abincin ta kalli Mama Tace Mama ko dai maganin bera kuka saka min zaku kashe Ni?Mama tana gyara daurin zaninta Tace haba Aamna kin taba ganin Iyaye sun kashe yarsu? Aamna Tace na nawa Kuma,bazan ci ba gaskiya wallahi,Ina so na Kara tsawon Rai,bana so na mutu yanzu sabo da Haka Ni bazan ci ba ko ruwan gidan Nan na daina Sha gaskiya. Babu irin lallabawa da lallashin Aamna da Iyayenta Basu Yi ba Amma Taki cin abinci ko ruwa Bata Sha ba,Baba ya kalle ta yace Ki shirya Aamna gobe zamu je Kauye gaishe da Yan Uwana da abokan arzuka,Aamna Tace Amma ba a fada min da wuri ba na shirya,shike Nan Allah ya kaimu goben Amma kafin mu tafi Zan sanarwa ogar mu sabo da gudun matsala,Ba damuwa Aamna cewar Mama. Aamna kwana tayi Bata ci komai ba duk da cewar taci a Restaurant dinsu,Washe gari da wuri ta nufi gidan su Saratu kawarta,Saratu tana bacci har Aamna ta Shiga aka Mata Sallama da Maman Saratu ta Mata bayani zasu Yi tafiya,Hajiya Tace Baki da matsala Aamna Amma kin San dai Baki da kudin fashin da zakiyi,a cikin Albashinki za a cire na Iya kwanakin da kika Yi bakya zuwa Aiki tunda kin San ba aikin Gomnati bane,Gomnati ce ake cin banza Ni Kuma ba Gomnati bace,Aamna Tace ba damuwa Amma,Hajiya Tace a dawo lfy ta Mike tare da haurawa sama,itama Aamna ta Mike ta tafi,dama sun Gama shiri Kaya Kawai ta canja wani lace ja me adon Golden, me Dan kyau Riga da skert,Ta sa takalminta na Sallah da jaka duka Golden,Zuhra Kawai aka Bari a gida sabo da makaranta suna Exam,Napep muka shiga zuwa Tasha daga can Muka hau Motar Sokoto tana ta Adduointa, sun Dade suna tafiya Amma sai kusan dare muka Isa can kauyen Su Baba da Maman su,Asalin gidan Iyayen Baba muka sauka a bangaren Baba,Dakuna biyu da toilet ne na Bulon Siminti Wanda Baba ne ya Gina ya sumulmule ko Ina da Siminti idan sunje can suke sharewa su zauna a gadon uban su,Ko wanne daki akwai Ledar tsakar daki da katifa katuwa da Bedsheet,sai kwanikan cin Abinci da Tukwane har da Reshio dinsu,komai na bukata akwai dai dai talaka,Mutanen gidan Suka tarbe su dake Babban gida ne a bangaren Kanin Baba wato Kawu Ismail muka sauka. Sai da suka ci abinci suka huta sannan suka gyara bangaren Baba ita da Mama, Bedsheet din Yana wanke a cikin kayansu suka shimfida abin su,a saman Katifun dakunan Guda biyu,wanka suka Yi tare da Yin Sallar Isha,Baba suna Kofar gida shi da Kaninsa da sauran dangi,suma dakinsu Mata ne Yan Uwa aka taru suna hira sai ga Baba da Kawu Ismail,ba tare da Bata lokaci ba Baba yace ke Aamna taso muje Ina Maman taku ta taso mu tafi muyi abinda ya kawo mu ba dadewa zamuyi ba,Hijab me Hannu Aamna ta Daura saman Riga da skert Dinta na jar Atamfa,Mama kuwa Mayafi ta yafa tare da Fitowa zasu tafi,Baba ya kalli Mama yace wannan tayani gantalin Wato baza ki daina yafawa ba ko? Har yanzu fa da sauranki Baki Gama Expire ba,Dariya Aamna tayi tare da sadda kanta kasa sabo da fadan Baba da Mama ya rigada yabi jininsu,Mama Tace Kai ka sani dai,Baba yace ya kamata ki daina Narka kibar Nan ke ba Wani abinci kike samu me Gina jiki ba Amma kullum Hawa kike kamar ana buga Miki Iska,Mama Tace sai ka fara rage taka kibar tukun,Haka suka tafi Suna ta cacar baki,Kawu Ismail kuwa fada yake ta yiwa Aamna lallai ta fitar da Mijin Aure,yace abokan haihuwarki daga me Yara hudu sai me Yara biyar a Nan kauyen,ita Aamna Bata taba sanin Mama da Baba Basu Suka haife ta ba,tasan dai suna Dan nuna Mata banbanci tsakaninta da Zuhra,Haka Dangin Baba tasan Suma sunfi son Zuhra,Haka ma Dangin Mama,Sai wani gida da ake kaita tun tana karama a cikin Sokoto city wani me kyau gidan mutanen Sudan ance Wai Yan uwane suma Gidan wani mutum suka je Malam me Almajirai,Bayan sun zauna Aamna sai ji tayi Baba suna ta Masa bayani akan bata samu Mijin Aure ba,Kuma ko zancen Aure akayi Aamna Bata kauna,Malamin Yana tauna goro yace Ashsha Aljan ne namijin dare ne wallahi take fama da shi,Mama Tace biri yayi Kama da mutum,Baki Aamna ta Bude tana kallon Iyayen Nata,Malamin yace yanzu Zan kwana Uku ba bacci Ina wani Aiki Amma dole aikin Nan kullum sai an yanka zakara Guda Uku har na kwana Uku,Baba duk talaucinsa sai yace dama na samu wasu kudi Nan take ya biya kudin zakaru tare da bawa malamin dubu goma kudin Aiki,yace Nan da kwana Uku ku dawo ku karbi wata laya wacce zata soke ta a cikin gashinta,Fuska Aamna ta Bata kamar zata saka kuka,Ace Allah Bai kawo lokacin Abu ba Amma Iyayen nata basa gani. Suna Fitowa Kawu Ismail yace saura wajen Malam Kare Aiki,Wannan malamin sanatoci layi suke Yi a Wajensa,Aamna ta girgiza Kai Tace Baba wallahi ba kyau,Wannan shirka ce baza a fadawa Allah bukata ba sai Malam,Baba ya kalleta cikin duhun dare yace ai ke Aljanu gareki sun aureki Bai ma dace a saurare ki ba sabo da ba a cikin hayyacinki kike ba,Yo ka biyewa sakarai cewar Mama,Kawu Ismail yaci gaba da cewa inshallah Kuna komawa zata samu Miji itama,Wannan malamin da suka je Wajensa Rubutu yayiwa Aamna a tafin Hannu yace lashe ai magauta ne Suka mata asiri kuma makwaftan ku ne,Takaici yasa Aamna Tace Allah ya tona muku asiri masu hada fada tsakanin Musulmai,Rankwashi Mama ta zubawa Aamna tayi Shuru,Lashe Kawu ya furta Yana zaro Mata Ido,Haka ba a sonta ba Tace Allah na tuba bana nufin kowa da sharri sannan ta lashe su Baba suna ganin Aljanu ne ke hanata Sha,Haka Suka je wajen wani malamin shima yayi nasa sannan suka jira Bayan Kwana Uku Suka karbo duk wasu Magungunan da aka hada Suka dawo ,Duk wani Rubutu da magani da Suka bawa Aamna Kan tayi amfani da su sai ta samu jikin katanga ta zubar babu Wanda ya sani,Laya Kuma Haka ta soketa da pin a gashinta sabo da kullum Mama sai ta duba gashin dole ta soke Laya a gashinta. Su Baba Basu Sani ba suna ta jira suga saurayi yazo neman Auren Aamna Amma Shuru,ga Kuma bikin Zuhra yana ta gabatowa,duk sunyi Anko da Dinku Nan su na biki duk wani shiri da za ayi mun Riga sunyi,Baba ya siyar da manyan shanayensa Guda hudu dake Kauye sabo da Haka ba Harkar Talauci sunyi komai cikin rufin asiri,Adam Ango ya hada musu Dinner zazzafa me kyau ranar Saturday,Sunday za a daura Aure a Kai Amarya,daga Aamna sai kawarta Siyama bata gayyaci kowa ba,Amarya dai taci Uban gayyar kawaye wurin Dinner,Biki saura kwana daya a fara Aamna tayi lalle da gyaran gashi,amarya kuwa ta Sha gyara sai sheki take zubawa,dangi na nesa sun zo sai tsiya ake yiwa Aamna kanwa zata Yi aure ta bar Yayarta,Haka suka Sha bikin Zuhra da Angonta Adam anyi an Gama lfy tare da Kai Amarya da gararta,gidan Adam madaidaici ne me kyau harda gate yayi kyau gidan,ga Yar motarsa me kyau Toyota,Itama Zuhra Baba ya Dage ya Mata Kaya masu kyawun gaske. Ahmad Yana kwance a makeken Gadonsa Yana zuba bacci,wayarsa ta dinga ruru gashi ya kasa tashi sai da kyar ya farka ba tare da ya Bude idonsa ba ya jawo wayarsa yaga number Mummynsa dama ta fada Masa zata zo ta ganshi a kaduna ita kadai kasancewar Daddy,Saddeeq da Humaira suna Saudiya Umrah,Cikin Muryar bacci ya Kara Wayar a kunnensa tare da Furta Hello Mummy......Muryar Namiji yaji yace da Allah me wannan Wayar sunyi Mummunan Hatsari Driver ya mutu ita Kuma tana asibiti da Allah ayi sauri azo,Firgigit ya farka Yace what....?cikin gigita yace please fada min Address din Asibitin,Nan take ya fada Masa,Da sauri Ahmad ya figi machine dinsa sanye da wando 3qutr da Riga t-shirt fara tas sai asibiti,a gurguje ya fada ciki Yana tambaya aka kaishi Emergency Nan ya Iske Mummy Rai a hannun Allah. Aamna Yau da matsanancin ciwon Mara ta tafi wurin aikinta gudun kar a hanata kudinta cas sabo da ba aikin Gomnati bane,a Haka take daurewa tun tana aikinta da karfin Hali har abin ya fara gagararta,Siyama ta kalla tana rumtse Ido Tace Siyama dole Zan hakura da aikin yau Hospital Zan wuce a duba min marata ya kamata ayi min scanning a gano min mene a wajen Nan,Siyama da tausayawa Tace Allah ya Baki lafiya kawata a dawo lfy sai munyi waya,Aamna ta daura After Dress a saman Uniform dinta Riga da wando ta fita tana tafiya a hankali ta Isa bakin Titi tare da Shiga Napep zuwa Asibitin da suke ganin Likita idan lalura ta taso,asibiti ne na Gomnati Amma ba laifi akwai kyau. Tana rike da mara hankalinta baya jikinta tana zuba Uban Sauri tabi wani Corridor,Gaf taji tayi Karo da mutum,wani kamshi me jarabar Dadi ya daki Hancinta,da sauri taja baya ko kallon Wanda ta buge Bata Yi ba,shima Bai ko kalleta ba hankalinsa baya jikinsa,Bayan tayi magana da wani Emergency ta nufa tana matse kwallar wahala gashi Bata fadawa kowa a gidansu ba,Karo suka sake Yi da juna kamshin mutumin dazu ta sake ji ya cika Mata Hanci Kamar Kar ta daina Shaka,Tsaki Yaja sosai yayi cikin Emergency Yana ta faman yiwa Doctors masifa,Yana cewa a bani Mummy na dole ne,Ni Nace bana son wannan Hospital din me Araha,a bani Uwata wannan so kuke ku kashe min Mummy a Asibitin Gomnati, Wallahi Mummy na ta mutum sai na daure ku,wani babban Likita ne yace Haba Malam Ahmad kake ko wa? Da masifa yace karka sake ce min Malam,Ni ba Malam bane,a masallaci ka ganni Ina Kiran Sallah ko Tafsiri kaga Ina Yi? Idan zaka iya Call me king,Doctor yayi Murmushi sabo da daga ganin Ahmad kasan inda tarbiyya take ma Bai nufa ba,Cikin tausasawa Doctor yace kayi Hakuri zamuyi Aiki iya yin mu a samu ta farfado wallahi Matukar ba a Bata agaji ba ka dauke ta to kafin kaje da ita wani Asibitin zaka iya rasa ta kayi Hakuri idan aka samo kanta sai ka dauke ta idan kaga dama ma ka tafi da abarka China. Aamna kwance take tana hawayen wahala Ana ta lallaba Ahmad Anki kulata,Cikin masifa Tace da Allah ku rabu dashi azo a duba marata Likita mayu sun kamani sun min Ajiya a marata watakil ma Tukunya ce a wajen ko wani karfen Kun zauna a wajen wannan muma ai ba daga sama muka Fado ba Kuma Nan gaba Aure zamuyi mu haihu,muma Iyayen wasu ne,Wani mugun kallo Ahmad ya aikawa Aamna sannan ya koma gefen Mummy ya zauna Yana cike da tashin hankali,Likita Yana zuwa kanta yace Rannan anyi Miki scanning nace ciwon sanyi ne dake sai kin dage da magani,Aamna Tace to ai har na gaji da maganin, wannan sanyi da naci yake jaraba Kawai,kankara nake Sha ko me?Ni ba Yar Madara ba Bamu da ko fridge ace wani sanyi,Ahmad sai lokacin ya kalli Aamna kadan tana kwance yace Doctor da Allah kazo wajen Mummy na ka rabu da wannan rubabbiyar Sanyi ya Gama kashe ta mijinta shike nan sai asosa Mata asosa,Aamna tunda ta kalli Ahmad Bata sake Kallonsa ba sabo da kyawunsa da wani mugun kwarjini da yake mata,cikin lokaci kadan Doctor ya yiwa Aamna Allurai tare da Bata magunguna,sai gata ta watsake ta warke yayin da Mummy itama ta farfado bayan likitoci sunyi aikinsu,Ahmad sai murna yake Yi,Mummy ta sa Hannunta tare da shafa sumarsa Tace karka fadawa Humaira da Daddy tunda naji sauki yanzu da ace akwai mace wacce zata kula Dani sai ta zauna har a sallame Ni,idan za a samo min Yar Aiki ma Zan biyata kudin jinya cewar Ahmad,Aamna ta dauki Handbag dinta ta wuce kenan taji Ana Neman me Aiki Sai gashi ta dawo baya da sauri tare da tambaya Nawa za a biya Ni? Mummy ta kalli Aamna sama da kasa Tace daga dubu Hamsim zuwa sama,Aamna ta Bude Baki Tace yanzu idan yau na fara jinya aka sallameki gobe dubu Hamsim Zaki bani? Ahmad yace kaji barauniya, Mummy ce ta kalli Aamna ta daga Kai Alamar ae,Aamna Tace Alhmdllh na karba zanyi Bari naje gida nayo Shirin jinya,Mummy Tace a dawo lfy tana rufe Ido sabo da da kyar take magana ba laifi Mummy ta Sha wahala. Agurguje Aamna ta koma gida ko abinci bata ci ba ta sanarwa Mama komai,Baki ta tabe Tace yo tunda kinki aure ai sai kici gaba da neman kudin tunda ke kudi ne a gabanki,Baba kuwa Baki ya tabe yace ba abinda kika sani sai neman kudi to a dawo lfy dama bikin Zuhra ya cinye Mana komai,ita dai Aamna kayanta ta bukata ta hada a karamar Akwati tayi wanka tare da yin Sallar Isha sannan ta wuce Asibitin abinta,tana tafiya kamar Namiji sabo da Tace ta daina Zama ta kirki. Tana Shiga ta Iske Ahmad ya jibgo kayan ci da Sha da duk wani abin bukata,Kallon Aamna yayi tare da galla Mata Harara cikin kallo na wulakanci,Aamna ta kalle shi itama tare da tabe Baki ta shiga rera Waka lalatacce....lalatacce ne ko a gidan su,da sauri ya kalle ta ransa a bace gashi ba damar fada Amma duk da Haka sai da Yaja Tsaki yace Talakar banza barauniya,Aamna tace ae naji da me kudi da talaka ai duk Allah yaga dama ya bawa kowa,You are very stupid....nayi magana dake? Ina wakata Zaki sa min ths your Smelling mouth,Mind your fucking Business ya Furta da karaji Wanda sai da Mummy ta farka tare da dafe kanta,duk abinda sukeyi tana jinsu, Nishi tayi Tace Son gobe a canja min Hospital wannan akwai sauro gashi ba Ac,Ahmad Yana maganarsa ta Yan duniya sai kace wani Me wakar Raps yace comfirm Mum,ki Dade kiyi karko and ki mutu AC Mum,Allah ya ja da nisan kwana,Mummy tayi Dan murmushi Tace Ameen a hankali,Aamna ta kalla tace dauki katin Nan ki Siyo maganin da ba a karasa siya ba,Ga kudi Nan a jaka ta,Aamna ta zuge jakar Mummy zata dauki katin da kudin,Ahmad ya fisge jakar ya dauko katin tare da zaro kudi a aljihunsa ya Watso a jikin Aamna yace Jeki,Aamna tayi murmushin bacin Rai Tace ba komai ta Eba ta fita,wurin siyen maganin taje ta Mika katin wani yaro matashi ne a ciki Yace dubu Uku da dari biyu,Me bada maganin da hantara yace ba canji malama,Dan Rainin hankali baza ki samo canji ba. Aamna ta Bude Baki tana kallon yanda yake masifa,Kai Malam kayi hankali da Ni Kanwar uwarka ce Ni da zaka dinga min magana Anyhow,Uban me kika Isa kiyi,Tas kake ji Aamna ta zuba Masa Mari Tace fito mu Buda wallahi Naga baka da tarbiyya,Wanda suke wajen ne Suka fito tare da raba fadan sannan Aamna ta wuce abinta ta siyo maganin a wani chemist dake wajen Hospital din,tana masifa an fada musu Ina tsoron fada da Namiji,In cakwumi Namiji,inci kwalarsa,muyi dambe ba komai ne a wajena ba,girman Kauye ce Ni,har yanzu da ragowar Tuwon dawa a jikina cewar Aamna har ta Shiga dakin da Mummy take tana fada cewar in Balla Namiji ba komai bane a wajena,In samu mutum in farke Masa makoshi Dan uban mazaje,Ahmad ya bita da kallo sororo Yana mamakin mace da tsaurin Ido Haka,Tsaki Yaja yaci gaba da latsa wayarsa. Amma ita Aamna ta manta ma da wata marar lafiya take jinya taci gaba da cewa ko wanne Namiji Dan iska,to Billahillazi girman Kauye ce Ni sai na soke mutum da kwalaba,Ahmad ya sake zaro Ido a ransa yace tab Wanda ya auri wannan yayi bye bye da duniya kawai,irinsu ne masu kashe mazaje,Aamna Ta fake da wayo tana zagin Ahmad Tace Dan Iskan mutum Dan Kawai Yana da kyau da kudi ai muma Muna da kyan,ae munji mu talakawa ne sai akayi kaka? Duk kudin mutum Dan ubansa malaikan mutuwa Yana Nan zuwa duk tsayin katanga da katon gate haka zai haura ya zare ruhin mutum,abi duniya a Sannu,Duk wani shiga katuwar mota Haka mala'ika zai zaro ran mutum,Wani mugun razana tayi sakamakon tsawar da Ahmad ya buga Mata,shut up kina min Ihu akan maralafiya Zan fa barar dake,Zan Baki certificate wlh watch your words,Mukus Aamna tayi a ranta Tace wannan shege ne shima. Babu yanda Mummy Bata yi ba Akan Ahmad ya tafi gida Amma yaki yarda ya tafi Yana Nan ya kafa ya tsare. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 11-15 DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa. Page naki ne FANCY HONEY Yana Zaune a gefen Mummy ita Kuma Aamna tana zaune a wata kujera,Mararta ce ta sake murdawa da sauri ta rike mara tare da kwala Ihu Mummy sai da ta Bude Idonta,Da Sauri Aamna ta samu gadon da ba kowa ta kwanta tana Nishi tare da Kiran Doctor,Likita ya shigo yace to yanzu me jinya ce zata Yi Jinyar wata? Aamna tana cije lebe Tace zanyi Haka Kai Likita ba ruwanka yawwa kayi aikinka Kawai wannan kudi Ina Zan bar shi,Dariya Likita yayi yace Aamna kike ko? Tace no Amy karka sake ce min wani Aamna Aemy(Amy)Baki Ahmad ya tabe tare da Bude wata Leda ya fito da manyan kwalaban giya masu tsada Yana korawa Abinsa Yayin da Mummy take ta bacci,tana kwance ta juyo tana kallonsa bata Gane giya bace tayi tunanin wani lemo ne me Dadi na masu kudi,tana ta Kallonsa tana faman Hadiyar yawu,Aamna Tace Wanda yaci shi kadai shi kadai zai mutu,kafin ta rufe Baki yace da Ubanki za a sani a kabari da? Aamna Tace wakata nayi fa,Nima ai wakar nakeyi ko na kulaki? cewar Ahmad Yana cin magani kamar zaiyi Naushi. Aamna ita kanta Tsoronsa take Yi Amma karfin Hali Irin nata yasa take maida Masa martani,Mummy tana kwance tana numfarfashi tasan me yake Sha sabo da taji warinta,baya kunyar uban kowa,sai da ya Gama Shan wacce zai Sha ya Mike Yana saka wayarsa a cikin wani Crazy 3qurt Jean Kan Mummy ya shafa tare da furta Allah ya Baki lfy Bari naje gida nayi wanka Zan dawo,Mummy Tace baza ka canja ba ko son so kake bakin cikinka ya kashe Ni? Murmushi yayi Kawai sannan yace Zan dawo Mum yanzu 11pm Zan dawo a Nan Zan kwana,aci gaba da Mana Addua Ina so na shiryu Amma Ina,A gabanta ya tsuguna,Mummy ta daura Hannunta a saman sumarsa tare da furta Allah ya shirya min kai Ahmad,Allah ya maka Albarka Allah ya tsare min Kai,Ameen My sweet Mum ya Furta Yana Jin dadi sannan ya Mike ya fita Yana takunsa da wani takama da Isa kamar Dan sarki,Machine dinsa ya hau tare da Bude wuta kamar zai tashi sama,Direct gidansa ya nufa ko da ya Isa gidan Toilet dinsa ya wuce ta Sha gyara ya sakarwa Kansa Shower tare da wanka da wani liquid soap me tsada da kamshi,Bayan ya Gama a gurguje yayi Sallar Magriba da Isha sabo da akwai Wasa da Addini,Yana Idarwa ya daga Hannu sama Yana Adduoi tare da rokar Allah Allah ka Bawa Mummy na lafiya. Yace cikin adduar Allah duk da ba Adduar Nan nake Yi ba kullum Allah Ni me laifi ne a gareka ya Rabbissamawati Wal ard Allah ka yafe min laifuka na ka shirye Ni,Ina so na shiryu ya Allah Amma na kasa ya Allah ka dafa min na shiryu,Allah kasa mu mutu Muna Musulmai masu Imani,Allah karka Bari muyi maka shirka,Ka rabamu da Wutar Jahannama,Ka Bamu lfy da tsawon Rai,Allah kasa nayi tsawon Rai Allah bana so na mutu da wuri ka ja kwana na,Ka rabani da cuttuttukan zamani, ya Allah ka raba mu da talauci ka Bamu dukiya ta halak me amfani,Haka ma ya yiwa Daddy da Yan Uwa da Musulmai,karshe yace yace Allah duk da ba damuwa nayi da Mata ba Mummy ta tana so nayi aure Ya Rab ka bani mace ta gari me so na tsakani da Allah,me Ilmin Addini Dana zamani,wayayya,ba Yar Kauye ba,Ya Rab zukekiya ko ko fara ko light chocolate wacce idan na kalle ta kawai Zan washe Baki ba tare dana shirya ba,mace Yar dagwas wacce ta Dan dire ta Dan baje daga kasa. Har zai tashi sai ya koma ya sake daga Hannu sama yace Ya Hayyu ya Qayyum na kawo karar Daddy wajen ka Allah kasa ya daina min fada kasa ya dinga so na,Allah kana gani dai Tsoho Nan nawa ya tsane ni kamar ba a son ransa aka haifo Ni ba,to Allah Kaine ka halicce Ni ya zaiyi Dani Allah kasa ya daina tsanata Yana gamawa ya Mike tare da zare jallabiyar da ya saka domin yin Sallah,ya dakko gajeren wando wani me tsada iya gwiwa ya tsaya Masa me Dan Fadi Yana da Aljihuna kala kala a jiki gashi Kalar ruwan kasa yasa Riga Armless baka me rubuyu a jiki da zanen fari,Pcap ya saka Kalar wandonsa Takalminsa ma na Yan gayu Wanda suka San mene wanka ya saka Kalar wandon,wow ba karamin kyau yayi ba Kamar a sace shi a gudu,damatsan Nan gasu Nan na mazaje mul mul irin na Wanda ke Dan Gym,turare yabi jikinsa sannan ya dauki key din machine dinsa ya fita,time ya duba 12am wani 24hrs shawarma joint ya nufa,Ko da ya Shiga ga mutane Nan Kamar Rana,Ana ta shige da fice,wasu Kuma suna ta Shan Shisha shi baya Harkar Hayaki,Take Away yayi na Abubuwan ci sannan ya nufo Hospital wurin Mummy. Bayan Tafiyar Ahmad daga Asibitin Mummy ce ta Dan yiwa Aamna magana da kyar Tace 'ya ta kin iya cire kudi a bank? Nan take tace ae,Tace duba handbag Dina ki dauki Atm card Dina ki ciro min dubu dari,Mamaki tayi lallai masu kudi ne,Haka ta dauka tana mamaki da Bata Santa ba Amma har ta yarda Da ita, Code dinta ta fada mata ta fita da sauri taje ta ciro,Handbag dinta ta sa ta zuba kudin da Atm card din,lokacin Likita yazo yace Hajiya anyi komao dakin da kike bukata ya Zama ready aje a biya kudi sai ku koma ciki. Yana zuwa ya Iske an canja wa Mummy daki Already Kuma dakin na masu kudi ne Idan kana da kudi sai ka biya kudin daki Guda karami a baka Kai Daya,Gado ne daban na me jinya a dakin da Kuma me cutar nata daban,cikin abubuwan Daya siyo ya Bari masu yawa ciki ta Bude ledoji Aamna taga Naman kaza gasashiya ga tsire daban,ga wata Hanta me ruwa ruwa,sai pounded yam da Miyar Egusi shima a take away daban,Sai Lemuka kamar hauka da fruits ga kayan tea,ga plates da spoons,cups etc,komai an tanada,Ido Aamna ta zaro kenan,Mummy duk jikinta inda taji rauni yayi tsami ko Ina ciwo yake Mata Allah yasa Bata karye ba Sannan Bata Yi Mummunan rauni ba Wanda zai wahalar da ita,Dan Nishi tayi Tace Yar Nan zo ki taimaka min naje bayi,Aamna ta Mike da sauri tare da Rike Mummy ta taimaka Mata tana sannu...Sannu Baiwar Allah Sannu Hajiya me kudi Allah ya tashi kafada,Mummy sai da Aamna ta Bata Dariya yanda take Abu kamar tsohuwa,Mummy tace Yan Mata Kamar tsohuwa,Aamna Tace ai itace Hajiya shekarata ashirin da Hudu Babana yace na tsufa gashi naki aure,kin San Baba a Kauye ya taso shi yasa halinsa Bai canja ba,Mummy Tace Uhm,Bayan ta kaita har Toilet sai ta rufo Mata kofa ta fito,Mummy Tace Miko min brush da toothpaste Zaki gani Dana ya kawo,Aamna ta duba ta dakko ta kawo komai da Mummy ke bukata ta Kai Mata,duk Abinda Mummy zata Yi tayi ta fito,Aamna taje da sauri ta taimaka Mata ta kwanta saman bed,a Haka ta samu tayi sallolin da ake binta tayi Addua sosai,Aamna Tace Abinci fa Hajiya?Mummy Tace bani pounded yam din na Dan ci,Amma ta dakko ta zuba a plate tare da cokali ta Bude Hanta da kaza tare da tsire duk a Gaban Mummy,Fruits ma ta yanka sannan ta hada Mata tea me kauri ta zauna tare da sa Mummy a gaba kamar ta samu Yaron yaye,Tace yawwa mashaallah Bismillah ta yanko sakwara da Miya Tace to Hajiya ayi hankali gashi Naga gefen bakinki kin danji rauni tana ta Bata a Baki sunyi Shuru kamar ba kowa,Mummy tana ta ci Tace Baki magana ne? Me zance Mummy sai dai idan tatsuniya Zan miki,Mummy Tace sai kace wata yarinya bana so,Sai da Mummy taci da yawa sannan Tace na koshi,Aamna Tace to Naman fa? Ta Furta tare da ballo cinyar kaza ta mikawa Mummy. Mummy Tace Alhmdllh na koshi,Aamna ta zaro Ido Tace Kazar Hajiya?kaza ce fa,Mummy ta girgiza Kai Alamar Bata ci,Aamna Tace inda ake arziki ba a tsiya Ni Bari na aikata,Nan Aamna taci Kazar Nan ta gaji ta ajiye sauran,taci tsiren taci duk sauran,Mummy kuwa kankana ta Sha taci Banana da Red Apple,Aamna Kam yau harka ta samu sai da taji zata yiwa kanta Illa sannan ta hakura,ta Mike kenan Tace Bari na wanke Hannu da kwanikan tana juyowa gabanta ya yanke yayi muguwar Faduwa ganin Ahmad a tsaye a jikin Kofa da Alama ya Dade a wajen,Fuskarsa ba kwayar Rahma a ciki,Idonta ta dauke a Kansa ta rabe ta gefensa zata wuce wani kamshi Wanda ba irin na dazu ba ya daki Hancinta sai da ta lumshe ido ba tare da ta shirya ba Haka ta wuce da sauri tayi waje,sai da ta wanke komai sannan ta dawo da su ciki ta Adana a tsaftace ta Iske Mummy da Ahmad suna magana da,Mummy tana ta Masa fada ya Bata Rai yayi Shuru,Aamna tana dawowa Mummy ta bar zancen,ita kuwa Aamna saman gadon da ba kowa ta kwanta tare da dakko Wayarta wacce take Ringing tana bukatar a kawo Mata dauki. Ganin kanwarta Zuhra ta daga da sauri,Tace Amarya bakya laifi,Zuhra ta zuba murmushi tana kwance jikin Angonta Adam tace nayi missing naki sis yau naji ban Iya bacci sai naji muryarki,Wallahi Aunty Amy Aure Niima ne,sai yanzu nasan Ni mutum ce Ashe a baya gunki ce Kawai,da ace nasan Haka ne da bazan Dade Haka ba zanyi Aure,Aamna Tace to me yasa bakiyi ba Ana Haihuwar ki ba,ai sai kiyi tun kina jaririya,Ke Aunty Aamna ke fa adawa kike da Aure,ki daina min sharri wa zai ki Aure? Kawai Ni abinda nafi so a aure shine na ganni Ina fasa kwai a kitchen Zan soya Ina kwas kwas a kitchen,Dariya Zuhra take yiwa Yayarta Kamar me,Aamna Tace ban San Iskanci Dan na fada Miki Buri na a Aure shine kike wani dariya,To Ni ba abinda nake so a aure face in cakare da kwalliya Ina kitchen Ina fasa kwai,Mummy tana bacci Ahmad Yana jinsu Amma wayarsa Kawai yake dannawa,Zuhra Tace Aunty to babbar Harkar fa ta soyewa? Aamna Baki ta tabe tare da Furta Dan tani a yanke shege na kowa a duniya a jefar,Ahmad Yana jinsu wannan Maganar Bai Gane me suke nufi ba. Zuhra Tace Aunty Amy Allah ya Baki kema Kalar da kike so Wanda zai biya sadakinki da shegen tsada,Aamna Tace ke na rage tsada na zaftare farashi na yanda su Baba suka damu Ina Ni Ina zaben Yawan Sadaki,Adam ne ya kwace wayar dake Hannun Zuhra tare da Furta sai da safe Aunty kitt ya kashe wayar Baki daya sannan ya ja Amaryarsa Suka kwanta ita kuwa Aamna kwanciya tayi itama tana latsa Wayarta gashi ta kasa bacci sabo da Ahmad Yana ciki Ta kasa kwanciya bare tayi bacci,Bacci ne ya dameta Haka ta kwanta tare da rufe jikinta da katon Hijab Nan take bacci yayi gaba da ita sai Ahmad shi Daya baiyi bacci ba,sai wurin 2am sannan ya bar Asibitin ba tare da kowa ya sani ba. Washe gari da Asuba Mummy ta farka da karfi a jikinta sosai kamar ba ita ba,Kawai rauni ne da Bai warke ba Amma jikinta fes taji,Da kanta ta lallaba taje Bayi gaba Daya kyankyamin Asibitin take Yi shi yasa ta kasa wanka,Sallah tayi itama Aamna Haka Bayan sunyi Brush da komai suna Azhkar Sai da suka Gama sannan Mummy Tace Aamna kike ko? Aamna Tace ae Tace Yau Zan sa a sallame Ni naji sauki Zan iya karasawa a gida tunda Ina da masu Aiki masu kula da Ni,Aamna tana murmushi tace mashaallah Alhmdllh Haka ake so Allah Kara lfy,Ameen Mummy ta furta,Biro da takarda Mummy ta mikawa Aamna Tace rubuta min Address dinki full sai accnt number dinki,Aamna ta karba ta rubuta komai,Nan take Mummy ta kunna Wayarta tayiwa Aamna transfer na dubu Hamsim,Farin ciki ya lullube Amy Tace Hajiya naji kararrawa na gode Allah ya Kara budi,Ameen Mummy ta Furta tare da mikawa Aamna katinta gashi ko Watarana Zaki neme Ni,Aamna ta karbe jiki na rawa. suna Haka sai ga Ahmad ya shigo cikin jallabiya fara Kar ta kirki,yayi mugun kyau,Nan take Aamna ta bishi da kallo a ranta Tace wannan Dangin Larabawa ne gaskiya,ko kallon Inda Aamna take baiyi ba ya koma wajen Mummy dinsa suka gaisa Yana ta murna taji sauki,Itama Aamna Bata kula shi ba ko gaisuwa,Kayan breakfast lafiyayye ya musu take Away Suka ci tare da godiya ga Allah,Wasa Wasa Mummy ba a sallame ta ba sai 4pm,Aamna tana gani Wata galleliyar mota tazo tare da tafiya da Mummy,Suka Yi Sallama Aamna ta shiga Napep sai gida,ta samu yan kudinta Bata da matsala abinta. Bayan Aamna ta dawo gaba Daya kayan da taje asibiti da su har na jikinta ta cire ta wanke fes tayi wanka dama a koshe take,Zama tayi a gefen Mama,Lokacin Baba ya fito daga daki yace yanzu Zuhra tana can a dakin mijinta tana zamanta lfy Abinta,abin kunya Yaya Guda Bata da ko saurayi ko me Gadi babu Wanda ke zuwa zance,Mama Tace an Rubuta Hatimin Annabi Yusufa har an gaji Shuru kake ji sai Neman kudi,Iskanci ne Kawai da samun waje shi yasa Taki fitar da mijin,laifinta ne cewar Mama Kuma kudinki kwandala mun daina karba kije da abinki,Aamna tayi Shuru har Suka Gama ta Mike tayi waje zuwa Kofar gida a kasa ta samu ta zauna dirshan tare da kurma Ihu iya karfinta tana wayyooooo.....Allah.....na shiga Uku na lalace.....Ina samari suke ko Dattawa ku fito ku Aure Ni,Dan Allah gani sadaka ga me bukata,,Ko me tallan rake ko Shoe shiner ko me Gadi,me Mata uku ma yazo Zan Shiga a ta hudu. Wasu ma tunaninsu tabin kwakwalwa ne ya kamata,sai Dariya akeyi Amma Aamna ko a jikinta,sai da taji Rana ta ishe ta sannan ta koma gida,tana Shiga Baba ya rike ta ram tare da zaro katuwar Sanda ya samu Aamna Kamar Allah ya Aiko shi ya shiga jibgarta kamar zai kashe ta,Mama tana Kara Mata Yar Iska mu Zaki kunyata a Unguwa,Ihu Aamna takeyi ga Yan hayar gidan ba kowa,Karshe ta tashi da kyar ba Mayafi jikinta duk kulun Sanda ne ko Ina da gudu tayi waje tana ihu,Baba baya gudun Abin kunya Kawai ya bita a million Suka zuba tsere layinsu rigarsa tana tashi Kamar mahaukaci Ana ta kallon ikon Allah,har saman Titi suna falfala gudu Baba Yana na koreki a gidana karki dawo daga Nan kiyi gaba,Aamna tana gudun masifa tana cewa wallahi sai na dawo me yasa aka haife ni,Ni Nace ku haife Ni Ina ruwana,Suna Haka zugar machininan su Ahmad Suka taho gaba Daya Suma sun kure wuta,Ganin Baba da Aamna suna falla gudu,Dariya ta kwacewa su Mashkoor, a wajen Suka ci birki,Ahmad ne ya bi Aamna da machine tare da sa hannunsa me laushi ya cafko Hannunta da karfi ya daga ta Kamar ya dauki tsinke ya cilla ta a bayan machine ta zauna daram,tana Jin dadi har da godiya Amma sai taga Ahmad yayi reverse ya juya da ita wajen Baba,Ta saki Ihu shi kuwa Baba zuciyarsa Dake tafarfasa yace Alhmdllh ya tsaya cak,a gabansa Ahmad ya Zana wani shegen kwabo da machine yaci birki sannan Aamna ta dire zata gudu Ahmad da shishigi ya samu ya yarfawa Aamna Mari ji kake gauuuu.....Nan take fuskarta ta kumbura ta zube a wajen kuwa,Baba yace na gode Dan Albarka,Ahmad ya kalli Baba da tsageranci yace Gata Nan Yi Mata dukan tsiya Ina Nan ba inda zata je,ko Kuma Ni yanzu nayi maka maganinta,Baba ya saki Baki yace Kai Malam Taya zaka marar min yata, Mace Budurwa ka mareta kalli yanda ka kumbura Mata Fuska,baka da hankali ne? Wata Mahaukaciyar Tsawa Ahmad ya yiwa Ba ba,Hey....tsoho,da sauri Baba ya rufe Baki jikinsa na mazari. Da yatsa Ahmad ya nuna Baba yace Kai tsoho baka Sanni ba Zan sa yarana su babbalaka,Baba yayi Mukus,Su Mashkoor suka saki Ihu da sowa,Kallon Aamna Ahmad yayi tana kuka,Tsawa ya buga Mata Dan Uwarki Ina Mayafinki? Irinku ne kuke sawa Ana yiwa Yara fyade a kasar nan,Dan uban Babanki Ina Mayafinki eyeeee yayi kanta da hargowa,Aamna ta Mike tsaye tana kuka Tace baka Gane Ni bane nice fa wacce nayi jinyar mahaifiyarka,wani dariyar hauka yayi yace ke dalla Ware so what Dan kinyi jinya,kyauta kikayi? Bar Nan wajen ko yanzu na Tara Miki gajiya,Aamna Tace wallahi sai dai mu Tarawa juna gajiya,Kai Malam Nifa ba ruwana muyi kokawa ba komai bane,baka Isa kaci min mutunci da Mahaifi na ba,sai mu Buda Nima fa Yar Tasha ce,tashancin Nan na Iya shi ta Furta tana dukan kirjinta,Tace baka San har yankan Aljihu nayi ba a kasuwa,su Mashkoor suka hangame Baki,Suka ga Kuma Ahmad Bai sa sun Mata duka ba,Jibson da Maganar Yan kwaya yace King kana fa jinta kana kallonta ka bamu Dama mu sassarata. Mutane tunda suka ga su Ahmad babu Wanda yayi gigin zuwa kallo Dan sun San halinsu,Baba ne ya cire Rigarsa daga shi sai wando dogo da Singlet ya mikawa Aamna yace lulluba mu tafi gida,Aamna Tace Ni a Haka Zan koma ba Kaine ka kwance min zani a kasuwa ba,ka biyo Ni Muna ta tsere Ana kallo duk da dama ai mun Saba,Baba zuciyarka bata da control Wai? Baba yace ai kece Aamna Yar Iska ce,kiyi aure kinki Ni fa duk na washe ki ma wallahi,shekara ashirin da Hudu zuwa da biyar ba ko saurayi,25yrs shine girma tsoho? Mashkoor ya tambaya,Baba yace ae ,to Jibson Yana tangadi yace to ke kiyi auren Mana,Aamna sai da tayi Dariya yanda ya fada da muryar maye,Baba yace ai Bata iya magana ba,Bata waye ba,kwana Nan Muka dawo birni,shekarar mu hudu kenan a birni,sai cin mutuncin samari takeyi na rasa yanda zanyi da ita tafi karfi na,Ahmad yayi Murmushi tare da da shafa gemunsa Yana wani rangaji ya furta Tsoho Bari na kaji idan tayi laifi Kawai ka kirani ka fada min har gida zanzo na kera maka ita,Baba yace na gode Dama ta ishe ni,ta gagareni,Aamna mamaki ya kamata,Tsawar data razana ta taji ance yafa rigar tsoho,jiki na Bari ta karba tare da yin Mayafi da ita,Tace wallahi sai na Rama Nima na iya tashancin,Baba yace kuce Mata ta taho mu tafi gida,da yatsa Ahmad ya nuna Mata Hanya ta juya salin alin tabi Baba suka tafi. Su Aamna suna tafiya wata Budurwa ta taho da gudu wajen Ahmad Tace Dan Allah kaga wani can Haka Kawai ya dameni da naci sai Maganar Batsa yake min nace bana sonsa yaki hakura Wai sai na bashi kaina ko yayi min fyade Dan yaga Kawai Ina tallan gyada tunaninsa Yar Iska ce Ni ta karasa da kuka,Ahmad Fuska a Murtuke yace Yana Ina guy din? Da yatsa ta nuna musu,Ahmad yace Boys kuje ku min maganinsa,ai kuwa Suka tafi Kamar an Aiko su Suka hau jibgarsa,sai da suka Masa ligi ligi sannan Ahmad ya karasa wajen tare da yarinyar,yace Kai Dan uwarka wannan kake so?Kai Dan Iska ne?zaka lalata Yar wasu Tace Bata sonka dole ne? Matashi Yana Nishi jikinsa duk jini Ahmad yace daga yau idan kaga wannan yarinyar hanyar da take idan kabi wallahi sai na yankaka,Matashin yace bazan sake ba,Zan gyara halayena,ayi Hakuri Oga,Ahmad ya Shure shi da kafa yace bace a Nan,ya tashi ya fece da gudu,Yace wa Yarinyar ki dinga saka Hijab idan Zaki talla,Tace to na gode yanlabai,ki daina talla ki Shiga makaranta ko kiyi aure,Tace to ai an kusa biki na Kuma Ina Islamuyya yace Good Ware ke ban son surutu,da sauri ta tafi tana murna. Tafiya sukayi sunyi nisa Suka samu wani yaro ya fisge Wayar wani a Hanya,Ashe Ahmad yaga abinda Yaron yayi ya arce,Sai da ya Bari Yaron yasha kwana sannan yabi bayansa,ya sauka a machine ya cafke Yaron a nutse ya dinga kashe Yaron da Mari yafi a irga tun Yana gani sai da Yaron ya sume,Wayar da Yaron ya fisge Ahmad ya karba tare da kwarawa Yaron ruwa ya farfado yace Kai barawo ko Nan take ya Kira police Suka Yi gaba da Yaron shi Kuma ya maidawa Babban mutumin da aka satar Masa,mutumin ya dinga godiya,yace yaro daga an kirani na dakko waya Kawai naji ya fisge,Ahmad Bai kulashi ba ya wuce gidansa Kawai su Mashkoor suka rufa Masa baya. Tunda suke tafiya Aamna kuka takeyi jikinta duk rauni,Baba yace kece dai kika jawo Kuma kin San Halina wallahi Sai in Miki jina jina,Aamna taci gaba da kukanta tana tafiya,Baba yace Jeki ki Siyo kayan Miya da Salat ki Shiga da shi gida,Aamna Tace bani kudin tana kuka,yace a aljihunki Ni Ina da kudi ne an fada Miki,Nima yau bazan ciyar da kowa ba wallahi tunda aka Dake Ni ta furta tana shesheka,Zan tsine Miki wallahi Aamna Naga kin rainani,Aamna tayi banza da mahaifinta,kwafa Yaja ya juya ya tafiyarsa inda zai je yace yunwa ta kashe ku, Zaki sani Zan dawo gidan ne,Aamna tayi tafiyarta da rigarta a kanta har Gaban me kayan miyar kusa da gidansu tana goge Hawaye tana sheshekar kuka Tace Dan...tala....Dantala... ba....bani kayan Miya na dari hudu.....Salat na na ... Naira dariiiiiiiiiiiii......sai ta karasa da sakin Kuka me karfi a Gaban Dantala,Dantala ya saba da halin Aamna yasan Kuma yanda dama suke fada da Babanta,Yace kiyi Hakuri,ita rayuwa ko da wa zaka zauna sai kayi Hakuri Aamna,da girmanki da shekarunki haba Haba,Aamna ta sake fashewa da kuka Tace Wal....wallahi....wallahi tallahi yau bazan ci abinci ba da yunwa Zan kwana,Kuma na rantse bazan Taya Mama Aiki ba,Dantala Ina da zuciya,Kawai duk an bi an tsaneni akan ban samu Miji ba,a kauyen mu kowa sai ya fada min bakar magana bana Iya Shiga cikin dangi na sakata na Wala,Haka a gida ace Iyaye sun tsaneka,Dantala yayi Dariya yace sai hakuri Aamna,Tace wallahi Watarana za a ga na mutu a tsinci gawata Kawai,kiyi Hakuri cewar Dan tala ya zuba Mata kayan Miya ta bashi kudin ta tafi gida. Tana yin Sallama Mama ko kallonta Bata Yi ba,kayan miyar ta Ajiye zata juya Mama ta rike Hannunta caraf,Tace wa kike wa raini Wai? Waye sa'anki a gidan Nan Dan Kan uwarki,Aamna tayi Mukus Mama ta shiga zuba Mata Rankwashi ba adadi sannan ta saketa Tace tashi ko na nayi ball da ke, Aamna ta Mike ta fada daki tare da sake fashewa da kuka,Ita kuwa Mama girkinta ta shirya shinkafa da Miya da salat. Wato Islamiyyar Asabar da lahadin ma kin daina zuwa ko Aamna cewar Mama,Aamna Dake kwance a katifa ta fito Fuska a kumbure Tace na girmi Islamiyya Ni,Duk abinda ya kamata na sani na sani na addini sabo da Haka zanci gaba da saurarar wa'azi Kawai a gidan Radio ya isheni zaman duniya,a kyale Ni inji da matsalata,Ni yanzu ba karatu ne a gaba na ba,Alhadisissani,salisu duk na Iya ya ishe Ni,Sira da Ishmawi na haddace quarter,Zikiri na iya,Qurani saura Izu goma nayi sauka to me Kuma zanyi,gishirin zaman duniya na sani ya ishe Ni,Mama ta rike Baki Tace tab ke Baki ji kunya ba 25yrs Baki sauka ba,to ai da a sauke ba a Aiki da shi gwara ka samu Izu goma kayi Aiki da shi,Bulala Mama ta dakko Aamna ta jawo kujera ta zauna daram Tace a tafke Ni ai na Saba,kamata kullum a Duke Ni to a Dake Ni,Mama kuwa itama akwai zuciya Nan ta dinga tsulawa Aamna Bulala iya karfinta,har ta Gama Aamna ko motsi Bata Yi ba ta tashi a nutse ta shige dakinta,Haka Baba da dare bala'i yakeyi Kamar me,Ita kuwa Aamna washe gari sai da taje chemist aka Bata magunguna,tana dawowa ta Hado kayan sawarta a Akwati ta fito sanye da Hijab Tace Zan bar muku gidanku gwara na shiga duniya. Baba ko a jikinsa yace a gaisar da Yan bariki maza Kar dare yayi a dawo lafiya,Mama ta tabe Baki Tace sakarai,Aamna tana ta jira a lallashe ta ko ace Kar ta tafi Amma taji Shuru,Tace Zan tafi fa bazan dawo ba,Baba yace to,Duniya fa Zan shiga Mama,Mama Tace madalla,Juyawa Aamna tayi ta fara tafiya ba Wanda ya kulata har taje bakin kofa,Tace baza ku kirani ba Wai? Tsaki Baba ya ja,Aamna tayi waje kenan taga wata dalleliyar mota me tsada,Wata Dattijuwa ce ta fito a motar,da wani Dattijo shima fari ya fito,Aamna taji an kirata,Matar ta kalla sai taga Mummyn Ahmad ce cikin shiga ta Alfarma,Aamna fara'arta ta karu har kasa ta zube tare da Gaida su,Mummy Tace ga Baban Ahmad,Aamna ta sake Gaida shi tare da rike Hannun Mummy Suka Shiga gidan. Baba da Mama sunga masu kudi Nan Suka rude,Baba yace laaaaaa Alhaji Ja'afar Kaine a gidan Nawa? Wanda aka Kira da Alhaji Ja'afar yace ikon Allah Malam Hussaini Umar dama a Nan kake yanzu? Baba yace ae wallahi,me ya kawo ku?Aamna dai da Mummy suna mamaki aka shimfida musu Tabarma,Aamna ta kawo musu pure water da lemo,Nan ta ebo musu shinkafa da Miya da salat ta Ajiye,Tace Baba kasan su ne? Baba yace kwarai kuwa zauna kiji labari. Labari AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 16-20 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne MAMAN SAMHA ZAINAB SABO BK UMMEEN SADEEQ BASMAM GLAM ALHUSNA(MRS IDRIS) Ni Hussaini Umar kamar yanda kika sani mu Uku Mahaifiyar Hajiya Maryam ta haifa,Kuma mu kadai ne a wajen Mahaifinmu Malam Umaru,Ni Yan biyu aka haife mu Ni Hussaini da Hassan,Hassan tun Muna jarirai Allah ya Masa Rasuwa sai Ni,daga Ni aka Haifo Kawunki Isma'il sai Kanwar mu Kursum wacce kika Sani a kauyenmu Sokoto take aure,Munyi karatun Muhammadiyya har muka girma Noma da kiwo muka gado, tun baya dama mu Bamu taso a cikin kudi ba sai rufin asiri,sai da muka girma lokacin aka hadani aure da Aishatu Yar Uwa ce itama auren zumunci ne,daga Nan Bamu samu Haihuwa ba har Ismail yayi Aure shima a can kauye,sai da ya haifi Yara uku sannan aka yiwa Kursum Aure a kauyenmu itama ta Haihu Daya,duk Ni Allah Bai bani Haihuwa ba har Iyayenmu Suka rasu sai Yan Uwa da dangi,wannan da kike gani Shine Alhaji Ja'afar Wanda shima a Sokoto na sanshi Amma Asalinsu Yan Yemen ne kasashen Larabawa,kasuwanci ya kawo su Nigeria Sokoto suna da company Wanda a lokacin suna da Company na Yogourt da Kuma kamfanin Dake sarrafa Fulawa,sabo da Haka suna bi kauyuka suna siyen madarar shanu da Alkama Wanda a lokacin sana'ar mu kenan a wajen mu suke siya,mun Saba sosai muna mutunci da Alhaji Ja'afar lokacin ya Dade da Auren Mummy har da yaronsu Ahmad Yana shekara bakwai lokacin,su dama masu kudi ne da danginsu duk suna zuwa,ita Mum Yar Sokoto ce,bafulatana ce ya ganta ya aure ta sabo da sonta da yake Yi,Tun Bai Jin hausa har ya koya ya Zama Kamar bahaushe shima ga matarsa bahausa,Tunda yayi Aure ya dawo Nigeria gaba Daya da Zama Amma yanayin Lagos ya fiye Masa Dadi shi yasa yayi gida a can komai nasu a can,Ni Kuma mun Saba mun Shaku,Ja'afar yana tausaya min rashin haihuwa,lokacin akwai wata Yar Uwarsa Hajiya Sumayya,Sumayya marainiya ce gaba da baya sai Dangi Su Ja'afar kenan, Danginsa ce Amma Iyayenta sun rasu,a cikin Dangin Summayya Ja'afar shi ya taho da ita Nigeria ta Dan zauna a Wajensa na Dan watanni, a Nan ta samu wani Wanda shi a Nan Nigeria yake shima Kuma a Sokoto Amma shima asalinsa Dan Sudan ne,ganin balarabiya fara sai ya zauce sabo shi Yana da duhu ma bakin Balarabe ne,aka hada su Aure da Sumayya,Dan Sudan dai yayi Aure Bayan shekara Uku Sumayya ta Haifi Yarta mace kyakyawar gaske aka sa mata suna Aamna,Idan baza ki manta ba Aamna Ina zuwa dake wani gidan Yan Sudan a Cikin garin Sokoto birni,duk Hutu Ina kaiki wajen wasu Dattijai,Aamna Tace ae,Baba yace to kakanninki ne na wajen Uba Aamna,Wannan Ja'afar da kike gani Shine Dangin mahaifiyarki Sumayya wacce ta Dade da rasuwa,Katsam Bayan ta haife ki da shekara Biyu Babanki Rahil menk ya gudu ya bar kasar,aka Neme shi aka rasa,sabo da taurin Kaine da shi,bashi da tausayi, Jaafar ya Shiga Bincike Ashe karya yayi ya auri Sumayya matansa Uku a Sudan da yaransa manya,Ashe Auren sha'awa yayi ya gudu ya barta,lokacin Jaafar ya bani Amana Kan na kula da Sumayya,Muna Haka ciwon Hawan jini ya kamata daga Nan sai ta kamu da ciwon sugar Bata Dade ba sai ta rasu,Ja'afar yayi kuka dangi suka zo suka tafi da gawar mamanki aka binne ta a can kasar su,ke Kuma kina Yar shekara Biyu Ja'afar yace tunda bani da Yara Allah Bai bani ba Kawai na dauke ki ya bani ke halak na kula da ke. Ni da Aishatu munyi murna muka dinga kula dake sosai sabo da Alkawarin Dana dauka shi yasa kika ga na barki kinyi har HND na dage na biya Miki sabo da bana so kiyi kukan Rashi,sannan takurar Aure da kika ga mun dage sai mun Aurar dake muna gudun kar wata masifar ta afka Miki ya Zama kin lalace a Hannun mu,shi yasa muke so mu rabu lafiya,Aamna Hawaye ya shararo Mata Tace Amma Baba ita Zuhra fa Kuma me yasa kuka fifita a kaina? Baba yace Zuhra Bayan kin shekara Hudu a Hannun mu Allah ya bawa matata ciki ta Haifo min Zuhra,kin San zuciya da Kuma son Kai da son da na daban ne,wallahi bazan boye Miki ba,muna haifar Zuhra gaba Daya Muka ji tafi shiga ranmu,a Haka ma kokari mukeyi muna danne zuciyarmu Dan kar ace kin lalace a Hannun mu Amma har ga Allah Aamna munfi son Zuhra da ke,shi yasa Baba Ni ka Bari nayi school Wato na lalace ita Zuhra iya secondary tayi aure,sannan har Sweety Zuhra kake ce Mata fa. Mama Tace ae ai munyi kokari ma duk abinda kike Mana ke rike kin ma ai munyi kokari bazan ji tsoron ki ba,Aamna Tace tunda na taso nasan Kuna duka na ku hantare Ni Ashe duk fakewa kukeyi da naki aure Ashe dama tsana ce?Mama Tace ke dalla fitsararriya lokacin da Danginki suka Yi watsi da ke shi Kansa Alhaji Ja'afar din gashi Nan ya sake zuwa ko duba ki,in Banda Dangin Babanki da muke kaiki kaf Dangin Uwarki ba Wanda ya sanki domin tunda Ja'afar ya Bamu ke ya tafi sai labari muka samu sun bar kasar ba a San Ina suke ba,sai dai Hana rantsuwa Muna Jin sunansa a Radio Yana tallafi iri iri a kasar nan. Alhaji Ja'afar dattijon kirki me Kamala yace Bari Nima nayi magana,lokacin Dana Baku Aamna yarda da aminci tare da tausayawa yasa na Baku ita Amana,ku kanku Kun San Ina da arzikin rike ta,Kuma Dana Baku ita sai Dana Baku makudan kudade Wanda Aamna zatayi karatu har matsayin Degree,Kuma Ni bazan ce ba kuyi kokari ba koma Mene kunyi kokari Kuma mun gode Allah ya saka,Amma Kun San dai Aamna na bada gudunmuwa na kudin daukan nauyinta,Baba yace kwarai muma min Sha wahala da ita,Bata da kunya Bata da tarbiyya gata Nan,Aamna Tace ai tarbiyyar kuce Ni Kuma wallahi Ina da tarbiyya, Haka tunda na taso nayi wayo nasan Kuna nuna banbanci tsakanin Ni da Zuhra,Ni za ayi ta dukana har girma na,Ja'afar ne yayi murmushi yace ya Isa Haka,ke Aamna Har abada Iyayenki ne ban son sakarci,Mummy Tace ikon Allah Ashe Aamna ce Yar Sumayya shi yasa na rasa Ina na santa mashaallah,Ja'afar yace lokacin da Muka Baku Aamna bayan mun koma lagos Arziki na ya bunkasa,daga Nan Kuma Mummy ta Haifo Kanin Ahmad Saddeeq,na tattara Muka koma Colombia da rayuwa,a Nan aka haifar min Auta Humaira Wanda Candy zata Yi kwana Nan,Haka Saddeeq shi nutsatse ne yayi aure da matarsa harda yarsa,Zaman da Muka Yi a Colombia shi ya jawo Babban Dana Ahmad ya lalace da shaye shaye,na rasa yanda zanyi da shi wallahi,mun rasa ya zamuyi ya shiryu,abin ya dame mu,Alhaji Ja'afar ya nisa tare da cewa yaki aure bare yayi wani Aiki Sai dai kashe kudi ya sani Kawai da shaye shaye. Baba yace tab Ahmad din?Aamna Tace Baba shine fa Wanda ya mare Ni ranar Nan da ka bini Titi zaka Duke Ni ka tuna,Wanda ka karbi number dinsa Wai zai koya min tarbiyya? Baba ya daura hannaye a Kai yace lailahaillallahu wannan kwallon shegen Yaron Dan giya? Ai yayi suna kaf gari an San da zamansu,sai dai Kuma Yana da Dan Hali me kyau ta wani bangaren,Daddy ya kwashe duk abinda Ahmad keyi ya fada musu yace wani abin ma Sai Kun gani da idonku wallahi na rasa yanda zanyi,Ashe Aamna ke kika Yi Jinyar Mummy? Dariya Aamna tayi Tace ae Daddy,Baba yace ja'ira Ashe ma Dan uwanki ne,Baba ya kalli Daddy yace game da matsalar Danka Ahmad Kawai a bashi Auren Yar Uwarsa Aamna a daura musu Aure ku Kai wa shege ita gidansa,Ni Kuma nasan Aamna itama irinsa ce Dan ba mutuncin gareta ba suje can suyi ta fadansu har a samu ko Allah zai shiriyarsu sabo da itama Aamna ba wata ta kirki bace Tace ta daina Zama ta gari,Nan take Daddy yace Kuma fa Haka ne Ahmad Yana bukatar jajirtacciyar mace marar tsoro,Mummy Tace hmm ai Ni Naga Drama a Hospital suka dinga fada da juna ba Wanda ke barin wani idan Haka ta faru zanfi kowa murna,Aamna kuwa Hankalinta ya tashi matuka sabo da tasan ma Ahmad kashe ta Kawai zai yi,Kuka ta saki Tace yanzu Dan shaye shaye za a bani? Sabo da anga Uwata ta mutu ubana ya gudu ya barni shine za a min Haka,Mama Baki Bude Tace Aamna mene Haka? Dan Uwanki ne fa,ai Hannunka baya rubewa ka yanke ya Yar, yo tun yaushe da azaba ta ishi mutum Nawa aka Yi Hannu da kafa mutum da Kansa zai kai Kansa Asibiti yace wayyo Allah Likita yanke min na huta cewar Aamna,Mummy Hannun Aamna ta riko tare da mikewa ta ja Aamna gefe tana Mata magana a kunne cikin Rada,Aamna ta washe Baki Tace to na yarda. Baba ya tabe Baki yace Alhmdllh Allah ya yanke Mana zaman Yahudanci,Daddy kuwa Dariya yayi kawai sannan yace akwai wani gidana Babba ne Dana Gina a Nan Kaduna ba nisa da Nan Unguwar Taku na mallaka maka shi halak malak,sannan Zan baka Million Uku ka ja jari,Baba Hanci ya rike kamar mace ya rangada Guda Ayyiriririri....,Dariya Aka dinga yi,Ranar dai sai da suka Gama shirya komai Har dangi an Kira a waya cewar Nan da sati Daya za a daurawa Aamna Aure, kowa yayi mamaki,ikon Allah Wato aure idan yazo wani shi kanshi a shekarar Bai San zaiyi auren ba,Aamna dai ko a jikinta sabo da sun Gama shirya sirrinsu da Mummy ba Wanda ya sani,Gidan da aka bawa Baba Suka tafi har furniture an zuba a gidan, flat madaidaici me dauke da part biyu,ko Ina yasha tiles ga flowers da komai,gidan a kalla zaici mota Hudu a ciki iya wurin parking,Aamna da Mama sai Murna,ranar Abba ya bada kudin auren Ahmad dubu dari biyu Suka tafi cike da murna,Zuhra Suka sanarwa komai murna Kamar me Ita kanta Zuhra dama ta Dade da sanin basu da Alaka da Aamna ko a kamanni Aamna da Larabawa take Kama,Ita kuwa Zuhra Ana ganinta anga Yar Mama da Baba,Yan Uwa da abokan azirki Suka dinga zuwa ganin sabon gidan su Baba,Aamna a waya ta Kira Kawarta Siyama ta fada Mata komai,ai Siyama Murna Kamar tayi hauka ga Kuma mamaki Aamna ba Yar su Baba bace Ashe Shuru akayi,Amma duk da Haka Aamna ta Sha Jin zancen a Kauye,idan ta tambayi Mama ko Baba sai suce karyar mutane ce,,Aamna zata ma riga siyama Auren ma Ashe,Washe gari tare da Siyama aka maida kayan su Aamna na bukata sabon gidansu,Faisal saurayinta shine ya dinga jigila da motarsa har Suka tare,Baba Kuwa Ya samu ya fara Harkar Sana'arsa ta siyar da kayan masarufi jari ya samu. Tunda an San Auren da za ayi ba Wani shiri aka Yi ba,Saura kwana biyu daurin Aure Mummy,Daddy,Mufida matar Saddeeq da Yarta,sai Humaira Auta da Sadeeq Suka taho Kaduna gaba Daya a gidan Ahmad Suka sauka,Yana ta Fushi shi fa an takura Masa da zuwa Masa gida,Bai San Aurensa za ayi ba. Ranar cikin dare Mummy ta haura sama Bedroom dinsa, Yana kwance Yana latsa wayarsa me tsada ga barasarsa a gefe Yana korawa,Mummy ta kalle shi tare da Zama saman Bed din,Yana ganinta cike da shagwaba ya dawo da Kansa saman cinyarta,Yana kallon Fuskarta Idonsa sai wani lumshewa sukeyi sunji kayan maye,Wata kwaya ya dakko a kasan Pillow ya watsa a cikin kwalabar giyar ya jijjiga,Nan take kwayar ta narke a ciki Yace Mummy Dan Sha kiji Zaki samu nutsuwa yanda na ganki nasan akwai damuwa,Murmushi Mummy tayi Tace please ban son hauka Ahmad,Ni zaka kalla ka Bawa kayan Maye?Dariya yayi yace to Mene ciki Dan kin Dan caake kema,Tsaki ta ja,Tace Magana nake so muyi,Ahmad yace Ina jinki Beautiful Mum,Harara ta watsa Masa Tace gobe ka shirya zamuje gidan Wasu Yan Uwan mu a gaisa,Nazo maka da manyan Kaya su zaka sa muje kaji?Baki ya turo yace kin San dai Ni bana gaisar da mutane,idan so kike kiji kunya Kuma to kije Dani Dan wallahi babu Wanda ya Isa nace Ina kwana ko Ina Yini bani da wannan lokacin,Mum Tace ae naji muje Haka,Yace sannan Kuma zanje da Giyata ne kin San bana Free karki ce ban fada Miki ba. Mummy ta jinjina Kai Tace Ahmad me yasa baka da tarbiyya da biyayya ne Haka? Ina mahaifiyarka duk abinda kaga dama fada min kakeyi,Baki ya tabe yace kin San dai bana karya gwara na fada Miki gaskiya,Kansa ta zame Dake kwance a cinyarta da sauri ya rike Mum yace please Mum zauna ki Sosa min Kai nayi bacci,sai kayi aure idan Haka kake so ai, Dariyar Yan giya ya shiga Yi ba ji ba gani yace Aure....Tab ai kuwa sai dai a dauki gawar matar,Mummy ta tsorata Tace Idan Muka daura maka fa Auren da ita sai me? Yace kisa ne hukuncinta,kasheta zanyi,Ni na tsani mata bare wani Aure Dan Allah Jeki Good Night ya furta, Tsaki taja Tace wannan Drugs din da kake Sha sune suke kashe maka sha'awar Mata fa,zaka yiwa kanka Illa,Murmushi yayi yace ai gwara Haka akan nayi Zina,Tsaki ta jasannan tayi ficewarta. Washe gari da Yamma Mummy ta kulle Ahmad a bedroom ta hanashi fita,Yana ta dukan kofa a bude shi Amma Mum Taki,yace aski zanyi fa yanzu I promise you wallahi Zan biki muje can,Sai lokacin Mummy ta Bude shi ya Sha ya bugu Yana tangadi ya fito ya fice,Machine ya Haye sai wurin Aski,Ai wani gashi Attach ya Siya Red and green yace ayi Masa calaba kitso me kyau,Gefe da gefe an kwashe gashin kadan,daga sama Kuma gashi Nan da yawa,Ai kuwa aka Masa calaba me Dan tsayi Suka zubo a kafada kadan,gemunsa ma Haka aka Masa Yar karamar calaba daga tsakiya da red attach,Kyawun da yayi ba a magana ka rantse daga England ya dawo,Kowa ya kalle shi zai rantse wani mugun arnen bature ne ba musulmi ba,Amma Fadin irin kyan da yayi Bata Baki ne sai dai ba tarbiyya idan an gani,duk inda ya gifta da machine sai Kallonsa akeyi,Mum suna Palo Suka ga ya dawo,Su kansu sunga kyan da yayi Amma Kuma bana Tarbiyya bane,Mummy tasan Halinsa Tace Kayi kyau,yace naga gidan da zamuje kin dauke shi da muhimmanci shi yasa nayi gyara na musamman. Sadeeq ya tabe Baki yace Amma ba tarbiyya ba,Zan ci Uwarka yayi Kansa Mummy ta rike shi,Mufida Tace Kayi kyau,yace yawwa matar mu,Humaira ma Tace Yaya Allah ya bani Miji me irin kyanka,Hannu ya Mika Mata Suka tafa yace Ameen,Ai Ni Handsome King ne,Daddy ya tabe Baki yace Kai dalla sakarai je ka shirya mu wuce, Ahmad Daddy yayiwa wani kallo ya Haura samansa Yana cewa azo gidan mutum a Dame shi,Gidanka ne Dan Ubanka gida na kace gidanka cewar Daddy shima,Mummy Tace Dan Allah karka jawo ya fasa zuwa ta bi bayan Ahmad tana lallashinsa Kar ya biyewa Daddy. Toilet ya Shiga tare da banko Kofar kamar zai ballata,Wanka ya sheka ya fito,Mummy tana gefen bed,ya shafa lotion ,Fuska ya Bata yace Mummy Zan cire Towel ki fita,Mummy tayi Dariya Tace to Babban mutum,Sai da ya Gama kalailaitarsa sannan ya kwalawa Mummy Kira,ta shigo da sauri da wata Arniyar farar Shadda me tsadar gaske Gezna,Harda Hula yace ohhhhh.....wannan Zan saka?....na shiga Uku wayyoooo ya Furta Yana zaga dakin kamar zai saka wuta a jikinsa. Ohhhh Mum....Mummy... Mummy....Mummy yake furtawa Yana zagata a dakin,Tace Ahmad Ni din ko? Fuska ya Bata yace na fasa zuwa akan na saka wannan kayan,Tace Dan Ni fa zaka saka,Ohhhhh.....ya sake furtawa Yana girgiza kafadunsa kamar Yaron yaye, Dariya Mummy tayi tare da fisgo Hannunsa ya zille Yana ta Bata wahala sai da kyar ya tsaya ya saka Boxers Kamar zaiyi Ihu Haka ya saka wandon Shaddar wani dai dai shi cif kamar an gwada dinkin zamani fitted na matasa,Singlet Mummy ta bashi ya saka sannan ya saka Rigar Shaddar me Hannu dogo links cif cif shi,ba karamin Arnen kyau yayi ba,Hula kuwa Mummy sai hakura tayi yace bazai saka ba,Haka ta barshi,tana kallo ya dakko farar sarkar Azurfa ta maza wata Yar siririya karama ya saka,Mummy Tace Kayi kyau kuwa Amma sai dai a hausawa ba tarbiyya bace,Yace Mum ku ai local ne Baku San wanka ba Sam,takalmi fari half shoe ya saka,wayarsa kuma Silver color,Glass Brown and white ya saka,Kowa ya kalli Ahmad yasan ba karya Allah yayi halitta a Nan,Mummy tana murna ta fesa Masa turaruka ya tsaya a gabanta yace ya kika gani,Babban yatsa ta daga Masa,Murmushi yayi Suka fito,Ai duka su Daddy sakin Baki Suka Yi suna kallon yanda yayi azabar kyau,Daddy farin ciki ya kamashi Allah sarki mahaifa,yace da ace Haka kake Yi duk da dai kitson da sarkar ba tarbiyyar hausawa bace ai da yafi sauki sauki, Sadeeq yace the Handsome King,Humaira Tace wow I'm proud of you Yaya King,Comfirm...Confirm ya Furta Yana wani basarwa yace Ina Mufida? Da sauri ta fito dauke da Yarta sun Sha gayu Suma,yace kinyi kyau matar mu, Sadeeq yace Kanin miji ne ke wannan wasan ba yayan Miji ba,Baki Ahmad ya tabe yace ku kuka San wani Kani da Yaya. Ko da aka zo shiga mota Ahmad yace Bayan anyi min gorin mota harda kwace motoci na a machine Dina zanzo,Daddy ne ya balbale shi da masifa Kai wanne irin banza ne Wai? Ana gabas kana Yamma dalla je ka shiga waccen motar,Ahmad yace wancan bakar Haba ai sai dai ku ku koma cikin bakar Ni da Mum mu Shiga fara ko na fasa tafiyar wallahi ku baku san wanka ba,Dole Haka Daddy ya kwashe sauran a Daya motar baka Sadeeq ya tuka su,Mummy kuwa suna fara ita da Ahmad sun hakimce a Bayan mota Driver Yaja Suka wuce sai sabon gidan su Aamna. Aamna kuwa dama Mummy ta sanar musu da zuwansu sabo da Haka ita da Siyama Suka shirya abinci iri iri sannan suka Yi wanka,Aamna ta shirya cikin wata sabuwar bakar Truskysh gown me adon Golden,tayi masifar kyau sai ta fito Kamar wata balarabiya,Baba ma Tasha shaddarsa,Mama tasa Atamfarta maroon,Siyama kuwa an zuba lace dark Green,Mama ce ta ja Aamna Bedroom ta zaro wata laya ta makale Mata a kanta cikin gashinta,Aamna Kamar tayi kuka Tace Mama har yau Kuna wannan shirkar ga ta Rannan a kaina kin hanani cirewa layu har biyu,Mama Tace ke dalla ta farin jini ce,Haka aka sawa Aamna dole ta yafa mayafinta Wanda ta Sha acuci,Wani guru Mama ta sake dakkowa tace lallai sai Aamna ta Daura a Hips dinta, Aamna zata Yi kuka Tace wallahi kin San naci kashinki da fitsari idan na tsine Miki sai ta Kamaki,Zan tsine Miki idan Baki daura ba,Aamna tana gani ta dage Riga har wandon ciki aka daura guru sannan ta maida kayan ta fito palonsu hadadde Kamar zata Yi kuka ta zauna tana Danna Yar Wayarta Vivo. Suna Haka Suka ji shigowar motoci,Aamna gabanta ya fadi,Siyama kuwa tuni ta leka ta window har Sanda Ahmad ya fito ta haukace gaba Daya tana lallai Aamna wallahi ku Larabawa ne da gaske gashi na gani,kalli danginki Kan uba kaga wani tantirin Dan Iska Amma duk yafi kowa kyau da iya wanka,Aamna ta Mike ta leka itama tace ai shine Angon,Siyama Tace Yau mun Shiga Uku kashinki ya bushe da gani Zaki ci Ubanki,Aamna Idonta ya kawo kwalla Tace wallah bazan taba sonsa ba,Dan giya ne,idan Kuma ya shiryu fa cewar Mama,Aamna Tace Idan ta dalili na ne sai na yarda Ina sonsa idan ya shiryu sai na gudu na barshi Kinga na taimaki Iyayensa,ko Dan Iyayensa Zanyi sabo da yanda suke mutanen kirki masu taimakon musulmai Bai ci ace suna da Dansu irin wannan ba,Siyama Tace bafa a Wasa da so,karki Bari ya kamu da sonki kice Zaki Wasa da zuciyarsa idan ya Gane ba sonsa Zaki ba kin Gama yawo,na Baki shawara idan Zaki so abinki ki soshi karki ce ban fada Miki ba Aamna ba a Wasa da zuciyar mutum a so,Aamna Baki ta tabe Tace wannan Zan so? Zan dai je da yanda Mukayi magana da Mum,ba ruwanku. Sallama sukayi aka amsa kowa ya shigo a nutse,Baba Yana musu Sannu da zuwa,Nan da Nan Su Siyama suka cika gabansu da Abinci sai lokacin Ahmad ya shigo ya tsaya Yana waya a waje,Ganin Aamna ya bashi mamaki yace Kai keeee......Aamna ma Tace kaiiiii......Ran Ahmad ya baci yace Wai Mum dama gidan wannan zamu wani zo? Daddy yace zauna Malam,Ahmad yace Ni bazan zauna ba Ku Gama mu tafi Ina da abin Yi,Siyama Tace tab a ranta,Zuhra ce ta shigo Amarya taci gayu Adam ya sauke ta,Itama gaisawa akayi ta zauna,Ahmad fafur kin Zama yayi ya zuba Hannu biyu a Aljihu ya tsaya kerere Kuma ba Wanda ya gaisar ko kallon arziki Bai musu ba,Baba shi Kam murna yakeyi Aamna ta samu Miji sai ya kalli Ahmad yace Sannu Sarkin matasa,na baka Sarautar Sarkin matasan Nigeria,Ahmad wani murmushi ya saki ba shiri,Aamna ta wani washe Baki itama ganin irin kyan da yayi,a Haka Daddy ya bada tarihin Aamna da dangantakarsu da Ita,Tsaki Ahmad ya ja tare da zaro Yar karamar kwalabar giyarsa a Aljihu ya kwararawa makoshinsa,Aamna ya kalla ya galla Mata Harara tare da cewa daina kallo na,Tace na kalleka din Kai da wanne idon ka kalleni,ransa ya sake tunzura ya kwada Mata Mari a saitin Idonta Nan take ta durkushe ta saki kuka,Da sauri taro ya watse aka dauki Aamna zuwa Asibiti,shi kuwa Ahmad a waya ya Kira Mashkoor ya dauke shi a machine suka Yi tafiyarsu. Daddy kamar bakin ciki ya kashe shi ransa ya baci ganin yanda aka mannewa Aamna Ido Daya da auduga da plasta Kuma akace Nan gaba sai an Mata aikin Ido,Tunda suka koma gida Basu ga Ahmad ba har kwana biyu ta cika Wanda itace Ranar daurin Aurensa Bai Sani ba. Mummy a waya ta Kira Ahmad ta sanar Masa da Aurensa,ya zaci Wasa ne ya dinga dariya yace Mummy kina da abin Dariya to idan hakane a daura Auren na Amince, Mummy tayi Dariya Tace ka yarda kace? Yace Yeah..Yana dariya Wai Wasa ne, Daddy kuwa ya tattara mutanensa Dana Baba a masallacin Unguwar har Mashkoor ya sa aka Nemo su duka sabo da Suma su Zama Shedu,Ahmad Yana can gidan Mashkoor Yana ta sheka bacci, Ranar Juma'a Ana Idar da Sallar Juma'a da Shedu walliyan Amarya da wakilin Ango suka karbi Aure Nan aka Daura Auren Aamna Rahil Menk da Ahmad Ja'afar Yabalash, Kan sadaki dubu dari,Su Mummy lefe suka yiwa Aamna na gaske Akwati goma Sha biyar,Ahmad ranar ya dawo gida sai gani yayi su Baba duk sun Hada kayansu zasu tafi ba Wanda ya kulashi,Mummy ce ta shigo Bayanta Aamna Amarya ce sanye cikin wani material Brown yasha kyau,idon Aamna Daya yasha plasta a manne da Daya take gani,Yana ganin Aamna ya Mike yace me wannan takeyi a Nan Mum?Mummy ta Bata Rai matuka Tace matarka ce Ahmad,Daddy ya shigo yace yau Shedu sun sheda an daura maka Aure da Aamna Yar uwarka Kuma marainiya sannan da Amincewar aka daura, ta Zama Amana a wajenka,ka sani Aure ba Wasa bane,idan kayi shirme Allah bazai Barka ba,Kuma wallahi ka koreta ko ka Mata Illa ban yafe maka ba Ahmad. Mummy Tace gata Nan wallahi kaji bazan rantse a banza ba babu Wasa yau aka Daura muku Aure shi yasa nace Rannan ka bimu muje na kaika ne Dan kaga surukanka,Nima kaji na rantse Idan ka koreta ko kayi gigin sakinta bani ba Kai ban yafe maka ba,Kuma Matukar ka saketa Allah ya Isa Nono na daka Sha,sabo da Haka gata Nan Amana da kayanta,Nan Ahmad yaga me Gadi Yana ta shigowa da kayan lefe Yana kaiwa sama Daya dakin da ba kowa Wanda Mummy ta zabawa Aamna a matsayin nata,duk abin bukatar Aamna an kawo Mata abinta,daga Nan Mummy Tace Mashkoor ku shigo,Suka shigo suna tangadi,Mummy ta kalle su Tace gwara da kuka zo yau nasan ku shaida ne a gabanku aka Daura Auren Ahmad sabo da Daddy da Kansa ya gayyace ku Kuma Kun gani,Mashkoor yace kwarai King a gabanmu aka Daura muna ta so mu fada maka Amma wayarka Taki Shiga gaskiya ba a kyauta Mana ba,anci Amanarka King a gabanmu muna gani aka Daura Sadaki dubu Dari Daddy ya bada cewar Jibson. Bash yace Kuma Daddy yace kayi aure yanzu mu rage zuwar maka gida wannan fa ba Adalci bane King,Ahmad da yayi mutuwar tsaye yace shima cikin kwaya me yasa Baku Hana an daura Auren ba,me yasa Baku rotsewa liman Kansa ba,Daddy ya kawo securities ko Ina King,Ahmad yace Good za aga abinda ba a so kuwa,Mummy Tace kaji dai gargadi Kai ka sani,ta kalli su Mashkoor tace lalatattun banza ku fita muje marasa tarbiyya,Haka Suka fito ransu a bace,Ahmad Yana kwalawa Mummy Kira kizo Mummy ki tafi da Yar mutane,Zan Mata Illa,Zan kashe ta ne,kizo ki tafi da ita,Mum....Mummyyy.....Ahmad ya dafe Kansa kwaya ta motsa Nan ya Shiga hauka da tangal tangal a palon,Aamna tana kallonsa a ranta Tace kaddara ta hau kaina na shiga Uku,me yasa na yarda aka Daura Auren,Wayar Hannunsa ya tarwatsa da kasa,Wandonsa Kamar zai Fado zabar Ass down na iya shege,Ya kalli Aamna yace ke bi Mummy ki tafi kafin na kashe ki yanzu,Aamna Tace wace zata bi Mummy? Ai wallahi Zama daram sai dai mu mutu tare,Zan Miki Illa fa,Illa ai ka rigada kayi min ita tunda ka nakasa Ni ka maida Ni me Ido Daya,waye zai aure Ni a Haka,ai Ina Nan a matarka Zama daram wallahi yaro baka Isa ba kayi kadan Aamna ta Furta da karaji tana dukan Table,yace ke Ni Zaki nunawa hauka,Kai din wa Kai din me,me ka Isa kayi,Ai ransa ya Gama baci ya bita da gudu Suka tafi tare,ta haura Sama da gudu zuwa dakinta tana shiga ya damko gashinta,Tace wallahi ai dambe ne Nima na Iya Suka rukuma kokawa. Kici kici suna Nishi Kamar zakaru,ya dauketa ya makata a saman Bed,ya bita zai jibgeta ta samu tare da makalkale shi ta cikwikwiye shi,Taki bashi damar dukanta,gata da karfi itama Suka dinga kokawa Baji ba gani,sai da suka gajiyar da kansu sannan ya saketa ya dawo Palo ya zauna a kujera Yana maida numfashi kamar Wanda yayi tsere Itama palon ta dawo gashinta ya watse ta zauna tana Nishi itama taji jiki. Yana Nishi yace kin gaji kenan?,Tace na gaji a Ina ai ban gaji ba sai dai mu mutu wallahi,yace to Bari na huta na samo power kiga yanda zanyi da ke,Aamna Tace Nima Bari tawa power din ta dawo ka gani idan Zan kyaleka. AsmaBaffa 10/26/21, 8:51 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 21-25 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER TA 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER 08033933642 Official By AsmaBaffa Page naku ne BESTYNBEELAT UMMU LATEEPHA M BELLO SA'ADATU TIJJANI UMMI DEEJAT NAFEESAT UMAR MUHAMMAD. Yana Nishi a ransa yace shegiya karfi ne da ita,Aamna kuwa mikewa tayi Tace Bari muje mu gaida Ubangiji wani kuwa sai dai su gaisa da barasa,a fusace ya Mike sai ta zura da gudu tare da fadawa dakinta ta saka key,Yana huci yace Zaki sani wallahi sai dai idan baza ki fito ba Useless kawai,Key din machine dinsa ya dauka tare da ficewa ya bar gidan gaba Daya,Ita kuwa Aamna wanka tayi tare da Gabatar da Sallar Magriba,tana zaune tana Azkhar har lokacin Sallar Isha yayi ta Gabatar sannan ta Mike tare Shiryawa cikin wasu kayan baccinta doguwar Riga ce red me sililin Hannu ta wuce gwiwa sosai ta Mata kyau,Kayanta ta Shiga Shiryawa sai da ta tsara komai fes sannan ta kwanta saman gadonta yunwa kamar zata mutu,Kitchen dole ta fito ta Nema Amma wayam babu ko Lipton a ciki bare wani Abu na dafawa,Kugu ta rike Tace Kan bala'i Bari ya shigo,Zama tayi tana jiransa Aamna Bata San shi sai safiya ko tsakar dare yake shigowa ba,Yana can Yana shaye shayensa. Bangaren Ahmad kuwa tunda ya fita wajen su Mashkoor ya je Suka zauna Yana cewa Mummy Wai kamata Ni za ayiwa auren dole, aure ban sani ba, Mashkoor da maye Yana karkace Baki yace Mum sunyi fuck up fa,Muguntar Daddy ce Kawai cewar Ahmad,Bash yace karka kyaleta kaci uban Yarinyar ai wallahi zata gani ko mu ka Bawa dama sai munyi maganinta,Ahmad yace Guys the things is Mummy tsinuwa tayi min akanta fa,Yar Iska Wai Dazu Dani zata Yi kokawa,Jibson Yana zuka hayaki yace Eyyyeeee.....hey this girl get heart woooo....but show her you are our king,Sweet Boy just Sample the Beb,Ahmad ya kalle su, su Biyar suna ta korawa ya daga zundumemiyar kwalaba ya kurba yace gata da karfi har Elbow fa tayi min a kirji,La'ilaaaaah....cewar Mashkoor Yana dafe Kai yace aci mamanta Guys,Ahmad cike da Takaici yace Hmmmm me....me...me....Mum tayiwa haka,a bani Auren wata Ina Zan Kai wannan nauyin Kai wallahi ma dole ta karba,she must Collect...am....wayarsa ya zaro ya Shiga Kiran Mummy dinsa,Mummy lokacin tuni suna Lagos ma,ta daga Wayar tace Ya akayi Ango,Kamar zaiyi kuka yace Mummy kizo ki dauke wannan Ajiyar Taki Zan fa Iya kashe ta,Zan kashe ta ne Mum,karfa ki sa nayi mummunan laifi tam,Tsaki Mummy tayi tare da kashe wayar Baki daya. Mikewa yayi Zumbur yace akan wannan trash din Mummy ta juya min baya,dole naci uban Yarinyar Nan,Zaga wajen ya Shiga yi,Ya dauki kwalabar Giya ya tarwatsa ta,kujerar da yake zaune ya dauka tare da yin jifa da ita,Su Kuma sauran sunyi tagumi kamar an musu mutuwa Wai Ana Taya Oga bacin Rai ne,Ahmad Bai koma gida ba sai 4pm ya shigo a make ya wuce palonsa tare da fadawa saman kujera ya kwanta Nan take bacci me nauyi ya kwashe shi,Ita kuwa Aamna da Yunwarta ta kwanta Haka da Asuba yunwa ce ta tasheta,Bayan tayi Sallah da Azkhar ta koma baccin Yunwa,sai 11am ta sake farkawa,Gidan ta hau gyarawa sai da ta Gama da room dinta da toilet sannan ta shiga dayan ta gyara,ta Shiga Dakinsa Nan taga Haduwar furniture gadon Kawai abin kallo ne, a Nan ta lalace tana kallo,sai da ta gaji ta gyara Masa ko Ina Neat Yana kyalli da sheki,Har Toilet duk ta Gama sannan ta dawo kasa a Nan ta ganshi Yana ta bacci hankali kwance,kitson calabarsa ta kalla ta leka Fuskarsa tana kallon Halittar Allah Iya Halitta,Tace tab Allah yayi Kira a Nan,waye zaiyi wannan in ba Allah ba,cikin Creazy Jean dinsa fatarsa duk a waje fara Kar da gashi kwantacce luf luf,Aamna Tace Uhmmmm.....sunanka Dan Zarra daga yau,kayi Zarra wallahi kafin a samu me Kama kafarka a kyau sai an tona,Habarta ta tallafe Tace kaga Dan baiwa....Fresh dashi...karya suke wani sweet Boy...ai wannan ya wuce Sweet Boy sai dai Honey Boy,Aamna tana nuna shi da yatsa Tace See Nose Alqur'an,Juyi yayi tare da Sosa Dan wuyansa,Aamna Tace ga Chest lafiyayye,Lips dinsa ta kalla ta Bude Dan bakinta tare da lumshe Ido Tace kiss mukeyi da shi ita kadai ta cuno Baki gaba tana feeling Wai suna kissing,Wani Iri taji a jikinta,Tace Kai da gaske na fara Jin dadin,Tunaninta ta kautar Tace kalli dalla ya wani kwanta da takalmi a kafarsa,a hankali ta tsuguna a kasa tare da zare Masa takalmin kafarsa a hankali ba tare da ya farka ba,Aikinta taci gaba da Yi sai da ko Ina ya dau kyalli da kamshi sannan ta leka waje taga me kula da Compound ya Gama gyara ko Ina na wajen,da Hijab a jikinta ta karasa wajen me Gadi,ya gaisar da ita Tace Musa ya kakeyi da cin Abinci a Nan gidan? Musa yace ai Hajiya duk wata Bayan Oga ya biyani kudin aikina Yana bani kudin Abinci na wata wata safe,Rana Dana dare,ai Hajiya Oga mutum ne me kyauta,Baki ga yanda yake taimakon na kasa ba,abinda nake so shi nake siya naci,ga kyautar kudi akai akai Yana bani,idan zanje ganin Iyali na Sha Tara ta arziki yake min,wayata ma Tekno dubu Arbain da biyar shi ya Siya min sabuwa dal,Aamna Tace yanzu dai kullum siyo abinci kakeyi? Yace me dadi ma kuwa Hajiya,tafiya Aamna tayi yunwa kamar zata kashe ta,Tace Bari ya tashi wallahi dole Nima ya dinga bani kudin Abinci na,Palo ta koma da Idonta Daya a manne ta Iske ya koma Bedroom Yana ta baccinsa,Bai tashi ba sai 2pm lokacin Yayi wanka ya hada Sallar Asuba da Azahar yayi ya shirya cikin jallabiyya ruwan toka,Yana zuba kamshi ya sakko kasa da Niyyar fita,Aamna wacce yunwa ta Gama cinyeta ta Mike da sauri ta kulle Kofar palon tare da sa key ta datse ta jefa key din cikin bra dinta tana kallonsa da masifa Tace wallahi ba inda zaka je sai ka bani kudin Abinci,matarka ce Ni a gidan Mijina nake sabo da Haka hakkinka ne nauyin ka ne ka sauke,Kai ya girgiza yace kina Neman rigima Dani,bana son Wasa da shirme,Ina da aikin Yi bani key Zan wuce Aamna Tace wallahi bazan baka ba sai ka bani kudin Abinci,Kai ya girgiza yace karki Bari kwakwalwata ta dau chaji Zan Miki Illa,Zan Miki Illa ki bude na fita ban son wasa,Aamna Tace wallahi yau baka Isa ba sai ka bani abinci,ka nakasa min Ido sannan zaka kashe Ni da yunwa,yace Mum ce ta kawoki kije wajenta ta Baki ko Ni Nace kizo gidana,bana sonki na tsaneki Akan me Zan Baki kudi na dalla Bude min kofa ya taso da masifa,Aamna ta rike Kugu sanye da Hijab Tace wallahi bazan bude ba,yace look ni bana taba Nonon Mata jikinsu ma bana tabawa ki dakko key ki Bude min kofa kin San Zan iya kwata a cikin Bra din Taki Kawai ban son tabawa ne ya Furta Yana yatsina Fuska,Tace Bazan Bude ba wallahiiii.. ta karasa da kukan wahalar Yunwa. Sauri yake yi zai fita sai ya koma Sama ya fito da kudi dubu Hamsim Bundle na Yan dari biyar biyar yace gashi Zan Baki badan Ina tsoronki ba badan Kuma tausayinki ba Dan Ina so na fita ne Ina da Abinyi,Kudin ta karba Tace da karka bayar Mana Idan ka Isa,kaji dai tsoro na Yaro woooooo......cikin tsawar data razana ta yace Open the door,Ba shiri jiki na rawa ta zaro key ta Bude Masa ya fice a fusace tare da banko Kofar kamar zai ballata. Ita kuwa murna da farin ciki ya kamata ta dauki dubu biyu ko wanka Bata Yi ba ta gyara Hijab dinta tayi waje,ko me Gadi Bata aika ba ta fice daga gidan,a Unguwar tana tafiya taga wani Resturant da sauri ta Shiga ciki tayi Order taje Away na Jullof rice with salat and chicken,ta siyo lemuka harda su Icecrewm Yogourt ta dawo gida ta baje abinta a Palo taci ta koshi tayi dam sannan taje tayi wanka tasa wani gajeren Wandonsa ta zabo fari ya Mata yawa Amma ta saka Haka,ta dauki t-shirt dinsa baka ta saka sun Mata yawa Amma abinka da me kyau sai tayi kyau,Haka ta gyara palon ta Karo karfin Ac tare da kunna kallo tana kallo ta wani can saman Hannun kujera baza ma ta zauna a kujerar ba ta tale kafafu tana Shan Iceream dinta tana ta Dariya a Haka ya shigo gidan ya sameta,Kallo ya bita da shi ganin kayansa a jikinta tana Shan Icecream,Wayar charger ya fisgo da sauri yace kayana are you Mad,Da gudu tayi cikin wani daki ya bita da kyar ta samu ta buya a toilet,yace Zaki fito ne,idan kin Isa kina ji ke kece ki fito,Tace kaima idan ka Isa ka shugo,baka kunya fada da mace,Namiji da Kai kaje kayi da maza Mana idan ka Isa a tumurmusa ka,Yace Zaki fito ne sai na Ballaki Kuma wannan kayan da kika sa wallahi sai dai a kone su ban Haka skin da ke Idiot ya juya tare da komawa palo. Tunda Aamna tasan tayi laifi Bata sake Fitowa ya ganta ba sai washe gari ta fito sanye cikin wani Lace fari Riga da skert daf da ita tayi kyau sosai Sanda ta shigayi tana tafiya a hankali,a main Palo ta Iske shi yayi Order Breakfast ya hada tea lafiyayyen gaske ga chips and Egg da farfensun kaji Yana ci hankali kwance,Aamna ta hadiyi Yawu ta fito a hankali yaji motsinta Amma ko kallonta baiyi ba yaci gaba da cin abinsa,a gabansa ta durkusa Tace Ina kwana Yaya Ahmad,sai lokacin ya kalle ta kadan Yaja uban Tsaki,tace Nima yunwa nake ji,wata Uwar Harara ya aika mata,Dan Allah San min ko na fita na siyo? Dama jiya na fita na siyo Abinci na manta ban nemi Izninka ba ka yafe min,Cikin tsawa yace Ina ruwana da rayuwarki Ni da Zaki tafi ma bangon duniya Ina ruwana,wallahi bazan je bangon duniya ba salon idan tashin kiyama yazo yajuju da majuju su fara ta kaina,Kinga ki daina Shiga harka ta,na fada Miki kiyi rayuwarki Mummy ce ta kawo ki to duk wahalarki sai ki fada Mata,Yar wahala Kawai,Yar walagigi Kawai,Ai kuwa Ni gaskiya Raina ya biya da wannan Abincin naka ka fada min Inda ka siyo naje na siyo ai Ina da kudi sannan ko ka bani naka na ci,Tana Gama fadin haka ta janyo plate din chips din gabanta ta fara ci Tace Dadi,sai ta dauke plate din ta gudu daki ta sa key,Ahmad ya dura wata Ashirya yace yau ba abinda zai Hana ban karyaki a gidan nan,Sa'anki ne ni? Aamna Tace ae daga bedroom,Sai da ta cinye tas ta fito lokacin ya bar gidan ma,ta kalli kwanikan Daya Bata duk abincin ya rage Bai cinye ba duka,ta zauna gaba Daya ta cinye sannan ta hau gyara gidan tana mita mutum sai yawon jaraba kullum Yana waje. Duk wani Aikinta sai da ta Gama sannan ta zaro Yar Wayarta Vivo ta Kira Mama suka gaisa da Baba,ta Kira Zuhra ma Suka Sha Hira,Siyama ta Kira karshe,Siyama Tace Amarya bakya laifi kin tafi kin barmu da Aiki a Resturant,Yaya Mutumin naki ko anyi abin ne? Aamna Tace Allah ya kiyaye na hada jiki da Dan giya,ke Siyama wallahi baya kaunar Mace,wannan ko tsirara Zaki zo gabansa baza ki birge shi ba,Dariya Siyama tayi,wallahi Aamna ga masifa kullum Fuskarsa ba Rahma Abu kadan Kuma sai masifa,wannan bazai shiryu ba,banga abinda za a Masa ya shiryu ba,to Ina ma yake Zama da har zai fahimci wani Abu mutumin da sai ya kwana a waje can ko sai cikin tsakiyar dare zai dawo,ga Dan Ido na Guda Daya a manne,Suna ta surutu har suka Gama ta fara karatun Qur'ani,Jin yanda aka banko kofa tasan Ahmad ne ko Sallama dama bayayi Yana shigowa yace ke koma dakinki kiyi karatunki ko ki koma masallaci ki tare,Ganin yanda ya shigo a buge sai ta tashi tsam tayi bedroom shi Kuma ya kwanta a saman kujera,Ya kunna tv ya kure volume karshe kida ya cika gidan a manyan speakers Yana sani yayi Kuma dole Aamna ta hakura da karatun Qur'anin sabo da yanda kida yake dauke Mata hankali,Fitowa ta sake yi,ai kuwa ya Mike a fusace yace ba nace ki daina matsowa inda nake ba ya dauki Remote ya jefe ta da shi da karfi ji kake kwas a goshinta,sosai taji zafi wajen ya kumbura yayi Mata kulu,Itama ta dauka ta jefa masa a bayansa,ta gudu ya bita cikin zafin nama Amma ta kulle Kofa Haka ya rabu da ita yace Zaki fito ne. Sai bayan Sallar Isha Aamna ta fito sanye cikin doguwar Riga Yar kasar masar,me shape sosai wata silver,ba karya tayi kyau,Mayafinta tayi Rolling ta dauki kudi ta fito,yau ma tayi sa'a sai ta ganshi a kwance Yana cin green Apple,Aamna cike da tsoro ta karaso inda yake wani kamshi yake na musamman,a gabansa ta tsuguna Tace Sannu da hutawa zanje siyo Abinci,Baki ya tabe sai da ya dauki mintuna yace Ina ruwana,mikewa tayi ganin masifa yake ji kadan yake jira sai tayi tafiyarta kuwa,taje tayi take Away sharp sharp ta dawo,Lokacin Yana Zaune Yana kallon wani American film, Sakwara da miyar kifi, ruwa Eva da fruits salat,tana ci tana kallon Film, . Wayarta ce ta hau Ringing tana dubawa taga Mama,da sauri ta daga,bayan sun gaisa Mama Tace Aamna ga fa kudin sadakinki Baki karba ba,Aamna Tace Ina sane da abina,suna Rai na,a ciki ki dauki dubu Goma kyauta,ki Bawa Baba dubu Talatin,Zuhra a Bata dubu bakwai,Siyama kawata a Bata dubu Uku Kinga dubu Hamsin ta Kare ko? Mama Tace Haka ne,to dubu Hamsin din a ciri dubu biyar a bayar Sadaka Allah ya Kai ladan kabarin mamata sumayya Allah ya Mata Rahma,a sake cire dubu biyar Abba na Daya gudu ya barni ayi Sadaka nayi tawasili da ita Allah ya shirye shi ya canja Hali,Mama tayi Dariya Tace ai duk kin rabar da kudin ba Haka akeyi ba,Zan dai cire na Bawa kowa abinda ya Dace sauran ai naki ne,Aamna Tace to koma dai mene abinda aka barmin a kaiwa Kawu Isma'il can kauye ya Siya wake da Alkama a ajiye idan sukayi tsada sai na siyar na samu riba,Nan fa Ahmad yace tab Riba kudin riba ai masifa ne, ka siyi Abu ka boye sai yayi tsada kazo ka siyarwa mutane,Wannan ba Business bane,Aamna Tace Kai baka ga laifinka ba barasa kwalaba Nawa kake dirkewa cikinka wlh kayi hankali Kar Hantarka ta tabu tam,Hannu yasa ya murde Mata kunne ta kwalla Kara,Mama ta waya taji Kara Tace lfy? Mama wani kwaro ne ya firgita Ni. Can Baba ya fisge Wayar yace ke Aamna Dan Ubanki kiwa fa mijinki biyayya,duk abinda yace kiyi bana son sakarci,Kuma ko me Zaki shuka ki shuka gaskiya kiyi gaskiya ato sabo da mu dangwali arziki da kyau,Aamna Tace yo Baba ai Gaskiya Ni a jinjina take da ita aka haife ni,dankwalin Aamna ne ya zame layar ta Guda biyu Dake soke a kanta suka bayyana,Ahmad Yana gani ya girgiza Kai a zuciyarsa yace mashirkiya,Ita dai Aamna abincinta take ci tana Dan juyowa ta kalle shi kadan sabo da faratansa na Hannu Dana kafa Daya Tara sunyi tsayi Kamar Arne Amma da gani suna Shan gyara wani fes da su sai dai ba a Yankewa,Allah yasa kayi bacci sai na yanke wannan uban faratan Aamna ta furta a ranta. Ganin tana ta Kallonsa Yaja Tsaki tare da mikewa ya dauki key din machine dinsa zai fita,Aamna Tace Ina zaka je da daren Nan Haka?Ni tsoro nake ji gaskiya,Kwafa Yaja a ransa ya furta Mummy ta Gama Dani,idan na Mata Illa tsinuwa ta hau kaina,juyowa yayi a fusace yace Allah ya taimakeki Ina son Nonon Mummy Dana yasha yabi lafiyar jikina Amma da kin Gane kurenki,Aamna ta kyalkyale da Dariya Tace au har yanzu Nonon Mummy Bai Gama bi maka jiki ba? Sanda aka haife Ni ko yaye Ni ba ayi ba aka samu cikin Saddeeq shi yasa ya cuce Ni na Sha gubar cikinsa,Aamna sake kecewa da dariya Tace ko shi yasa aka ce ka Dade a tsumbure baka girma ba Dan Mummy Tace har cutar koshokwo kayi Haka Kawai Aamna tayi karya Tace Mummy ce ta fada Mata,ai kuwa shi da saurin Fushi kwaya tana sashi saurin Fushi ai Kan Aamna ta rufe baki yace uwar Koshokwo nayi,Aamna ta Mike zata gudu Suka dinga zaga palon Nan sai ya kamata ya dake ta Itama ta guduwa,ta samu tayi waje Compound da gudu,fita yayi Yana huci ya hau lifan dinsa ya fice sannan Aamna ta dawo ciki abinta. Bayan Sati biyu da Auren Aamna kullum fada sukeyi da Ahmad ba Wani mutunci, Mummy ce ta Kira Aamna Tace,bayan sun gaisa Aamna ta saki kuka Tace Mummy wallahi kullum sai munyi fada ya Duke Ni saurin duka ne da shi Kuma yaki siyo kayan abinci kullum sai dai naje na siyo ko na aiki me Gadi shima Haka Mummy, Dariya Mummy tayi Tace Kuma wallahi Ahmad ya Iya girki sosai a haka,kin San nice na sallami Peter me dafa Masa abinci, Aamna ki Kara Hakuri,bazan turo Miki kudin Abinci ba Yana da kudi,kece Zaki San yanda zakiyi Masa dole ya Baki kudi ki zuba abinci a store kin Gane,ae naji to ta furtawa Mummy,Bayan sun Gama Wayar Aamna ta zauna tayi tagumi tana saka Taya zata sa ya siyo Mata kayan abinci ko ya bada kudin ta siyo tunda kudin hannunta sun kusa karewa. Bayan tayi Shirin bacci cikin wata Riga da wando farare masu laushi ta zuba kyau ciki,a Palo ta zauna tana jiransa ai kuwa taci sa'a yau Ana Sallar Isha ya shigo gidan Yana tafiya da kyar da yanda yake Gadara ya nuna yau baiyi shaye shaye da yawa ba,Sannu da zuwa Aamna ta Furta,ko kulata baiyi ba Direct sama ya haura ya fada toilet,wanka yayi ya fito tare da Gabatar da Sallar Isha ko Addua baiyi ba ya Mike ya saka wasu kayan bacci dark blue me digon fari Riga da wando,fresh milk ya sha sannan ya kwanta a Gadonsa Nan take bacci ya kwashe shi me nauyi,Aamna ta biyo shi dakinsa Wanda Bata shiga sai idan zata gyara,a hankali tayi knocking Shuru taji,tayi Sallama Shuru,sai ta bude Kofar a hankali saman bed ta hangoshi ya wani Yi dai dai Yana baccinsa,Aamna tayi murmushi Tace Allah sarki yayi bacci,a gefen bed din ta zauna a hankali gefen kafafunsa,Nan take ta tuna da taga faratansa ya Tara sun Sha gyara,Room dinta ta koma ta dauko razor blade sabuwa dal ta bare,a tsorace tayi shahada ta Dan rike Yatsansa kadan sannan ta fara yanke Masa farcensa daya Tara Yana gayu da abinsa,ta fara yanke su Daya bayan daya,gashi da nauyin bacci har ta Gama hannaye Bai ko motsa ba Kawai baccinsa yake Sha,ta dawo kafa ma ta yanke Masa tas ta gyara ta kwashe farcen data yanke ta zuba a trash da razo din duka,ganin Bai da Niyyar tashi ta hakura itama ta koma dakinta Bayan ta kashe Masa hasken wuta ta Dan rufa Masa blanket sabo da taji sanyin ac yayi yawa. Itama komawa tayi dakinta ta kwanta abinta,sai 2am Wayarta ta tashe ta sakamakon saita Alarm da tayi, Mikewa tayi tare da Gabatar da Sallah Nafeela raka'a hudu tayi Adduointa sannan ta koma ta kwanta,sai Asuba ta sake tashi tayi raka'atanil fijr tare da Sallar Asuba ta zauna ta Gabatar da Azkhar sannan ta koma bacci,10am ta tashi ta hau gyaran gidan,Compound kuwa me Gadi ya Gama gyara ko Ina har Garden,Dakinsa ta shiga karshe taji karar ruwa alamar ya tashi Yana toilet,bedroom din ta hau gyarawa komai ya koma neat dama shi Sam Bai da kazanta akwai tsafta,ko Ina kamshi ne ke tashi,toilet ya Bude ya fito daure da towel a Kugunsa karami Kuma a hannunsa Yana goge wuyansa ga kitson kalabarsa Nan sabo an canja Masa sabo sai wani sheki yake Yi Bai jika gashinsa ba sabo da Attachment aka saka yellow, red and green,Aamna jikinsa ta kalla lukwi lukwi sumulmul,Fuskarsa a daure ko kulata baiyi ba ya tsaya a jikin Mirror Yana karewa Kansa kallo,Muryarsa taji yace Sexy Guy,gemunsa da Sajensa ya shafa yace Fresh Guy,Aamna ta zaro Ido taga Yana ta yabon Kansa Yana kallon Kansa a mudubi Yana shafa kitson kalabarsa,Toilet din ta shige ta gyara masa a ranta tana jinjinawa tunda take gyara Masa gida Bai taba nuna yaji Dadi ba ko abin ya birge shi ba,harkarsa Kawai yake Yi,Tana wanke toilet taji Muryarsa Yana Kiranta Bush girl.....Bush girl....tsoro taji Kar Taki zuwa ya Mata duka a banza Fitowa tayi da sauri Tace gani,Wani murmushi ya saki me tsada yace Good girl Ashe kin Gane sunanki,da Hargowa yace Ina wani perfume a Nan sabo? Murmushi Aamna tayi tace ai na dauke shi Ni zanyi amfani da shi sabo da Naga na Mata ne Kai Kuma Namiji ne,wani Ashar ya dura yace kin San tsadarsa kuwa? Yo ba gidan mijina bane,Kuma ma kayan Mijina ai Nawa ne ta karasa da shagwaba,Tsaki Yaja yace why are you always looking for my trouble? Idan na balla ki hmmm common dakko min kafin Raina ya baci,Aamna Tace Idan kana son na baka ka bani kudin Abinci ko ka siyo kayan abinci a gidan Nan yanda Zan na girki da kaina. Wani Takaici ya kamashi ji yake kamar ya harbeta yace bana Baki kudin abincin ba uban me Zan Miki,Aamna Tace Ni ka bani Dan Allah yau naje kasuwa na shirya store da kitchen dina,kana min fuck up fa a gidana,kanta yayo Aamna ta fisge towel dinsa ya Fadi kasa ya dawo zigidir, da sauri ya dauki towel din ya daura kunya ta balain kamashi,Abu na farko a rayuwarsa da yake Jin kunya Bai so aga tsaraicinsa Amma wannan Yarinyar ta cuce shi,Aamna takawa tayi zata gudu ya cafko ta ya dakko belt din Wandonsa tana Ihu ya riketa Kam ya dinga tafkarta iya karfinsa,tana ta Ihu tana cewa banga komai naka ba,kayi Hakuri,bazan fadawa kowa,bazan cewa kowa ga Kalar abinka ba,ganin zai Mata Illa a banza Tace Tsinuwar Mummy a kanka,Yana huci Idonsa yayi jajir ya tsaya cak Yana haki,Ita kuwa Aamna da Dan Idonta Daya a manne ta Mike tana kuka Wiwi,ta koma toilet din ta karasa wanke Masa tana kuka ta fito zata fita kenan ya shirya cikin wasu kana Nan Kaya farare tas marasa nauyi wandon pencil irin na shakatawa a gida da Alama ba fita zaiyi ba yau,rafar kudi Yan dubu dubu ya jefo Mata yace gashi Nan ki Siyo Uwar kayan girki,last warning ba ruwana da ke,karki sake Shiga harkata,ke magana ma ban so ki min,Aamna Tace ai wallahi baka Isa ba Mijina Guda ai dole na maka magana,Kwafa Yaja yace to kuwa Zaki ci Ubanki wallahi. Key din machine taga ya dauka Ashe fita zaiyi Ba zato Aamna ta sa key din kofarsa ta kulle ta cire key din ta jefa a bra dinta Tace Yau ma baza ka fita Muna dakin Nan zamu yini sai dai yunwa ta kashe mu,lips dinsa ya tamke tare da rufe Idonsa kam tsabar bacin Rai,yace ban so Tsinuwar Iyaye ta shafe Ni,sannan gwara nayi komai Akan na taba Nonon mace Bude min kofa ko yanzu na karasa Miki idon Daya,Aamna ta tsaya sanye da Atamfa Riga da skert na lefe ne sun kamata sosai,Tace tunda aka auro Ni baka taba ko Dan Rungume Ni ba,Please yau kafin ka fita Ina bukatar warm Hug,just ordinary Hug,Nima yau Ina so na motsa jam'iyata,kina hauka ne? Meke damunki,Ni zanyi Hugging naki? wata Dariya yayi yace Ashe nine ma na ganki nace Ina so,kanki akwai motsi lallai,Aamna Tace to lallai zamu kwana a Nan,tsayawa Suka Yi a Gaban kofa har na tsawon minti biyar ba Wanda yayi magana,nisawa yayi tare da girgiza gashinsa yace open the door,Aamna tace Baby Hug me Mana ka fita abinka,tunani ya tafi idan ya duketa Mummy dinsa,idan yace zai kwace key sai dai ya zura hannunsa a Boobs dinta shi gaskiya Bai son taba Nonon Mata,Baya Yaja kadan yayi Dan tangadi sannan yace Okay ya runtse Idonsa sannan ya Bude hannayensa,Aamna tana murmushi taje ai kuwa ya cakumeta irin bai iya ba Kawai cakumarta yayi ita Kuma tana sani ta kankameshi ya fisge jikinsa da bala'i yace bazan tabaki ba din,kinyi kinji Dadi Bude min kofa,Tace yanzu kuwa ta dakko key ta Bude Masa ya fice a fusace,ya hau machine dinsa kenan sai ga Aamna ta fito da gudu tana wait wait...da masifa ya juyo sai yaga Ashe wayarsa ce ya manta,Tace ka manta wayarka Baby,fisge Wayar yayi tare da Mata wani kallon banza ya Bawa machine dinsa wuta ya fita,Aamna kuwa wanka tayi ta shirya tsaf ta Kira Siyama kawarta suka je kasuwa,duk kayan Abinci na more rayuwa sun siyo dai dai gwargwado,tare suka dawo a taxi Suka shirya kayan a Store tsaf,kitchen kuwa komai na amfani akwai dama,sabo da Haka Jullof rice sukayi da wake taji kayan lambu da nama,Zuhra ce itama tazo ganin Amarya suka zauna suka ci abinda suke so,sannan suka gyara wajen,Palo Suka dawo suna kallo,Zuhra Tace Kan bala'i gaskiya gidan Nan ya hadu ba karya,Siyama ta Mike a saman doguwar kujera Tace har wani bacci nake ji ga ac ta ko Ina,Suna kallon wani Indian Series suna Hira sai ji sukayi an banko kofa,Siyama da Zuhra sai da suka firgita,ita kuwa Aamna ta Saba ko a jikinta tasan shine,ya shigo dauke da Ledar take away a hannunsa,Yana ganin Baki ya sake daure Fuska Kuma ko Sallama baiyi ba Sannan kallo Basu ishe shi ba bare su sa ran zai musu magana,ba Wanda yayi magana yazo har inda Siyama ke kwance a doguwar kujera yace cikin tsawa keee....tashi Zan kwanta a Kan kujerata,ai da sauri ta hantsilo kasa ya haye tare da kwanciya ya wani Mike Yana wata Mika,su Zuhra sai kallon kallo,Suka Yi tsit a palon sannan Suka ce Ina Yini? Banza Iska yayi da su,da Tsawa yace bani remote ya dakawa Zuhra tsawa,ta Mika Masa abinsa Wai Gadara yake gidansa ne. remote ya dauka da Gadara ya canja Chanel suna kallo ya Shiga wata Chanel ta Yan Iska Wanda a tashar Watarana har Xxx suke saka wa,sannan sai tallan Magungunan maza Dana Mata na Kara karfin gaba,da tallan kayan sex,Shi Kansa Bai taba kallon Chanel din ba sabo da su Zuhra ya kunna,ai kuwa sai Suka ga Ana Nuno maza da Mata tsirara,sai aka koma tallan condom na maza,Yana kalla yayi wani murmushi yace mun gode Allah ya Kara basira turawa,ya kamata fa ku yo Mana wanda yafi Haka kauri wannan fashewa yakeyi Bama Jin dadin shiga da fita,Mata aka nuna daga pant sai Bra,Ahmad yace wow see Bebs wannan zata Yi min,Wata kanjamammiya aka nuna,yace ke dalla matsa Jibson ke son irinku, kunya ta lullube su Zuhra Suka Mike tsam tare da yiwa Aamna sallama,Tace tun yanzu zaku tafi Haba Dan Allah? Ai ko kulata basuyi ba suka hada karansu sukayi waje,tuni suka bar gidan. Yana ganin Haka yayi Dariya ya canja Chanel ya koma kallon kwallon kafa,Aamna ce ta dawo daga rakiyar su Zuhra,da kukan shagwaba ta shigo tana dire diren kafafu tana Haba Dan Allah....Haba...Dan... Allah Baby, wani Haushi ta bashi Takaici yasa Ahmad ya zaro Wayar charger ya kifa Aamna da ita ta gudu dakinta ta kulle Kofar ya dawo Palo Yana masifa Ni Zaki yiwa shagwaba,Baki San na tsani wannan haukan ba,aikin banza Kawai,wani Ihu ya saki Yana kallon yatsunsa na kafa Dana hannu,Jin Ihu sa yasa Aamna ta yo waje ba shiri tana cewa lafiya? a tsorace yake lokacin shi yasa yace fingers Dina,farce na Dana Tara Ina ji da su an yanke min,jikinsa ya kalla tsaf yace Aljani ne,Amma wannan ya cuce ni,Dariya Aamna ta dinga Yi Tace nice ta fece da gudu daki. Rasa abinda zai Mata yayi sabo da bacin Rai wuka ya dakko a kitchen ya ajiye a kusa da shi yace yau Zaki ga abinda Zan Miki ba ruwana da wata Tsinuwar Mummy. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 26-30 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne AGRA ANEESAH UMMIN HIBBAH ASMAU YUSUF RAHMA FARHAT MRS MJ PHAATIMAH Ranar Aamna Bata sake Fitowa ya ganta ba kullum sai ta tabbatar ya fita take Fitowa tayi abinda ya kamata har kwana Uku sannan yau Bayan tayi Sallar Isha taci abincin data dafa Tace Fitowa zata Yi ai ta San yanzu ya huce,a hankali ta fito sanye cikin wani Bum short sky da Riga t-shirt red ta zuba kyau ciki,tana Fitowa taga shima ya banko glass door din palon ma'ana yanzu ya shigo kenan,Yana ta uban tangadi ya fada saman kujera shirim Yana magana a hankali cikin maye shi kadai,Aamna ta kalleshi taga bacci zaiyi ta lallabo a hankali Tace ka koma bedroom ka kwanta,ya furta barrrr.......niiiii....aaaaa.....aaaa....Nan.....Aamna Tace no Nan bazai maka dadin bacci ba tashi ta Kama hannunsa kenan ya fisge hannunsa,sake rikewa tayi Tace taso ta janyo shi ya Mike da kyar Yana tangal tangal a Haka ta kaishi sama ya fada saman bed dinsa,tsugunawa tayi ta zare Masa takalmansa a hankali,ganin har ya fara bacci ta Karo Masa karfin Ac din ta kashe Masa light ta fita ta barshi tana tunani,Palo ta dawo ta zuba Uban tagumi tana mamakin Ahmad kullum cikin shaye shaye baya Free Sam,Tace wannan wacce kaddara ce Haka ta sameni,da wacce zuciyar Zan iya daukan wannan masifa,gashi na Bari an daura Aure ya zanyi,Sam bana birge shi duk shigar da nayi Bai taba kallona ya nuna na tafi da shi ba duk da Nima ba so nake ya Yana ba. Taya zai shiryu Haka,Ido ta lumshe ta kwanta a saman kujera tana ta sake sake a ranta. Dakinta ta Mike zata tafi Bayan ta Gama kashe kayan wuta ta sake leka shi ta gani ta hango shi kuwa Yana ta bacci Amma ya dunkule waje Daya Yana ta Rawar sanyi kamar zazzabi ne a jikinsa,dama taji jikinsa ya dauki zafi dazu,kamar ta wuce sai ta fasa ta shiga bedroom din,a gefen bed din ta zauna tana tunanin me zata Masa,Tsaki ta ja kadan ta shiga zare Masa Riga a hankali,jikinsa ta taba zafi zauuuuu,Toilet ta shiga ta ebo ruwa a Bowl da towel karami ta shiga goge masa jikinsa a hankali,kirar jikinsa ta shiga karewa kallo tana Dan goge Masa jikinsa da Towel,ita mamakinta Sam a face baiyi Kama da me Shan giya ko wani Drugs ba,idan baka sani ba baza ka taba ganewa ba,sai dai acting dinsa yanda yake abu ba tarbiyya kana gani,Ac din ta kashe gaba Daya sannan taji zafin jikinsa ya Dan ragu,a hankali take girgiza shi tana tashinsa Me Burkutu....me Burkutuuu.......Shuru,taceme giyaaaaa.....Shuru,ta girgiza shi shuru, Kuma Yana numfashi sai da ta Dade sannan taga ya dafe Kansa da Alama ciwo yake Masa Yana Nishi kadan yace Ohhh my God,a hankali ya Dan Bude idonsa,ba a wani hayyacinsa yake ba,ya fara Mika Hannu jikin Drower yace i need to take my drugs,Drower din ta Bude da sauri mamaki ya kashe ta ganin kwayoyi iri iri Kamar hauka duk na Maye,Salati Aamna ta saki Hawaye ya shararo Mata ta shanye da kyar,ta Dan duba Drugs din sai taga paracetamol,shi ta ballo ta dakko Masa ruwa da sauri ta Mika Masa Yana daga kwance ya karba ya Sha abinsa a kwance shi ba Wani ganeta yake Yi ba. Zama ta ci gaba da Yi gefen Bed din tana ta faman gyangyadi,so take Yi ta ga ya samu sauki,a ranta Tace ko Ina ruwana oho,Amma tunda dai lalura ce Bari na jira,tana Nan zaune taga ya fara Juyi ya hada uban zufa alamar zazzabin ya sauka,ac ta kunna Masa,cikin mayen baccinsa yace Mummy yunwa Zan Sha ruwa,Aamna ta kalle shi taga bacci ma yake Yi,da sauri tayi kasa ta hau dafa Indomie lokacin 11:30pm, sharp sharp ta Gama ta dakko da kankana wacce ta yanka Nan take,da sauri tayi sama,ta ganshi zaune a gadon ya jingina bayansa a fuskar bed din ya lumshe Ido,still ba Riga a jikinsa. Aamna ita ke shirmenta ba ganeta yakeyi ba ya bugu da yawa dishi dishi yake hango ta shi yasa ya kyaleta da lafiya yake da tuni taci duka,sabo da samun waje saman bed din ta haura ta zauna a gefensa Tace ga abincin,you have to eat something sabo da kafi Jin sauki,a hankali ya juyo ya kalleta ya turo lips dinsa gaba,Tace haba na Mummy ci Mana karka kwana da yunwa akwai Dadi wannan Indomie taji Hadi kaci sai kayi Santi,Kansa ya dauke can gefe,Aamna Bata hakura ba harda rera waka Wai Dan tuzuru....ya dawo mata,.....yanzu....da ba'ayi maka aure..... ba wa zai dafa maka....Oya Fadi kaima tana tafi,Dake a bige yake sai yace shima Nine Tuzuruuu......yawwa to Bude bakin ta furta tare da ebo Indomie a fork,.....ya Bude da kyar Yana kumbura,ta zuba Masa tana murmushi Tace Ehemm....mutumin kirki...maza Kara ci ta sake ebowa ya karba a bakinsa,Tace Good King...oya again....ya karba,yaji tayi Dadi sosai tana ta bashi Yana ci Yana ganinta dishi dishi. sai da ya cinye tas ta dakko kankana Itama Haka ta dinga bashi baya ko magana sai da ya Sha da yawa sannan yayi gefe can da Kansa Nan ta Gane ya koshi,ta Balle ruwa ta tsiyaya a glass cup ta bashi Nan ma a Baki ya shanye ta Kara Masa ya shanye,Tace Inye King din ba,Harara ya Aiko Mata tayi shuru,ta tattara kwanikan ta maida kitchen,shi kuwa Yana Jin karfi a jikinsa wanka yayi sai lokacin Yayi Sallar la'asar ,Magriba da Isha sannan ya kwanta bacci ya sake gaba da shi. Aamna shugowa tayi taga yayi bacci ga sallaya alamar Sallah yayi,baya kashe light sai ta kashe Masa tare da sake feshe room din da wani Room freshner me Arnen kamshi ta rufe Masa kofa taje itama ta kwanta. Washe gari da Ihu ya farka Daya tuna kamar jiya Aamna ce ta shigo,Nan ya tunano me tayi,wani ransa ne ya baci shi kadai ya dinga masifa har yayi wanka ya fito cikin wani gajeren wando ruwan toka da Riga brown t-shirt,Lokacin Aamna ta cakare cikin wani wando legins tight,pencil tayi kyau duk na lefe ne, Yar rigarta yellow me siririn Hannu cibiyarta a waje,a kitchen take tana shirya Breakfast kamshi ya cika gidan,ji tayi kamar ya fito da sauri ta fito ta sawa Kofar palon key Yana kallonta yasan cewa zata Yi bazai fita ba sai ya Bata kudi ko wani Abu,dama da fushinta ya tashi yau,yace tun kafin na Miki duka ki Bude kofa ko ki Fadi abinda kike so na Baki,bani da lokacin shirmenki yau,Aamna Tace Breakfast zaka ci sannan ka fita,kullum Ina matarka baza kaci Abinci na ba yau ba inda zaka fita a gidan Nan,sabo da ma baka da lafiya baka Gama murmurewa ba,Ahmad yace shine jiya kika shiga Zaki min fyade? to ta Allah ba Taki ba,nafi karfinki,Wai harda wani cire min Riga ke Uwata ce ko ubana,ke Wai matata ko?Dariya ya bawa Aamna Tace ae naji zauna ka jira Ni,idan naki fa?,kitchen ta shiga da sauri ta Hado komai a tire ta kawo gabansa a Palo ta Ajiye Tace Bismillah kayi ka ci na Bude maka ka tafi,sai da ya dauki lokaci sannan yace badan Ina tsoronki Zan ci ba,Dan Ina da abin Yi ne kawai yau,Aamna Tace a Haka zaka fita da gajeren wando? Ina ruwanki munafuka Uwar gulma ya Furta,Shuru tayi Tace Enjoy your meal,Bread ya dauka ya gutsira ya kurbi tea sau daya,sai ya dauki chips Guda hudu yaci yace to Bude min na fita,ba musu ta Bude masa,zai fita ya zuba Mata Rankwashi me zafi ya fita abinsa,Ihu ta saki kadan ta zauna ta cinye abincin nasa,shi Kam Machine dinsa ya hau ya fita da shegen kitson calabarsa,Wanda sai dai ayi ta binsa da kallo. Tunda ya fita Bai dawo ba sai cikin tsakiyar dare,yau anci sa'a Bai Sha komai ba,hannunsa dauke da Ledar take away na abinci,a gajiye ya shigo Amma yaga Aamna zaune tana kallon American film,Sannu da zuwa ta furta,Baki ya tabe ya haura sama abinsa ko kallo Bata Kai matsayinsa ba. Bayansa ta bi a hankali Yana jinta Bai kulata ba,Yana Shiga bedroom dinsa Wanda ya Sha gyara kamshi ne Kawai ke tashi,kafin ta Shiga ya kulle kofarsa tare da murda key Yana faman Jan Tsaki,Dariya Aamna tayi tana daga jikin Kofar Tace ya jikin naka? Kai ya girgiza yace Uwaki yake ciki,,ta rasu fa marainiya ce Ni,Yace to tayi ta mutuwa Mana Ina ruwana,Wai ke Baki da zuciya ne? Aamna Tace ae bani da ita My Husband,tana Jin tsakinsa ta juya ta koma dakinta ta kwanta abinta tare da Adduar bacci ta kwanta. Shi kuwa Abincinsa ya zauna yaci ya shiga toilet yayi wanka tare da brush,cikin kayan baccinsa dogon wando da Riga me dogon Hannu silver color wani yadi Silk sharara,Sallaya ya shimfida ya fara jero sallah ba nutsuwa ba komai da saurin masifa kamar zai tashi sama,idan yayi ruku'u ko Gama dagowa baya Yi zai sabe da sujjada, kafin kace me tuni ya idar tun daga Azahar har Isha,ko Addua babu Ya Mike Yana tunanin ma kamar Sallar Isha raka'a Uku yayi Amma ya fuske tare da furta Ina laifi ma na karasa raka'a dayar a raina Kawai ta cika hudu nayi ya fada saman bed yayi kwanciyar ruf da ciki sai bacci. Washe gari 9am ya tashi kasancewar baiyi shaye shaye ba,Room din dake cike da kayan Exercise ya shiga Yana ta motsa jikinsa sai da ya Dade sannan ya fito sanye cikin kayan gym dinsa bakake yayi kyau,Yana Fitowa ya Iske Aamna har ta Gama gyara ko Ina na ciki,kamshi yaji a kitchen lekawa yayi ya hangota tana ta soye soye, Shiga yayi fuskar Nan ba Rahma cikin Muryarsa ta Yan kwaya yace bani kasko zanyi girki,Aamna Tace ga wasu Nan ka dauka Mana Kuma ma ai gashi Ina girkin da Kai sai muci wannan,cike da bala'i yace da wannan nake so nayi,gidanki ne ko Ubanki ya Siya min kayan kitchen ne? ai kayan Mijina Kaya nane Kuma wallahi bazan baka ba,baka Isa ba kayi kadan kayi karami da yawa na baka kaskon nan, sabo da Nan gidan Mijina nane Kuma gida na yawwa eheee ....Mari ya dauke ta dashi garin Jin zafin Mari Aamna ta saki ludayi ya Fado saman kafarta gashi yasha Mai na suya me zafi Nan take ya kone Mata wani Dan bangare a kafarta,Ihu ta saki ta durkusa kasa Amma duk da Haka Bai kyaleta ba ya tallafe Mata keya ya dauke kaskon da man Baki Daya da dankalin ciki ya watsa a cikin Sink,har kankon ya Bari cikin Sink,sabon kasko ya dakko ya fara Girkinsa,Aamna ta Mike cikin bacin Rai da Hawaye a fuskarta ta tattaro karfinta ta durma Masa duka a gadon baya ta arce da gudu,shi ko jin zafin dukan ma baiyi ba,ita Tunaninta ta Rama,Zuma ta dakko tare da shafawa a kafarta iya inda ya kone,Palo ya dawo da kwansa soyayye da tea da wani snacks Kamar bread,Aamna Fitowa tayi dama tasan shi Bai zuwa Dining Sam,Yana Palo zaune saman kujera ya wani kishingida a Haka yake cin abinci,Aamna a ranta Tace duk abinda ya shafi Sunnah da dabi'a ta Musulmai baya Yi Sam,abinci a kwance za a ci,a kasan center carpet ta zauna tare da nannade kafafu kamar wacce zatayi karatun Qur'ani ta zuba Masa Ido,Hannu ta zura da sauri ta zari soyayyen kwai fefe Daya,ta fisge snacks ta balli Rabi ta Ajiye Masa,ta Buda tsakiya ta sa kwanta ciki ta rufe,Bai ko kulata ba,tana ta ci yasha tea da yawa saura Rabi ta dauke cup din ta gudu,dama ya koshi shi take uban gudu da tayi zamanta ma shi baida time dinta yanzu. Mama zaune take a Palo tana gyara wake Baba yayi wanka ya Sha Yar shaddarsa zai tafi kasuwa ya daga Hannu sama yayi wata Hamma tare da Mika yace Alhmdllh Aishatu sakayau nake jina,Kamar wani sabon musulunta,ji nake Kamar yau aka Yi min wankan tsarkii,sabo da mun Aurar da Yaran Nan mun huta Kuma Alhmdllh Bamu siyar da akuya ta dawo tana goge Mana danga ba,Mama Tace Bari Kai dai Baban Zuhra ai idan na tuna musamman Zuhra tana can tana zamanta lafiya sai naji Ni kamar Ina cikin watan Ramadana Naga Kuma Daren lailatul qadri,ita kuwa Aamna mun fita ko ba soso ba Sabulu,ta koma bangaren danginta suje can su karata,gashi Dake so suke su Aurawa Dansu Dan Giya har da bani jarin Million Uku cewar Baba shima,Mama Tace yo ai mun gano wayon badan Allah aka Bamu ba,harda wani gida ,Baba yace ai Ina sani na kwantar da Kai na nuna musu mutunci na hada dabara nace su bawa Aamna auren Ahmad zai shiryu. Hahaha Mama tayi Dariya Tace Dantijara wannan ai bazai taba shiryuwa ba,ita Kuma Aamna nasan kwadinyin tsiyarta shi zai zaunar da ita shi yasa kaji shuru,ko mun Mata waya sai Tace lafiya suke,Munafuka cewar Baba tana can tana Shan wahala,yanzu da zamu je sai Munga ta rame,Kaga yanzu har tayi kusan wata Guda da Aure, kudin Sadakinta data Bamu mun karbe ba ruwanmu sauran Kuma da Tace a siya Mata wake a ajiye a Kauye fa? Baba yac ae gobe fa zamu je gidan Aamna sabo da karta gano cewar Bamu damu da ita ba ko Bamu dauke a matsayin 'ya ba sai mu tafi Mata da kudinta mu Bata muce Kar tayi wannan sana'ar Kawai ta kashe kudinta,Mama Tace ita a dole me Neman kudi Ubanwa zai barta tayi Sana'a, Dan taga kudin sadakin Zuhra mun siya Mata Saniya a Kauye Ana kiwo shine itama tace a siya Mata wake,Mama Tace ai baza mu Bari ta Gane komai daga wajenmu ba,kamar yanda ta taso a Hannunmu ba yabo ba fallasa ita Bata Isa Tace Bamu sonta ba Kuma Bata Isa Tace muna sonta ba to yanzu ma hakane,musamman yanzu da ta auri jinin kudi,a hankali zamu dinga zararta kudi,so nake Nan gaba ta Bude min katafaren shago na siyar da kayan sawa na Mata cewar Mama,Baba Yana dariya yace ai Ni Kinga na samu jari. Amma naga Harkar tayi min kadan dole Nan gaba Nima ta Kara min jari,Mama Tace na karbo wasu layu da guru idan munje Zan sa ta Kara daura su so nake sai na mayar da ita Yar bori da wayo sabo da idan Mijin nata ya gani yace malamai take bi kaga bazai taba sonta ba bare ta zauna a daula,lokacin mun yagi rabon mu,idan ya sako ta sai ta dawo ta zauna a shago na Wanda Zan Bude Nan gaba da kudin surukanta ta dinga siyar min da kayan. Baba Yana dariya har da buga kafa yace kin iya planning,tunda Bata auri talaka ba Allah ya canja lamarinsa Kinga muma harka ta Bude sai mubi a Haka mu yagi rabon mu. Siyama kwance take saman tsohuwar katifarta sai faman Juyi takeyi tana murmushi ita kadai tare da matse pillow a hankali Tace Kai idan ban ganshi ba yau bazan samu nutsuwa ba,Wasa Wasa a hankali sonsa ya Shiga Rai na daga ganinsa sau biyu sau uku,wata zuciyar ce ta gargade ta tace to Faisal din naki fa,Kuma Wanda kika haukace akan sonsa Mijin babbar kawarki ne, wata zuciyar Tace so so ne Amma son Kai yafi,a fili Tace duk yanda naso kawata ta samu farin ciki ai Bai Kai ga kaina ba,Kuma ma mene tunda Allah Bai haramta ba,abinda ya Dace na San yanda zanyi ya Gane Ina sonsa,kafin kawata ta rigani gwara Ni na rigata,zumbur ta Mike Tace dole na Kori Faisal na daina sonsa,Sam baya birge Ni yanzu,Akan Ahmad Zan iya koyar Shan barasa Nima Indai zai so ni,ta yanda Zan bullo kenan Nima na nuna Masa Ina Sha nasan zanyi Nasara,Mikewa tayi tsaye tare da jawo Wayarta ta danno Number Aamna. Aamna kuwa daidai wannan lokacin 11am su Mashkoor su Biyar ne Suka zo tare da cike palon suna ta kurbar giya,Ahmad Yana kwance,Aamna ce ta fito sanye da Arabian gown black da Alama fita zata Yi,ta gansu a palo,kallo Suka bita da shi Banda Ahmad da ko kallo Bata ishe shi ba,Mashkoor ne ya galla Mata Harara ya furta anzo an aure Mana Sarkin mu,kina Bata Masa Rai a banza,Jibson ya ja tsaki,Aamna dai Bata ko kulasu ba,wurin Ahmad ta karasa ta Dan dukar da kanta saitin Fuskarsa Tace zanje kasuwa ba kayan Miya da kayan lambu ka bani kudi da Izni,Tsaki Yaja yace dalla Wai Ni na kawo ki ne,ki tafi ko Ina kika ga dama,Kudi ya jaro dubu Ashirin ya jefa Mata a Fuska yace dauki ki bani waje mayya,Su Jibson Suka kyakyace da dariya ba ji ba gani,Aamna ranta ya baci ta Harare su tayi waje abinta. Napep ta shiga har kasuwar kayan Miya,duk abinda take bukata sai da ta siya,ta zuba komai a Napep zasu tafi Kiran Siyama ya shigo Wayarta,Fuskarta dauke da murmushi Tace Yar halak ya kike? Siyama Tace Ina Kofar gidan mijinki kina gida na shigo? Aamna Tace Ina kasuwa wlh Amma bani 10mnt yanzu Zaki ganni,Kawai ki shiga gidan Ahmad Yana Nan da abokansa kije kafin na zo Amma ki kula karki kulasu zasu iya Miki wulakanci,Siyama Tace to tare da kashe wayar Tace dama ba Dan ke nazo ba ai ta shiga taci Uwar gayu cikin lace Riga da skert wani ruwan kunun kanwa,Sallama tayi tare da Bude Kofar ta shiga dauke da Sallama,wani kamshi da sanyi ya daki Siyama, Siyama a ranta Tace shegiya Aamna akwai iya gyara,babu Wanda ya amsa Sallamarta cikinsu,shiga tayi Kawai ta zauna a wata kujera da bakowa,Ahmad ta kalla Suka hada Ido ta bangale Baki da murmushi Tace Ina kwanan ku,Suka kece Mata da dariya banda Ahmad da ya sake hade girar sama data kasa,a ransa yace an kawo min yarinya gida danginta sun dameni da zuwa gidana,Siyama tayi Shuru tana ta kallon Ahmad Kamar zata cinye shi,gefen Bash ta zauna Tace lemo kuke Sha ne? Kallonta Suka Yi Suka sake kwashewa da dariya,Bata hakura ba Tace Kai dama na sanka ma Brown ake ce maka ko ta nuna Mubaraq Brown,Siyama a ranta Tace Kan uba Taya Zan samu ko number Daya daga cikinsu ne? Tana wannan tunanin sai kuwa Jibson Sarkin son Mata yace Yan Mata kin hadu fa,Siyama tayi murmushi hankalinta na Kan Ahmad,Jibson yace da Allah bani number dinki Mana,ai da sauri Siyama Tace to dama abinda take so kenan ta kulla alaka da wani a ciki ko zata samu hanyar Shiga jikin Ahmad ta Haka,ta Bawa Jibson number ya Kira ta Nan take tayi Saving tana cewa ya matar gidan Bata kawo muku girki bane? Abdul Tawaga yace ta fita fa,Cab Miji yayi Baki Amma matar baza ta kawowa abokan Miji abinci ba wannan wacce irin mace ce,Ahmad ne ya kalli Siyama kadan ya dauke kai,Tace Bari ta dawo ai dole ma na tayata ta shirya muku better,Jibson yace da kin kyauta Uwar Kinibabba,Siyama ta kalleshi da sauri Wato itace Kinababba,yace dama yunwa muke ji,suna Haka sai ga Aamna ta dawo da fara'a tayi Sallama. Siyama ce Kawai ta amsa itama da fara'a Tace kawata kin dawo kenan,Aamna ta mikawa Siyama Hannu Suka tafa tace kinsan Ni jinin Larabawa ce Zan koma na tuno da Dan larabcina na Islamiyya Marhababiki ya Siyama,Kyaifal Ummati? Siyama tana Dariya itama da kalkala Tace Alhamdulillah...Alhamdulillah,Shukran cewar Aamna,Kujera ta nunawa Siyama tare da Furta Ijlis kawata,Siyama ta koma ta zauna tana cewa jalasna ya kawata,duk sai da suka Bawa su Jibson Dariya,Ahmad Kam Kawai Dan Baki ya tabe sabo da shi Yana mugun Jin larabci Dan Basu Sani bane. Zama Aamna tayi itama,Siyama Tace Hauwa'u kuwa tace tana Gaida ki,Hauwa'u Yar class dinmu,na Gane ai kice Ina Amsawa na gode,Siyama da larabci tace Ma Fi mishkla,ya kamata mu shiga kitchen ayiwa abokan mijinki girki Bai kamata su zauna da yunwa ba,ya kike Abu kamar Baki San darajar mijinki da abokansa ba,Aamna Bata kawo komai a ranta ba Tace Kuma fa Haka ne muje to ki tayani. Kitchen Suka Shiga Siyama tana ta wani kwarkwasa Wanda take Yi Dan shi Bai gani ba su Jibson sune Suka bita da kallo suna Hadiyar yawu. Fried rice suka Yi hadaddiya taji hadi da soyayyar kaji,ga zobo sun hada me Dan Karan dadi,salat ma an hada daban,a Dining suka shirya komai tare da gyara ko Ina sannan Siyama da Shishigi tazo Tace mun Gama guys gashi can a Dining,Ahmad Bai ko motsa ba sai su Jibson ne Suka zagaye abinci suka far Masa,kafin kace me sun cinye komai suna Santi sun shanye komai,Siyama tana zaune a cikinsu Suka ci tare sai taga Aamna ta fito da katon tire da wasu miyagu food flasks na musamman komai ta jera a Gaban Ahmad kasancewar tasan Bai zuwa Dining side. Serving dinsa tayi komai ta zauna a gefen kafafunsa tace tashi kaci Abincin,Siyama ta Bata Rai tana daga can Dining ta tsura musu Ido ranta a bace tana Jin Ina ma itace a wajen Ahmad Haka ba Aamna ba,Abinda Aamna ta fuskanta Kamar Bai da lafiya kwana biyu tunda yayi zazzabin Nan,Bata San tsabar kwayace ba take sashi Yana slow. Ka tashi please tun safe baka ci komai ba,Ahmad yaki tashi,Siyama ta saki murmushin Jin dadi,a hankali Kuma da ya gaji ya Mike tare da Zama ya saki jiki sharaf yayi wani Slow ya tsaya a Haka yaki Kuma magana. Aamna tasa spoon ta ebo abincin Tace to Bismillah,kamar bazai karba ba sai Kuma Yaja Tsaki tare da bude bakin kadan Tace ka Bude Mana ya Dan Kara budewa ta zuba masa,Kamar Yana tauna madaci Haka yake ci,a hankali yace kice waccen Yar Uwar Taki ta bar min gida kallo na take Yi bana son kallo,Dan kar ya fasa cin abincin Aamna Tace to Bari ka Gama cin abincin tana ta bashi a Baki Yana ci sai uban Tsaki yake ja,ya ci da yawa yasha Zobon ya daure Fuska Kuma yace cikin tsawa ta bar gidan Nan,ba Aamna ba Siyama ita kanta sai da ta firgita ta Mike ba shiri,ya kalli su Jibson yace daAllah kuje Ina son Zama Ni Daya Yana magana ya girgiza kitsonsa,gaba Daya Suka ce an Gama sarki Suka kwashe kayan mayensu Suka Yi gaba,Siyama ta kalli Aamna tayi murmushin yaudara Tace kawata na wuce,Aamna ta Mike ta saka Hijab Tace muje na rakaki,har bakin Titi ta raka Siyama,ta Bawa Siyama dubu Uku tace gashi kawata kiyi kudin Napep. Siyama ta karbe Tace na gode kawas,Aamna Tace kiyi Hakuri da korar da ya Miki wallahi banji Dadi ba Amma Kinga ba yanda zanyi da shi idan kin dawo next time sai na Bude Miki kayan lefen Nawa ki zabi abinda kike so ciki,Siyama ta washe Baki Tace na gode kawata ai na matsu na fara daukan wanka zanzo jibi sai na zaba,Aamna Tace ba damuwa Amma me kike ganin Zan bawa Zuhra itama?Siyama ta daure Fuska Tace zuhran data auri me rufin asiri uban me za a bata,irin mu ai mune muke bukatar taimako,Aamna Tace haba Siyama ya Zaki canja Hali Allah ya Hana mutum zaiyi Alheri ka Hana hakan,ko mutum Yana tayar da Kai da million ai Alheri Dadi gareshi Kuma ma ai kamar Yar Uwata ce tare Muka taso itama abinda take so zata zaba,me Napep ja muje dalla cewar Siyama cikin Fushi,Dariya Aamna tayi ta juya gida,tana zuwa ta tura Kofar palon taji Gam an rufe,tasan Ahmad ne ya rufe Wato Bai so ma ta shiga Kar a takura Masa,Murmushi tayi Kawai ta Danna door bell har ta gaji Bai bude ba,a bakin Kofar ta zauna ta zuba tagumi Tace kaddara kenan,Allah ya jarabce ni,Kwalla ce ta cika Idonta taf. Wasa Wasa har Magriba tayi Bai Bude ba sai jikin tap taje Wanda ke Garden tayi Alwala tare da Gabatar da Sallah a Nan tayi har Sallar Isha sannan ta dawo tayi bugun duniya Ahmad Yana can Yana baccinsa yaki budewa Kawai Kuma Yana sani yayi haka.. A bakin Kofar Aamna ta zauna tare da jingina da jikin bango a Haka bacci ya kwashe ta,har 9am lokacin Kuma Mama da Baba sunzo kawo Mata Ziyara,a Nan Suka hango ta,Mama Tace cab ga Alama mun gani Aamna Bata cikin Jin dadi,Baba yace Yar jakar uba gwara duniya ta koya Mata hankali ko ta koyi darasi,gida har gida sai Takaici a ciki,Allah yasa ba Zuhra bace a wannan halin, Mama ce ta taba jikin Aamna da Kalar tausayi Tace tashi Aamna,firgit ta farka taga gari ya waye sai Rana ta gani kwall a kanta,Salati tayi ta Mike tsaye cike da kunya Bata so su Baba suka ganta a wannan halin ba sabo da tasan zasu shiga damuwa. Baba yace Ashe yau za ayi yaki a gidan Nan,yata Dana rike da Hannu na muka Raine ta in dauka in bada ita Amana Amma a wulakanta min ita Haka karya ne wallahi,ba a haifi mutum ba,Baba Yana bala'i ya kaiwa Kofar Naushi zai daki kofa Mama ta kifta Masa Ido tare da yin wuf ta damko hannunsa tana Haba Baban Aamna da Zuhra Haba,gidan suruki ne Bai kamata ba,Abi komai a Sannu,Aamna tana Jin tsoro Ta durkusa a kasa tana rokon Baba tana Dan Allah Baba kayi Hakuri ka rufamin asiri,Kayi min Rai Baba wallahi idan kuka tafi Ni zai duka,dukan tsiya zai min,a hakan ma ya muke karewa kusan kullum sai ya dakeni,Dan Allah Baba ku tafi gida Ni zanzo,Kamar gaske Baba yace Ina ai wallahi yau sai na Kira Uwarsa da ubansa Akan Haka baza mu lamunci wannan ba,Mama tace ai batun tafiya gida Bai taso ba akwai abubuwan da mukazo tattaunawa da yawa sannan Kuma yau a Nan zamu yini muci mu koshi muna Nan har sai ya Bude Kofar,Aamna ta dafe Kai Tace wayyo Allah na Shiga Uku,Baba Kar ya wulakantaku a gabana bazan jure ba sai dai ya kashe Ni a kanku Dan sai na Rama,Ashe akwai hargitsi da balbalin bala'i kuwa yau a gidan Nan cewar Baba ya nemi waje ya zauna daram,Mama ta gyara Mayafinta ta zauna itama,Aamna kuwa Tap ta nufa tayi Alwala tayi Sallah sannan ta dawo wajen,Suna zaune sai Suka ji baram an Bude kofa da karfin tsiya,kamshi ne na daban ya daki hancinsu,Yasha wata jallabiya Brown Yar tsangalalliya Takalminsa flat Brown yayi kyau kace baya Shan komai,Fuska ya sake daurewa ganin Dangin Aamna,Tsaki Yaja da karfi ya furta sai kace Uban tsohonki ne ya Gina min gida,Kun da dameni da wannan tsofaffin Banzan,Aamna Tace wallahi ba sune tsofaffin banza ba sai dai in naka ne na banza na wofi. A fusace ya juyo Yana huci yace Mummy na data auro min ke wacce ta nace tana sonki kika zageta yau? Jikin Aamna ne yayi sanyi Tace ai ba da ita nake ba Ni,ko kaji nace Mummy? Mummy ai na fika kaunarta Aamna ta wayance Kar yaci ubanta,Baba ne yayi karfin Hali yace ae da ita ake din sai me? Aamna Tace Ni bada ita nake ba Baba,Mama Tace Iyyee.....Juyawa Ahmad yayi yace Zan dawo gidan Nan zamu hadu ya Haye machine dinsa ya bashi wuta sannan ya dage kafa Daya sama yazo har Gaban su Baba ya kotse machine din tare da bashi wuta ya bulbulesu da hayaki ya fita a tsiyace. Aamna ce ta daka tsalle tare da nuna Bayan Ahmad da yatsa Tace sai nayi maganinka zaka dawo ne sai ka sani,sai na cije ka wallahi a gadon baya,Iyayen Nawa zaka yiwa haka,zaka San ni Yar halak ce. Mama Tace ke dalla rufe Mana Baki, banza matsoraciyar banza kin Gama cika Mana Baki gashi a gabanki ya ci Mana mutunci Baki ce komai ba sai da ya tafi,Baba Kuwa Takaicin Aamna yasa yace tir dake Aamna muje ciki mu kiyi Mana girki muci mu Sha. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA🌵🌵 31-35 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne MAMAN MURTALA HAFSATOU 'YAR BAIWA INNARO AISHA SALIHU UBAIDAT HARUNA Aamna da sauri ta fada kitchen sabo da so takeyi suyi sauri su tafi,babu Bata lokaci tayi musu farfesun kaji,ta musu jallof din taliya Tasha kifi da kayan lambu sai lemuka da ruwa ta kawo musu,Suka zauna Suka dinga kwasar girki, Baba Yana yin Loma Daya yace Allahu Akbar sai na tuna da Uwar dakina Dake Kano Hajiya Sahura lokacin da aka kaini almajiranta na Zama Yaron gidanta,Haka take dafa Taliya Malam Kamar daga Otel(Hotel),Mama Tace taji tarihu kaga inda tsiya tayi tafiyar dogon zango,ai a Nan gidan Tsiya Balaguro tayi ba tafiya ba cewar Baba,Aamna tana ta dariya Tace ai kudi yake bani da yawa,kwana na Daya na fara fita,ba ruwansa da wani Ni Amaryace inda Naga Dame nake zuwa,Baba ya tsurawa Aamna Ido yace indai akan irin wannan cefanen ne ki dinga ficiwarki daga Nan ki dinga biyowa ta gida kina yaga mana. Sai da suka koshi,Baba yace zuba min wani farfesun a flask na tafi dashi idan munje gida zamu ci da breadi,Aamna cikin sauri ta samo flask karami ta kwashe ta bar kadan ta hada musu harda lemuka,cikin lefenta ta dakko wata atamfa da turaruka ta bawa Mama atamfar turaren Kuma ta bawa Baba,Sai Jin dadi sukeyi,Mama ta zuge Jakarta ta sake zaro wata laya da guru na damtse ta mikawa Aamna Tace ungo Bude Damtsanki ki daura wannan,Aamna ta Bata Fuska kamar zatayi kuka Tace Mama Kinga fa wani a hips Dina kince idan na cire Baku yafe min ba Haka kaina layu ne fa har biyu idan zanyi wanka nake cirewa Ina Yi nake maidawa Kamar yanda kika ce shima Kar na cire,Mama ta Bata Rai Tace saka wannan layar a gashinki itama ki soketa ga pin Nan a jiki Kuma wallahi kika cire Bamu yafe ba,Aamna ta karba ta soke Laya ta Uku cikin gashinta,ta dauki guru ta bude farin damtsenta ta daura,Dake tana da haske sai ya Mata kyau. Mama Tace to Haka ake so,sai magana ta karshe zamu Kira surakanki a waya mu fada musu kina cikin wahala zamu dauke Yar mu idan suna so ki zauna sai sun turo Mana kudi sabo da Haka ko sun kiraki sun tambaya kice Haka magana take wallahi idan kika ce ba Haka ba kinji mun rantse sai kin bar gidan Nan ta karfi sannan sai Kinga matakin da zamu dauka a kanki. Aamna tace Haba Baba Wai me yasa kuke Haka ne,Ni fa ba sonsa nakeyi ba,Kuma ma Ni Nan gaba barin gidan zanyi Akan me zaku karbar Musu kudi,a gidan Ubanwa Zaki bar gida? Sai mun Gama kwasar rabon mu tukun yarinya,Shuru Aamna tayi Tace shike Nan to kuje Allah ya kiyaye Hanya na gode,sauri takeyi su tafi Kar ya dawo gidan,Mikewa sukayi ta rakasu Suka tafi,Suna tafiya ta dawo ta hau gyaran gidan sai da ko Ina ya fito fes sannan taci abinci ta sheka wanka tayi Sallar Azahar,Kwalliya tayi cikin wata English gown silk maroon,me Hannun vest tayi mugun Mata kyau ta fito da shape dinta matuka,Fitowa tayi ta koma kitchen ta duba farfesun data ragewa Ahmad,Sai tayi cabbage soup ta Sha kifi tayi sakwara,me Gadi ta bawa sauran ta Ajiye ta zauna a Palo tana kallo,Bayan tayi Sallar la'asar tana karatun novel a Wayarta taji ya shigo Yana waya yace Daddy Kuma me ya same shi? Yana asibiti? Bazan zo ba Allah ya bashi lafiya ya furta tare da Zama a saman kujera ya rufe Ido tare da dafe Kansa. Duk da baiyi Sallama ba sai tace me ya samu Daddy din? Wani kallon wulakanci ya Mata yace ina ruwanki ko son gulma,na fada Miki ki daina shiga safgata Zan Tara Miki gajiya wallahi tam,Shuru tayi Tace abincin fa? Baza'a ci ba ko dole ne sai naci girkinki? Wai me yasa kike son takura min ne? Sabo da Kai Mijina na ne shi yasa,Baki gaji da duka bane Naga Alama,Kai baka gajiya da fada da mace? Ko kunya baka ji fada da mace,idan kana Jin Kai Namiji ne kaje can waje kuyi da maza Mana kaga yanda zasu maka jina jina,ka zauna a Nan Ni sabo da mace ce sai dukana kake Yi wallahi sai Allah ya tambayeka,ranar lahira sai Allah ya Kamaka da hakki na,Murmushi yayi na rainin hankali yace sai na karasa wannan idon Daya shima a manne shi,Sai lokacin Aamna ta tuna ma Idonta a manne yake,Haka duk inda aka ganta sai dai taji Ana ta Mata Sannu da Allah ya sawwake,tana sani Tace zo na yanke maka farce gasu Nan sun fara taruwa,kwanciya yayi a kujerar tare da juya Mata Baya yace wannan karon wallahi kika kuskura ko da Wasa kika taba min farce saina ballaki a gidan Nan,ka godewa Allah ba sajenka da gemunka na yanke ba,Banza ya mata yana tunanin Daddy da akace Hawan jini ya kamashi saura kadan yayi paralyse. Damuwa ya Shiga a ransa sosai gashi shi bazai iya Addua ba baida time,juyowa yayi Aamna ta kalleshi da sauri,Je kiyi Alwala,tsoro ya Kama Aamna a ranta tace ko hakkinsa zai karba yau na Shiga Uku maybe nafeelar sunna zamuyi daga Nan sai Sex,Idonta ne ya kawo kwalla Tace Alwalar me Kuma? Fuska ya Bata yace Zan fa zaneki wallahi kije nace kiyi Alwala ki zo,Aamna Tace wayyo Uwata na shiga Uku,shi ya manta ma Daren farko Ana Alwala da Nafeela,Aamna tace ka Bari sai dare Dan Allah kayi min Rai,Yace Bari na tashi kiga tsayi na,da sauri ta tafi tayi Alwala ta fito da Hijab a Hannunta tana kuka Hawaye shabe Shabe a fuskarta,Alwalar kikewa kuka duk tsoron Allah naki da kurin Sallah da waye waye,Aamna tayi Shuru tana Hawaye Tace Dan Allah kayi hakuri ance da zafi,zafin me? Alwalar ce da zafi? Ya tambaya Yana zaro Mata Ido,Sallayar Dake Hannunta ta shimfida yace to kalli gabas ki fara Nafeela,Aamna Tace bangane ba,ba tare zamu Yi ba? Yace Kiyi Nafeela nace ki yiwa Daddy Addua Allah ya bashi lafiya a madadi na,Ni bazan iya Yi bane. Baki Aamna ta Bude sai lokacin taji kunyar kukanta na banza na tunanin banzan ta,Tace Bari ayi magrib,tana yin Sallar Magriba ta fara Nafeela. Haka tayi ta Nafeela tana yiwa Daddy Addua Allah ya bashi lafiya,sai da ta idar Tace nayi to,ko magana baiyi ba,Wayarta ta jawo ta Kira Mummy, bugu Daya ta daga Bayan sun gaisa Aamna Tace Mummy ya jikin Daddy din? Mummy tana murmushi tace waye ya fada Miki? Aamna ta saci Kallonsa yace in kika ce Ni na fada Miki sai na karya ki yau,Aamna Tace lokacin da kuke waya Ina wajen,Mummy Tace okay da sauki sosai gobe ma muke sa ran Sallama mu koma gida,yaya fatan dai rigimar Bata Yi yawa ba? Aamna Tace ae Mummy,Baba ya kirani jiya,Gaban Aamna ya fadi,Mummy Tace banji Dadin abinda suka Iske Ahmad ya Miki ba,naga Baba yaji Haushi da yawa yace zai dauke ki daga gidan,Kunya ta Kama Aamna Tace Mummy ki kyale Baba rikicin tsufa yake Yi. Dariya Mummy tayi tace Mama Kuma Ashe Business take so ta fara lokacin Muna cikin damuwa a asibiti abinda ta Nema Bai samu ba sai dubu dari hudu ta samu kacal Amma Inshaallah Zan Kara Mata wasu,Aamna tayi Shuru sabo da Matukar kunya da nauyi data ji, Tace kuyi Hakuri Mummy wallahi Ni ba sa Hannun na ciki,ban San zancen ba ma,Mummy ta fuskanci Aamna ta Kuma Gane su Baba Kawai kyalewa tayi,karki damu Aamna na fihimci lamarin,kici gaba da Hakuri Zama Dan Allah kinji,Aamna Tace Inshaallah ba matsala,kina bukatar kudi ko wani Abu? Aamna tayi murmushi Tace a'a Mummy ba abinda nake bukata komai Yana Yi min idan na tambaya,kin tabbatar? Aamna Tace ae Mummy kiyiwa Daddy Sannu da jiki a gaisar min da Humaira Kuma,Mummy ta dinga yiwa Aamna godiya sannan ta kashe wayar. Ahmad ransa ya tunzura Jin irin godiyar da Mummy ke Mata to uban me tayi ake gode mata,Cikin masifa yace ni baza a gode min ba Dana dauki kaddara nake zama dake cikin kunci sai ke Za'a godewa Ana wani sa Miki Albarka ke ga fitsararriya ko? Harda wani Jin dadi kina to Mummy...ya makale Murya tare da gwada muryar Aamna yanda take magana,Aamna Tace Wai Kai me yasa baka da kirki ne? Yace ke dalla rufe min Baki ke Wato an Baki lasisi ko harda wani Kara siyo waya Vivo sabuwa,wannan ba gata bane, ke ga tsigalalliya ko kina wani girgiza da kafada ya gwada girgizar Aamna Idan tana masifa,Aamna ta kyalkyale da Dariya gashinsa ya girgiza tare da gyara sabon kitson calabarsa,Aamna Tace shike Nan Zan Kai karar ka wajen Mummy,Yace idan kina yiwa bushashen tsohonki kije ki Kai karar tawa ki gani idan akwai Wanda ya Isa ya tankwara Ni ko yasa naji magana,an fada Miki wani Jin Magana nakeyi. Baki Aamna ta Bude Tace ai Ni tsoho na ka ganshi me kiba ne,Ashe Ahmad ba Baba yake nufi ba yasan Baban Aamna na asali Dan Sudan wani mugun bushashen tsoho ne,ramarsa ta baci tunda lokacin da wayonsa Bai manta shi ba,Sai yace kije ki binciki tarihinki yarinya kiji waye tsohonki Dan lukuti ne ko kuwa,Aamna ta Mike tsaye tace Allah ban yafe ba sai na cijeka ta fado Kansa Kamar wata Kura ta Bude Baki da gaske ta Kai Masa cizo a wuya,wuyanta ya cafka da hannunsa ya shaketa sosai ta fara kakari Idonta ya firfito kamar zata sheka lahira ya hankadata gefe ta Fadi a kasa dabar, mikewa yayi zai fita ta jawo rigarsa Iya karfinta,ya juyo ya dauketa gaba Daya ya jefata saman kujera Kamar Yana wrestling,Aamna ta cakumo kafafunsa ya Fado gefenta,Idonsa Wanda ya canja yayi ja sabo da kwaya ta motsa ya watsa Mata wani kallo ai sai ta Mike ta arce da gudu. Key din machine dinsa ya dauka ya fice abinsa ya hau machine kenan yaji an jefo Masa Robar ruwa a Kansa kwas,Kansa ya daga sama yaga Aamna ce ta baya balcony dinta ta sama tana cewa aje a Kai karata wajen human Right idan an isa,ko kazo ka dokeni,Yatsunsa ya wara ya Mata dakuwa Wato ambola Aamna ta Masa gwalo,yace zamu hadu ne da karfi yanda zata ji,mu hadu Mana gani ta matso jikin karfen wajen Dan Allah taho mu hadu tayi girgizarta da kafada,saura kadan yayi Dariya ya matse yace Fuck you....Aamna Tace Dadi ne da shi come and fuck me,Dariyarsa ya guntse yace Yar Iska ce ke ai,nafi karfin Iska sai dai Guguwa,Machine dinsa ya kotse yayi waje abinsa ya barta tana ta dariya. Tunda ya fita Bai dawo ba sai wurin 4am ya shigo a chake yasha da yawa,tunda ya Shiga Dakinsa Bai tashi ba har gari ya waye,12pm Aamna ta Gama komai tana ta duba shi Bai tashi ba,Haka taje ta wanke Masa toilet ta gyara dakin bed din ne Kawai bata gyara ba kasancewar Yana kwance,Fitowa tayi ta zauna sanye cikin doguwar rigar Shadda purple ta Sha kyau,sallamar Siyama ta ji,ta Mike Suka Rungume juna Siyama Tace ba Zama nazo Yi ba maza muje na zabi kayan,Bedroom Suka haura Aamna ta bude Mata akwatuna Tace zabi,da mamaki sai taga Siyama ba hankali duk kayan masu tsadar take zabewa har ta zabi kala biyar ta koma Kan Arabian dress,ta zabi English wear, ta zabi Inners,Aamna gashi ita Tace ta zabi abinda take so tana ji tana gani Siyama ta zuba a katuwar leda,Aamna Kamar ta kwace Amma ta danne zuciyarta Suka fito haka,suna Fitowa Ahmad Yana Fitowa ya Sha wanka cikin kana Nan kayansa kamar kullum 3qtr da t-shirt marasa nauyi ne da Alama ba fita zaiyi ba,Kallo Daya ya musu yace Mene a Nan? Ya dakawa Siyama Tsawa. Da sauri Aamna ta firgita Tace ka...Kaya...kaya ne na lefe kasan Ana Dan bawa kawa wasu abin,Ya Mika Hannu yace bani cikin tsawa....Siyama jiki na rawa ta Mika Masa ledojin ya fisge kuwa tare da budewa yaga Kaya da uban yawa,ya kalli Aamna yace waye ya Siya Miki kayan Answer me,Aamna Tace Mummy ce,yace ke ta siyawa ko wannan jakar ya nuna Siyama da yatsa,Aamna Tace Ni,yace to ba don Mummy tana sonki ba ta siya Miki shine Zaki bayar sabo da ba kudinki bane,Mummy ta me yasa bakya respecting din Mummy ne Wai duk son da take miki,Siyama ya kalla yace last warning duk abinda Zaki ki tsaya a Downstairs main Palo Kar na sake ganinki a sama Nan,sabo da idan na sake ganinki baza kiso abinda Zan Miki ba,baza kiji dadin abinda Zan Miki daga ke har kawar taki,bi hanya....ya furta da karaji,Siyama tayi kasa da gudu,Aamna zata bita yace wait...tafin hannunsa ya Buda kamar zai mareta yace karaso ki Mari kanki da kanki. Aamna da sauri tazo ta Kara kumatunta a hannunsa,yace Baki ji zafi ba da karfi Zaki taho ki taskawa kanki mari,Matsawa tayi baya ta taho da gudu tare da hannunsa da Hannunta ta Kara kumatunta a tafin hannunsa da karfi ta taskawa kanta Mari yace Good tare da murde Mata kunne yace daga yau idan kika sake ebar wa Mummy Kaya kika bayar sai na babbalaki nayi raga raga dake. sannan duk kayan Dana Baki kudi kika siya idan na samu kin bayar zaki ga abinda Zan Miki,Aamna Tace sabo da tsumulmula ko me? Yace yes...son kudi ne Dani...Ina son kudi...kayan ta kwashe ta maida daki sai murna takeyi gwara Daya kwace dama Bata Yi Niyyar bayarwa da yawa Haka ba,kafin ta fito tuni Siyama tana Napep ma sabo da tsoro gashi Kuma tana sonsa a Kansa take ta wulakanta saurayinta ya rasa me yayi mata ya kasa Gane Kan Siyama. Aamna cikin Fushi ta dawo Palo ta zauna kan kujera me kallon wacce Ahmad ke zaune sai harararsa takeyi,Tace abinda kake min Sam bana Jin dadi kawayena da Yan Uwana gaskiya gaskiya bana son abinda kake musu,bana wulakanta naka Nima karka wulakanta min nawa ehe,Nifa akan wannan bazan fa yarda ba,Nima kwayar Nan na Iyata,aikin Yan giya na iya shi nima,Haka Kawai in Banda kaddara ma Dana dorawa kaina,ga maza can suna kauna ta,ga masu kudi na gari masu Addini Wanda zasu kula Dani naki yarda dasu,banga laifinka ba laifi nane,Nan..nan Affan ya dawo daga malaysia ya dawo da kudi da mota Yana rokata naki yarda,Nan su Deeni Dan gidan Dan Majalisar jaha sakakina yasa kawata ta kwace min shi Ina ji Ina gani, ga bushashena Kamalu naci Masa mutunci a banza ya gudu. Dama ance kamatuddini tudan yanda nace Masa bushashe Haka tun ba ayi nisa ba gashi ka Rama Masa Ni Babana Mahaifi kacewa tsotsatse,tun anan duniya gashi Ina gani Allah na tuba Amma gaskiya Ina cin ubana a kasar nan,Ina karba a jikina wallahi,ta ko Ina duniya ta min daurin Alawa ko Ina ba sauki anyi min kika kaka,na Shiga tsaka me wuya,Baki Gama Shiga masifa ba yanzu kika fara tunda kika yarda kika aureni cewar Ahmad ,Aamna tana huci Tace Ina ma mu Mata aka bawa damar saki ko kishiya wallahi da tuni na maka saki dari da talatin da biyar, ko na auro maka kishiyoyi har Uku,kishiya na farko Mashkoor babban abokinka Zan kashe makudan kudade na auro shi sabo da na huce takaicinka,na biyu na Nemo tsohon saurayina Affan,na Uku nayi manage da Mubaraq Tawaga Kai Kuma Kaine Uwar gida,ai wlh da kaga wulakanci,duk ranar kwananka ba abinda Zan tsinana maka sai dai sha'awa ta kashe ka,Amma a sauran kwanan su Affan kullum asubar fari zaka ga mun fito yin wankar tsarki. Dariya ce ta Kama Ahmad yace ai ke dakikiya ce shi yasa kike wannan tunanin,Namiji Daya ma wallahi yafi karfinki Indai ya amsa sunansa Namiji Irina bare har maza hudu,,Dariya Aamna tayi Tace a Ina ka amsa sunanka namijin Kai dalla duk kwayoyi da giya sun Gama kashe ka,Kai da tsoron Boobs ma kakeyi,Ahmad yace ae naji ai tsoro halak ne,bana sonsu ne shi yasa,Ni ba birgeni sukeyi ba Mene abin sha'awa a Nan Abu cako cako Haka a kirji ba kyan gani,ka taba Abu kamar wani jikin mage ba dadi Haka yagwalgwal,Dariya Aamna take tayi Tace na fada maka kwayoyi sun kashe ka,ka daina Sha wallahi ka samawa kanka lafiya,wannan abubuwan ka tambaya kaji mu kanmu idan Muka je wanka dadin wanke su muke ji bare Kuma maza,Kama fara sonsu tun yanzu sabo da idan na gaji duk ranar dana je na kalli film jam'iyata ta motsa zanzo ne dole ka koyi sonsu. Fuska ya Bata yace ko da Wasa kika zo Zaki Sha duka ne, tunda ke Baki da kunya Ni Ina da kunya ni Fulani ne ni,Aamna yau tana mamaki Ashe Yana magana Haka,Tace Kaine me kunyar lallai,Shi yasa nace wa Mummy ta Bari na samo yarinya karama Yar secondary wacce Bata San komai ba me hankali da kunya Amma Mummy Taki yarda ta dakko min me Degree wacce ta Gama balaga a waje ta fitsare kafafunta. Aamna Tace kamar ka sani ai idan muka wuce 22yrs to Kar muke ganin kowa,Ahmad yayi Shuru Bai sake magana ba har ta Gama surutunta ta koma kallon Indian film,Yana ta kallon soyayya ya tabe Baki yace bani remote,Mika Masa tayi ya canja Chanel ya Kai Wrestling,yace ga inda ake abin arziki ba love ba,kasa ta lalace komai love,gidan radio love,Yan film love,writers love,matasa love,tsofaffi love,tsoho ya tsufa maimakon ya Bari aci gaba da dama Masa kunu Yana Sha har ya koma lahira a'a sai kaji ya Kara aure ko aji matarsa ta Haihu,tsohuwa sai aga tana Shan maganin Mata abin haushi ta Aiki mutum siyo min Zuma da gumbar Mata zaka ce,Aamna ta kyalkyale da Dariya harda rike ciki ya gwada yanda tsohuwar ke magana tana makyarkyata da Murya,Shi kuwa ko Dariya bayayi kamar ba shine yake Maganar ba. A Ina kaga tsohuwar ta fada,jajayen lips dinsa ya tsuke, Baki ya turo gaba Yana girgiza Kai kwaya ta motsa yace Maman Jibson ce take Aiken wani Dan yaronta Islamic chemist,Aamna tayi Dariya Tace Sallar Azahar lokaci yayi kaji ana Kira,ba yanzu zanyi ba sai ta nuna luguf,zata sake magana ya daka Mata Tsawa karki dameni Dan Kinga nayi magana dake Ina cikin Good mood ne Daddy ya warke karki kawo min raini ba Dan arziki bane ni yawwa kije kiyi sallarki ba ruwanki Dani,ko ke nake yiwa Sallar? An fada Miki zanyi Abu Dan wani Dan Adam ne eyeee? Aamna Tace a'a,yace to ki daina shiga hurumina,bana Shiga harkarki ko Kinga Ina Shiga rayuwarki? Ina ruwana da rayuwarki,Ina ruwanki da harkata,Tace babu yace to San Inda dare ya Miki ko na zubar Miki da hakora,Sum sum Aamna ta wuce taje tayi Sallah,ko da ta fito sai gani tayi har ya dafa Indomie da kwai ga coffee ya hada Yana sha abinsa,Yana gamawa yayi ficewarsa,Kitchen ta Shiga itama. Wasa Wasa Har Aamna ta kwashe wata Uku a gidan Ahmad kullum a haka suke ba Wani canji,halinsa ya ishe ta,ta Gama gajiya da zaman gidan gaba Daya,yanda ta sanshi tun farko Bai canja ba,ga Kuma Siyama da ta nacewa gidanta kullum shi Kuma Yana ci musu mutunci Wanda Haka Sam baiwa Aamna Dadi a gabanta Ana ciwa kawarta mutunci sabo da Bata San kudirin Siyama ba,Siyama tuni ta sallami Faisal ta sa an mayar Masa kudin auren da ya kawo,Faisal ya shiga damuwa Amma ba yanda ya iya Haka ya hakura bayan ya Sha fama da zuciyarsa,Siyama kuwa Bata fadawa Aamna ta Kori saurayinta ba sabo da kar a gano ta,gashi kullum Kara son Ahmad takeyi kamar hauka. Bangaren su Mama kuwa tuni kusa da gidansu ta bude katon shago tana siyar da Inner wears na maza da Mata,masu kyau take siya idan anyo order daga kasashen waje,ta gyara ciki komai glass da glass ne Dan karamin shago, Baba ne ya cika Mata kudin Suka Bude abinsu sannan a Kofar shagon daga gefe kayan kamshi take siyarwa citta,barkono,kanunfari da masoro da su Kimba da gyadar curry etc,tana Zama a shagon da kanta sannan ta sa wani yaro a ciki Dan makwaftansu da taga Yana da Dan hankali tana biyansa Dan abinda ba a rasa ba,Zuhra Bata San duk abinda ke faruwa ba sabo da ita Bata Bayan su Baba,duk abinda suke Yi Bata Jin dadi tana Kuma kokarin yi musu Nasiha,ganin Haka sai Suka daina fada Mata komai,gidan Aamna kuwa Bata zuwa sosai sabo da halin Ahmad taga baya son Baki a gidansa. Da Yamma Aamna tana share sharenta tana mopping ko Ina Ahmad Yana kallonta ta gama,sai kunci yakeyi Yana faman huci,duk abinda take Masa baya gani,tana gamawa da ciki ta fita compound kasancewar me Gadi Musa ya tafi Kauye wajen Iyalansa sai Nan da sati biyu ko Uku zai dawo,Duk girman Compound din Haka ta gyara shi,Ahmad ya fito yace sai ta wanke Masa machine Haka ta wanke Masa tas,ta Sha wahala da kyar take mikewa,Yana Fitowa ya kalli Tyre Kawai ya juyo ya kwashe ta da Mari a saman Idonta Wanda yake mata ciwo,Botikin ruwan data wanke Masa Machine ya dauka ya juye Mata ruwan a kanta gaba Daya,Aamna ta fashe da kuka yayo kanta ta matsa gefe sai ga Siyama ta shugo da sauri Tace lafiya Ahmad????....Kafin ta rufe Baki ya fyallawa Siyama nata rabon marin Yana cewa Yan Iska matsiyata,Aamna duk dukan da ya Mata Bata ji haushi ba sai Akan ya Mari Siyama,Machine dinsa ya buga ya fice,Siyama ta fara zuga Aamna Tace wallahi ki bar gidan Nan Aamna Idan ba so kike Watarana a tsinci gawarki ba,Wannan Bai da hankali kwaya da giya sun Gama da kwakwalwarsa,tun dare Bai Miki ba ki bar Masa gida,gwara ki rasa aurenki Akan wannan halin da kike ciki,auren me auren wahala,Iyayensa su na can sun barki idan an kashe ki Basu da asara,Dansu Yana raye suna da kudi abinsu kece a kasa Aamna ki Kama gabanki kinji na fada miki. Aamna Tace Mummy fa ba Haka Mukayi da ita ba,Mummy din banza,wallahi ki farka daga mafarki Aamna ko sonsa kikeyi? Da sauri Aamna Tace Allah ya kiyaye min tir na so wannan mutumin,Siyama taji Dadi a ranta Tace to ki hada kayanki ki tafi gidanku na tabbata Baba bazai Bari ki dawo ba ki fitar da kanki daga wannan masifa,Aamna Tace gaskiya kika fada na gode Siyama ke me kauna tace Inshaallah yau a gidanmu Zan kwana Bari na hada kayana idan ya dawo da wuri Zan tafi yau idan Bai dawo ba gobe da sassafe Zan taho,Siyama Tace yafiye Miki Ni na tafi ta fice abinta,Duk Hirar da sukeyi Ahmad Yana jinsu ashe Daya fita da machine ta Kofar me Gadi ya shigo Dake Kofar me Gadi biyu ce akwai ta ciki akwai ta waje,Dama shi ya gaji da su so yake ta bar Masa gida ya samu Freedom ya gaji da shishingi da take masa,yafi so ta Kori kanta da kanta sabo da Mummy Kar taga laifinsa,farin ciki ya kamashi,sabo da tayi sauri ma ta bar Masa gida sai da 5pm tayi sai gashi ya dawo gidan da fara'a Yana ta rera wakar Bob merly Yana girgiza Kansa Yana lumshe Ido har Palo. Sharhi Dan Allah AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 36-40 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE. ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne ZAHRAH RAMALURV JIDDAH ZEEY SOORAJ HAJIYA ABOU SERLMAH I LOVE MY SAIF Aamna Tana kitchen kamshi na tashi ta fito tare da furta Sannu da zuwa,Annurin fuskarsa ne ya gushe ransa ya dugunzuma ganin Bata da alamar tafiya,Tsaki Yaja yayi waje abinsa Bai dawo ba sai 9pm zazzabi ya dawo da shi gida,tana kallo a Palo taga ya shigo Yana kankame jiki Yana Rawar sanyi da sauri ya fada saman doguwar kujera ya dunkule,Aamna Tace lafiya? Harara ya watsa Mata tare da furta duk bake kika jawo ba,bakin cikinki ya zuba min zazzabi,Aamna Tace au nice? da wacece idan ba ke ba Kawai kinzo kin tare min fili da Fadin gida,ba dama na samu Freedom na Wala Ni da gida na,Dariya tayi Tace to Yi hakuri,bazan hakura ba sai kin bar gidan Nan cewar Ahmad,Ni kwata kwata ba kaunarki nakeyi ba,Sam Baki min ba tsarin zubinki gaba Daya Bai min ba,Aamna Tace duk kyan Nan nawa? Wani kyau ne Dake an fada Miki kyau nake Nema idan kyau ne naje na kalli kaina Mana har Zaki fada min kyau? Dariya ta Kama Aamna yace ke Baki da kunya ko tsagera ko fitsararriya ko? Idan ba tsaurin Ido ba ki kalle Ni kice me? Ki tafi gidanku na gaji Dake Ni,Ina Nan daram wallahi baka Isa na bar gidan Nan ba. Bargo ta Mike taje ta kawo tare da lulluba Masa Tace ko na shigo ciki na Dan jona maka heater? Wlh idan kika shigo bargon Nan yau Allah ne yasan irin dukan tsiyar da Zan miki,Dauko min magani a dakina paracetamol da ruwa,Aamna taje ta kawo Masa ya Mike ya karba ya Sha,Tace ko a Kira Likita ya maka Allura maybe Malaria ce,Ni ba a min Allura babu Wanda zai sokar min duwawu ko Hannu,Ina ma Likitanci na karanta ko Yar Hygiene din Nan da wallahi sai na tsira ma Allura cewar Aamna ta furta tare da daukan waya ta Kira likitan da Mummy ta hada ta da shi Wanda ke duba Ahmad,Bayan sun gaisa ta fada Masa,a daren yazo ya duba Ahmad ya rubuta magunguna yace malaria ce,Bayan ya tafi Aamna ta Aiki Musa ya siyo Magungunan. Lokacin jikinsa yayi sauki ta hado Masa cous cous da miyar kwai ta kawo ya karba yaci ba laifi ta bashi Magungunan Tace sha,yace sai ki dura min ta karfi bazan Sha ba,Aamna Tace okay sabo da ba kwayar maye bace ko? Yace ae ai Wanda baya shaye shaye ya bar Dadi ya furta da slow, Zan fadawa Mummy Allah gwara ka karba ka Sha, ki fada Mata Mana tsoro nake ji ke Baki ga ba Wanda yake fada min naji bane?na gani Dan Allah ka Sha zaka daina zazzabin,Da kyar ya karba ya Sha yace gobe bazan Sha ba,ya tashi ya koma bedroom dinsa, kwana Uku Aamna tana fama da shi da kyar ta samu ya Gama shanye maganin Kuma ya warke fes. Siyama ce ta kwada Sallama tare da shigowa,ta Iske su Mashkoor a palon lokacin Aamna tana bedroom tana bacci,ko nemanta Bata Yi ba ta zauna wajen Jibson ta kalle su Har Ahmad Wanda ke latsa waya,Ta kalli kayan mayen tace gaskiya Kuna birge Ni wallahi,Musamman idan na kalli giyar Nan Dake cikin dundumemiyar kwalaba,Ina so inga Ana daga Dunduma a duniya,Suka kwashe Dariya banda Ahmad,Jibson yace kaji fa sabo suna Wai Dunduma,Siyama taji Dadi Tace Ni ko Mijina naga Yana daga Dunduma bazan damu ba Zan koma Taya shi Sha ne, Mashkoor yace Baki da hankali mu kanmu so muke mu daina mun kasa Amma ke kina mace kina wani Eh yane Haba Yawa kike,Siyama taji haushi a ranta ganin Bata birge su ba sai ta tashi zata haura sama wajen Aamna Ahmad ya daga Mata Uwar Tsawa yace idan Baki bar gidan Nan ba wallahi na tashi ko ya Mike a zabure Yana cewa Upstairs din na Ubanki ne? Ko da kwandalar Ubanki aka gina gidan da har Zaki kallar min sirrin Dakuna,Shegiya da kanki Kamar butar Shayi, da gudu tayi hanya ta fice. Jin Hayaniya Aamna ta tashi ta fito itama tana murje Ido Tace lafiya naji Hayaniya?Takalminsa ya cire a zuciye ya Wulla mata yace ai duk ke kika jawo Ina Zama na lafiya Yan Iska Kun dameni a gida wallahi ranar lahira sai Allah ya Kamaki da hakki na,sai Mala'iku sun jibge ki da almudun bakin karfe,Su Mashkoor cikin kwaya Suka ce Kuma ta saman kwakwalwarki zasu dirka miki kinzo kin Sa abokinmu a bacin Rai,Dariya ma Suka Bawa Aamna Tace Dani da ku zamuga Wanda za a jibga a lahira kuci gaba da Shan kwaya ku gani,Kana jinta fa King cewar Jibson,Ku kyaleta Bata da hankali ai. Bayan wasu kwanaki Aamna Sam zaman gidan ya ishe ta shi yasa kullum sai ta fita siyo kayan Miya ko kifi ko nama etc Dan kawai ta Dan shakata,yau ma Shiryawa tayi ta tafi kasuwa zata siyo vegetables, Duk da Haka Siyama Bata hakura ba ta dawo gidan Aamna ta Iske Aamna ta tafi kasuwa,yau ba ma Jibson,Ahmad,Mashkoorsu Uku suna gidan suna kallon ball suna shaye shayensu,su Jibson sun turnuke palon da Hayakin Shisha da Wiwi,Ahmad kuwa Giya yake Sha a kwalabar Yana dagawa,Ganin Siyama ransa ya sake baci Amma baiyi magana ba,Jibson yace mayya an dawo ne? Mashkoor Yana tangadi yace Chaiii....Wai ko harda ke aka Daura Auren ne? Ko Mata biyu aka bashi Bamu Sani ba?to wallahi mu dai Iya Aamna muka ji ance an daura Aure mu ita Muka sheda an daura da ita cewar Mashkoor,Jibson ya kalli Siyama yace ke muna wajen fa har mandiri aka kada Ana Waka Ana Ahmad Angon Aamna Gam.. Gam... sannan kizo ki Raina Mana hankali. Siyama tayi banza da su sai ga Aamna ta dawo Siyama ta Mike Tace balarabiya kin dawo? Da murna Aamna ta wani tuno Dan guntun larabcinta Tace Marhababiki ya Siyama ta wani Rungume Siyama har da Yi mata kiss a kumatu Wai ita Balarabiya,Siyama da munafunci Tace Aina tazhab? Wai ina taje, Azhab Ilal suk cewar Aamna wai da larabci taje kasuwa Wanda da kyar suke tuna Dan abinda suka tsinta wani ma ba daidai suke fada ba,kiyi Hakuri na Dade ban San kinzo ba,Siyama Tace Ma Fi mishkla,Mashkoor yace cab da Kun taimakawa kanku Kun daina Sam Baku iya Larabcin ba,bakinku ya dafe da miyar Kuka zaku Raina mana wayo Baku Iya komai ba,Jibson ya nuna Ahmad yace da kun San irin Larabcin da King keyi ai da Sai Kun Mari kanku da kanki sabo da haushin kanku zaku ji. Aamna Tace Kai ku kiyayeni matar oganku ce Aunty ya kamata Kuna kirana bana Wasa da ku,Dariya sukayi Suka ce Aunty Balaraba daga yau,tun daga wannan Rana kaf abokan Ahmad sai dai sucewa Aamna Aunty Balaraba ita Kuma amsawa takeyi. Washe gari da dare Aamna ta kawowa Ahmad Abinci ganin baici komai ba tun Rana,Ashe hakan data Yi shi haushinta yaji ya tsaneta ya gaji da takura Masa da take yi Kawai ya dauki abincin ya watsa Mata a jikinta stew din Allah yasa ba zafi ta Bata Mata riga,Taji Matukar haushi har ta fusata Tace barin gidan zata Yi ,da sauri ta dakko mayafinta,Yana ganin Haka sai murna ta kamashi,Aamna sai ta ganshi har murmushi yakeyi sai ta fasa tafiyar ta dawo gabansa Tace ranka ya Dade zanje na siyo Abu a shago tayi waje,ransa yayi bakikirin sabo da bacin rai tashi yayi ya tafi wajen Me Gadi Musa,Musa Yana Zaune a Bench Yana waya da matarsa Ahmad ya zauna a Bench din. Musa cikin wayarsa yace da matarsa na Baki Ruhina gaba Daya,da sauri Ahmad ya kalli Musa yace baka da hankali idan ka Bata Ruhinka Kai Kuma ya zaka Yi da rayuwarka kenan ka bata Ruhin ka mutu kenan? Musa ya dagawa Ahmad Hannu Wai yayi shuru yaci gaba da cewa Ni gaba Daya na Baki duniyar Nan gaba daya ma Uwar gida na,Baki Ahmad ya bude da bala'i irin na Yan kwaya yace Kai...wai...to nufinka idan ka Bata Duniya mu da sauran mutane da muke ciki mu tafi Ina a Ina zamu zauna?ko sama ta Daya zamu koma,Musa ya kashe wayar yace a'a ikon Allah Oga Ni Matukar zata ji Dadi ku tafi sama ta goma Mana,Ahmad yace Kai Musa wallahi Indai zaka ci gaba da wannan furucin na soyayya wani ka Bata Duniya wallahi sai na koreka a aiki,akan me Dan wulakanci Muna zaman mu lafiya cikin duniya kace wani kayiwa wata banzar matarka kyautar ta,Baki Musa ya Bude sai Kuma ya tuna Ogan nasa Dan giya ne kwakwalwarsa da motsi Kuma Bai taba soyayya ba shi yasa. Musa yayi Dariya yace Allah huci zuciyarka Oga ai duk kalaman soyayya ne ai duk abin karya ce,Kenan duk karya kake mata? Ahmad ya tambaya Musa yace ai Dan aji Dadi ne,yace kenan soyayyar da ake fada duk karya ce? Musa yace duk ita ake zugawa juna,Nima fa Oga cewa tayi ta bani zuciyarta,Baki Ahmad ya bude yace to yau duk sai kunci ubanku wallahi maza tashi ka dakko Cooler dole ta Ciro zuciyarta ta baka ka saka a Cooler,Musa Dariya ta Gama Kama shi,Yace zaka Yi Dariya da kyau yau sai naga ta inda zaka Ciro Ruhinka Dan Ubanka,Kai ba mala'ikan daukan Rai ba komai ba kace wani ka Bata ranka Dan Ubanka gashi kana motsi kana numfashi yau sai ka Bata ka mutu yanzun Nan,Musa ya sake kecewa da dariya shi Ahmad Bai San soyayya ba,yace tsuguna yau sai ka kinkimi duniya a kanka Baki Daya ka Kai mata har kauyenku sannan bayan ka Kai Mata mu Kuma kazo kasan inda zaka Kai mu,Musa yace kayi Hakuri Oga na fasa Bata wallahi bazan Bata ba na Kuma fasa karbar zuciyar Tata,Ahmad yace Yan iskan banza da ka Bata mu gani mana,Kun zauna Kuna biyewa Mata ya Mike ya fice daga gidan. Aamna zaune take suna waya da Mummy,Mummy Tace Aamna me kike so a duniya ki fada min ko mene Zan Baki,Aamna Tace Mummy da gaske ko mene?Mummy Tace kwarai ai tunda kika iya jure Zama da Dana Ahmad a wannan halin ba abinda bazan Miki ba,Aamna Tace dama Ni burina idan na samu kudi naje Hotel na kama daki nayi kwana Uku Ina Shan ac,azo a gyara min room nayi order abinci naci nayi bacci,sannan Buri na na biyu idan samu kudi nayi wanka da ruwa Eva ko Swan,sannan naci abinci na wanke Hannu na da ruwan Roba,Dariya Mummy tayi Tace Anya kuwa Aamna kin Kai 25yrs ko kema kin fara Shan kwayar ne?Dariya Aamna tayi Tace Allah Mummy,to shike Nan ba yanzu ba ki Bari sai Nan gaba cewar Mummy sannan ta kashe wayar. Da dare Ahmad zaune yake a bedroom dinsa Yana Danna System Aamna ta shiga dauke da tiren Abinci ta Ajiye Masa,Tsaki Yaja da masifa yace ce Miki akayi yunwa nake ji? Bazan ci ba ki dauke abinki tun kafin nayi fatali da shi,Wayarsa ce ta shiga Kara yaja tsaki sannan ya dauka yaga Humaira ce kanwarsa dagawa yayi,yace sis ya akayi ne Mene ne Zaki dameni? Yaya dama gobe zanzo na kawo maka Ziyara,Fuska ya Bata yace ke karki zo min Ni Kun dameni kije gidan Saddeeq Mana sai Dole waje na Zaki zo wannan Candy da kika Yi ai ta zame min masifa tunda damuna zakiyi Dan Allah ki fadawa Daddy ya saka ki a University da wuri Haba,Dariya Humaira tayi ta Shiga rokonsa Dan Allah Yaya so nake fa nazo na ganka please.....Shuru yayi mata,Tace Yaya Dan Allah zanzo kaji....ke mayya karki lashe ni ki tsotse min bargo yau she Zaki zo? Kwana biyu ko Uku Kuma Zaki Yi,Tace to Gobe Yaya da wuri zan bi flight sai kazo ka daukeni a Airport,Alright sai kinzo murna Humaira ke Yi harda godiya,Aamna tana jinsu ta dauke Abincin tayi gaba,me Gadi ta kaiwa gaba Daya. Washe gari 2pm Humaira ta sauka,Aamna gani tayi ya Sha wanka cikin kananan Kaya wasu masu kyau ya fito ya hau wani machine dinsa Irin na Yan achaba Quilin ya tafi Airport,Humaira ta ganshi a machine ita Bata taba Hawa machine ba,ta Rungume shi tana murna ya janye jikinsa Yana dariya yace sis bana son wannan haukan kin girma ku Yan Lagos Baku da tarbiyya,Dariya tayi Tace Kai Yaya Kai fa yanzu muharramina nane fa,ku dai Kawai Kun dauki aladun turawa ya furta tare da rike Mata Hannu yace Oya hau mu tafi,ta kalli machine Tace Yaya kasan fa ban Iya hawa machine ba Kuma ai ya kamata ka aro mota ko ta abokai ce ka dauke Ni,Wanda Basu da motar kuma fa gasu Nan Ni ban Iya aro ba idan Zaki hau ki hau ko wallahi na tafi na barki iskancin banza Kawai ya fara bala'i,Humaira tayi Dariya Tace Kai Yaya ta ja kitson calabarsa tace da a Kano ne da tuni Yan Hisba sun Kamaka,Yace su ma Wanda suka Raina suke wa. Daukanta yayi tare da daura ta a saman machine din,Jakarta Kuma ya daura a gabansa ya figi machine Kamar zai tashi sama Haka yake fyalla uban gudu da Humaira tana ta dariya ita Dariya yake Bata. Aamna tana cin abinci a Dining suka shugo,Humaira ta taho da gudu zata tafi wajen Aamna Tace laaa Auntynmu...Auntynmu...da sauri Ahmad ya cafke ta yace ke wace Auntynki? Baza kije wajenta ba wajena kika zo ko wajenta? Humaira tayi Shuru yace muje sama,Murmushi Aamna tayi tace Barka da zuwa kanwata,Humaira ta dago Mata Hannu zanzo mu gaisa Aunty.....fisgar Hannunta Ahmad yayi Suka tafi sama Yana Hararar Aamna,Aamna Dariya tayi Kawai duk tayi laushi ta nutsu sabo da Duniya garata takeyi. Hana Humaira Fitowa yayi sai da ya tabbatar ta shiga wanka sannan ya fita ya Mata take Away na abinci Wai baza taci na Aamna ba,Yana dawowa ya Iske Aamna da Humaira suna ta Hira suna dariya,Muzurai ya fara Yi ya karaso tare da fisgo hannun Humaira yace wa yace ki kula min kanwata ko kanwarki ce? Aamna tayi Masa shuru kawai, a palon Suka zauna Humaira gudun masifarsa yasa taci abincin nasa ta koshi,Humaira Tace Yaya yanzu a machine kake yawo?gaskiya Daddy Bai kyauta ba,Ke share wannan zancen Ni nafi Jin dadin ma machine Dina,Aamna ya kalla yace Baban wasu kuwa ko Tyre Bai da ita bare mota,Aamna Dariya Kawai tayi,Humaira tana ta Mata magana da Ido,itama Aamna tana maida Mata da Hannu da ido,Ahmad idonsu Kawai yake gani Yana motsi, tashi yayi Kawai ya fice abinsa,Nan Humaira Suka zauna da Aamna suna ta Hira abinsu. Tunda Humaira tazo Aamna ta samu kawa har fita kasuwa sukeyi da yawo Ahmad ya kyalesu harkarsa yake yi,Haka shima Humaira ta takura Masa Wai sai ya kaita yawo a Machine,da ya fita da ita yawo yau suna ta zagawa duk Wanda ya kalli Humaira sai yayi Masa bala'i. Wani guy ya ga Humaira kyakyawa ta birgeshi suna tsaye da Ahmad a jikin machine Yana ce Mata Sis na fada Miki kina saka Nikaf tunda ku Kuna kula da Addini Kawai ku rungumi Islama hannu biyu kina saka Hijab da Nikaf kin fa girma tam,I'm warning you Sis,Humaira tana ta dariya shima ya kalleta ya dinga dariya a jere a jere irin ta Yan Kwaya ba kakkautawa,Humaira Tace Yaya kaima kana ganin kyanka Mata sai kallonka sukeyi,Ke dalla rabu da su sun kalle Ni a banza ai duk wacce ta Soni to Allah ya jarabce ta sabo da ban Dace da a so ni ba sis,Humaira taji tausayinsa kwalla ta cika Mata Ido Tace Yaya Wai waye ya koya maka shaye shaye ne Wai? Handkerchief din Dake hannunsa ya zabga Mata a Fuska yace muje gida Yana Juyawa yaga saurayin Nan ya kafe Humaira da kallo,a fusace ya nufi wajen saurayin yace zaka lalata min kanwa Dan uwarka me kake kallonta kana ayyanawa a ranka? Kana Nan kana ta kallonta kana ayyana wani Abu ko ya Kai Hannu zai chakumo shi Humaira ta rike shi tana bashi Hakuri Dan Allah Yaya ka barshi mu tafi,Fisgewa yayi ya dauki wani karfe da ya gani a kasa zai buga masa,Humaira tace ka gudu wlh,Matashin Nan ya arce a tamanin Dan yaga Ahmad ya birkice lokaci Daya ya haukace,Masifarsa ya maida Kan Humaira yace gobe Zaki tafi,Kuka ta saki Tace Allah Yaya Ni sai nayi sati Daya,Zan mareki gobe ki shirya ai kinyi 3days tafiya dole hau machine mu koma gida. Tunda suka tafi yake masifa Yar wa na lalata da Za'a lalata min kanwa,Bana kallon Yar kowa shine za a kalli kanwata,ko Wannan Yarinyar da akace matata bana kallonta shine wani zaizo ya fara ayyana wani Abu a ransa a Kan kanwata. Humaira da suka koma gida Bayan ya fita ta Bawa Aamna labari,Aamna Tace kwaya ce fa ke sashi wannan zafin zuciyar,Humaira Tace Aunty kina kokari Allah ya bada ladan Ibada,gashi gobe yace dole Zan koma ya zanyi, kiyi Hakuri ki tafi kawai,ai dole cewar Humaira,Haka kuwa washe gari 11pm ya Kai Humaira Airport ta koma lagos. Yau ma kamar ko yaushe Jibson da sauran abokan Ahmad suna Palo suna kallon ball sai ga Siyama ta shigo,Aamna Tana kitchen tana girki ita tana mamakin yanda Siyama ke sintiri a gidanta,Fitowa tayi suka gaisa ta samu wuri ta zauna Aamna ta koma kitchen abinta,Jibson ne ya Sosa gashinsa me uban yawa Wanda ya Gama kone shi ya dawo fari irin na Yan Ball,yace gashin Nan nawa ya kamata na Dan rage shi naji kaikayi yake min,Ahmad ya kalli Siyama Fuska ba Annuri yace ke Sosa Masa gashinsa Mene amfaninki,Siyama ta Bude Baki kamar zata Yi kuka Tace Ni wallahi ba Yar Iska bace,Tsawa ya daka Mata Sosa Masa karki Bari na tashi,Siyama ta Mike jiki na rawa ta tsaya a Bayan Jibson ta nutsa yatsunta a sumarsa tana Sosa Masa,Ido ya lumshe yace shi yasa nake sonka Sarkin mu,Kaji wani Dadi da taushin Hannu,Aamna ce ta fito mamaki ya kasheta,Siyama ta kalleta Tace mijikin ne yace sai nayi ta karasa da Hawaye,Aamna Tace ke Kuma ga banza ko dalla cire hannunki,Ahmad yace tana cirewa ke Zaki Sosa Masa,wallahi baka Isa ba Kai din banza ta janye Siyama Tace na tafi gida,Siyama ta fice da sauri ta tafi,Jibson yace Aunty Balaraba me yasa kike Mana bakin ciki ne? Respect your self Jibson Ogan naku ma Bai Isa ba bare ku ta ja tsaki ta haura sama. Washe gari Ahmad wani wankan Sugar ya dauka ya fito Yana wani tattala kafafu Yana Bouncing ga Uwar Gadara Mashkoor ne yazo da machine dinsa Quiln ya dauke shi tsabar basa jin Magana Ahmad baya ya juya ya hau machine ta baya sun hada baya da mashkoor Yana kallon baya shima me tukawa ya kalli gaba,Headphone ne a kunnensa Yana Jin wakar Shaggy da Sean Paul reggae music,Wani uban gudu Suka tsinkawa a Machine lokacin Aamna taje gidan Zuhra a Hanya suka hadu Mashkoor yace ai sai Aunty da karfi,Da kallo ta bi Ahmad irin zaman tijarar da yayi,Zaginta yayi da Hannu ganin tana kallonsa,Kanta ta dauke ta shiga Napep abin ma Dariya ya Bata. Su kuwa Basu tsaya ko Ina ba sai a Bank,ya Shiga ciki masu bin layi kowa Matsawa yayi ya Basu waje Ganin rigima suke Nema,Wani Dan matashi waya ya dauka Yana kusa da Ahmad Yana waya da budurwarsa kasa kasa yace Baby zuciyata kullum Dake take bugawa,da ace Ana bude zuciya Dana Bude Miki Kinga tawa yanda sonki yake dankare a ciki,Ahmad Yana ji ya juyo da masifa yace to Dan Uwarka sai kaje Likita ya yanka maka kirnjin a gabanta ta gani,Wai kowa sai karya a gidan Uwar wa zuciyarka take bugawa da ita a ciki mutum ne zai Shiga zuciyar mutum ta buga da shi,Ina zuciya Yar karama zata dauki nauyin mutum zaka wani ce da ita take bugawa a ciki,da karfi yake magana ai kowa hankalinsa ya dawo kansu sai Dariya akeyi wani tsoho yace yaro kayi gaskiya wallahi wannan karyar ce ta shigo yanzu ta kalaman soyayya. Tsaki Ahmad Yaja ya fitar da kudi masu yawa, wani yace bawan Allah ka Adana kudin Nan Kar ka hadu da Yan Iskan gari,Mashkoor Yana gefe yace ai mune da kanmu baka gani bane mune ai Yan iskan da kanmu a Nan,wa ya Isa ya zare Mana ido,aka Yi Shuru matar tana irgawa Ahmad kudi tana ajiyewa ya galla Mata Harara yace ke ni fa bana son Daudu Yar Daudu idan Baki iya aikinki ba wallahi na Kai kararki a koreki banza,Wai ke ma'aikaciyar Bank harda wani sa glass da Suit ke a dole kina samun salary,Yan Yara daku Kuna rainawa mutane wayo kuka sake kwanan bank Dinku tattalin arzikinsa zai durkushe mu daina Ajiyar kudi,Duk ma'aikatan sun San Ahmad Yana zuwa Yana musu tijara shi yasa Yana zuwa suke sallamarsa ya tafi,suna gamawa Mashkoor yayi wani Bouncing Suka juya Ahmad yace My man oya muje... muje....Yana wani Gadara,Wandonsa Daya sabulo ya danja kadan,Zasu fita kenan sai ga Aamna ta shigo itama zata ajiye kudi a bank,Ahmad ya kalleta Kamar ba matarsa zata wuce su ya riko Hannunta tare da sa damtsenta ya sakalo wuyanta yayi masifar kunyatata a mutane sai ayi Mata kallon karuwa,Fisgewa tayi ya dauke cak tare da Sabata a kafada yace Muje kudin cefanen kika taho ajiyewa bank Zaki tara? sabo da kar mutane suyi Mata kallon karuwa Tace Dan Allah ka ajiyeni Ina matarka Wai kullum sai kaci Zali na,kaje gida your food is ready, Ni ka ajiyeni wallahi,Ana kallo tana wutsil wutsil yayi waje da ita,Wasu suna cewa kanwarsa ce sabo da suna yanayin Kama sosai,wasu Kuma suce da gaske matarsa ce,wasu suce ko karuwarsu ce,Wani yace ai kuwa wannan zata Sha wahalar Zama da wannan bakin kadarar,wanne ubane Yana gani ya bawa wannan auren yarsa oho. Wajen Machine suka fito,Kamar Yana da hankali shi ya fara Hawa machine din sannan ya Mata Tsawa yace hau,Haka ta hau bayansa Mashkoor ya fige su kamar zai tashi sama,ya dinga kwanto a titi Yana ratsa motoci sai ihu sukeyi Aamna tsoro ya kamata ta kankame Ahmad yace wallahi idan Baki sake Ni ba sai na jefo ki a tsakiyar kwalta,kin sakinsa tayi har suka kaita bakin gate yace sauka,ta sauka yace kina Wasa da Mummy ta kawoki Nan kina wani yawo anyhow,Aamna tayi banza da shi ta shiga gida,Bai Dade ba ya dawo ya Iske ta baje saman Kujera tana bacci,ruwa ya ebo a kitchen ya sheka Mata a Fuska ta tashi a firgice,Harara ta balla Masa ta Mike ta wuce Bedroom dinta tana saka ranar da zata bar gidansa domin ta gaji. Garin Lagos Unguwar Masu hanu da shuni Mummy tana zaune Tare da Humaira a wani gida na ubansu Wanda idan ka kalli gidan ka kallo gidan Ahmad duk kyansa sai ka ganshi gidan talakawa,Humaira ce ta dauki waya Tace Mummy Bari na Kira Yaya naji,Ahmad ta shiga Kira Yana ganin Sis ya daga da sauri tare da furta sweety,Dariya Humaira tayi Tace Yayana ya kake yace Ina lafiya sis ya school,ai nayi Candy Wai ka manta na fada maka Yaya? congrat...Congrat Sis,Yaya Ina matarka? Zamuyi fada fa Ni nasan wata ne Kawai dai nasan Wacce Mummy ke so karki dameni Zan kashe wayata,Sorry Yaya ke ba Wani Yaya kauyanci ne karki Dora min tsufa da wuri wani Yaya,ki kirani Ahmad Dina sak ko King,Mene wani Yaya,ai girmamawa ne Yaya,bana son wani girmamawar mutane a wajena ke dalla Ware kiit ya kashe wayarsa Yana tsaki,Mummy ta kalli Humaira tace ai halin Ahmad sai shi na rasa inda ya gado halin Nan,Allah ya kyauta. Faratan Ahmad sun Kara tsayi sosai,Aamna tana zaune a Palo Yana kwance ta juyo ta kalle shi,Fuska ya Murtuke,Kallonsa ta sake Yi tana kasa a zaune ta jingina da kujerar da yake kwance,kanta ya dafe tare da Danna kanta kasa,Kara ta saki ya fisge dankwalin Atamfarta ya zabga Mata duka dashi,layun Dake kanta ya kalla ya saki Dariya yace nasan na fiki daraja a wajen Allah duk Iskanci na,ke shirka kikeyi yarinya duk Sallar da kike Yi ba a karba,munafukar banza kullum Sallah da karatun Qur'ani Ashe wurin bokaye kike zuwa,shi yasa Allah ya hadaki aure Dani ya daura Miki kaddarar Zama da me cin ubanki,Allah ne yasan irin Barnar da kike yi,Ni duk Iskanci na bana zuwa wajen boka,bana daura guru da Laya,Yan Iska irinku ne masu yiwa Miji Miya da jinjin Haila,fada min ke wanne kikeyi? Aamna Tace Ni wallahi bana zuwa wajen malam,karya kike munafuka,Ni nasan ba Banza Mummy ta auro min ke ba,kin shiga Uku kuwa ke da Jin dadi sai dai ki gani a makwafta,Aamna tayi Mukus ta Mike tare da cire layun gaba Daya ta yaye Hannunta ta Ware gurunta,ta daga rigarta ta zaro na Hips,Baki Ahmad ya bude yace kin Shiga uku,Uku ma sau dubu kika shiga,Ni ba ruwana da tsafinki ki maida abinki kece Zaki ga ba daidai ba a duniya,Zuciyarki ba Allah oh a Haka Shuru Shuru Dake sai daukan carbi da sallah,Ana karatun Qur'ani Ashe duk bana tsoron Allah bane,asubar fari za a jiyo muryarki har makwafta ya makale Murya tare da gwada Muryar Aamna yanda take karatu Wai Allazikhalakhal samawati wal'ard.....Ashe bana tsoron Allah bane wallahi sai Allah ya tambayeki. Aamna tayi Mukus yace ai dole kiyi Shuru ki kalleni kice me? Watarana sai Allah ya Toni asirinki. Dariya Aamna take Yi ta fara warware layun a gabansa da gurun,ya kalli takardar me Rubutu yace ga harafin A'lif da Hya'un can Wato Sunana kenan Ahmad gashi can na gani,Aamna ta tattara ta kone komai,yace a banza yarinya Yar bori mutuniyar banza,Harararsa tayi ya Mike ya bita zai daketa tayi daki da gudu Yace ki dake Ni ki hanani kuka ki min asiri in gani da Ido na ki dawo Kuma ki harareni Ni ban harareki ba sai ke,Zaki fito ne. Washe gari Aamna gajiya tayi ta fito lokacin zai fita tace Yau zaka nemeni ka rasa a gidanka yau Zan tafi gidan ubana,wani farin ciki ya Kama Ahmad yace Dan Allah da gaske kikeyi? Aamna Tace da gaske yau a gidan ubana Zan kwana,wani murmushi ya saki yace gaskiya ban taba sanin kina da kirki ba sai yau,Sabo da Haka yau dole Nima na gwangwaje ki,fada min me kike so? Aamna ta turo Baki ta samu waje,yace ai yau ko me kike so Zan miki,Aamna ta Kama shagwaba Tace koma mene ka bani kyautar Ina so,Ido ya zaro Mata wasu farare tas sai da ta tsorata Yace Gaskiya Zan fada Miki ke Yar Albarka ce babarki ta iya haihuwar Yar halak Haka nake so,yanda kika faranta min yau ace ban Miki kyauta ba nayi asara bani da amfani Kawai na mutu yanzu,Dariya ta Kama Aamna duk akan Tace zata bar Masa gida shine yake wannan murna Haka,wannan kiyayya wacce iri ce,Tunaninta ya katse Mata yace shirya kizo mu tafi na kaiki Shopping ki zabi abinda kike so na ban kwana,Dan Allah Kuma idan kin tafi karki dawo har abada kinji,Aamna Tace to,yace ko Mummy Tace kice a'a ke ba 'yarta bace ta juya Humaira Yarta data haifa Amma ba ke ba,Aamna Tace to,yace Ina jiranki,Da gudu taje sama ta canja wata Arabian gown Dark green me adon black ta Sha kyau ta fito. Machine dinsa ya gyara ta hau ya fisgeta Suka tafi sai wani katafaren Mall,tare suka shiga yace Ina jiranki zabi duk abinda ya miki,Aamna Bata zabi komai ba ta wuce Bangaren Gold ta zabi wata sarka me kyau da zobenta da Dankunne,yace shike Nan abinda kike so? Tace ae,Kai ya girgiza yace to dauka,Haka ta dauka yaje ya biya kudin Suka tafi,ya maidata gida zai fita Tace to saka min da Hannunka kaga anjima Zan tafi,yace ai yau ba abinda Zaki ce banyi ba tunda Zaki bar rayuwata na huta kawo,Mika Masa tayi ya saka Mata sarkar da kansa da dankunnen,Yatsanta ta Mika Masa ya sa Mata zoben,yace Nice one, karfe Nawa Zaki tafi? Aamna Tace 6pm yace Good,ya Mike zai fita Yana ta murna yau zai rabu da Kaya ya huta,Aamna Tace Idan ka dawo sai na tafi,yace to ai da wuri kuwa Zan dawo ya fita Yana ta murna Kamar an Masa albishir da Aljanna,Tun kafin 6pm ya dawo gidan ya shigo Yana wakar Bob merly Yana Bappalo Soldier........Ye...yiye....yiye.....Yee...Yee....yiye... Sharhi fans Dan Allah. AsmaBaffa 10/26/21, 8:52 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 41-45 FREE PAGE DUNIYA TA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne ZEE NANDU KALTUMA ZANNA SADEEY(QUEEN) TEEMA'S COLLECTION .Aamna daga kitchen ta fito tana amsa Masa wakar tasa tana girgiza Kai ta kwala da karfi Ohhhhh.....yeyi..yiye...your.....bappalo soldier....tsit Ahmad yayi murna ta koma ciki da Alama Bata da Niyyar tafiya,Girar sama data kasa ya hade kamar an Aiko Masa da Mummy ta rasu,Aamna kuwa Bayan ya fita zuciyarta ce tayi sanyi ta huce,kafin ya dawo Allah ya yayyafawa zuciyarta sanyi da Hakuri sai ta fasa,Siyama kuwa tunda ta tafi tana sa ran Aamna zata bar gida take ta murna tana uban Kiran Aamna akan taji ko ta bar gidan Amma karshe ma Sai Aamna data Kira Aamna tana dagawa sai taji tana dariya Tace ke Siyama na fasa tafiya na huce,na tuna ma fa Dan kwaya ne ba a ba'a hankalinsa yake ba nayi Masa Uzuru,ko ba komai ma ai Ibada nakeyi,aure Ibada ne zanci gaba da Masa Addua Allah ya shirye shi,Siyama ta danno Mata ashariya Tace wannan bazai taba shiryuwa ba,Ibadar me aure ne kadai Ibada a duniya,Aamna Tace Sanda Zaki auri Faisal ai masifa kika Kama Yi min akan nace kinyi gaggawa yanzu Kuma Ni da gidan mijina Zaki shigo kina min katsaladan a gidan aure na,kin fa Sanni Siyama ki daina uzura min Ina ta Miki Kara bakya gani,Ya kashe Ni ma Mana Ina ruwanki,Siyama Tace Iyyeee....Mrs Ahmad shike Nan kije ki zauna a wahalar,Tsaki Aamna tayi tare da kashe wayarta. Yana Zaune sai kunci yake faman yi,Aamna ta kamo Sunna tv taci sa'a kuwa an saka Wa'azin Malam Ahmad Tijjani,Yana magana akan hatsarin shaye shaye,Yace yanzu Duniya Malam ta lalace da shaye shaye,maza,Mata,Yara,manya,Dattijai,abin haushi ma Yara kanana matasa sun Gama kashe kansu da shaye shayen kayan Maye,abin Allah wadai matashi lafiyayye ya jefa Kansa a halaka,ya Zama marar amfani a rayuwar Musulmai,Musulunci bazai Yi alfahari da su ba,Shan Alkhabis,baza a Sha Aldayyib ba,Mene Alkhabis? Alkhabis shine abinda idan anci ko an Sha bashi da dandano me Dadi a Baki sannan a jiki Yana cutarwa,Aldayyib shine a Baki da Dadi a jiki Kuma Yana da amfani me kyau. Ko matasa jira kuke sai an lissafa muku a Alqurni ance Giya,taba,Wiwi,har Ana kawo ayar Allah Kuna cewa babu Aya,Ina Iyaye wallahi ku farka,Matasa maza da Mata Kuna da hankali,shaye shaye na kwaya,na hayaki na ruwan barasa da sauransu bashi da amfani ga rayuwarku sai cutarwa,Kun Zama marasa amfani a cikin Musulunci,shaye shaye shi kadai yana barna ba adadi a wajenka matashi,na farko shine Kai da lafiya kunyi bankwana,zai kassara maka lafiyar kayan ciki da dama,sannan babbar Illa zai rabaka da Allah,zai rabaka da addinin Allah,zai hanaka Sallah ko kayi ma kana cikin maye baza a karba ba,Azumi ma Sai ya hanaka domin zaka dauka ka kasa kaiwa sabo da dole sai ka Sha kayan Maye zaka zauna lafiya ya Gama bin jininka,sannan zaka sabawa Iyayenka babbar matsala sabo da dole sai ka kangare,ka bijire musu zaka cutar da su. Kasan kuwa wa ake cewa iyaye,ya ku matasa wallahi wallahi ku guji fushin iyaye,masifa ne Mahaifiyar ko Mahaifi su zubar da Hawaye a kanka,basai sun maka Addua ba Kai da ganin dai dai a rayuwarka sai in ka tuba sun yafe maka,wani abin haushin ma Iyalinsa zai dinga zalintar matarsa da yaransa,ya mazaje ku San hakkin matanku mataye Kuma wallahi wallahi kuji tsoron Allah duniyar Nawa take,bakwa ganin halin da ake ciki mafi yawan alamomin tashin kiyama sun bayyana,nuni ake mana mu Kara gyara Hali lokaci Yana matsowa,wallahi a Haka Ana da saura da saura Ana ganin kamar da saura a Haka za a wayi gari aga manyan alamomin tashin Alkiyama sun fara Bayyana..... Ahmad Yana ji ko a gefen rigarsa sabo da yaji Wa'azin Daya fi wannan zafi ma, Canja Chanel yayi yace idan Kinga dama ki gayyato malaman Nigeria kaf su zagayeni ki gani idan zanji na gyara,Aamna Tace ikon Allah a ranta Tace lallai wannan bazai canja ba gwara na nemi mafita,Giyarsa ma taga ya dakko ya Balle Yana korawa, Tsoronsa ya sake shigarta,jiki a sanyaye ta koma dakinta,a palon ya dinga zage zage tana ji,Haka tayi kwana Uku lokacin tuni taje ancire Mata plasta da aka manne Mata ido,sai ganin Idonta yayi tar da Alama ba abinda ya sameshi,Kallo daya ya Mata yace makaryaciyar banza,Shuru tayi sabo da ta gaji da kulashi Yana dukanta,da Yamma kwayarsa ta motsa Aamna taga yanayinsa ba mutunci,taja mutuncinta tana zaune a Palo Siyama ta kwada Sallama,tana shigowa Ahmad ya daka Mata Tsawa yace koma inda kika fito,da sauri ta juya ta fita,Ya zaka koreta?Aamna ta tambaya yace ke wallahi idan Baki daina min magana ba Zan sa wuka na Miki yankan rago,Aamna Jin irin kashen kashen rayuka da akeyi yanzu sai ta tsorata tayi sama da sauri kayan sawarta akwati biyu da duk wani abin bukata shi ta kwasa tayo kasa,Murna wajen Ahmad ba a magana,ko kulashi Bata Yi ba tayi waje,da kanta ta Bude gate sabo da me Gadi baya Nan,Tana fita Napep ta Shiga da kayanta sai gidansu. Su Mama suna ganinta sun San ma matsalar,Baba yace ya Koro ki ne? Aamna tana Hawaye Tace a'a nice Naga bazan Iya Zama ba Yana min barazana da rayuwata shi yasa na taho Kawai,Mama Kamar gaske Tace Allah sarki kiyi Hakuri komai zai dai daita,dama nasan wannan ba abin yarda bane,karki koma ko Iyayensa sun zo Kuma ko me za ayi karki koma,Aamna Tace dama bazan koma ba,kin San shagona yanzu sai kici gaba da kular min da shi kawai sai na sallami Yaron ciki,Aamna da murna Tace Kinga na huta da zaman Kawai,Mama Tace ae kina hada hadarki da customers me ya dameki da wani banza,Zauna ki huta sai gobe ki fara zuwa cewar Baba,Allah sarki Aamna sai murna takeyi. Washe gari kuskuren Aamna da su Baba sun Aamna matar aure da igoyoyi a kanta Bata nemi Izni ba ta shirya ta nufi kantin Mama,Yaron Dake ciki shi ya nunawa Aamna komai yanda abin ke tafiya sannan ya tafi gida shi dadi ma yaji sabo da Mama Bata biyansa Hakkinsa yanda ya kamata sai wahala a banza,Wayar Aamna ce tayi Kara ta duba sai taga Mummy ce,Sai lokacin ta tuna da Aurenta,dagawa tayi Suka gaisa sannan Aamna Bata boye ma Mummy ba ta fada mata komai,Mummy cike da damuwa Tace kinyi kokari Aamna bazan ce ki koma ba,na hakura kiyi zamanki Kawai Ina Jin Ahmad bashi da rabon shiryuwa,Zan ci gaba da Masa Addua,to Mummy Maganar fita fa?ko naje ya bani takardar saki,Mum Dariya tayi Tace karki nemi saki Ni na Baki Izni ki fita duk inda ya Dace Amma ki kula ki Kama kanki ki sani da Aure a kanki,to Inshaallah cewar Aamna sannan Suka Gama waya ,Siyama ta Kira ta Bata labari,Siyama sai murna Tace kinyi dai dai wannan shine magana karki sake ko da Wasa ki koma,ai dama bazan koma ba cewar Aamna kin ganni Ina kula da shagon Mama,Kinyi dai dai kawata Nan suka Sha Hira sannan suka kashe Wayar,Aamna Ana zaune a kujera ga table da kayan aikinta na calculation,Haka ta kwashe kwana Uku tana zuwa Kantin ta Gama Gane komai tana ta ciniki. Ahmad kuwa Bayan Aamna ta bar gidansa shi Bai ji wani damuwa ba ko a jikinsa,ci gaba yayi da shakatawarsa musamman da ya samu Mummy bai ji ta Masa fada ba,Su Mashkoor suka dawo gidan suka tare kullum sai shaye shaye sukeyi,Ranar da Aamna ta cika sati Daya cif da barin gidan Ahmad ya fito a machine a hankali Yana tafiya a nutse,Aamna ta fito kenan tana aunawa wani yaro barkono karaf suka hada Ido da shi zai wuce,Ido ya tsura Mata itama Haka ya Mata kyau da yawa,Machine dinsa ya karawa wuta ya bar wajen,fasa zuwa yayi inda yayi Niyya ya koma gida abinsa,tunda ya dawo Aamna ce ke Masa gizo a fuskarta,Kawai fuskarta yake tunanowa,Tsaki Yaja ya shige Bedroom dinsa ya kwanta Nan take bacci ya kwashe shi,Mafarkin Aamna ya Shiga Yi suna zuba soyayya tana jikinsa a kwance. A Matukar zabure ya farka Shuru yayi Yana tunani,yace ah....wannan wanne irin tsafi ne? Gashinsa ya girgiza Kamar Yana korar kuda Haka yake karkade Fuskarsa Yana masifa ki bar Fuska na daina ganinki,a'ahhh.....ki daina fito min a Fuska Ina kallonki,wannan wanne masifa ne Haka?.....Ni.....ya nuna Kansa da yatsa ni Zan zauna Ina tunanin mace,kamata Ni a'ahhhh....chaiiii......mikewa tsaye yayi ya kaiwa Iska Naushi yace Zan fasa Miki Baki fa......shi kadai yake ta abinsa a bedroom kamar sabon kamu,Zama ya sake Yi sai Kawai ya tafi tunanin Aamna...Tsaki Yaja yace again....Wai wannan wacce irin yarinya ce ki fitar min daga ido na daina ganinki....kasa ya sakko ya durkusa ya daga hannaye sama Yana Allah ka gani dai Yarinyar Nan sai Tunaninta nakeyi,Ina ta ganinta a Ido na,bazan Iya ba....nasan ni me laifi ne a gareka,nayiwa mutane da yawa laifi Allah karka Yi Fushi Dani ka jarabce Ni da yarinyar nan,Allah kasa na daina ganinta,Allah na tuba,ya Mike tsaye ya sake juyowa da karfi Yana tangadi yace Allah nayi Addua Kuma ban daina Tunaninta ba,kirjinsa ya dafe tare da furta wayyooo....my Heart woooo ....Ina ta ganinta fa ya Allah,Ya girgiza Kansa ya shiga zaga dakin Yana safa da marwa Yana Ohh....ohh.....Ni ta fita daga Ido na,ta fitaaaa.....a Haka ya yini Yana sambatu har dare yayi Bayan ya jero sallolinsa na yini Guda yace Bari na kwanta bacci da wuri ko Zan daina ganinta a idona,Yana kwanciya ya kasa bacci sai tunanin Aamna tana Masa gizo,Shi kadai yace kunga yau bazan iya bacci ba sai tunaninta yau an shiga Uku.....mikewa yayi zaune yace kaiii....yau bazan Iya bacci ba sai na ganta....naji idan ban ganta bazan samu nutsuwa ba,...Amma Bari naje na ganta nasan idan na ganta zan daina ganinta a idona...waiiii....ya akayi ne nake so sai na ganta,Kawai so nake Naga Yarinyar Nan yanzu yanzu,Kawai gidansu Zan tafi yafi sauki ai Zan Gane gidansu ko na Kira Mashkoor ya raka Ni gidan sabo da ai sunje daurin Aure zasu Gane gidan,a hankali yace Amma idan na Kira Mashkoor asiri na zai tonu Kuma na Gama kuri da cika Baki a gabansu abin kunya ne a ganni naje wajen mace,macen ma wannan yarinya,Amma fa gaskiya idan ban ganta ba bazan samu nutsuwa ba Dole na tafi,agogon Dake hannunsa ya duba yaga 9pm yace Bari naje ko ta katangar gidan ce na haura na ganta,gashi wani kunyarta nake ji da tsoronta bazan Bari ta ganni ba. Cikin dare ya dauki pcap ya saka sannan yasa face Mark a Fuskarsa Wai Dan kar a ganshi yaji kunya an ganshi a wajen mace,Musa Wanda jiya ya dawo shi ya bawa key din machine yace Musa zuciyata yau wani Bugawa takeyi bazan Iya tuki ba kaini wata Unguwa,Musa ya karbi key ya hau shima Ahmad ya hau sanye cikin kayan baccinsa wando gajeren da Riga me gajeren Hannu ko a jikinsa Haka Suka tafi,Yana ta nunawa Musa Hanya da kyar ya samu ya gano gidan tunda an taba zuwa dashi sau daya,can nesa da gidan yace Musa ya ajiyeshi,ya sauka yace ka jirani a nan bance ka biyo Ni ba,Musa yace to Oga,Face mark dinsa ya gyara ya bi ta can bayan gidan,Kamar Biri Haka ya Dane saman katanga Dake Bata da tsayi Haka ya haura gidan su Aamna lokacin Baba ya fito zai rufe gida. Ahmad ya labe Bai ganshi ba,Baba ya kulle ko Ina ta gidan,Bai San ya rufe kofa da barawo ba,Ahmad yace yanzu Ni ba abin na shigar musu gida ba,Kuma yanzu Taya zata fito na ganta? Ai wallahi idan Zan kwana bazan tafi ba sai na ganta,Yana tsaye har wurin minti goma sai yaga an Bude kofa an fito sai yaga Aamna ce sanye cikin kayan bacci ta fito da bucket,Ahmad ya Kara labewa ya gyara tsaiwa Yana kallonta Yana zuba murmushi yace kalli Hanci Dan Allah me kyau a Nan wajen.....Uhmmm .....Allah yayi baiwa, panties yaga ta Shanya Guda Uku da Bra Guda biyu,Aamna tafi so ta Shanya Rana ta dake su sabo da kashe kwayoyin cututtuka,Bata son Shanya su a inuwa tasan gobe Rana zata dake su. Ta Gama shanyawa Yana ta kallonta Mama ta fito tace Aamna ki shigo da kujera ciki Tace to,Ahmad yace kaji sunan ma Aam....nah.....my Aamna...no sunan gayu Ahmnaa....Yes...Ahmnna vs Ahmad...A&A kenan a'a wannan Dadi Haka.....kumatunsa ya Mara kadan yace to yanzu Zan Iya tafiya nayi bacci,Zabura yayi yace Kai Nafa haukace,wannan fa hauka ce,Ahmad Ni king Haka Kawai na zauce akan Yar Yarinyar nan,Tsaki Yaja yace Nafa haukace gaskiya....lallabawa yayi ya sake haurawa ya bar gidan,Musa ya hango shi ya taho Yana ta murna Yana murmushi Bai San dalili ba,Machine ya hau Suka koma gida,ranar wani irin bacci yayi me dadin gaske. Washe gari Yana farkawa da Aamna ya farka a ransa,Tsaki Yaja yace Wai na ganta ma bazan huta ba...Haba zuciyata me yasa Wai kike min Haka ne,jiya kinsa naje na ganta yanzu ma so kike ki Kara ganinta Baki koshi ba wannan wanne irin tsafi ne Yarinyar Nan tayi min ne,da safe sai na farka da ita Haba which kind juju be that? Ni ba sonta nake ba duk harkar love...love ba ruwana da shi Amma Kuma so nake na sake ganinta Haba nooooo.....ya Furta cikin karaji,Sannan cikin slow Yana yarfe Hannu yace idan na ganta anjima ai shike Nan Kuma sai na huta,ai abin kunya ne kamata Ina son ganin Yar yarinya,zuciyarsa ya dafe yace sai wani tsoronta nake ji zuciyata tana wani bugawa Haka Kawai idan na ganta to daga yau bazan sake zuwa ganinta ba aikin banza,tunani ya shiga Yi yace Naga kamar ma samari na zuwa wajen Baby dinsu da Kaya Decent,to Amma Ni ai ba Baby na bace,Kuma fa sai taji Dadi idan idan ta ganni da kayan hausawa? Murmushi yayi ya koma Gaban Mirror ya duka Yana karewa Kansa kallo ya shafa calabarsa yace gani kyakyawa ai dole ma na birge ta,hannayensa ya Buda a Gaban mirror ya saki murmushi yace chaii....see fine Boy.....oh..oh....baya Yaja sosai Yana kallonsa yace huuuu...Kalar birgewa kaga Kalar birgewa yesss.....Bari nayi wanka, Fuska ya Bata yace to Mene sai wani murna kakeyi zaka ganta aikin banza,Ni wallahi wani banza ne ma akan mace Subhannallahi ya Dan Mari kumatunsa kadan yace Bari na gwada Kalar murmushin da Zan Mata Nan fa ya shiga sakin murmushi kala kala Yana kallon kansa a karshe ya Dan yake kyawawan hakoransa yace ae tsaya dai dai Nan wannan yayi yawwa ae....sai ya wuce toilet. Tunda ya shiga ciki Yace yau wankan na musamman ne so nake na Kara haske Nan fa ya shiga dirzar fatarsa ba ji ba gani,yace bana wanka da soso yau Zan koma Yi da soso sabo da na fita fes,dubawa yayi bashi da soso,towel ya daura Bayan ya dauraye jikinsa ya fito a Haka daure da towel har wajen me gadi,kudi ya mikawa Musa yace ungo maza ka siyo min soson wanka,karka sake ka dakko min na jarirai me laushi me karfi zaka siyo Wanda Ina wanka Ina Jin radadi,Musa yayi Dariya yace irin namu na talakawa kenan? Karka Bata min time sauri nakeyi Ina da abin yi akan wannan soson wallahi Zan iya sallamarka daga Aiki Matukar baka siyo Wanda zai wanke min fatata sosai ba,Musa ya karba da sauri ya fice,Minti biyar ya dawo da soso me shegen karfi ya bashi. Wanka ya sake Shiga Yana dirje jikinsa Yana rumtse Ido sabo da zafin soson,Haka ya Gama tas ya fito Yana goge jikinsa yace yawwa Iska tafi shigata Ina Nan Ashe Ina ta cutar kaina da ace da irin wannan nake wanka tun farko ai da nafi Haka haske da Zama Fresh. Lotion dinsa ya shafa me kamshi ya shiga gyara kitsonsa yace ya kamata nayi sabo wannan kwanansa biyar ya fara tsufa Amma Bari dai naje,sai da ya Gama feshe feshensa sannan ya Bude ma'ajiyar kayansa Yana binsu da kallo yace Suit Zan saka ko me?can ya hango shaddoji da yadika masu tsada da kyau Wanda Mummy ta kawo Masa lokacin da za a daura aurensa kala bakwai,Wata Shadda ya dakko sea Blue Tasha dinki me kyau Hannun dogo me links,Nan ya sa Boxers ya fara kici kicin saka wando Wai Bai iya ba,da kyar da wahala Yana uban Nishi ya saka cif cif shi dinki ya zanu,Singlet ya saka yanda Mummy ta koya Masa sannan ya saka Rigar Shaddar wacce ta Sha guga ga kamshi Shaddar nayi sabo da me tsada ce,calabarsa ya gyara ya shafe Kansa da man gashi me kamshi Nan take ya dauki sheki,Fuska ya kalla ya matsa baya Yana kallon kansa a mudubi ya hau taje Sajensa da gemusa,fuskar ya goge sosai ya gyara sai gashi ya fito fes da shi,Sarkar azufarsa wata sabuwa ya dakko ya saka,Yana cewa duk da hausawa basa so Amma tana min kyau sai na saka sabo da wannan shine wankan sugar sai da ya Gama ya fesa turaruka masu kamshi,Ya tsaya jikin mirror ya kame a wajen yayi mutuwar tsaye yace ya Ilahi Ashe Haka nake? Dan Allah kalli kyau a wajen Nan ai Dole ma na birge,ya sake kallon kansa yace ah.. ah kalli kyau Dan Allah,irin wannan saurayi ai sai an wanke Hannu daka taba,wani Dan lipgloss na maza ya dauka ya Dan goga a lips dinsa yace yawwa.....Kar Kuma na Zama Dan Daudu Mana ya Isa haka....tsayawa yayi yace to me zance Mata idan naje Kantin nasu? Tunani yayi yace na tuna ma Bari naje,Illar idan na ganta sai naji tsoronta Kuma Haka Zan daure,Fitowa yayi Yana Taku dai dai Yana wani Gadara,yace me kyau sai da takama Nan ya Shiga wata tafiya Yana takama Yana basarwa,Musa Baki ya Bude tunda yake a duniya Bai taba ganin me kyau irin Ogansa ba,Bai taba ganin wankan da yayi ya zuba Uban kyau Haka ba sai yau,Musa yace Oga gaskiya kayi kyau,Murmushi yayi yace Allah Musa? Musa yace wallahi Oga Kar fa kasa Mata su haukace,Dariya Ahmad yayi ta Jin dadi yace Musa yanzu kana ganin duk wacce ta ganni zan birge ta? Bafa soyayya nake nufi ba Kai Musa Ni kasan ba ruwana da soyayya,Musa ya kalli sama ya nuna sama da yatsa yace Na rantse Oga duk wacce ta ganka sai ta kwana tana tunaninka yau ita da bacci haihata haihata,Machine Ahmad ya hau Wanda Musa ya wanke Masa Shar,a hankali yake tukin sai binsa ake da kallo da gani an San Yafi karfin yawo a Machine ko Ina ya gifta sai an koka. Aamna kuwa yau wanka tayi ta shirya cikin doguwar rigarta peach color ta lefe ce tayi rolling da mayafi ta dauki hand bag da takalminta me Dan tudu Kalar adon rigar Golden tayi kyau ta dauki bokitin chin chin da takeyi da kanta tana siyarwa a shagon wannan da kundinta takeyi tana samu Yar riba,da kanta ta gyara kantin fes ta shirya komai sannan ta zauna tare da dakko Wayarta tana karanta novel,idan masu siyan Abu sunzo ta Basu ta koma karatunta. Tana zaune ta dukufa taji machine yayi parking a bakin wajen,kanta ta dago da sauri Jin wani kamshi na daban me Dadi,Ahmad ta gani Wani tafiya yayi da Imaninta ita kanta sai taga kamar yau ta taba ganinsa,zuciyarta ta hau Bugawa da karfi,Kallonsa takeyi ba kyafta Ido tare da Mikewa tsaye,Babu alamun fara a Fuskarsa Yana wani Isa,a cikin ransa Kuma wani kwarjini ta Masa yaji wani tsoronta da shakkarta,duk kwarin gwiwarsa sai ya neme shi ya rasa,jikinsa yayi sanyi a hankali ya taka zuwa gabanta ya tsareta da idanunsa,Itama shi take kallo,can ganin Shirun yayi yawa sai Tace am...me kake so zaka siya Ahmad? Yayi Shuru ya kasa magana,ta kalle shi tayi murmushi Tace wow kayi kyau Wannan shigar tayi maka kyau,Wani sanyi yaji a ransa dama Dan ita yayi Kuma ta yaba,a hankali yana Ina Ina yace shi...shigar...ta...tayi Miki?da sauri ta daga kai Tace sosai wace zata ce ma baka Yi kyau ba,Yaji wani Dadi ya jinjina Kai kawai,sharewa tayi Tace me zaka siya? Kasa magana yayi sai da kyar yace Uhm....uhmm.....Yana ta kallon shagon Yana so yaga me zai iya siya....gumi ya hada Nan take tsabar abinda yake ji a ransa da kwarjinin da ta Masa gashi Bai Iya yiwa mace magana ba tunda ya taso a rayuwarsa wannan ne na farko,Tace Kayi magana Mana me zaka siya? Yace Uhmm....ahhh....ehmmm.....can ya hango chin chin yace Chin chin tare da nunawa da yatsansa,murmushi tayi Tace na nawa? Yace na....naira dari.....murmushi ta saki ta bude ta zuba Masa Guda uku dari cif a farar Leda ta Mika Masa,karba yayi Yana ta kallonta yace Zan....Zan...Iya Zama a Nan naci? Tace me zai Hana shigo ciki,kujera fara ta jawo Masa a ciki ya zauna Suka jere taci gaba da karatun Novel dinta. Kallonta Kawai yake ta faman Yi idan yaga zata dago sai yayi sauri ya dauke Kansa,Daya gaji sai ya fara cin Chin Chin din,harga Allah baya son chin chin Amma Haka yake ta ci Yana kallonta,ita Kuma tana ji a jikinta Yana kallonta duk sai ta kasa sakewa da kunya,juyowa tayi karaf suka hada ido,Tace ya kake kallo na? Yace kallo? Kallo Kuma? Ni na kalle ki ai kece ma naga kina ta kallo na tun dazu ya fada Yana dauke Kai,Tace Ni nake kallonka din? Yayi Murmushi yace ae Mana,Kai ta girgiza taci gaba da karatunta,cikin Wayar ya leka yace me kike karantawa? Novel ta bashi amsa, ko kana karanta Novel? Yace No...me zanci da Harkar love ai Ni sai dai dambe, murmushi tayi Kawai. Yace me yasa Mata kuke son Love ne? Wannan duk Bata lokaci ne,Dariya tayi Tace Kai baka so ta juyo tana murmushi wani kyau ta Masa ya gigice zuciyarsa taci gaba da bugawa,kasa magana yayi ya rike Hannunta wani mugun shock taji ko Ina a jikinta yace Ring din ya Miki kyau,Tace na gode Hannunta ya dauka ya maida Mata saman cinyarta yace kina boye Hannun Nan Kar wani yaga ya Masa kyau da yawa ya yanke Miki shi ya tafi dashi gida,Dariya ta dinga Yi shi kuwa ita Kawai yake kallo,komai nata Dariya a ransa ya furta,Yana sani ya dinga cin Chin Chin din kadan kadan sai da ya Dade lokacin Azahar tayi sannan ya Mike yace Zan tafi Tace ka Gaida gida yace to Zan fada Masa,Dariya ta sake Yi ta rako shi har bakin machine dinsa ya hau ya tafi da mugun gudu,Tun kafin ya karasa gidansa ya tsaya a Hanya ya cire rigar Shaddar tasa sabo da zafi yake ji ta dame shi Bai Saba ba,a kafada ya sakale ta har zuwa gidan. Da murna ya shiga Yana sauka a machine ya zaro dubu biyu ya damkawa Musa yace je kaci pizza Musa yau Ranar murna ce,Musa yace Allah Oga? Allah kuwa cewar Ahmad ya sake zaro dubu biyu yace kudin lemo ne wannan,Musa ya daka tsalle Yana murna da Ihu har Ahmad ya tafi ya sake dawowa ya zaro dubu Daya yace ungo Musa ka sawa matarka Kati a waya ku kwana kula hirar ku ta Yan karya Kuma karka sake ka Bata duniyar mu Dan Bamu San Inda zamu shiga ba idan ka bata.,,Musa yace Allah Kai sai kayi,Ahmad ya daga hannaye sama yace nine nan yayi ciki Yana wata tafiya ta musamman. Yana shiga ya cire duka kayan jikinsa ya watsa su a inda yake Tara wanki,saitin zuciyarsa ya dafe tare da furta shu'uma har ta dawo dai dai,Wato har wani bugu kike Yi a hankali da kika ga bana gabanta ai shike Nan kin kyauta,zuciya kin kyauta hakan ya Miki kyau kin Mai Dani wani Wawa Akan yarinya karama Ina ta zubar da aji na ai shike Nan Zaki sani ne. Washe gari ma wani sabon wankan yayi tare da saka wani yadi Milk color sharara da shi ya Masa kyau matuka an kashe shi da dinki na haduwa,wani takalmin ya zabo me tsada,waje ya fito ya mikawa Musa takalman yace sauri ka kaiwa Shoe maker ya wanke min yanzu Ina jira,Dan Allah Musa kayi sauri ka kawo min su Suna kyalli,Musa ya fita da gudu ya tafi Bai Dade ba ya dawo,Ahmad ya shirya tsaf kyau ba a magana yace yau barkono da citta Zan tayata siyarwa,yau ma Aamna tana zaune ta Gama sallamar wani ya siyo Singlet sai gashi ya Parker machine,Aamna tayi murmushi Tace Sannu da zuwa,Irin Dan gayun Nan harda wani basarwa Direct ya shige ciki ya zubawa Kansa chin chin yace na Naira Dari biyu yau Zan siya Aamna Tace to,Zama yayi Nan ma Yana kallonta duk kunya ta isheta,Wani magidanci ne yazo yasan Ahmad da irin iya shegensu mamaki ya kamashi ganinsa a Haka da wannan shiga ta Kaya,Bai taba ganinsa da shigar hausawa ba,Kuma Yana Zaune a shago kamarsa me kudi,Shuru yayi yace a bani barkono da citta,Aamna ta Mike zata zuba da sauri Ahmad yace No zauna Bari na tayaki Mana Haba,Tace Kai din? Bai kulata ba yace na nawa? Yace na Hamsim,Aamna tace ga kullin Hamsim can ka saka,ya dauki bakar Leda ya saka Masa ,Citta Kuma Tace gongoni Daya zaka zuba,ya fito ya auna gwangwani Daya ya zuba,mutumin yace babu gyara? Ahmad yace a gindinku kuke so mu kare ne Ina laifi ma duk arahar Nan Baku gani ba,Tsaki Yaja ya dauki citta Daya ya jefa masa a Leda yace gashi Nan anyi gyara,Mutumin ya karba ya tafi shi Kuma ya dawo ya zauna a ciki,Aamna tana ta mamakinsa. Wata Budurwa ce tazo Tace Aamna nazo siyayyar,Aamna Tace to shugo,Budurwar tayi layin bra da panties ai Ahmad Yana ganin Haka sai ya juya baya tare da rufe Idonsa ruf har sai da matar Nan ta Gama zaba ta biya kudin ta tafi sannan ya Bude Idonsa,Dariya ya bawa Aamna Yana jinta tana ta dariya,yau ya Dade sai Yamma lis ya koma gida,sai mamakin Kansa yakeyi Wai Kamar shi shine zai siyar da citta,Yana kwance a palonsa yace gaskiya na Gama fadowa nayi asara wallahi,Kansa ya dungure yace kayi asara kai Kam Ahmad. Wasa Wasa kullum Ahmad sai yaje ya Taya Aamna siyar da Abu har wurin sati Daya,gaba Daya su Mashkoor sun daina ganinsa,idan sun Masa waya ma zasu zo gidansa sai yace Kar suzo baya gida ya tafi Unguwa,yafi so ya zauna shi kadai yayi ta tunanin Aamna Yana Jin dadi,Kwaya da giyar da yake Sha duk ya rage ba sosai ba sabo da tunanin Aamna. Yau kin zuwa yayi gaba Daya Bata ganshi ba har duba Hanya takeyi ko zata hango shi Amma Shuru duk ta kasa sukuni ta shiga wani Hali,gashi Bata da number dinsa Kuma baza ta iya cewa ya Bata ba. Sai washe gari yau cikin wata maroon suit ya fito kamar a jikinsa aka dinka yayi kyau matuka 3pm yazo wajen,Aamna ta taso da sauri tana murna a ranta a fili Tace me ya hanaka zuwa jiya? Ya rasa me zaice zuciyarsa tsoro yake ji....yace...ahmm...karya yayi yace kaina ke ciwo jiya,Tace Eyya Sannu ya jikin? Da sauki ya furta tare da tsayawa a gabanta Yana so ya fada Mata me yake ji a ransa Amma ya kasa....yace dama Ina so muyi wata magana ne,akwai abinda nake so na fada Miki,Aamna tace Ina jinka tana ta faman kallonsa,kasa fada yayi ta Masa kwarjini sai ya waske yace kina cin kifi tarwada? Dariya ta kamata Tace sosai ma ai Ina sonsa ya,girgiza Kai yayi Murmushi Wanda ya tafi da Imanin Aamna,yace to gobe Zan kawo Miki da yawa ko yau kike son ci? Aamna Tace goben ma yayi,Yana so ya fada Mata shifa zuciyarsa ta kasa sukuni Amma ya kasa sai yace Zaki Zama kawa ta?Aamna ta kalle shi tace me zai hana,murmushi yayi yace to daga yau mun Zama kawaye ko? Tana Dariya ta Mika Masa Hannu sukayi musabiha Tace na Zama kawarka kaima ka Zama aboki na,yace ae dama Ina so na dinga shawarwari Amma Banda kawa,Aamna Tace Ina abokanka fa?Tsaki Yaja kadan yace ai Bama wani haduwa yanzu sosai,taji Dadi a ranta Tace to shugo ka zauna,no tafiya zanyi Ina da wajen zuwa yau,Aamna Bata so hakan ba Amma Tace to shike Nan sai goben,ya hau machine yayi tafiyarsa gidan Mashkoor. Yana zuwa ya samu Mashkoor shi kadai, Mashkoor yace Kai me Zan gani yau Kaine da wannan shigar lafiya king? Kafadarsa Ahmad ya buga yace ba lafiya ba yanzu ma taimakonka nazo Nema,ku kawo min agajin gaggawa, ka tashi mu tafi gidana akwai magana,Mashkoor yace to,Giyar da Mashkoor yake kurba ita Ahmad ya tiltila a cup ya Sha ya sake Sha yace muje,a machine suka tafi gidan Ahmad. Aamna tana so ta fada Masa anjima da yamma zata tafi Sokoto ganin Dangin Babanta Amma Bai zauna ba bare ta fada Masa Amma sunyi waya da Mummy ta San da tafiyar. Shi kuwa Mashkoor Yana palon Ahmad suna zaune Ahmad yace kasan Kai abokina na ne Zan fada maka ne Kawai sabo da yanda muke da Kai,Kai kadai Zan fadawa halin da nake ciki,Mashkoor da muryar Yan kwayarsa yace Ina jinka King,Ahmad ya kwashe kaf abinda yake ji a zuciyarsa game da Aamna ya fadawa Mashkoor,Mashkoor tsoro ya kamashi Yaja da baya Yana tangal tangal a zaune yace Sarkin namu Guda ah'ah,Ahmad cikin rada yace Ina fada maka idan na ganta zuciyata sai naji tana wani kida tana rawa tana wani foli..fafo..lifo...fil...fil....dardariya Mashkoor yake Kamar me,yace ah'ah duk Kai kadai? Ahmad yace Ina fada maka Dan uwarka Yana dukan kafadar Mashkoor kana ganin Wasa ne bafa Wasa nake ba kana wani Yi min Dariya Dan Iska Kawai wallahi zaka bar gidan Nan, Mashkoor yace na daina Ina jinka,Ahmad yace Ina fada maka ba sai naji Ina tsoronta ba,Ah'ah Mashkoor ya furta da karfi yace wannan Yarinyar da ko Nonon kirki babu? Duka Ahmad dirka Masa a baya yace be careful matata ce ba Budurwa ba, Mashkoor yace dalla ba so bane sha'awarta kakeyi Kawai kaje ka dakko ta ka lallabata kaci abinka ka barta,Wani dukan Ahmad ya kaiwa Mashkoor yace Kai dalla Ni ba wannan nake so ba,baka ganewa Ni Kawai nafi so mu zauna tare da ita idan Dan wannan ne zamu iya shekara Nawa da ita sai Sanda take so zanyi wannan fa ba Maganar Wasa bane,Mashkoor yace cab abin Babba ne asiri tayi maka,Haushinka taji daka koreta ta maka asiri. Ahmad yayi Shuru,Mashkoor yace Zan taimaka maka akwai wani malamin Baban mu zamuje da Kai Nan take zaiyi maka Rukiyya a cire maka tunaninta ka dawo normal asirin data maka ya karye,Ahmad sai ya tuno layoyin Daya taba gani a Kan Aamna,yace Mashkoor kaima kayi magana tashi mu tafi wajen malamin Nan Yarinyar Nan Yar bori ce muje a gwada, Mashkoor yace yawwa kasan yanzu duniya ta canja Wai Yan Mata Dan masifa da bin malamai suna shirka suna tsafi akan maza,Wai mace taje tayi shirka Dan wani ya aure ta ko taci kudin wani,wata ta mallake Miji etc,kawaye sai su cika Mota suyi Kauye Wai an tafi wajen Malam akan wani ya aure su ko taci kudi,ko ayiwa kishiya da yaranta,shi yasa aure yanzu baya Zama Ana ta Yi Ana Sako Mata barkatai,duk macen data auri Namiji da asiri ta sani wallahi idan ya karye sai saki,yanzu shirka Kawai akeyi an ma daina cewa malamai sai bokan Kan dutse,mutane suna ta maida kansu arna Basu Sani ba. Tafiya sukayi me uban nisa zuwa wani Dan Kauye,Wani dattijo kazami Ahmad ya gani,Mashkoor bayan sun gaisa ya Gabatar da Ahmad da abinda ya samu Ahmad,tsohon yace ku bada dubu biyar kafin alkalami,Ahmad ya zaro ya bawa Malam,Malam yace saura kudin Aiki dubu goma,Ahmad yace Aiki baiyi ba za a baka kudi? Dattijon yace Kai ka cika son kudin tsiya ka bada kudi a rabaka da masifa,ciwon so ai masifa ne,Ahmad yace Nifa ba soyayya nakeyi ba,nace maka tunaninta Kawai nakeyi,Ni nayi love Allah kiyaye, gashi nan yarinyar ta Gama kashe maka zuciya cewar malam,Ahmad ya bada dubu goma shi Sam da gani yasan karya ne wannan cin kudi Kawai zaiyi. Saman Tabarma yasa Ahmad ya zauna,Bayan ya zauna ya Bude Qur'ani ya dinga karatu a Kan Ahmad Yana zaga shi sai da ya Dade sannan yace an Gama Alhmdllh Aiki yayi kyau kuje gida daga yau ka Gama da shafinta, Mashkoor Yana murna ya dinga godiya,Ahmad Baki ya tabe shi baiji canji a ransa ba,Sai dare Suka koma gida,suna dawowa wanka sukayi Suka ci abincin da Suka siyo a hanya,Ahmad ya kalli Mashkoor yace Mashkoor Nifa so nake yanzu Naga Yarinyar Nan,Da mamaki Mashkoor yace ah'ah Kuma dai? Yanzu duk aikin da Malam yayi har kanajin ta a ranka? Ahmad yace tashi ka rakani gidansu Zan haura katanga idan ban ganta bazan iya bacci ba yau dole sai naji muryarta ko na ganta,Mashkoor yace dare fa yayi ka duba lokaci 11pm fa,idan zaka rakani to idan baza kaje zanje Ni Daya,Dan kaga Ina fada maka sirrina zaka wulakanta Ni,Mashkoor yace muje Amma idan munje me zaka ce da su a wannan Daren me zamu ce? Ahmad yace muje Kawai,machine suka hau a daren Suka tafi Kamar mayu. A bakin gate Suka tsaya tare da kwankwasa gidan,Baba ne ya fito Jin bugu yaki karewa Yana budewa tsoro ya kamashi ganin su Ahmad ya tabbatar giya suka Sha shi yasa Suka zo da wannan Daren yasan basa hayyacinsu,lafiya? Baba ya tambaya,soshe soshe Suka Kama Yi, Mashkoor yafi Baki shi yace dama...dama..munzo duba Aamna ne sabo da munji labarin Bata da lafiya,Baba yace sabo da kwaya ta gaya muku karya sai kuzo min gida a wannan daren? Kun firgita mu Ni da matata,to Aamna Bata Nan ta tafi Sokoto tun yamma dazu tace ta sauka tana can Dangin Babanta sai Nan da kwana hudu zata dawo,Kirjin Ahmad ya buga Kamar zaiyi kuka yau bazai iya bacci ba Matukar Bai ji muryarta ba,Baba zai juya yace sai da safe da Sauri Ahmad ya kalli Mashkoor ya Masa rada kace ya Bamu number dinta,Da sauri Mashkoor yace Dan Allah Dan Bamu number dinta Muna so muyi Mata ya jiki,Baba yace Wai uban waye yace muku Bata da lafiya fatan ba takura Mata zakuyi ba,da sauri Ahmad yace a'a Kawai Sannu zamuyi Mata,Baba ya Harare su sabo da Bai so Haka ba Amma sabo da kwarjinin Ahmad yace bani waya na sa maka,da sauri Mashkoor ya Mika wayarsa Baba ya sa Masa number a ciki Yace kuje garam ya rufe gidan,Ahmad ko a jikinsa sai murna Suka hau Machine suka koma gidan Ahmad. A Palo Ahmad yace Kira ta awaryarka muji, Mashkoor ya kalle shi da mamaki yace da wannan tsohon Daren? Ahmad yace Dan Allah ka kirata naji muryarta Ni bazan iya Mata magana ba zuciyata bugawa takeyi,kayi magana da ita kasa a handsfree idan naji muryarta shike Nan Zan samu nayi bacci yau,Amma Matukar banji muryarta ba yau bani ba zaman lafiya, Mashkoor yace abin har ya Kai Haka mun shiga uku?Tsaki Ahmad ya ja, lokacin Aamna ta kwanta ta fara bacci taji Wayarta tana ta Kara,dubawa tayi taga bakuwar Number AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 46-50 FREE PAGE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE MASU SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Page naku ne RUKEY MUAZ LEEMAT ~- MINERH KHADIJA DANDAWAKI HUMAIRA MUHAMMAD AMINA ADAMU USMAN Tsaki taja tace waye wannan da wannan daren? Kin dagawa tayi har ta katse, Mashkoor ya kalli Ahmad yace King Bata daga ba a kyaleta tayi bacci,da masifa yace ka Kara kiranta Mana,to tana bukatar tayi bacci fa cewar Mashkoor,Bata bacci da wuri na sani ka sake Kira Wai me yasa kake min Haka Zan sa ma poison a lemo ka Sha ka mutu ka kirata again, Mashkoor yace Nifa baza ka Jani cikin haukarka ba,Kawai ka shigar Ni ciki mun haukace yau gaba Daya bansha ko kwalaba Daya ba mun Kare akan kwaila,wata Harara Ahmad ya aika Masa Nan take Mashkoor ya sake Kiranta lokacin wata Budurwa Yar Uwar Aamna Minal ta kwanta a gefen Aamna Tace Wai waye yake ta Kira ne Haka? Aamna Tace ban sani ba,Bari na daga naji cewar minal ta dauki Wayar tare da dagawa, Mashkoor yace an daga....an daga...Ahmad yace ehem Yi magana Mana. Mashkoor yace hello Aunty Balaraba Mashkoor ne? Minal tace ba ita bace Yar uwarta ce Minal ce,Aamna tana ji ance Mashkoor ta Mike zaune,Mashkoor yace ehem Dan Allah Bata kusa me Wayar? Minal Tace gata ma Bari na Bata, Wayar Aamna ta karba,Lokacin Ahmad ya gyara Zama tare da furta ehem a hankali, Mashkoor yace Aunty Balaraba Barka da dare,yawwa Mashkoor ya gida? Lfy Alhmdllh,dama...dama...Ni da King munje gidanku ance bakya Nan kinyi tafiya,Aamna Tace Yana Ina King din,Tsoro ya Kama Ahmad shi Taya zai iya magana me zai ce Mata, Mashkoor yace Bari na Baki shi ya mikowa Ahmad Wayar. Yana karba sai da yayi minti Daya Aamna tana ta faman hello hello sannan yace hello cikin Muryarsa da ya saita me Dadi ta nutsuwa....uhm...ahm...ahhh....munje gidanku dazu ance bakya Nan? Aamna Tace eyya sorry Friend Ina ta so na fada maka Bamu hadu ba Amma jibi Zan dawo Inshaallah,Ahmad yace okay...Allah ya kaimu, Mashkoor da rada yake cewa matarka ce fa ka daina wannan abin taya zaka barta tana tafiya inda taga dama Haka? Ahmad Bai kulashi ba yace Friend sai da safe Bai San me zai ce ba,Tace okay bye ta kashe Wayarta,Ahmad yace Nifa ba Maganar Mata nake maka ba ya za ayi Naga na birgeta shine magana Kawai,Dariya Mashkoor ya dinga yi yanda Ahmad duk yake ta murna akan yaji muryar Aamna,yace to yanzu Zan iya bacci,Mashkoor yace ka haukace Nima ka sani na Zama mahaukaci,Bari naje nayi bacci,Ahmad yace ungo wannan banzar akwakwar Wayar taka tunda nadauki number dinta,Ae ai dole ka zagi Wayar tunda ta Gama biya maka bukatarka. Washe gari da sassafe Ahmad ya farka ya dawo Palo inda Mashkoor yake bacci ya dinga dukan Mashkoor a gadon baya,da kyar Mashkoor ya farka Yana masifa Wai Dan Allah mene Haka jiya ka hanani nayi bacci yanzu ma Haka Mene ne? Baka tashi da wuri mene yanzu abin tashi again,Ahmad yace Yarinyar Nan nake so ka kirata ku gaisa sai ka sa min Wayar a Handsfree naji muryarta,Tsaki Mashkoor Yaja da muryar Yan kwaya yace wai a'ahhh....wannan wanne bala'i ne Haka? Okay kace min kawarka ce Kai ba sonta kakeyi ba wa yace maka Ana Kiran kawa Haka a waya,so kake Yarinyar Nan ta tsaneka sabo da yawan takura Haba su Mata basa son takura,kana nutsuwa fa King,Shuru Ahmad yayi yace okay Bari to bazan kirata ba sai ta neme ni Zan daure,Ehemmmm...Abeg jeka kitchen ka Mana girki King kasan ka iya girki cewar Mashkoor. Ba karamin dauriya Ahmad yayi ba yaki Neman Aamna a waya,Aamna taga Shuru Bai nemeta ba ranar da ta dawo Kaduna yau Ahmad Yana kitchen shi da Mashkoor suna magana Yana girki sai ga Kiran Aamna ya shigo wayarsa,Wata nutsuwa Ahmad yayi tare da cewa yeee...ta Kira ni...daga Wayar yayi yace Hello.....Kawata,Aamna Dariya takeyi Wai Dan rainin hankali ma ba matarsa bace kawarsa ce ma,a Wayar Tace dama fada maka zanyi na dawo dazu,Wata Uwar Zabura Ahmad yayi sai da Mashkoor ya firgita,Ahmad yace Kin dawo lafiya Kamar Yana gabanta har wani zufa yake Yi,Tace lfy Alhmdllh,yace Zan zo gobe,okay Aamna ta furta ta so ace yanzu zai zo Amma Wai wani gobe, Wayar ya kashe ya saki Dan Ihu yace she done come back Yana dukan kafadar Mashkoor, Mashkoor kallon mamaki yake Masa Kawai ganin king dinsu ya haukace. Wanka sukayi Mashkoor ya dauke shi Suka tafi Shopping Wai Ahmad shaddoji zai siyo da yadika masu tsada za Masa dinki sabo da ya birge Aamna. Ko da Suka shiga inda ake siyar da shaddoji da yadikan maza Ahmad ya kalli me kayan ya zaro Masa Ido yace Guy Kalar birgewa muke bukata masu tsada,Me Shadda yace gasu Nan ku zaba,Ahmad ya dinga zaba Mashkoor ya koma gefe Yana ta kallon ikon Allah har ya Gama sannan Suka wuce wurin tela,Ahmad yace Kai tela fa Wanda yasan me yakeyi yawwa idan kasan tela bana kirki bane karka kaini, Mashkoor Yana ta Dariya yace Wai Ni Kam ko Lilamin Masallaci za'a nada ka ne? Ko kula Mashkoor Ahmad baiyi ba,wani Shagon dinki Suka shiga,Ahmad yace Bari na gwada basirarsa Kai tela nawa zaka min Dinki na karshen tsada? Tela yace dubu bakwai, dubu biyar dubu goma sama da Haka,Ahmad yace wannan dinkin da gani bana arziki bane baka iya komai ba baka San me kakeyi ba Malam ja can dalla, mu bar Nan, Mashkoor ya sake daukansa Suka tafi Wani wajen na masu tsadar dinki Amma da kyau,Ahmad Yana ji an zuga Masa tsada yace yes.. .yanzu nasan Kai telan kirki ne Nan ya bashi kayan,yace auna Ni ko Ina dai dai Ni, wallahi ka min hauka sai na sa an kone shagon dinkinka da kayan ciki sabo da Haka don't Mess up,tela yace zaka ga Aiki ai bana Wasa,sai da suka Gama komai Suka je ya siyo takalma Designers da agoguna etc. Sai dare Suka Gama sannan Mashkoor yace Zan tafi gida,da masifa Ahmad yace akan me ai wallahi ba inda zaka je Sai an Gama tsare tsare da Kai, Mashkoor yace Nifa na gaji Haba ka rike Ni na kwana na yini Yar giyar ma ban Sha ba tun jiya Ni bazan iya ba, baza ka saka Ni a wannan haukar ba,Fuska Ahmad ya Bata tare da furta Kai meke damunka ina magana kana magana are you mad? Shuru Mashkoor yayi yace to kayi Hakuri na zauna Amma a kawo min ruwa da kayan aiki,Nan Ahmad ya koma bedroom dinsa ya kwaso kayan shaye shaye ya ajiye musu Suka dinga Kora abinsu,Ahmad Yana murmushi yace yawwa na tuno nasan dole tana yin Facebook babu Wanda baya Facebook a duniya,Nan take ya fara latsa wayarsa Yana duba Facebook Yana Searching sai dai Bai San sunan Baban Aamna ba,Amma sai ya gwada Aamna Hussain,Nan take sunan Aamna ya bayyana da hotonta,Yana murmushi yace Yes....see fine Beb,see Beb....naaa..wow...see her lips...oh.....My God...a'a...kaga kyau Haka,...fuskar Wayar ya shiga nunawa da yatsa Yana shafa gemunsa Yana murmushi yace abinda kike min baya dacewa,bakya kyauta min Sam,ki daina...ki daina Tam.....Mashkoor ya saki Baki Yana kallon ikon Allah, Pictures dinta ya shiga dubawa kala kala can ya hango Aamna da wani saurayinta a pic Wato Affan,Glass din wayarsa ya shiga Rankwashi da karfi a saitin Affan Yana ka...ga...shege...Dan... Iska,me yasa zaka tsaya kusa da ita....mugu....Tsaki Yaja ya fita daga Facebook din gaba daya Yana Fushi yace Taya zai tsaya a kusa da ita aikin banza,Cikin Maye Mashkoor yace Wai...Wai...ba kace kawarka bace?Yeah Ahmad ya furta,yace to Mene na damuwa Haka? Maganar gaskiya King ka fa haukace. Ahmad Yana Zaune yayi Shuru Mashkoor yace ya akayi ne? Yarinyar Nan nake so na gani yau da Daren Nan Amma bana son ta ganni kuma bana so ta San na ganta Kawai na ganta a boye ba tare da ta ganni ba,kaga yanzu 10pm muje ka kaini sai na tsallaka gidan, yau ko bacci takeyi har dakinta sai na ganta,Mashkoor tsoron Ahmad ya shige shi Kamar zaiyi kuka yace Wai Mene yake damunka kafa haukace King,Kaga Idan zaka kaini Malam ka kaini Zan zuba ma guba a abinci ka mutu Tam, Mashkoor yayi Dariya irin ta yan kwaya yace muje,a daren Suka hau machine suka tafi,a nesa da gidan Mashkoor ya sauke Ahmad,Ahmad yace karka tafi Ina ganinta Zan fito mu wuce,ta Kofar gidan Ahmad yabi ganin a bude Basu rufe ba,kamar barawo Haka yake Sanda yace bana so ta San Zan kalle ta,da sauri yabi ta bayan gidan wajen Flowers,Baba ne ya fito Yana masifa Dan Iskanci sai a bar gida a bude tun yaushe nacewa shedaniyar Yarinyar Nan ta rufe gidan Nan Amma dake Aamna ba Yar Albarka bace ta bar gidan Abude,Ahmad Yana ji Baba ya zagi Aamna sai ya kasa jurewa Yana bayan ginin gidan yace karya ne kaina Mara Albarka.....tsorata Baba yayi ya rasa a Ina yaji an ramawa Aamna ya shiga waige waige ko zai ga mutum baiga kowa ba,Tsoro ya kamashi ko aljanun Aamna ne suke tare Mata fada,da sauri ya rufe gidan ya kulle ko Ina ya koma ciki da saurin gaske. Ahmad ta Kofar kitchen yabi Dake kitchen akwai kofa ta waje ta ciki sai yabi ta Nan ya shiga Palo Yana shiga Baba ya shigo da sauri ya fada bayan kujera ya buya,Baba Yana masifa ya kulle Palo ma ya sa key, yace aikin banza kitchen dinma a Bude aka barshi Bari na rufe,kafin ya karaso Ahmad da rarrafe ya koma Bayan Daya kujerar,Baba ya kulle kitchen Yana cewa beraye sun fara addabata a Palo naji Kamar sun shiga cikin kujeru Bari gobe da wuri Zan samo mage tayi maganinsu. Ahmad Yana ji a hankali yanda Baba bazai ji ba yace Baba nine ba bera ba,Baba dai dakin matarsa ya shige,Sai ga Aamna ta fito sanye da wata guntuwar rigar bacci fara silk me siririn Hannu,Ahmad ya baza Ido Yana kallo Nan ma a hankali yanda baza taji ba yace Kai bakya kyautawa Baba fa idan Yana ganin irin wannan abin sai Shedan ya shiga zuciyarsa,wallahi sai ya Ayyana wani Abu gaskiya ki gyara,ba kishi nake ba Amma ki gyara,Aamna Bata San Yana yi ba taje kitchen ta fara dafa Indomie,cikin karfin halin Ahmad ya fito fili ya tsaya a Bayanta tare da Harde hannayensa a kirji Yana Shan kallo,a hankali ya Mika hannayensa biyu tare da wara su yace in Dan tallafooooo......hips Ido ya lumshe,Aamna Bata sani ba harda wakarta tana me so na....me so na....Ahmad Yana amsawa a hankali Yana Nuna Kansa Yana gani...gani....Aamna ji tayi kamar ana magana a Bayanta Matsawa tayi da Niyyar juyowa tuni Ahmad ya koma Bayan jikin bango daga Palo ya labe taga ba kowa,ci gaba tayi da aikinta ya dawo shima Yana ta kallonta har ta Gama ta dauka a plate sai ta tsaya dakko ruwa a fridge ta ebo pure water biyu tare da furta Allah sarki a gidan Mijina kuwa Ruwan Roba nake sha,kafin ta Gama gyara kitchen ta fito Ahmad yayi sauri ya shige Bedroom dinta Wanda yaga ta fito daga ciki. Bayan labule ya buya abinsa Aamna ta shigo tare da dannawa kofarta key tana Waka Tace yawwa Bari na kwashi harka ta zauna a gefen bed tana ci tana latsa waya tana Dariya,shiko Ahmad ta bayan labule yace kalli murmushi Malam Kamar wata flower Haba ai wallahi Babu Wanda ya Isa ya ja da Allah,wata baiwar Allah duk duniya kowa da kamarsa daban da Computer ce ke kera halitta ai da tuni tayi photocopy na Aamna ta yafi mutum dubu,Amma Kuwa Allah kowa hancinsa daban,bakinsa daban,Dariyarsa daban,kukansa daban,girarsa daban,kafa,Hannu,Kai,komai daban Allah kenan. Aamna Bata San da mutum ba Tace zafi Bari na sake wanka ba tunanin komai ta tube rigarta ta jefar,Ahmad ya zaro Ido yace tab gaskiya ban kyauta ba Zan kalle mata tsaraici ba Izni,Idonsa Daya ya leko ta labule yace tab Ni idan kika dawo gida na karya ne ki Haifi wani yaro,Ni da yarona zamu Yi takara kenan akan Abu daya Ni da shi ai karya ne,Yarana kuyi Hakuri Uwarku ta ja muku baza kuzo duniya ba akan wannan yaki zanyi da ku,Juyawa tayi yace lahaula fiii......see Ass uhmm....Ganin ta juya baya sai ya juro hannunsa Daya ta labile yace na taba suuu......da sauri ya janye hannunsa Kamar walkiya ganin zata juyo ta kamashi,Towel ta dauka ta shige toilet,sai da yaji karar ruwa sannan ya fito daga inda ya boye,Indomie ta rage yace Bari naci ragowar ta ko na samu karama da tabarakinta ya dauke ya cinye,ruwan data rage ya shanye tas harda tsotse bakin Ledar pure water Wai ya tsotse bakin Aamna,kafin ta fito ta Bude kofa Ahmad ya dauki Wayarta ya turata bakin kofa sannan ya Bude Kofar ya fice da sauri,ta kitchen yabi ya fita tare da haure katanga,ko Ina ya bar kofofin a bude sabo da dabara ya hada. Aamna da sauri ta fito daga toilet Jin karar key an Bude Mata kofa,mamaki ya kamata taga Wayarta a bakin kofa ita data barta a saman bed,abincinta data rage taga an cinye,da sauri ta fito tana duba gidan sai taga an Bude Kofar kitchen ko Ina,ga handkerchief an jefar,Ihu Aamna ta saki tana Baba barayi,barayin waya Baba,Baba ya fito da Aamna ta nuna musu kitchen,Baba yace abinda nake gudu kenan munafuka ai ke kika jawo kece ba Kya rufe gidan,Baba yace Bari na duba Naga me aka sace min,startime wacce ake Kamo tashar kallo Baba yaga wayam an sace,Hannu ya Dora a Kai ya kurma Ihu yace dubu goma Sha biyar dita,Radio dinsa da yake Jin labarai itama a Palo ya barta yaga an sace ta itama,Baba Takaici yace me yasa Dan Ubanki ba a sace wayarki ba Aamna? Aamna Tace ai Nima an cinye min ragowar abinci na da ruwa,wayata ma Allah ne ya kiyaye barayin suna bude kofa na fito daga Bayi da gudu shi yasa suka jefar da wayata garin gudu Basu sace ba,Baba yace ai tsafi sukeyi da tsafi suke Shiga gidan mutum ko ka kulle da key a banza,Mama Tace matsiyata Allah ya takaita Suka koma tare da kulle ko Ina. Mashkoor Yana Kan machine Yana ta jiran Ahmad har 12am ya fara gyangyadi ma Sai ga Ahmad ya fito ta baya da sauri Hannunsa dauke da Radion Baba da Startime din su Aamna wayo ya hada sabo da a tabbatar barayi ne. Mashkoor ya gano plan din abokinsa ya dinga sheka dariya yace sata har gidan surukai wannan wanne irin Dan Iskan suruki ne? Dariya Ahmad yayi yace yau nayi farin gani,tunda nake a duniya sai yau na kalli Abu mafi kyau a duniya,Duk kasar wajen da kaje? Cewar Mashkoor,Ahmad yace ai wannan duk ba kallo bane,Basu da komai me kyau,ai Country me kyau Yana jikin Aamna,Kansa ya dafe yace kaina Juyawa yake kaini gida Kar na Fadi na sume,Rawar sanyi nake ji da mun sani mun dakko Jibson ko banza ya dafe Ni juwa nake ji, Mashkoor yace me ka gani ne Haka? Cikin muryarsu ta Yan kwaya Yace New worldddd....my man,jiri nake ji....yau idona ya samu Karin karfi gani tarrr nake ganin komai,idona ya washe yau,Yau ko me Shan Carrot juice Bai Kai idona kwari da washewa ba,Fess nake gani,Mashkoor Yana ta Dariya yace barawon Suruki,yace ai dole idan ba Haka ba sai su fara Bincike suna sa Ido Watarana su kamani. Baba da safe cikin Fushi ya tashi an sace Masa startime da Radio yace wallahi kullum nayi Sallah sai na buga Tabbatyada duk Wanda yayi min satar Nan Allah ya bayyana shi,Dubu goma da motsi ai ba Nan take ba Kuma duk sakakinku ne ya nuna Mama yace Mene amfanin mace wacce Bata tattala kayan mijinta Bata kula da dukiyar mijinta komai naki Baki San adani da tattali ba ke Kam Baki Dace da matar aure ba da tsohuwar bazawara kika Yi Kama wacce mijinta ya Dade da rasuwa,Mama ta bude Baki Tace Wai ni na sace maka ne wannan wacce masifa ce akan Dan abinda Bai Kai ya kawo ba,Idan kinji haushi yau ki biyani cewar Baba,Mama Tace Zan biya ka Amma kaje Nima Allah ya isa,Baba yace ae ki biya naji Allah ya Isan. A ranar Mama ta aika aka siyo Mata sabuwar Radio da Startime,Baba yace kin taimakawa kanki. Aamna cikin wata doguwar rigar lace ta shirya sea green and milk ,takalminta,Mayafi da jaka duk milk tayiwa Mama sallama Mama Tace Yau ki dawo karfe biyu sabo da Zaki Mana wanki,to ta furta tare da ficewa zuwa Kantin,tunda taje take jiran Ahmad Amma Bai zo ba har 2pm lokacin ta rufe shagon ta wuce gida,20mnt da tafiyarta lokacin Ahmad ya Sha wanka cikin wata sabuwar Jallabiya me tsada ruwan zuma Kamar yanda ya Saba ta tsangale Masa,Takalminsa ma ruwan zuma yayi kyau tare da daura agogonsa me tsada,Sabuwar kitson calabarsa ya gyara tare da Kama ta yasa Black band ya daure ta a tsakiyar kansa,wani uban kyau ya sake tsulawa, Mashkoor Yana ta zugashi yace ai dole ma ta rude,Kaga Handsome,shi Kuma a Gaban mirror ya tsaya Yana kallon kansa sai da ya Gama yace yau ba sauki bazan kalleta ba karta ce Wani sonta nakeyi, Mashkoor yace Good ka ja ajinka ba yanzu ba kwaila Kar ta Raina mu,da Masifa Ahmad ya furta wace Kwailar dan Uwarka? Ya bi Mashkoor zai ci ubansa Mashkoor ya gudu daga room din Yana dariya. Kwafa ya ja ya fito tare da hayewa machine dinsa ya fita sai shagon Aamna Amma sai ya ganshi a rufe,Wanda ke siyar da takalma a kusa ya tambaya yace Ina me shagon Nan? Yace yanzu ta rufe tafi gida naji tana cewa zata Yi Aiki ne,Okay Kawai Ahmad ya Furta ya hau machine dinsa zuwa gidan su Aamna,har cikin gidan ya shigo da Machine dinsa,Aamna ya hango a jikin tap da tarin uban wanki a gabanta na Mama Dana Baba,Sanye take da Vest fara da Skert din atamfa wata maroon,gashinta har gadon baya Bata daura dankwali ba tana ta fama,Mama zaune take tana hutawa Kawai abinta tana ganin Ahmad ta Bata Fuska,ya manta ko Sallama baiyi ba ya karaso da Izzarsa yace Mama Barka da Rana,Baki Mama ta tabe Bata amsa ba Tace sai ka koyi Sallama sai na amsa maka gaisuwar taka,Baki ya tabe tare da yin Sallama ciki ciki ya kumbura Baki Kamar me shagwaba,Mama ta amsa tana hararsa sabo da bakin ciki,Juyowa Aamna tayi tana ta Kallonsa yanda yayi kyau,Murmushi tayi Tace Kawana Sannu da zuwa,Ahmad yace kawa ya Hanya,Lokacin Baba ya fito yace yau me Zan gani bayan auren da kuke da shi kun sake komawa sababbin kawaye Kuma? Mama Tace tayani jin sabon salon bariki, Ahmad Bai kulasu ba tunda wacce yazo wajenta tana Nan Ina ruwansa. Mikewa tayi tsaye suna facing juna juciyarsa sai bugawa takeyi duk sai ya nemi kwarin gwiwarsa ya rasa,a hankali yace wanki kike Yi me uban yawa duk ke kadai,Aamna Tace ae ya na Iya,Kallonta yayi da azababbun Idonsa masu narkar Mata da zuciya yace Bari na tayaki,Aamna tayi Dariya Tace Kaine ka Iya wani wanki kalle ka fa ko Sabulu ai baka iya wankewa ba,komai fa Yi maka akeyi,Nifa super Man ne Ina da karfi da kike gani na har noma Zan iya zuwa gona nayi,Zan Iya nome Miki gonar data fi girman gidana lokaci Daya,karfa ka Sha wahala,ya nuna Kansa yace Wasa kike Dani,Aamna ta Mika Masa kujera ya kalli kujerar yace ba Aiki kike so ba sai kace wata mace na zauna a kujera Allah kiyaye a tsaye Zan tayaki kawo bucket ki gani,Baba da Mama Suka saki Baki suna kallo suna Jin haushi su Kuma gashi Basu Isa su iya ko Masa Maganar banza ba. Bucket Aamna ta kawo Masa har biyu ya nannade Hannun jallabiyarsa dake me dogon Hannu ce,agogonsa ya cire ya ajiye gefe,Yace Ina kayanki a nan? Aamna ta Tace ka gansu a nan,yace Miko ta kansu Zan fara,ai kuwa ta kwaso ta bashi a gabansa kala hudu sai su Hijab da Vest yace idan an Gama sai kije ki cire na jikinki suma a wanke su yau baza ki kwana da Kaya masu dirty a gidan Nan ba,Baba Yana gefe yace Uhmmm.....Sun kasa magana suna tsoro Dan kwaya ne sai ya birkice musu yanzu. Ahmad wanki ya fara baya wanki Yana wanke kala Daya Hannunsa ya fara Dan fashewa Amma ya maze yaci gaba da abinsa,Kugunsa ne ya fara ciwo sabo da sunkuyo amma idan ya Kalli Aamna sai ya fasa mikewa ya huta sabo Kar ya Gaza,Haka ya wanke kayan Aamna fes ya kwashe kayan Baba da Mama Yana tayata suna wankewa ya kusa wanke na Baba,Mama ganin banza ta Fadi sai tace ke Aamna tashi ki barshi ya karasa wankin ki Shiga kitchen ki Mana girki,Ahmad yace ya Zaki ce ta tafi? Mama Tace Kai kace Super Man ne ai sai ka karasa ita ta Mana girki, to Aamna ta furta ta tafi ta bar Ahmad,tana tafiya ya Mike tare da dauraye hannunsa ya kwashe Takalminsa a Hannu da agogonsa da wayarsa,Mama Tace ya zaka daina aikin,dama yayi masifar gajiya,da masifa yace Ni na gaji bazan iya ba dama na gaji yayi tafiyarsa da sauri,Mama tana Kai...Kai....Amma ko juyowa baiyi ba ya hau machine dinsa ya bar gidan. Mama da masifa ta shiga wurin Aamna Tace to ya gudu sai ki Koma ki karasa yace ya gaji shi,Dariya abin ya ba Aamna dama tasan karfin Hali ne Kawai Haka ta fito ta karasa Mama tana ta masifa taje taci gaba da aikin girkinta. Ahmad kuwa a gajiye ya shiga gida Yana dafe Kugunsa ya Iske Mashkoor Yana kallo,Yana yatsina Fuska ya zare rigarsa daga shi sai Singlet da gajeren wando ya fada saman kujera Yana bawa Mashkoor labari yace yau wanki na tayata wash...bayana...taimaka ka siyo min pain killer a chemist kazo kayi min gashi da ruwan zafi wayyooo bayana My waist Yana magana da kyar yace yatsuna sun fashe ....Ni..Ni...nine nace Super man ne Ni, Mashkoor ya dinga dariya yaje ya siyo Masa ya dawo tare da hado ruwan zafi ya dinga gasa jikin Ahmad,shi Kama sai Kara da wayyo,Kwana Uku Ahmad Yana jinyar jikinsa kafin ya warke ya dawo normal lokacin Aamna Bata ganshi ba. Yau Juma'a cikin sababbin dinkunansa yasa wata farar Shadda kamar ka sace shi yanda ya zuba kyau,calabarsa ya daure ya shirya Yana kamshi, Mashkoor ya kalle shi yace ban taba tunanin zaka ja Ni cikin Harkar Nan taka ba,kwana Uku ko Kofar gida ban leka ba wannan wacce masifa ce Wai,Gemunsa yake tajewa Yana shafe shi da wani turare Mai kamshi yace Ni fa na fara gajiya da Harkar wani Kawa da Abokin Nan ya kamata ta San me nakeji a Raina,Mashkoor yace ka bani dama Ni naje na fada Mata kana sonta,Baka da hankali an ce maka sonta nakeyi Kuma ko sonta nakeyi wani ne zai fada Mata Ina sonta ba Ni ba,ai Ni abinda nakeji a Raina game da ita Zan fada Mata ba Wani love ba. Mashkoor yace to yanzu fada Mata zaka Yi? yace ae direct Zan sameta gaba da gaba na fada duk irin abinda zuciyata takeyi idan na ganta yau yau din nan,Allah ya bada sa'a cewar Mashkoor,Fita yayi abinsa Musa me Gadi Yana a dawo lafiya ranka ya Dade,Ameen ya Furta yiyiwa Machine dinsa key ya fita zuwa Shagon Aamna,tana tsaye tana sallamar wata ta siyi kayan kamshi ta hango shi yayi parking,Murmushi tayi Tace Sannu da zuwa,Kasa magana yayi sai kallonta yake Yi har ya karaso inda take ya tsaya a gabanta daf da ita Kamar zai shige cikinta Kuma ya Bata Rai zuciyarsa ce Kawai take bugawa,kasa fada Mata yayi yace ya gida fuskar Nan a daure,Lfy Alhamdulillah ta furta tare da cewa shigo ka zauna Rana,shiga yayi Yana ta Fushi,Tace fushin me kakeyi yau Haka? Kadan ya kalleta Bayan ya zauna a farar kujera yace da zuciyata nake Fushi ita nake nunawa bacin Raina,Dariya ce ta Kama Aamna Yana ta kallonta a ransa yace kin cuceni zuciyata bazan yafe Miki ba Kuma yau Bari na koma gida sai kinci ubanki,Me ta maka zuciyar Aamna ta tambaya yace Ni kadai na San irin wulakancin da take mini Amma ba komai Yaja kwafa,Aamna ta sake kecewa da dariya Tace kana da abun Dariya wlh,Kawai sai ran Ahmad ya baci shi ga abinda ya dame shi ya fada ya kasa fada duk akan Aamna Dan rainin hankali ta sashi a gaba tana ta dariya,a ransa yace na koma ma abin Dariya na koma Comedian ba komai yayi Shuru. Har ta Gama dariyar ta dakko Gyada soyayya Tace ga Gyada muci,ganin tasa hannnu a Ledar ta Eba tana ci sai shima zai Eba Aamna Tace tsaya na bare maka,bare Masa tayi Guda biyar ta zuba Masa a tafin Hannu Tace to ci,kallonta yayi sannan ya zuba a bakinsa Yana daga zaune Yaja baya yayi wani tangal tangal Kamar zai Fado Aamna ta rike kafadarsa da sauri tana tambaya lafiya???yace Dadi ne ya kwashe Ni sabo da hannunki da ya shafi jikin gyadar nan,Dariya Aamna tayi Tace Kai Ni nayi zaton ma wani Abu ne,wani English novel ta dakko na love tana karantawa Tace ka San littafin Nan? Na Mene ya tambaya? Love Novel ne Baki ya tabe yace sai ku wannan ai,Mayafinta ne ya Dan zame kadan gashin Gaban goshinta ya bayyana wani yala yala,Hannu ya sa tare da jawo mayafin ya gyara Mata Aamna dai mamaki yake Bata kamar ba shi ba,duk irin kiyayyar Daya nuna Mata tana ina ne? A ranta Tace Anya ba Yana da manufa a kaina ba kuwa? Gaskiya Zan nemi shawarar Siyama. Kiran Sallah aka kwala Sallar Juma'a,Aamna ta kalle shi tace yanzu za'a fara khuduba sai muje Sallah ko? Da sauri ya girgiza Kai yace a gida zanyi anjima,Jam'i Yana da Lada fa? Yace na fiki sani ai, kin San kuwa Islamiyya Nawa nayi a duniya? Kin San saukata Nawa? Aamna Tace Dan Allah muje tare,a ransa yace Yarinyar Nan fa zata fara juyani karka sake wannan Yar tatsitsiyar ta juyaka a banza,ai ba sonta kakeyi ba da har zata juyaka,wata zuciyar tace Amma idan kaje Sallar zata ji Dadi zata samu farin ciki,Kumatunsa ya Mara a hankali yace Kar ka Bari ta juyaka ka dawo hankalinka,mikewa yayi yace Zan tafi,Tace Nima tafiya zanyi zanje gidan Zuhra,yace kin fiye yawo to na fasa tafiyar Zama ya koma yayi Dole ta zauna,Lokacin Sallah yayi Yana kallo tayi Alwala tayi Sallah a Nan shagon,tana idarwa yace Sannu da kokari,Fuska ta Bata tace Dan Allah kayi Sallah Kar lokacinta ya wuce,Shuru yayi Kuma yaki tashi sai yaga tayi Fushi ta zauna,Fuskarta ya leka kadan a ransa yace akan Haka har tayi fushi,Bari to na Yi Amma badan fushinta ba,Mikewa yayi tana kallo yayi Alwala ya Tada Sallah murna tayi ta saki ranta ta juya tana kallonsa a nutse yayi sallarsa kasancewar Bai Sha komai ba,Yana idarwa ya Mike ya fice tare da tafiya ko Sallama bai Mata ba. Mashkoor kuwa Yana can a gidan Ahmad tare da su Jibson gaba Daya Yana ta Basu labari yanda Sarkinsu ya lalace,duk sukayi tagumi suna jimami,Jibson yace ai kuwa sai munje har inda yake tayata siyar da citta mun kure shi,yanzu King ne ya lalace Haka abin haushin Akan wannan Yar Yarinyar Aunty Balaraba cewar Bash,Mashkoor yace yanzu idan kaga shigarsa Daya canja kamar Limamin masallaci,Salati suka saki Tawaga yace duk akan Yarinyar nan lallai sai munci ubanta kuwa tunda ta mayar Mana da King Haka, Mashkoor yace Uhm Baku gani ba har wani sharemu yake Yi ba Amma muyi Masa Uzuri ai King ne sai abinda yace,Allah sarki masu shaye shaye da hankalinsu sun San Amana da abokantaka duk abinda dayansu ke so suna so,sannan basa mantawa da Alkhairi da zaman tare,shi yasa sun Shaku da juna sosai. Ko da Ahmad ya shigo ya Iske su tafawa sukayi ya haura sama,Yana shiga wayarsa ya dauka tare da Kiran Sis dinsa Humaira,Humaira Tace Yaya na? Ya kake? Ba lafiya sis Dan Uwanki ya fada cikin bala'i,Humaira ta tsorata sabo da Bata taba Jin yayanta Haka ba,Kamar zata Yi kuka Tace Yaya mene ya sameka? Sis wata ce Nan idan na Ganda zuciyata kamar zata fito ta fado,sai ta dinga Yi min kida me zaki,Humaira Tace Kamar ya? Yace idan fa ban ganta ba bana iya bacci,sai na ganta nake samun nutsuwa,Haka idan naji muryarta sai naji Kamar wani kidan goge sabo da Dadi,gashi tsoronta nakeyi sai naji na kasa fada Mata me nake ji,Yanzu ya zanyi? Humaira tayi zaton zaice Aamna ce Amma yace Mata wata,Amma duk da Haka tayi murna yayanta ya fada soyayya,Tace Yaya kaje ka sameta karka ji tsoro Kawai ka fada Mata me kake ji,ka daure Haba Yaya kamarka wace zata ce baka Mata,Sis Nifa ba sonta nake Yi ba Kawai dai Ni na fada Miki abinda nake ji,Humaira tayi Dariya tare da furta ka fada Mata karka ji wani shayinta kaji,yace to sis Zan gwada ya kashe wayar,lokacin da yayi wanka su Jibson sun tafi sai Mashkoor sai shi. Ahmad dakin Aamna ya Shiga Wanda ta bari,cikin kayanta data Bari ya zabo wani Mayafi Baki ya fito Palo wajen Mashkoor tare da jefa mayafin a jikin Mashkoor yace Man tashi ka yafa mayafin Nan za mu gwada practical akan yanda Zan furtawa Aamna me nake ji game da ita,yanzu ka yafa mayafin Nan Kaine a matsayin Aamna Ni Kuma Zan zo na gwada ya zan bullo Mata idan naje, Mashkoor ya dinga dariya harda buga kafa,ya Mike yayi Rolling da mayafin Aamna ya taho Yana yanga tare da wani shanye Hannu,a Gaban Ahmad ya tsaya tare da Yi Masa fari da Ido ya wani tsotsi lips yace Hey.....harda rike hips da Hannu Daya yanda Mata ke Yi,Ahmad Dariya ta kamashi shima ya kalli Mashkoor yace to ai Ni gemunka ne idan na kalla Taya Zan maka magana Ina ganin gemu dalla jiba Muscle dinka damatsa na maza,jiki Kamar katako, Mashkoor ya sake makale Murya Yana fari da Ido yace Dan Allah kayi mu gwada ai Kawai Kamar shooting Film ne Oya fara Mana nine Aamna gani. Ahmad Yana daga zaune ya fara magana Kamar zaiyi kuka,Baby Idan na ganki zuciyata wani Dancing take min,Idan kika min murmushi kuwa har wani Rawar galala zuciyata take min,Sannan Ni sai naji Ina shakkar Yi Miki magan....da sauri Mashkoor ya dakatar da shi yace dalla Haka zaka Yi lallai zata Raina ka Haka maza ke magana wani gadangatsai Taya zaka burgeta oya canja salo Action.....Ahmad yayi Gyaran Murya tare da gyarawa ya kalli Mashkoor zai fara magana sai ya sheke da dariya yace wallahi idan na kalli Damatsanka hankalina Bai kwanciya bana kallonka a Aamna ga gemu da saje haba,Kayi sauri Dan Allah wannan fa Kamar Film ne gwada Ina jiranka Mashkoor ya furta Yana wani Fari da Ido Yana karairaya Kamar Dan Daudu,Ahmad mikewa yayi tsaye yace Ni bazan iya ba kallonka nakeyi wani Gardin banza dalla bani ya fisge mayafin daga jikin Mashkoor tare da ajiyewa a gefensa, Mashkoor yace kaga matarka ce fa ka daina wannan abin ka fadawa Mummy ta fadawa Aamna ta dawo gidanka kaga shike Nan. Ahmad yace baka da hankali Nifa ba Wai wani mu zauna tare ko wani Sex ba,ya za ayi na birgeta,ya za ayi tasan me nakeji a Raina game da ita shine Kawai dawowarta gidana ba shine mafita ba,Ni ba wannan nake so ba,Dan dawowarta ai ba matsala bane Kawai Ni ka Gane nufi na,idan ta San halin da nake ciki Nan gaba Sanda taga tana so sai ta dawo gidana Ni wannan ba shine damuwa ta, Mashkoor yace Amma sai kayi ta wahalar da kanka kana tsallaka musu gida,Kai banza ne bana so ajina ya zube ta Gane Ina son na kalleta ko wani Abu,ai abin sai da dabara cewar Ahmad. Da dare 9pm Ahmad suka Isa gidan su Aamna Mashkoor Yana jiransa a can bayan gidan,Wai shi lallai Bai so Aamna ta Gane Yana son ganinta sai dai ya kalle ta a boye. Sharhi AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 51-55 KARSHEN FREE PAGE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. NA KUDI NE MASU SHIGA GROUP DARI BIYU 200 NE ACCOUNT NUMBER 0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER 08033933642 YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER +227 90 79 59 39 Official By AsmaBaffa Kinfi karfin page NAFEE Allah ya bar kauna Page naku ne MAMU GALADIMA AYUSHEE MOM PAPI AND ALAMEEN OUM ABULKHAIR HAUWANCY COOL LIFE S.Y.SAGAGI RA'AYYS I HAFSAT UMMY MANGA MAMAN ARFAT MAMAN YASIR M DEWU HAUWA A CHINDO HALIMA GODIYA TA MUSAMMAN DIYAR KATIBI UMMIN HIBBAH UMMA KHURSUM ASMAU YUSUF UMMIN DEEJAT BESTYNBEELAT Yau Baba Bai dawo da wuri ba,Aamna Kuma dawowarta kenan daga gidan Zuhra Mama Tace tazo ta tayata dafawa Baba abinci,ko hutawa Bata Yi ba ta shiga wajen Mama a kitchen suna girki,ta Kofar gate Ahmad ya shigo gidan,ta windown kitchen ya leko dai dai lokacin Mama ta dago kanta sama Kawai Harshen Ahmad ta gani ya Mata gwalo ya bace. Amma Bata San shi bane Tace Kinga kamar Harshen mutum ta window ya min gwalo ya bace Aamna,Aamna ta sheke da dariya Tace wallahi Mama yanar Ido ta Kamaki sai munje asibiti an duba idonki,Mama ta dage ita fa sosai taga Harshen mutum,Aamna ce ta maida abin Dariya shi yasa Mama ta hakura Kawai, shi kuwa ya gansu a kitchen ai ta Kofar Palo ya shigo a hankali ya shige Dakin Aamna,bed din Aamna wani me kyau ne na karfe irin na kasar waje Dan madaidaici Amma kasan bed din Yana da tsayi mutum zai iya Shiga kasan Bed din ya buya gashi ta gyara bed din ta saki bedsheet har Yana taba kasa ma'ana ko mene a kasan Bed din baza a iya gani ba,lekawa Ahmad yayi ya kuwa shige ciki ya kwanta abinsa,Bai Dade ba Aamna ta shigo dakin tare da dannawa kofarta key,Abincinta ta Ajiye a plate da ruwa harda lemo mirinda,ganin ba kowa a dakin ta kulle ko Ina sai ta hau tube kaya,dama dabiarta ce idan ta kulle Kofa ta dinga tubewa daga ita sai pant ba komai a jikinta,Ahmad yace yau ma idona zai samu Karin karfin gani Ni da ciwon Ido haihata haihata ya Dan leko ta kasa,Baki ya bude ganin Aamna da pad a jikinta da Alama period takeyi,Yana kallo ta dakko wata pad din da bakar Leda ta shige toilet sabo da Gadarar ba kowa ga towel a Hannunta Amma Taki daurawa ta tafi da shi a hannu. Fitowa Ahmad yayi ya Bude plate din yaga rice and stew da Naman rago yanka Uku sai salat a gefe,yace da a gidana ne sai kinci nama kin koshi duk Loma Daya sai kin hada da yankan nama,Sorry My world ya rufe Mata tare da komawa kasan bed,ta Dade tana wanka kafin ta fito tana goge jikinta ta fara shafa lotion ta cire guntun Towel din tana ta shafe jikinta,Ahmad Idonsa Yana waje ya leko yace sunanki me Tinjim daga yau,sai data Gama sannan ta saka Riga da wando na bacci masu laushi ta zauna ta tare da fara cin abincinta da mamaki yaga ta cinye tas ta shanye lemo da ruwa,a hankali yace Allah yasa Ina da kudi Zan iya ci dake Amma da talaka kika aura ai ke Kam shikenan sai dai Gomnati ta kawo dauki, Popcorn yaga ta dakko a wani katon Bowl ta Ajiye a gefen bed ta kwanta tana latsa Wayarta tana ci a hankali,idan ta eba ta cire Hannunta tana can tana Danna waya sai ya zuro Hannu ya eba ya cinye a kasan Bed, suna Haka taga wayam Wai har ya Kare,Aamna ta dinga mamakin kanta Wai har ta cinye popcorn din,ta kashe Wayarta tare da kashe light ta kwanta tana adduoi kafin ta Gama Adduar bacci ya kwashe ta. Sai da ya tabbatar baccinta yayi nauyi sannan ya fito a hankali da Dan hasken wayarsa yayi amfani tare da Kare Mata kallo,Aamna ta baje a saman Bed,cinyoyinta Suka tafi da hankalinsa Hannu yasa tare da shafa su a hankali yanda baza ta tashi ba,motsi tayi kadan tare da sake wangale su,Ido ya Kura musu yasa Hannun ya janye rigarta sama sosai ya kallesu son ransa, ganin kamar zata farka sai ya daina, Kansa ya duka a saitin kirjinta tare da kwantar da Kansa a Kirjinta yaji wani laushi sai ya lumshe Ido Nan take yaji ya fara Jin bacci,da sauri ya tashi Jin ta hada zufa sosai sabo da Rashin wuta bare a kunna fanka,Mifici ya gani a can gefen bed din nata,Dauka yayi a hankali ya shiga yiwa Aamna fifita ba ji ba gani Kamar me jinya a gadon asibiti,Aamna cikin bacci taji Iska me Dadi tana Ratsata ta sake gyara kwanciya tare da Jan numfashi me Dadi,Murmushi yayi yaci gaba da Mata fifita sai da Hannunsa ya gaji sannan yaga Kamar zata farka sai ya ajiye mificin ya lallaba ya bude Kofar a hankali ya fita Allah yasa Bata farka ba Kuma Bai hadu da kowa ba har ya bar gidan, Mashkoor Yana ta uban jira ya hauro ya fito Suka tafi gida. Hannu Dayan Wanda ya shafa Cinyar Aamna sai Ahmad ya daga shi sama kada ya daina amfani da shi Kamar Wanda aka yiwa lallen Sallah,Mashkoor yace lafiya Wai me ya samu Hannun rauni kaji ne?yace ai wannan Hannu yau ya Zama special bazan na aiki da shi ba,Kai ko Gaisawa da maza bazai Yi ba sabo da jikin Aamna Yana makale a jikin hannun Nan, Mashkoor yace ka shiga Uku wallahi king. Bayan Kwana uku Siyama ce ta Kira Aamna lokacin Aamna tana shago Tace gani Nan zanzo Miki Ziyara,da murna Aamna Tace to sai kinzo,15mnt da yin wayarsu Ahmad yazo sanye cikin 3qutr da t-shirt hannunsa dauke da wata katuwar leda baka,Murmushi Aamna ta saki tare da Furta Sannu da zuwa,jajayen lips dinsa ya turo gaba da shagwaba,Ledar ya kawo gabanta tare da ajiyewa ta Bude yaga kifi tarwada da yawan gaske,murmushi ta saki tare da Kallonsa Tace yanzu baka manta ba Ashe Kuma ma ai Rannan ka Aiko Mashkoor ya kawo min kifin harda kaji da yawa fa,Ba kince kina sonsa ba? Ae ta furta yace to ai shine na kawo Miki,Kuma kaji ai Naga a gidan Baba bakya cin nama kina koshi shi yasa duk sai ramewa kike Yi,Dariya Aamna tayi Tace Ni bana son sharri duk kibar Dana yi,Kallonta ya tsaya Yana Yi har ta Gama dariyar,ke komai naki Dariya Wai Ina rashin kunyarki tayi ne da surutunki? a baya masifa kike min da Shishigi me yasa yanzu kika daina? Aamna kanta ta danga sama tayi fari da Ido Ahmad a ransa yace Mashaallah ko iya wannan aka barni da shi ya isheni farin ciki na sati Guda idan na tuna shi. Mikewa tayi tsaye tana Masa Murmushi Tace Kaine ka gyara min halaye na,kaci ubana da yawa sai lokacin na Gane Allah Daya,a hankali yanda baza taji ba yace ai Nima yanzu uban Nawa kike ci na Zama wani banza,Bakinsa taga Yana motsi Tace me kace? Cewa nayi Ni ba abinda na Miki kece kike min shishigi,Siyama ce tayi Sallama gabanta ya Fadi ganin Ahmad da Aamna a tsaye daf da juna kamar zasu Rungume juna,Fuska ta Bata tana Hararar Ahmad sabo da kishinsa,ita ba hassada takewa Aamna ba Kawai son Ahmad ne yayi tasiri a ranta taji dama ita ce. Laaa Siyama kinzo cewar Aamna,Ahmad juyowa yayi Amma ko kallo Bata samu daga gare shi ba ya maida hankalinsa cikin Shagon,Nan Siyama ta shige ciki ta zauna tana satar kallon Ahmad,Ledar dake gaban Aamna take ta faman kallo taga kamar Abu na motsi ciki,Ahmad ganin tana ta kallon Ledar ya tabbatar Aamna sai tabawa Siyama kifin Nan itama ko su raba tare sai ya leka Daya shagon ya Kira wani yaro Wanda Ahmad yasan Yaron kusa da gidan su Aamna yake ganinsa shima gidansu makwafta ne,Yaron Yana zuwa Ahmad harda shafa Kansa yace Dan magyatso kasan gidan su Aamna? Yaron da Ahmad ya Masa suna da Dan Magyatso yayi dariyar sunan sabo Yaron Kalar yunwa ne,jikinsa tsilili cikinsa Dan kato sabo da Almajirin gidan Wasu ne a kusa da gidan su Aamna,yace ae nasan gidan Ina shiga ma idan an aikeni,Ahmad yace ka iya machine? Yaron yace sosai ma ai Ni nake yo cefane a machine din gidan Uwar dakina,Good cewar Ahmad yace ungo key din machine Dina jeka gidan su Aamna ka kaiwa Mama sakon Nan kace gashi inji Aamna,Yaron yace to ya karba ya hau machine din Ahmad ya tafi,Siyama ta so ace ta karbi kifin ko Quarter ne itama taje gida sun Sha farfesu Amma tana kallo Ahmad ya dauke Dan mugunta. Tunda Siyama ta Shiga shi ya fito ya tsaya a waje,Aamna Tace ka shigo Mana yace a'a Machine Dina nake jira tafiya zanyi,Siyama ta kalla tace ina zuwa kawata ta fito Wajensa suka tsaya,tana ta Kallonsa a ranta tana ayyana irin kyansa,Shi kuwa ganin tana kallonsa harda Kara gyarawa Kamar za a dauke shi hoto,idan ta kalla ta kalla sai ya sake canja style din tsaiwarsa Haka yake ta Mata ya tafi da hankalinta sai daga baya ta lura da abinda Ahmad ke Yi Yana ta canja style din tsaiwa,Dariya ce ta Kama Aamna ta danne kadan tayi Murmushi Kansa ya shafa tare da mazewa kamar ba shine yayi ba,Hannunsa Aamna ta rike ya Janye hannunsa da sauri,Aamna tace lafiya? Kitsonsa ya Sosa yace ba komai Kawai Ni ba a taba min jiki kin sani ko kin manta ne? Baki Aamna ta tabe Tace daga an Dan rike maka Hannu sai kace Dan gwal? Yace ai nafi gwal Ni,Harararsa tayi a ranta tace Dan ma na Dan nuna Masa caring shi illarsa Bai San arziki ba,Ganin ta harareshi yace Jaraba tare da miko Hannun yace ungo cinye shi ki huta,Bige Hannun tayi tana Dariya Tace bana so,Suna Haka Yaron ya dawo da Machine din Ahmad ya karba tare da bawa Yaron dubu biyu,ya dinga Murna yana godiya,Ina Handbag dinki? Ahmad ya tambayi Aamna. Tana ciki yace dakko min ita,me zakayi da ita Fuska ya Bata yace ki dakko Mana Ni ba Mudubi ko powder dinki Zan gani ba nasan ku ba Uwar komai a jaka sai Kuna boyeta,Dakkowa tayi tare da Mika Masa yace Bude abarki ki rufe idonki Kuma,Aamna ta zuge jaka ta rufe ido,ganin Haka Siyama ta leko tana kallo Ahmad ya zaro kudi masu yawa Yan dubu dubu ya zubawa Aamna a jaka yace to Bude,Bude Idonta tayi taga kudi dama Bata da kudi tayi broke Bata da ko sisi gashi tana son siyen abinda ba a rasa ba na bukatar rayuwa,taji Dadi sabo da ya Bata lokacin da take bukata Tace Na gode Allah ya Kara budi Amma sunyi yawa kamar,Kansa ya dauke yace na tafi Mummyta ta aikeni tun dazu wani waje zanje na Mata Abu,Aamna Tace Kai dai kana son Mummy kullum Mummy,ai Mummy ta daban ce,Mummy na tafi Mummyn kowa cewar Ahmad,Aamna Tace Nima tawa tafi ta kowa,Murmushi yayi yace kin nemi Number Abbanki kuwa? Aamna Tace me Zan Masa tunda ya manta da ya auri Uwata ya Kuma haife Ni idan na karba me Zan Masa? You are not Serious Haka aka ce Miki Iyaye suna laifi?Shuru Aamna tayi Watarana tana mamakin Hankalin su Ahmad,gasu dai suna tafka abin tsiya sai Suna Abu Kuma na basira da hankali, a fili tace Suma Yan Uwan nasa Dana je Sokoto nace su bani number dinsa Suka ce wallahi wurin shekara Uku kenan duk sun kasa Samunsa sai dai suna Kiran Yan Uwa na can kasar sunce yana Nan lafiya Kawai dai yanzu yayi retire a aiki Bai da aikin Yi ga Yara da Mata sun Masa yawa wahala ta kamashi,Ahmad ya girgiza Kai yace tab nasan yanzu ya sake kanjamewa Allah Sarki Abbinki,Aamna Dariya ya Bata ta bigeshi a kafada kadan Tace Wai Mene Haka ka dameshi Akan ramarsa, Murmushi yayi yace Bai yuwa ya rasa waya sai kace a Nigeria ai can ba a wannan talaucin, Ni Zan nemo Miki number dinsa,Aamna Tace Okay thanks, Machine dinsa yayiwa key tare da tafiya abinsa. Siyama tana zaune ta kumbura tayi fam kamar ta fashe tace ke dai Aamna kinyi asara,wallahi Baki da hankali to wannan abinda yake nuna Miki ba so bane,Kar ma ki yaudari kanki Ahmad bazai taba shiryuwa ba ko jiya naje wajen Jibson a club Suka kwana suna shaye shaye suna rawa,Aamna Tace karya kikeyi Siyama wallahi Ahmad baya rawa,Yana Jin kida Yana bin Waka Amma in Banda ya Dan kada Kansa ba abinda ya taba Yi na rawa,Da kike cewa bazai shiryu ba kece Allah,Ina ruwana da Club dinsa,Siyama Tace Iyye to Bari kiji idan Baki sani ba Neman Mata suka koma Yi yanzu,kije ki tambaya Ahmad lallabaki yakeyi ki saki jiki da shi ya samu biyan bukata,Aamna Tace karfa ki manta Mijina ne,ko ma me yayi Hakkinsa ne ko ciki ya min akwai me zagina a duniya? Wai me yasa kika tsani Ahmad Haka ne Siyama? Siyama Tace sabo da Ina sonki kawata Ina kaunarki bana so ki fada wani Hali,Aamna tayi shuru....Tace to yanzu me kike so nayi? Karki bashi dama Kawai Kuma karki yarda da shi karki Bari Zuciyarki ta fada sonsa cutarki zaiyi,ki kiyaye Aamna bana so na ganki cikin wani Hali,plan suka hada Miki,Ahmad tun Yana yaro kangararre ne a Haka ya girma a tunaninki dare daya zai shiryu sabo da ke? Kiyi tunani fa,wanne duka da wulakanci ne Baki Sha ba a Wajensa? Ai Ni nake tsokanarsa Aamna ko a lokacin Ni ke shiga harkarsa da ban kulashi ba babu abinda zai min,Siyama tayi Dariya Tace kina Abu kamar yarinya 25yrs Sam Baki da wayo Baki da hankali Ni Naga wani Tsoronsa kike ji ma kina wani biye Masa,Dan giya irin wannan Dan kwaya abin kyama cikin Al'umma mutanen da Basu San darajar kansu ba bare ta wani Nan fa Siyama ta dage ta dinga zuga Aamna tana fada Mata karya,har ta Gama sannan Aamna Tace Ni fa bazan iya wulakanta shi ba,Kuma bazan iya masa komai da zai Bata Masa Rai ba,Kawai dai nasan bazan Bari na fada sonsa ba,ko cewa yayi Yana so na Zan Amince Amma badan so ba Zan Amince Dan nayi kokari na canja shi ya dawo mutum Kamar kowa ya daina wannan shaye shayen shine Kawai abinda Zan iya Dan na taimaki Iyayensa,Siyama tace ya dai fiye Miki Ina Baki shawara karki fada sonsa. Bayan wasu satikai Ahmad Haka yake ta wahala da zuciyarsa ya kasa fadawa Aamna idan yaje da Niyyar fada sai ya kasa babu irin plan din da Basu hada ba da su Mashkoor Amma idan Ahmad yaje Gaban Aamna sai ya kasa furtawa,Yau Suna zaune da Mashkoor suna shaye shayensu Mashkoor yace yau shine Plan na karshe King idan baka iya fada Mata ba wallahi gidan Nan Zan Bari kaje ka karata,Ahmad ya daki Center table yace yau Dole ne na fada ma Dole babu fashi mene plan na gaba?wayarsa ce tayi Kara Yana dubawa yaga Bash ne abokinsu dagawa yayi yace ya akayi ne guy? King ku fito Umman Jibson ce ta rasu a asibiti ciwon Sugar dinta ne ya tashi Ana kaita Hospital ta fece wallahi,Ba ko Salati Ahmad yace yanzu Ummati ta ware itama? Yace kwarai kuwa Kun manta yau Kuma ake Sadakar Arba'in din Baban Tawaga da ya Dier shima ya kamata ku fito fa Jibson Yana wani Hali, Mashkoor ya kashe waya tare da kallon Mashkoor tashi mu tafi Ummati ta arce itama shikenan mijinta yayi asarar matarsa Allah sarki Shan maganin Mata ya Kare Abbin Jibson Kuma karya ta Kare Dadi ya kare Masa ya Gama Shan rabonsa, Mashkoor yace Kai tsohuwar Nan ai ta godewa Allah ai su Kam sunci duniyarsu me zasu ce da Allah mu ware kawai. Machine suka figa Suka tafi Ahmad ya kalli Musa yace Kai Musa ka taho ta'aziyyar Ummatin Jibson kaga ku na kirki ne wala'allan adduarku tafi Shiga,Dariya abin ya Bawa Musa ya danne ya nuna jimaminsa yace gani Nan kuwa Bari na kulle gida,Ahmad yace biki ya same mu sabo da yanzu mutuwa ta koma biki Yan iskan mutane su taru ayi ta kwasar girki, Mashkoor yace Ana kaita kabari muje a agazawa su Jibson da tallafin kayan abinci kasan babansu ba harka Yana Shan wahala,Haka ne fa Guy cewar Ahmad,ai kafin kace me Yan shaye shaye ta ko Ina abokan su Jibson suna ta sauka wasu a mota wasu a machina, da su aka yiwa Ummatin Jibson Sallah aka kaita,Tabarmar su daban a Kofar gida sunyi jungum jungum Ana zaman makoki,Jibson ya dunkule waje daya a tsakiyarsu tare da sunkuyar da Kai kasa Yana Dan Hawaye motsi kadan sai Yace Uhmmmmm........Uhmmmm.....su Kuma abokan suna Sorry...sorry....Guy,Baban Jibson Yana kusa dasu Yana jinsu da mutanensa shima Ana karbar gaisuwa,duk Wanda yazo yiwa Jibson gaisuwa yace Ashe Ummati ta rasu? Jibson sai yace da Uwata ta mutu gwara Ubana ya mutu wallahi,Kowa yazo sai Jibson ya fada Masa da Uwata ta mutu gwara Ubana ya mutu Abbin Jibson Yana ji Yana ta Jan kwafa,wasu kuwa dariyarsu Kawai suke dannewa. Tawaga ne yazo ya kotse machine tare da bulbule mutanen wajen da hayaki ya sakko wajen su Ahmad ya Bude hannaye da sauri Yana takowa Yana an Kuma...an Kuma Yan Uwa an Kuma jama'a...suka ce cikin jimami an Kuma Guyu......ciki yazo ya zauna yace Yau akayi Sadakar Arba'in ta Abbana Ni fa yanzu gaba daya na koma Wani shege....shegeee ne Ni Kawai bani da uba...kaf mutanen wajen babu Wanda Bai Basu Dariya ba Amma wasu Haka suka danne sabo da wajen Mutuwa ne,wani Wanda ake cewa Gayu yace ai Nima Ina cikin Shegun mu mun Zama 'yayan shege to ba uba ai Kawai ka Zama Dan shege....wani Ana kiransa Jagu Dan wiwi a cikinsu yace wannan abin idan na tuna ba karamin kuka yake sani ba ya fashe da kuka shima Yana cewa Nima Ina cikin 'yayan Shegu,Wai su Kawai idan baka da uba ya mutu to ka koma Dan Shege,idan Kuma Uwa ce to ka Zama cikakken Maraya komai girmanka. Ahmad ya dafa Jibson yace ai gwara na Zama Shege akan na Zama Maraya Jibson,Mummy ta Mutu ai Kawai ku kaini kabari da Raina Nima ku binne,Mashkoor yace mu Kuma mu zauna da wa idan mun binneka shike Nan muma Bamu da kai? Ai bazai yuwu ayi biyu babu ko daya ba,Ana ta kallonsu Dariya ta cika mutane Amma an kasa Yi sabo da mutuwa kowa sai ya bar wajen yake Dariya,Wani Dan Majalisa yazo Ta'aziyya,Baban Jibson ya Kira shi yace ga babban Dana can,Jibson ya karaso wajen,Dan Majalisa yace Sannu da Hakuri Allah yaji kanta yaro kayi Rashi,Jibson yace Babban Rashi yau na tabbata Maraya Dan Allah ku bani mukami a Gomnati na shugaban Marayu na Nigeria da Uwata ta mutu wallahi gwara Ubana ya wuce sau dubu dubu,Danmajalisa shima abin Dariya ya bashi gashi da yanda suke Maganar abin Dariya ta Yan maye. Kudi ya zaro dubu Ashirin ya mikawa Jibson yace gashi ko ruwa a siyawa Mutane Jibson yace Allah kiyaye na karbi bakin kudi,wannan bakin kudi ne tunda baka bani ba sai da Uwata ta mutu zaka bani wanne amfani zasu min,Baban Jibson ya daka Masa Tsawa Amma Jibson yace wallahi bazan karba ba,da karfi ya daga Murya Dan wulakanci sai da aka ga Uwata ta mutu Za'a taimakeni duk an wani cika Mana Kofar gida Ana cinye Mana Dan abincin Daya rage Mana,Dame zamu ji da cinye abinci ko da jimamin,kowa Yana ci Yana wani jimami,Mata Yan Uwa suna kuka suna ta girki Ana Dora tunkunya Ana saukewa wallahi baza mu lamunci wannan ba,Ahmad ya mike shima yace a barmu da abinda ya dame mu na rashin Ummati mun gaji tun safe muke bi layi layi na mutane Muna rabon ruwan Sha da Abinci,Tawaga yace aikin banza Muma Haka Dan kudin Sadakar da aka Tara Mana da abincinmu cikin sati Daya aka cinye shi tas ga tarin Yara an mutu an bar min,Baba ya dinga aure aure ya Tara Yara Ashe duk Haihuwar da akeyi Ni ake haifawa ban sani ba, wallahi da nasan hakane da kaina Zan dauki matan Baba na kaisu asibiti Dan ubansu duk a daure bakin Haifarsu,yanzu ga Yara can sunfi ashirin Ni kadai ne Babba Kuma ba Wani Abu ya mutu ya Bari ba gona ce Kawai a Kauye Guda biyu. Ina Shiga gida Yara suna zare Ido Yan kanana turagutsa ba Wanda zai iya aikin karfi to wallahi a Nan ma tunda Ummati ta rasu Baba baza ka Kara aure ba wallahi ko wace zata aure ka sai mun farke Mata ciki,Ahmad yace bazai yuwu Iyaye ku dinga aure aure Kuna mutuwa Kuna bar Mana masifa ba,ga yanda kasa take ciki yanzu a mutu a bar maka Yara Kai kanka da kyar kake iya rike cikinka, daga yau mun Zama masu yaki da Aure auren Iyayenmu maza,duk tsohon Daya matsu zai Kara aure to ya Nemo juya wacce Bata Haihuwa ko Kuma aje a cire Mata mahaifa. Jibson yace Iya Ummati Abbi ya aura Amma Haihuwar ta Sha Uku Haba jama'a sai kace macen Zomo, Guda Daya ne ya rasu Sha biyu suna Nan cas da me zanji gasu duk mata,ko wacce na shiga Yaya kudin makaranta,Yaya kudin kitso,Ya..ya..ya...masu auren ma yau Fa'iza mijinta ya hanata abinci ta dawo gida an auno Mata shinkafa ta tafi da ita,gobe Safiya mijinta ya mareta ta kawo Kara,jibi Zakiyya mijinta ya korota to a gaskiya bazai yuwu ba,daga yau kunci abincin karshe gobe ko koko ba me Fitowa da shi wallahi. Mutane suna ji Ana ta kallo wasu suna zanzarewa Baba shima yasan Yaran sunyi gaskiya tsoro yake ji Kar a cinye Dan abincin nasu su fada wani Hali Amma sun tozarta shi ya zaiyi dole ya kyalesu tunda su suke siyo komai abokan,Ahmad kadai mota guda ya sauke musu ta kayan abinci da safe,Haka duk abokan kowa iya karfinsa sun kawo tallafi daban daban,Kuma ko ba mutuwa sune suke taimakonsu basa kukan rashi. Ranar da akayi Sadakar Uku suka Kori kowa Suka ce Sunna sak ba zaman makoki ya Kare,Ranar Bash ya tafi gida ya Iske Mamansa tana Aiki yace Mama Yaran naki Mu bakwai kika Haifa Dan Allah Mama karki sake Haihuwa Haka,Mama ta kalle shi tayi murmushi Tace baka da kunya Bashir Ni kake gayawa Haka? Wato ka Sha ta maka yawa zaka zo ka min hauka ko? Bash yace Mama Naga darasi Yaran Nan Ni fa kuke haifawa kina ganin Yayana ba lafiyayye bane yanzu nine kamar Babba gashi Mama da kuruciyarki,Dake ita Maman Bash sai ka rantse ba ita ta haife su ba,Allah ya Bata kyan jiki karamin jiki gareta sai ka rantse Yayarsu ko kanwarsu,Bash yace Mama gobe Monday ki shirya zamu je asibiti ki duba abokina,Mama Tace Allah ya kaimu Bashir. Washe gari da Sassafe Bash ya dauki Mama zuwa Asibiti,wajen Likita Mama taga sun shiga,Bash yace Likita gata na kawo maka ita akan Maganar da mukayi,yace matarka ce ko me? Kawai Bashir yace Matata ce, Maman Bash Dake akwai saukin Hali ba ruwanta yaranta Kamar abokanta tana kallo Bash yace a Mata Allurar Family planning Haihuwar ta Isa Haka,Likita yayiwa Mama tambayoyin da Suka Dace itama dama ta gaji da Haihuwar,Test aka Mata Bata da ciki Nan Likita yayiwa Maman Bash Allurar wata biyu,yace idan time ya cika ku dawo Karku tsallake,Bash yace an gama,ya figi Mamansa a Machine suka dawo gida,Kuma Mama Bata fadawa mijinta ba sabo da Bash yace karki fada Masa kin San Baba Dan gargajiya ne sai dai yaga Shuru kin daina Haihuwa,daga yau Haihuwa ta Kare a gidan Nan sun Isa Haka, Mama tana ta dariyar su Bash. Bayan Mutuwa ta lafa anyi Sadakar Bakwai Aamna yau kwana bakwai Bata ga Ahmad ba,duk ta Shiga damuwa ta Kira wayarsa Bata shiga,Bata San mutuwa aka musu ba,Shi kuwa Ahmad da dare Bayan sun Gama shaye shayensu da safe 7am ya koma gida, Mummy ya Kira a waya, yace Mummy Ina cikin wani Hali,danki ya fada soyayya jiya jiya na gano cewar Soyayya na fada,Farin ciki ya Kama Mummy Tace wannan wacce me sa'ar ce? Bata kawo Aamna bace tunda yace wata ce tasan da Aamna ce zai ce Aamna ce,ta so ace Aamna ce,Mummy Tace to itama tasan kana sonta ko me? Ahmad yace Mummy kwarjini take min na kasa fada Mata,zuciyata idan na ganta bugawa takeyi,Mummy Tace karka damu Son ka cire tsoro Kai fa Namiji ne ko wace kaje Ni na baka dama ka fada Mata duk irin son da kake mata,Ni Mummy Umarni na baka ka furta Mata karka ji tsoro,ta dinga zuga Ahmad tana dorashi a Kan hanya,suna Gama Wayar yaji wani kwarin gwiwar da Bai taba ji, yace Mummy ce ta bani Umarni,wannan Umarnin Mummy ne naje na fada Mata. Ai zumbur Ahmad ya mike sanye da 3qutr blue da Riga Armless wata white and sky,ba Wani shiri ko wani wanka da canja Kaya na Kamala,lokacin zuciyarsa ta Gama tunzura, Kansa Kuma ba Wani saiti tunda jiya an cake da yawa,7am da sassaffe ya tsaya a Kofar gidan su Aamna ya Shiga dukan gidan Baji ba gani kamar zai balla musu gate,gaba dayansu a tsorace Suka yo waje Baba,Mama , Aamna tare da Siyama sabo da ranar Siyama a gidan su Aamna ta kwana,Baba Ne ya bude kofa,ko kulashi Ahmad Baiyi ba ya fada gidan a fusace da Masifa hankali a tashe Yana Bala'i ya tsaya a Gaban Aamna Dake tsaye sanye da kayan bacci ya nunata da yatsa da karfi a gigice ba nutsuwa Yana haki yace Kin hanani sukuni...tun Sanda na ganki Bayan kin bar gidana kina shago...zu..zuciyata...ta kasa sukuni...Dora Hannu yayi aka ya sake nuna ta da yatsa da sauri da sauri yake magana ba kakkautawa Yana zaga compound din gidan Yana Wallahi na rantse.....ko idona na rufe bana bacci fuskarki nake gani kina min gizo....kullum idan na ganki zuciyata bugawa takeyi...Ina Jin tsoronki......ko yaushe bani da sukuni....burina kullum na ganki....ko naji muryarki.....bana...Bana Iya motsi sai da tunaninki......komai nakeyi kece a Raina....kece.... kike min gizo....sunanki idan aka ambata sai zuciyata ta buga.....Haka nake tsallakowa gidanku cikin dare in labe inyi ta kallonki.....Rannan ma Dan karku kamani nayi muku basaja na sace muku startime da Radio....Baba ya kurma Ihu tare da nuna Ahmad yace Kaine??......Ahmad Bai kulashi ba yaci gaba da bayani....yace kusan kullum da dare sai na shigo gidan Nan na ganki baki sani ba....har dakinki nake buya na Sha kallonki tsirara kin shiga wanka......da Ni kike rufe kofa a room Dinki duk abinda kike Yi Ina kallo....kunya ta lullube Aamna ta sunkuyar da Kai kasa. Ci gaba yayi da bayani yace duk abinda nake Miki Dan kiji Dadi nakeyi.... komai Danke nakeyi....har zuwa shago Dan na ganki naji Dadi ne.....Yan....yanzu ma....zuciyata bugawa takeyi wallahi Ina sonki....sonki nake Yi...da ban Gane sonki nakeyi ba sai yanzu.....Murya ya canja Kamar me kuka ya hada zufa Yana haki yace Yan....yanzu....ma tunda nazo gabanki zuciyata Bugawa takeyi.....idan Baki yarda ba taba kurjina kiji ya cafko Hannun Aamna ya daura a kirjinsa saitin zuciyarsa yace kinji?...kinji?....Aamna Tace ae naji ta zame Hannunta.....Siyama,Mama,da Baba suna ta tabe Masa Baki sabo da basa son abin,shi kuwa Bata su yake ba ci gaba yayi da cewa Wallahi Allah Sonki nakeyi......idan Baki yarda ba Kira number ta kiga sunan Dana saka Miki a Kan number dinki,Aamna ba musu ta latsa Wayarta ta Kira wayarsa sai ga Sunan Daya sa Mata ya Bayyana MY WORLD. Bai tsaya ba yaci gaba da bayani Yana tonawa Kansa asiri Wai duk cikin bayyana soyayyarsa a gareta ne. KARSHEN FREE PAGE ASMABAFFA. 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: P🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DAN ALLAH KARKI FITAR DA NOVEL DIN NAN BADAN NI BA DAN GIRMAN ALLAH, IDAN BAKI BIYA BA KARKI KARANTA DAN DARAJAR ALLAH. DUNIYA TA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 55-60 Official By AsmaBaffa Page naku ne mutanena Yan Albarka UMMI DEEJAT ALHUSNA Yace nine....Nine.....Ni ....ya rasa me zai ce ma karshe yace Ni...dai Dan Allah Ina sonki kinji....kinji....ya kafe ta da Ido Kamar zaiyi kuka,Mama ce tace ai taji ka kaje kawai....kallon Aamna yayi yace na tafi kawai? Ae jeka cewar Baba,yace Kawai? Suka ce ae jeka zata baka amsa daga baya,shi Kam tuni yaji zuciyarsa wasai tunda ya amayar da abinda ya dame shi sai Kawai ya juya ya tafi abinsa zuciyarsa Kuma na tsoron amsar Aamna da zata bashi Nan gaba,Haka ya koma hankalinsa ya kwanta ko Bata ce tana sonsa ba ya fada Mata sakon zuciyarsa. Gaba Daya ya samu su Mashkoor a gidan su Bash,yace to yau dai anyi ta Ta Kare yau na bayyana Mata,Ihu Suka saki na murna tare da tambayar me Tace? Yace Wai zata bani amsa daga baya,Tagumi Suka Yi Suka ce zaman makoki Bai Kare ba,Yarinyar Nan da raini take kamarka kace kana sonta Tace wani sai Nan gaba ma zata bada amsa,Gaskiya Aunty Balaraba Bata Yi ba sam,Nima Ina tsoron lamarin Nan cewar Mashkoor yarinya tsigigiya duk ta gigita Mana Kai,Ahmad yace wallahi Ni kaina zagin kaina da kaina nakeyi,kullum sai na shiga daki na tsinewa kaina sannan na fito,wannan abin tsinuwa ne Man cewar Tawaga. Aamna kuwa Bayan ya tafi Mama Tace masifa wannan wanne irin tsagera ne Haka ba ko kunya bare Kara,Baba yace Yaran karshen tashin alkiyama ne in Banda tambadewa kai mtswww Baba Yaja Tsaki,Siyama kuwa ranta yau idan yayi dubu ya baci,kallon Aamna tayi Tace Kar dai ki Kai kanki hallaka wallahi,Mama Tace Idan taje ya kasheta ai ita ta huta da Duniya Dan wannan zai iya yiwa mutum yankan rago,Aamna ce ta kalle su Tace ba Wanda zai fada min abinda ya kamata nayi,Ni matar aure ce Kuma matarsa,sannan Ni na San dai dai sabo da Haka ba sonsa zanyi ba taimakonsa zanyi na taimaki Iyayensa idan ya shiryu shike Nan sai na barshi,Zuhra ce tayi Sallama ta shigo ta Iske zancen, Siyama tana tabe Baki tana bada labari,Zuhra tayi murmushi Tace mashaallah Alhmdllh,Ke Aamna wallahi idan Zaki so abinki ki so shi tsakanin da Allah,ba'a Wasa da zuciyar mutum musamman Daya zurfafa Haka wallahi idan kika yarda bayan kin San ba sonsa kike Yi ba wallahi Kinga yanda yake zai iya komai,mijinki ne ki so abinki ki koma ki zauna lafiya,ke da Allah ya taimakeki ma iya shaye shaye ya tsaya baya Neman Mata da sauransu,karki Raina Masa hankali baza kiji da Dadi ba na Nan gaba,kiyi amfani da ilimin.....ke dalla rufe Mana Baki banza Shashasha cewar Baba,so kike ya kashe ta,ai Ni abinda nake so yanzu ta Amince Masa Kamar gaske sai mu samu mu dinga zarar kudi a jikinsa inda ya makance a kanki Haka nasan har aikin hajji sai ya kaimu,Zuhra Tace haba Baba haba Bai kamata ba,zuwa Makkah Dole ne?, Kuna cikin rufin asiri Iyayensa sun Gama muku komai a rayuwa,Baku da Muhalli Suka Baku Muhalli,Muna cikin talauci Suka fitar damu daga wannan gashi Kuna cikin rufin asiri,ci,Sha,sutura duk kunfi karfinsu Amma Baku godewa Allah ba. Dan Ubanki wanne rufin asiri ko motar Hawa bamu mallaka ba cewar Mama,Siyama Tace ai Kar ma ta wani koma gidansa,Aamna Tace Ni dai ba Wanda zai koya min komai,Kuma bazan taba karbar kudinsa ba ku daina sa rai,Nima ba gidansa Zan koma ba,Zan dai Amince Masa Dan na canja shi na taimaki Iyayensa badan komai ba sabo da Haka kowa ya Adana kalamansa,Zuhra tace to kuwa wallahi Baki tunani ba Kuma wallahi Ni na fada Miki sai kinyi da na sani Kuma sai kinyi kuka da idonki,Karki bada kofa aci kudinsa Kuma ki so shi ki kula da mijinki Aamna meke damunki haka? Allah ya gani na Baki shawara duk Sanda kwabarki tayi ruwa karki zo inda nake,Baba yace ai ke dabba ce Zuhra,Siyama Takaici yasa ta Mike ta tattara nata ya nata Tace Idan kin tsaya ya kashe ki ke kika jiyo Nan gaba Zaki ga amfanin shawarata karki biyewa Su Baba sabo da karki fada sonsa,sannan Kuma karki dauki shawarar Zuhra,Baba yace kaga Munafuka Dan Ubanki sai munci kudinsa Kuma baza ta bi shawararki ba tamu zata bi,Kuma karki sake zuwa Mana gida algunguma,Siyama tayi waje cike da kunci,Zuhra ta mike tace Aamna a buga game lafiya Allah yasan me gaskiya,Baba yace koma dakin mijinki Dan ubanki,Aamna ta Mike Tace Ni ra'ayina zanyi ba shawarar Wanda Zan dauka,Baba yace Zaki ci Uwarki Sumayya ta lahira,dama bakin halin Ubanki kika gado Wanda ya gudu ya barki,marar gata marar cikakken asali tunda Ubanki guduwa yayi ya barki,Tambadaddiya cewar Mama. Bayan Kwana biyu Ahmad shi kadai a katafaren palonsa Yana Zaune Yana kallon wani wrestling,tun ranar da ya furtawa Aamna Bata neme shi ba shima Bai nemeta ba har kwana biyu,Wayarta ta dauka ta fito tsakar Gidan can ta baya ta Kira Ahmad,Yana Zaune yaga Kiranta ya shigo,zuciyarsa ce ta Shiga lugude Haka dai ya daga,Yana dagawa ko gaisawa basuyi ba Tace Amsarka Yes na Amince Ina sonka Nima,tana Gama fada ta kashe Wayarta cike da kunya tana ta wani murmushi ita kadai,Shi kuwa tsalle ya buga tare da Kiran Mashkoor a waya,Yana dagawa yace Tace ta Amince tana so na,Yeeee....Mun lashe zabe Mashkoor ya furta Yana kuri yace ta Isa Tace Bata sonka ita din banza,haba Fesh King irinka ai karya ne,Ahmad Yana kashe waya ya Kira su Jibson Daya bayan Daya yana fada musu Suka ce Dole ayi kamarin party yau a gidan Mashkoor karfe 10pm na dare za a fara. Mummy ya Kira tana dagawa yace Mummy ki tayani murna ta Amince tana so na,Dariya Mummy tayi yanda taji Danta ya zauce Tace na tayaka murna Ahmad,yace thanks Mum,suna gamawa ya Kira Humaira Nan ma ya fada Mata,ya Kira Mufida matar Kaninsa Sadeeq ta dinga tsalle da Murna Saddeeq Yana kallonta yace kin haukace kema ai, Saddeeq da Daddy kuwa ko kulasu baiyi ba Basu San ma me ake ciki ba sai da Mummy ta fada musu,Daddy Baki ya tabe yace wannan mahaukacin Ina zaiyi wani hankali ai Ni na hakura, Saddeeq yace wlh kuwa Daddy,Harararsa Mummy tayi sannan yayi Shuru. 10pm su Ahmad aka Sha wanka gaba dayansu ba Wanda Bai kure wanka ba aka tafi party gidan Mashkoor anan suka taru harda wasu abokan daban an gayyato su tare da Yan Mata zuka zuka,ranar Giya da kwaya taci kwal ubanta,ansha kida Wanda zasu Iya rawa sunyi har kusan Asuba Ana Abu daya. Musa kuwa ya tafi ganin gida Kauye Bai San me ake ba,Bayan komai ya lafa Ahmad baya Kiran Aamna Sam,sannan Kuma tunda ta Amince Bai je wajenta ba,sannan ya dawo da sa kana Nan kayansa kamar da,Shaye shaye ne dai dama tunda tunaninta ya sashi a gaba ya Dan rage kadan. Aamna kwana biyu taji Shuru sai Kawai Tace Bari na bashi mamaki,5pm ta fito ta Sha uban wanka cikin wani Fari da bakin material cikin na lefenta me kyau da tsada yasha uban dinki Kamar Readymade,tayi kyau kamar a sace ta,Takalminta me tsini da jaka bakake,Mama Tace Ina zuwa Haka? Karya Aamna tayi Tace gidan wani bikin kawar mu zamu je da Siyama,Baki Mama ta tabe tare da Furta shine harda uban gayu Haka idan wani ya tareki a hanya yace Yana sonki fa? Shuru Aamna tayi Tace sai na dawo tayi waje,Already me Napep din data Kira Yana jiranta a kofar gida,Shiga tayi Suka tafi,a bakin gate din gidan Ahmad aka ajiyeta Aamna ta Shiga buga gidan,me Gadi baya Nan shi yasa Ahmad Bai fito da wuri ba,taci sa'a Yana gida,Sanye cikin black jean pencil da Riga t-shirt me gajeren Hannu wata ruwan toka ta Yan birni,Yana Gadara ya fito ya Bude kofa,ai mamaki yasa ya tsaya cak,Farin ciki ya lullubeshi,yace wow...My World.....oh....ya juya Tare da tafiya yayi Yar safa da Marwa yace ya akayi Baki ce min Zaki zo?Murmushi Aamna tayi Tace Surprise...kallo ya Kare Mata tare da furta Ohhh.....kinyi kyau Beb....duk wanka nane? Aamna Tace ae Mana,Hannaye ya Bude tare da Matsawa ya rungumeta kadan yace Sannu da zuwa,Yawwa Aamna ta furta tana Jin kunya tana murmushi. Yace Feel free gidanki ne fa shigo ciki,ta na shigowa yace Yi Hakuri Bari na rufe gate duk ya rasa inda zai sa Kansa,Yana Rufewa ya dawo da sauri ya Sha gabanta Yana tafiya da baya da baya Yana cewa kece a gidan Nan yau? Kika zo wajena Kai yau kin Gama min komai My world,Dariya tayi shima yayi Dariya,Tsayawa tayi cak shima ya tsaya suna facing juna,tana Dariya Tace Ka nutsu karka Fadi,yace idan na Fadi a kanki wani Abu ne? Idan na Fadi ma Sai na tashi ai kin cancanta a Fadi a kanki,Rigarsa ya cire daga shi sai dogon wando,surarsa ta bayyana,Aamna a ranta Tace gaskiya Namiji ne,wow kalli jikinsu sumulmul,Da rigarsa yayi amfani kafin Aamna ta taka waje Sai ya share Mata hanyar da rigarsa Haka suke ta tafiya Yana cewa My World yana ta murna, Aamna tana ta dariya har Palo Suka shiga da sauri yasa rigar ya sake goge Mata saman kujera sannan yace to zauna,Zama tayi ya tsuguna a gabanta tare da daura Hannayensa saman cinyarta yace me Zan kawo Miki My world? Aamna Tace koma Mene,Alright ya Mike tare da daukan hanyar kitchen,har ya tafii sai ya dawo yace karki damu kinji yanzu zanzo,to Tace ya fada kitchen,abincin Daya dafa dazu Jullof rice ta Sha Vegetables da nama ya kawo Mata a plate tare da ruwa da lemo. Plate dinma Kalar Design dinsa shape din zuciya akayi sosai ,Zata Bude abincin yayi saurin dakatar da ita ya Bude tare da nuna Mata plate din taga shape din love ne,Dariya tayi Tace wow....gefenta ya zauna tare da tsiyaya Mata lemon da ruwa a glass cup yace oya eat,Spoon ta dauka ta ebo abincin taci taji Dadi sosai Tace wow wannan Dadi Haka,Murmushin Jin dadi yayi Yana kallonta tana ta ci da sauri da sauri sabo da ya Mata Dadi,Santi ta fara Yi Tace Kuma Kai ka dafa? ae Mana ai kin San Ina girki na Iya, Aamna Tace gaskiya ne ta ebo a spoon ta Kai bakinsa Tace kaima ci mana,ganin ita zata bashi da kanta ya Bude bakin ta zuba masa,Bakinsa ya kulle Kam tare da fadawa saman kujerar ta baya ya kwanta flat Wai zata kashe shi da love,tana ta dariya yace Hannunki zai kasheni sai abincin ya Kara wani dandano,Mikewa yayi tsaye yace Dole nayi celebration Yana zaga palon Wai duk murna ce ta bashi abinci a Baki. Sai da ta Gama ci ya kwashe kwanikan ya maida kitchen ya dawo tare da Zama a gefenta,birgeta yayi sabo da yanda ba ruwansa da jikinta ya nuna ba jikinta yake so ba ita yake so, Gaskiya Zan dawo ka koya min irin girkinka,tagumi yayi tare da zuba Mata Ido Yana ta kallonta Yana murmushi,tafin Hannunta ta saka tare da rufe fuskarta tana Dariya tana cewa Wai Mene na wannan kallon haka? Hannunsa yasa cikin slow dinsa ya cire Hannun data rufe fuskar yaci gaba da kallonta, kafadar sa ta ture gefe cike da shagwaba yace Ni ki kyale Ni na kalli abuna...,Ci gaba yayi da kallonta kamar Yana Gaban tv ya sa yatsa ya taba Hancinta,ya taba girarta,Murmushi tayi tana Wasa da yatsunta,Mikewa taga yayi Zumbur kamar zaiyi duka ya daki Center table da hannunsa yace idanba sai na kwana Ina kallonki ba kafiri nake,ta sheke da dariya,Yana tsaye a gabanta ya Dan zaga kujerar da take zaune yace kutmar an Gama kure karshen kyau,ke Zan Iya mutuwa idan na rasaki,Aamna ta Bude Baki ya Buda hannaye Yana tsaye a gabanta yace da gaske Hmmm,da sauri ya koma ya zauna ya girgiza kitsonsa,Aamna tana kallonsa Yana ta Bata Dariya,tunani ta Lula da manufar data Amince sai taji tausayinsa,Hannunta ya rike tare da Tambaya My World me yake damar min ke? Murmushi ta kakalo Tace ba komai Kawai na tuna Abu ne,Okay Amma Bai Kamata Muna tare kina tuna wani Abu ba ko? Kai ta daga Masa tare da jingina da jikinsa ta kwanta tana lumshe ido,ita dai tana mamakin su Ahmad tsafta iya tsafta duk cikinsu kowa Dan gayu ne,a ranta Tace sai Hali yazo Daya ake Abota. Bacci zakiyi ne ya tambaya? Kai kawai ta daga Masa yace ai yakamata kiyi Balance Beb ya fada da Dan karfi sabo da su maganarsu kusan basa yinta a hankali sai sunga dama ko ansha me sa Slow,Saman doguwar kujerar ya zauna tare da Mike kafafunsa sosai ya Kuma ya Bude su sannan yace to kwanta,ta baya ta kwanta sosai a jikinsa kanta Yana saman kirjinsa,Hannayensa yasa ta cikinta ya rungumeta,tana ta baza Ido taga ko ta saman Kirjinta zai rungumo hannayensa Amma Ina sai taga cikinta ya Rungume,a kunne ya rada Mata yace My world me kike so? Ba komai ta furta gaba Daya jikinta ya mutu wani Iri take ji a jikinta gaba Daya sha'awarsa take ji,ta rasa me yasa ko ya zai taba ta ko ya matso daf da ita sai taji gaba Daya hankalinta Yana Neman guduwa daga jikinta sumamman kamshinsa,shi Kuma yaki ganewa ko romancing dinta yayi,a ranta wata zuciyar Tace to Ina ruwanki da Romance dinsa ke da ba sonsa zakiyi ba canja shi kawai zakiyi. Duk da Haka kasa sukuni tayi sai mutsu mutsu takeyi,tayi mikar ta sake yin Mika Amma ina,Kara tayar Mata hankali yayi yanda yake ta Mata rada a kunne Yana cewa mene ne ko Baki da lafiya ne? Kince zakiyi bacci Kuma sai mutsu mutsu kike yi ko bakya Jin dadin kwanciyar ne? Aamna Tace ae Ni canja kwanciya zanyi,yace to a ya kike so ki kwanta Kuma? Aamna Tace Ni irin kwancinyarka zanyi ta ruf da ciki,Dariya ma ta bashi yace a jikin nawa? Ae ta furta yace to ai ko me kike so,Juyawa Aamna tayi suna facing juna sai ta lalace a kallon kyawunsa kuma,Sajensa ta taba ya matsar da Fuskarsa gefe tare da rufe Ido yace kunyarki nake ji,Badan kece kika taba sajen Nan ba My world ai da wata ce yau idan na dinga dukanta a gidan Nan sai ta Gane Allah Daya ne,kin San ba karamin raini bane mace ta tabawa namiji gemu da Aljihu,Dariya ya bawa Aamna Tace akan gemun? Yace kin San Nawa yake ci kuwa a kullum? Aamna Tace a'a yace to a bar kaza cikin gashinta kawai, tsokanarsa Aamna ta sake Yi taci gaba da tabawa tana shafawa ta ja kadan,Yace Hmmm kiyi ta yi ai yanzu kin rainani wuyanki ya Iska yanka,Su Jibson ne suka banko kofa tare da shigowa gaba Daya. Wani Kara Suka saki, Mashkoor ya koma jikin kofa ya manne a jikin Kofar ya riketa Gam Yana me Zan gani,Jibson ya murza idanuwansa yace tare da dafe kirji ya Nuna ta da Yatsa yace daga Amsar soyayya shike Nan har anzo Nan wajen? Yanzu abin har yayi nisa yazo Nan kwana Uku kacal? Baki Aamna ta bude tace Ina ruwanku Wai ba mijina bane budurwarsa ce Ni da zaku ce Iskanci mukayi? Tawaga yayi mahaukaciyar Dariya yace ke Aunty Balaraba karki zo ki lalata Mana Oganmu baya kula Mata shi,dama kin jawo ya shiga wani Hali a Kan sonki wallahi kika ci amanarsa sai mun soke ki da mashi, ki kula ba'a Wasa da mu,mun San halinku mata, Mashkoor ya galla Mata Harara yace Bamu shirya Haihuwa yanzu ba,mu ba yanzu zamu Tara Yara ba sai mun Gama inganta rayuwarmu yawwa,Aamna dama ta Saba da iya shegensu Tace matsalarku ce ta maida hankalinta Kan Ahmad,Ya kalli su Tawaga yace ku koma Daya palon Kuma idan kuka sake Mata magana anyhow zaku sani,Baku da hankali She is My Woman fa,Yi Hakuri master an daina daga yau Dariya sukayi da murmushi Suka kalli Aamna Suka ce Sannu Aunty Balaraba Allah ya Kara girma ayi Mana afuwa,Ahmad ya koma kallon Aamna suna ganin ya daina kallonsu suka dinga gallawa Aamna Harara suna Jin haushi Dan su Basu yarda da Mata ba mayaudara ne zata yaudari abokinsu,daya palon suka koma. Wurin Magrib Aamna Tace tafiya zanyi dare ya fara,Fuska ya bata Yana Zaune ya saki wani jiki Yana ta shagwaba kamar Yaron yaye ya turo Baki gaba Yana wani motsa Kansa yace Ni ban gaji da kallonki ba idan kika barni Ni kadai Zan Zama......sai ya canja muryar Yara Kuma da Waka yace Lonely....... Lonely.....oh....lonely.....Dariya Aamna keyi kamar sabon kamu,Tace kasan Mama zasu min fada fa...lokacin Mashkoor ya fito zai dakko lemo yaji abinda Aamna Tace karaf yace wannan Yafi Mama power a kanki ko a wajen Allah Shi yake da iko a kanki ba wata Mama ko Baba ba,kin Gama Raina shi Yana aurenki ki dawo gidan Mana idan gaskiya kika kulla a ranki,Ahmad ne ya cire ta kalminsa da sauri ya wulwulawa Mashkoor zai kwada Masa, Mashkoor ya goce takalmin ya Fadi a kasa,Tafiya yayi da Niyyar cin uban Mashkoor Amma Mashkoor ya gudu wancan palon,Tsaki Yaja yace yi Hakuri muje na ajiyeki a gida to. Machine dinsa ya hau Aamna ta Haye itama ya fisgeta Suka tafi,a Kofar gida ya sauke ta sannan ya koma gida. Da masifa ya Shiga wajen su Mashkoor yace wallahi idan Naga Wanda ya sake Yiwa My woman magana sai naci ubanku,iskancin banza, Mashkoor yace kayi hankali baka San Mata ba,idan Aunty Balaraba gaskiya ta kulla a ranta ta dawo gidanka Mana kuyi rayuwar aure,Taya zata tafi Kuma Tace tana sonka Taki dawowa inda kake, wallahi kabi a hankali mata Basu da Imani Tam,Ahmad Tsaki ya ja yace Ni ance maka Zan Mata Dole ne idan tana so da kanta zata dawo ka daina damunta,Tawaga yace shike Nan mun kyale ku yanzu Abinda ya kawo mu Baban Mubaraq Brown ne ya kawo mu. Ahmad yace me ya faru Yana kallon Mubaraq,Mubaraq Brown da Muryarsa ta Yan kwaya yace Guys jiya Ina Shiga gida Wai na kure Hajiyanmu ta kulle kanta a daki tana ta Rusa kuka kaiii...abin fa ya caja min Kai,nace Hajiya me ya faru Tace ai tsohon Nan ne zai Mata kishiya,Tawaga ya daki Cinyar Ahmad yace abin haushin My Guy wata bazawara ce mijinta ya mutu ya barta da Yara biyar,Wai gaba Daya zai dakko ta ya aure ta da Yaran,Ahmad yace Uhm da ace ta daina Haihuwa to da sai muce yayi taimako ya tallafi marayu,ya kamata dama a dinga kula da marayu Ana samun masu Hali suna daukan nauyi kaga da an rage masifu,Jibson yace Kai Bari masu kudi sun daina taimako tunda Ummati ta rasu kwananta ashirin yau babu Wanda ya tallafamin da ko Sabulun wanki sai ku abokaina,Brown yace Dan Allah a duba matsalata,Sukayi Dariya Tawaga yace kaga a hasashe idan Ya auri me Yara biyar ta taho da su gidanku kaima Babanka idan da tsawon Rai a hannunsa zata haifi Kamar biyar ko shida kaga a lissafi Shida ga biyar Sha Daya kenan,Brown ya dura Ashar yace a Tara da mu Yaran Hajiya Guda tara,Ashirin cib cib cewar Jibson,Suka sheke da dariya. Ahmad yace kaga ko zaben Shugaban kasa kuka fito iya gidanku sai ku kayar da Jam'iya Guda ko kusa Jam'iya ta lashe zabe,Dariya Suka dinga yi, Mashkoor yace idan a Iya shida Amaryar ta tsaya kenan ai yanzu Mata sun daina wata Tara kafin su Haihu,Ahmad yace Musamman idan da Abinci kaga idan zaka bawa Mace abinci taci ta koshi ta samu nutsuwa ai wallahi duk buga kwallo sai cikin raga,Jibson yace sai dai kaji a goalll.....idan ka sake ma duk kwallo Daya a biyu ko Uku take Yan Uku Yan biyu za ayi ta zubo maka,Suka kyalkyale da Dariya, Mashkoor yace kutmar dosan Uwa idan aka sake kayiwa matarka family planning na shekara Hudu Dan karta Haihu idan Allah yaga dama sai ka Gama tsarinka sai tazo Karo maka Yara cikin farko ta Haifo maka Yan Uku ko Yan hudu ko Yan biyu ta maka Yan biyu sau uku a jere,kaga shekarun da Bata Haihu ba Ashe Tara maka yaranka akayi Hhhhhhh suka sake sakin Dariya.. Ahmad yace wallahi ta sake ta Haifo Yan hudu har abada ita da Haihuwa ko dai ta tsaya ayi planning na kirki ko tayi gidan ubanta,Tawaga yace gaba Daya tsoron aure nakeyi sabo da wannan,Ina son Mata Amma ko Dan wannan jarabar Haihuwar tasu Daya ta ishe Ni,sabo da kowacce sai ta zube nata,idan kana da kudi ma Mata ma har gasar Haihuwa sukeyi sabo da aci gado in ka mutu, Mashkoor yace Kai Sarki Kaine zaka iya korar Aunty Balaraba Dan Tace zata Haihu? Inda ka susuce me zaka iya ai sai abinda taga Dama,Ahmad yace to sai na dinga amfani da Condom ba shike Nan ba,fashewa wani yakeyi cewar Jibson,Ahmad yace to idan baza tayi planning dinba Ni sai naje ayi min a kashe kwayoyin Halittar yaran Dan Uwatasu kaga inta buga kwallo ba cin ball na dawo Dan Arsenal kawai kwallo ba ci gaba,Suka dinga dariya. Ahmad yace Amma yanzu a kiyayi Mata ba irin Iyayenmu bane na da,Indai mace zata samu shinkafa taci ta koshi,ga dankalin turawa,ga nama,doya...kaga doya ka guji bawa matarka doya naji ance tana sawa a dinga haifar 'Yan biyu 'yan Uku,Hhhhhh Suka sake sakin Dariya Ahmad yaci gaba da cewa ku daina Dariya gaskiya ne,yawan Shan Madara,da jarabar kwadayin mata su dinga girke girke to yanzu Mata sun daina wata Tara dauke da ciki ai wata shida shida suke Haihuwa yanzu,shekara Biyu Yara uku,Brown yace Ni yanzu a dawo wajen Baffa na,Ahmad yace ai Babansa Yana da Rai,Brown yace kwarai Ina da kaka a raye,gaskiya Kai Dan gata ne har wani Kaka ne da Kai Bai mutu ba? Bash ya tambaya,Ahmad yace wajen kakan zamuje lallai a dakatar da auren Nan yaran sun Isa,idan sunki yarda sai mu koma Kan bazawarar Baffa a cikinmu wani zai shigar Kamala mu dinga zuwa zance wajenta. Kaga zata ga yaro sabon jini me zatayi da tsoho shike Nan ta daina son Baffa,Dariya Suka Yi harda ihu, Mashkoor yace King Ni za a Bawa wannan fannin,Ahmad yace no Jibson ne zaiyi kaga Jibson shi a cikinmu dama Yana kula Yan Mata Sarkin yaudara ne, Jibson yace ai wallahi na yaudari Mata sunfi dari Kuma abin haushin duk Wanda na yaudara ban taba samu nayi ko Sex da su ba,a duniya sau Biyu nasan na taba Sex da wata guntuwar yarinya me Kama da kofin shayi Me Hannu,King yace ku kyale ma wani Kakan Brown baza su yarda da mu ba, Kawai mu fara Shirin zuwa wajen Bazawara,Kai Brown ka Nemo Address din gidansu da sunanta. Brown yace naji kanne na suna cewa sunanta Sameera,Tawaga yace kwanon cin abinci kenan Sameera fa tab,Bash yace daga yau sunanta kwano babu wani Sameera kwano kawai,suka tafa. Tunda Aamna ta koma gida ta kasa sukuni Kawai Ahmad take tunani da Kuma sha'awarsa Tace yanzu ko Dan Romance Haka akeyi,yanzu saurayi da Budurwa ma basa zance su tashi lafiya mazan yanzu sai Allah ya shirya,Amma Miji Guda na kwanta a jikinsa na tashi wani garau da shi Anya Ni mace ce kuwa,Wata zuciyar ce Tace to Mene yaje da jikinsa,tana wannan tunanin bacci ya kwashe ta,Washe gari da Sassafe Ahmad ya Kira Aamna tana dagawa ko gaisawa Bai Bari sunyi ba ya marairaice tare da furta Dan Allah nazo na ganki yanzu? Ba Zama zanyi ba Kawai bakin gate Zaki leko Dana ganki Zan wuce to sai kazo ta furta tare da mikewa da sauri ta fada wanka a gurguje ta shirya cikin wata silk Yellow and red doguwar rigar material,Powder ta shafa da lipgloss ta fesa turaruka duk Dan a birge shi,Mayafi red ta yafa sai gashi ya kirata a waya yace fito na zo,da sauri ta fito Mama da Baba sai gani sukayi tayi waje da sauri ko kulasu Bata Yi ba tana ta kamshi,da Murmushi ta fito,ya kalleta sosai ya sake leka fuskarta Yana zuba murmushi yace kwalliya kika Yi min? A'a dama nayi abata cewar Aamna da karya,Yace Ina Zaki je to? Tace dama Hospital nake so ka kaini,Me ya faru da ke ya furta a tsorace Tace wata takarda Zan karbo,Yace to kin shirya Tace ae yace hau mu tafi,kafadarsa ta dafa sannan ta hau suka tafi. Suna zuwa da Mamaki sai Aamna ta ja Ahmad Office din Doctor Tace Likita gamu a rubuta Mana Tests din da zamuyi na medical checkup,Ina so cikin Nan nasa ta nuna cikin Ahmad Tace a Bincike min shi sosai,koda,hanta,Huhu da sauransu duk a tabbatar min da lafiyarsu,Haka jininsa ma ko Ina a Masa test,Dan kar yaji Haushi Tace harda Ni Nima ayi Mana tare,Doctor yace to Nan take ya rubuta musu tests ya turasu Lab,Ahmad baiji komai ba tunda tana so Bai San manufarta ba sai ya bita Suka je aka ja jininsu sannan aka musu scanning ko Ina Kamar yanda Aamna ta bukata,Dake private ne Nan take Likita yace ku jira Kawai result ya fito ku tafi da abinku,Zama sukayi Ahmad yana rike da Hannunta,kudin ma shi ya biya komai,sai wurin Bayan 12pm aka ce suje su karbi Result ya fito,Suna karba Suka shiga Office din Likita Suka zauna,Likita ya fara Bude na Ahmad ya Gama duba kowanne yace Kaga Kai Alhmdllh Allah ya taimakeka lafiyarka kalau,komai naka Normal ne baka da wata matsala gaskiya,Yace gashi Genotype dinka AA ne shima,Ahmad yace na sani ai Ni Ina ganin Likita duk shekara Ana duba Ni,Aamna taji kunyar abinda tayi zarginta shaye shaye ya Gama illata Ahmad,Ahmad cikin kuri ya bigi table din likita yace Doctor duba Mana nata mu gani Kuma mutum idan ba lafiyayye bane yaci ubansa a Nan wajen, Doctor ya dinga dariya shi da Aamna Wato da Aamna yake kenan. Doctor ya bude na Aamna yana dubawa yace Alhmdllh kema lafiya kike Amma kina da matsalar Cold Bladder sanyin mafitsara Wanda Infection ne ya haddasa,Maganin ciwon Sanyi Za'a rubuta Miki Kuma sai kin dage kafin ya warke,sai Genotype dinki AS ce ke Wato carrier,Kinga Allah ya taimakeki mijinki AA ne baza ku haifi me Sickler ba Kun tsallake rijiya da baya, Doctor yace Kai kana mijinta ya akayi sanyin be Kamaka ba? Ahmad yace Amarya ce fa ai Bata tare ba,Gidan ne ba a karasa hadawa ba shi yasa nace tayi zamanta a gidansu sai an Gama,Kuma ka Iya Hakuri? Ahmad yace ae Mana Kuma kullum sai naje zance,yanzu ba gashi hakurina ya taimakeni ba da yanzu ta shafa min asosa,Dariya Aamna tayi Tace zaka ga Asosa wallahi. Likita dai maganunguna ya rubuta Mata masu zafi,Ahmad suka je aka siya, Allura za a Mata ta kwana biyar,yau za ayi Daya Kamar zatayi kuka,Ahmad ne ya riketa Kam aka Mata a Hannu,Aamna harda kukan shagwaba na ganin Miji na kusa, Suna Hanya a machine yace Wai ke Baki da kawayen kirki ne sai wannan banzar Siyaman? Aamna Tace ai Siyama bani da kamarta ita take dorani a hanya me kyau,Take doraki a keken bera dai wannan ce ta kirkin? Fushi Aamna ta fara Wai ya tsani kawarta. Lokacin suna zuwa kusa da wani masallaci anyi Kiran Sallah,Aamna Tace tsaya kayi Sallah a jam'i,tunda tana so sai ya tsaya a masallacin sai ya tsaya, tana waje ya Shiga ciki a Jam'i yayi Sallah yau,Yana Fitowa tana ta murna,Hararta ya Yi yace Sallah 12:30pm Bata Nuna ba,Kin jawo Nayi Sallah tun tana Danya sharaf,Aamna Dariya tayi Suka tafi ya ajiyeta a gida Yana ta Fushi. Zai tafi ta tsaya Tace ba ko Sallama? Kansa ya dauke ya kalli can gefe,zuwa tayi da sauri tana Dariya ta riko Hannunsa,Idonsa ya rumtse sabo da har kwakwalwarsa yaji wani yarrrrr, Kiss ta manna Masa a Bayan hannun Tace I love you,da sauri ya kalleta yace da gaske? Kai ta daga Masa tana murmushi,Sakkowa yayi daga machine tare da rungumeta yace I love you too,a kunne ta rada Masa idan anyi Kiran sallar la'asar kaje masallaci Kuma ka Dan zauna kaji Wa'azin liman Naga masallacin kusa da gidanka Ana wa'azi bayan Sallar la'asar,Ahmad Bai kulata ba ya hau Machine ya tafi gida. Zaune suke a gidan Ahmad,Tawaga,Jibson,Bash da Mashkoor,Kiran Sallah aka kwalla,Ahmad ya mike zumbur yace My world Tace naje sallah yau,Kirji Tawaga ya dafe Yana zuka Wiwi yace what....me zanji? Sallah ka manta mu Bama Sallah sai ta Nuna ligigif? Dariya Mashkoor yayi yace ai kwana Nan za a bashi limancin masallacin Unguwar, ku tashi muje muje ai muma ba arna bane Dan uwarka King cewar Bash. Tafiya suka Yi tare gaba dayansu,Gaf da za a Tada Sallah sukayi Alwala sai kallonsu akeyi sabo da kitson Ahmad da gyaran gashin su Jibson kadai abin kallo ne,Ahmad ne kadai da Yar tsangalalliyar jallabiya fara Amma duk cikinsu daga me 3qtr sai me Creazy jean,sai dai kana gani kasan ba kazamai bane Yan iskan Yan gayu ne Kawai jikinsu suna kashe Masa kudi,Limamin Unguwar yasan su musamman Ahmad Bai taba ganinsu a masallaci ba sai yau Kuma Suka hau sahun gaba shu'umai,. Bayan anyi Sallah an idar masu Zama Jin wa'azi Suka zauna har su Ahmad,Yau sai liman ya fara wa'azi akan Karin aure,ko wanne Namiji yayi kokari ya Kara aure,Ahmad ya kunna recording a wayarsa ya ajiyewa Aamna tunda itace Tace yaji wa'azi Kuma yayi Aiki da shi gashi ya fara da Jin falalar Kara aure mutum ya auri mace sama da Daya. Malam yace idan Namiji Yana talauci zai iya Kara aure Allah zai Iya Buda Masa sanadiyar wannan auren,Tawaga ne ya daga yatsa Sama yace Ina da tambaya Malam,Malam ganin irinsu Nan take yace Ina jinka samari,Tawaga yace cikin darajaka da kankan da Kai tare da mutuntuwa Malam karya kakeyi. Baki Malam ya bude ya kallesu Jibson yace kwarai kuwa katuwar karya ma,cikin Yaran Malam wasu Suka Mike da Niyyar tarewa Malam,Malam ya dakatar dasu tare da kallon Tawaga yace Kai bani hujjarka da kace ba Haka bane,ka daina gyarawa wani ba Haka bane Kawai karyace malam,ba hadisi ko Aya na karyata ba Kawai abinda ke faruwa,Babana kafin ya mutu talaka ne Haka Kawai karambani yasa ya Karo aure ai kuwa talaucinsa ya karu,Gomnati Watarana ta bada tallafin dubu dari ai sai Baba ya sake Karo ta Uku da kudin talauci ya sake dannowa gidanmu karshe wahala ce ta Kori matan biyu aka bar Mamata yanzu Yaran suna Nan rututu shi Kuma ya rasu an bar min nauyi sannan kace wani Ana samun Budi,ga mutane Nan yanzu da yawa ko mace Daya ya aura sai kaga duk ya fara lalacewa wahala ta isheshi yana dana sani. Jibson yace ance Wai Malam ko matashi Niyyar aure yayi Allah zai Buda Masa ya kawo Masa yanda zaiyi yayi auren? to Ni Malam Niyyar aure nayi shi yafi sau dubu sannan yanzu zancen da nake maka Zuciyata a kudurce take da Niyyar aure Amma kwandala bana samu abokaina su suke daukan nauyi na sannan kazo wani kace,Bash yace Kai Malam yanzu ba irin da bane rayuwar yanzu daban take ku San abinda Zaku dinga fada,wancan satin naji wani malamin yace idan matashi baida aikinyi Kar ya sake yayi Aure sabo da rayuwar yanzu,Haka Rannan wani yace Mata Kar su sake su auri mara sana'a,yanzu Kai Kuma kace ayi sama da biyu,Ahmad yace da Allah ku dinga duba littatafai sosai kafin ku fadawa jama'a wani abu,Ya za a dinga zuwa Ana Raina Mana hankali mun rasa inda kuka dosa wannan yace kaza wannan yazo ya karyata. Malam ya kalle su yayi Dariya yace Dana fara Wa'azin ai sai ku Bari na Kai Aya,da sai ku tsaya bayan na Gama fadar falala ai zanzo nayi bayani akan Kuma wannan matsalar da kuka ambata Amma sai kuka rigani,Dariya Tawaga yayi yace karka zo Mana da gyara Malam Kawai mun kureka ka zugo ta yawwa,Kai ku tashi mu tafi Sallah Kuma da Muka bika Allah ya baka ladan Jan Sallah Amma wa'azinka 0/0 baka ci ba,Suka Mike suka fice. Liman sallamar mutane yayi yace gobe zai Dora daga inda ya tsaya ya fita da sauri,Liman hamshakin me kudi ne Dan kasuwa ne na gaske,Su Ahmad ya dakatar a wajen masallaci suna tafiya,Tsayawa sukayi Liman yace cikinku duk ba me aure?Ahmad yace Ni ina da shi Amarya ce Bata tare ba Amma ta kusa,Yace mashaallah ai Kai na sanka a garin Nan har mahaifinka na sani,Ahmad ya tabe Baki,Jibson ya kalla yace Kaine kace kayi Niyyar yin aure baka ga Budi ba ko? Jibson yace kwarai kuwa,Liman yace to kaje ka Nemo yarinya Ni Kuma na tsaya maka har gidan Zama kyauta Zan baka aikinyi me tsoka Kuma Zan maka komai na auren,Jibson yace Malam karfa ka min Alkawarin Yan siyasa baza kaji da kyau ba,Malam yayi Murmushi sabo da yasan Basu San shi waye ba,Karfa ka bashi gida irin na talakawa talak idan irinsa ne ka rike abinka Bamu shirya aure ba sabo mu mun tsara Dole matanmu suji dadin duniya shi yasa Muka hakura da Aure muna talauci jira mukeyi sai munyi kudi cewar Mashkoor,Bash yace yawwa kaji dai Malam,Malam yace cikinku ma idan akwai Wanda yayi Niyya ya fada,Tawaga yace Marayu kannena sun ishe Ni ma Ina Ni Ina aure banyi Niyya ba, Mashkoor yace Ni kuwa Muna da Hali ra'ayi ne banyi ba,Banga wacce ta min ba,Malam yace Ina da Yara kaje ka gani idan da wacce ta maka a ciki, Mashkoor yace rabani da Yar malamai tazo tayi ta zunduma min Hijab a gida,idan nayi magana ta jawo Aya gwara wacce ta rike izu biyu na Sallah Yar jahila jahila Haka,Dariya suka bawa Malam yace duk Sanda ka shirya kazo ka gani dai, Mashkoor yace bafa zanzo zance gurin yarka ba ta malamai Dan Hannu bazan rike Mata bare Yar runguma a fara min wa'azi ai sai anyi aure etc bazan zo ba,Bash yace Ni ka ganni Malam a ministry of Environment nake Aiki Ina samu,Kuma Iyayensa ma duk ma'aikata ne Kawai Ni sai fara doguwa,idan ba fara ba taje,Malam yace idan Allah yasa kuma ka fada son bakar fa? Yace sai tayi bleaching Dole na siyo Mata mayamayai ta koma fara,Dariya Malam yayi yace Kai Dole sai fara? Bash yace ko bamagujiya ko arniya Matukar fara ce an Gama,ko a gidan karuwai take ba ruwana,Ni dama Malam ban damu da wata mace Virgin ba,Nafi son wacce ta San komai yawwa,Ni mace taje da Virginity nata ba ruwana,Kuma Ni ban taba Zina ba Kawai Ni Ba ruwana da wani virginity. Malam ya kallesu Kawai ya zaro check na kudi,ya rubuta dubu dari uku ya bawa Tawaga yace gashi kaje ka kula da marayu idan wani Abu ya taso na iliminsu ko auren wata ko wani Abu ka sanar Dani Zan tallafa,Tawaga ya karba da mamaki ya dafa Ahmad yace Malam sai kace wannan Abokin Nawa king shi yake mana irin wannan kyaututtuka,Malam ya kalli Ahmad da mamaki Ashe Yana da tausayi,Kudi ya zaro ya Basu dubu goma goma kyauta har Ahmad ya mikawa,Jibson ya kyaftawa Ahmad Ido Wai ya karba sai ya Basu su Kara,Ahmad ya karba,Tawaga Dake tura machine dinsa ai sai ya buga machine tare da zanawa Malam kwabo a gabansa,Jibson yace karya ne wani ya kawo ma raini a garin Nan,Maganar dazu daka fada a masallaci Muka karyata ka yanzu mun gano gaskiya ce,Wuhuhu Mashkoor ya daga hannaye sama Yana jinjinawa Malam,Bash yace sai kayi Malam mun baka Shugaban limamai na Nigeria wallahi,Malam dai Kai ya girgiza Kawai tare da komawa masallaci inda motocinsa suke na Alfarma. Ahmad kuwa Jibson ya bawa nasa 10k din yace ungo ka siyawa su Aymana littafan makaranta naji sun maka waya ance a siyo musu Books yace wallahi ga naji sunce gobe ma za a koresu daga school sabo kudin makaranta Abba Mutum biyu ya biyawa saura su takwas kowanne dubu goma Sha biyu,ga Jamila zasu Zana waec, Kuma Dan Iskanci baka fada ba? cewar Mashkoor, suna komawa gida Ahmad ya turawa Jibson dubu dari da Hamsim, Mashkoor ya bada dubu talatin,Shima Bash ya bawa Jibson 20k ,Tawaga yace kudin sun Isa da za abiya ko da Kari sai a ciri wani Abu a Nawa,Jibson yace ai sunyi yawa ma ciki har sai na siya musu taliya da macaroni dama sun Kare,tausayin Abba nakeji duk ya rame. Ahmad yace yayi rashin Ummati ba Dole ba,Jibson yace sai na ganshi a Dan dakinsa yayi malahooo....yayi tagumi bashi da kawar Hira sai dai idan mun shiga ko su Aymana suje su tayashi Hira,Amma lokacin da Ummati tana da Rai sai dai kaji dariyarsu kyalkyalkyal,Ahmad yace muje mu samo Masa Dattijuwa wacce ta daina Haihuwa mu aura Masa ita ya rage zafi. Mashkoor yace mu samo Masa me kyau mu siya Mata kayan gyara ta dinga birge shi irin Ummati suka Kama Dariya tare da cewa Haka za ayi,ga case din Brown gobe za a fara Suka fara shirya plan abinsu,Jibson yaje aka canja Masa salon Aski me kyau na Dan Kamala Amma fa Sumar akwai yawa ta matasan yanzu,Sajensa da gemunsa yasha gyara dama gashi wani chocolate kyakyawan matashi,Kaya kuwa Shadda sababbi aka dinka Kala biyar za a hurewa Bazawarar Baffan Brown kunne,Shi kuwa Bash Searching yake na inda za a samowa Baban Jibson Bazawara me Dan kwari. Tun safe Aamna ta fara amfani da Magungunan Infection dinta,ciwon yaji magani da Allura ya tabo shi sai ta fara Jin kaikayi a gabanta,dama Likita yace idan ta fara Sha zata ji sabo da an tabo ciwon,Sanye take cikin wata Riga karama me Hannun Vest fara da tight baki,Ahmad ya Mata waya zaizo da dare zai Bata labarin Wa'azin da Tace ya zauna ya ji,Bata Yi zaton cikin gidan zai shigo ba,sai Jin sallamarsa tayi a palonsu,Mama ya gaisar ta amsa sama sama Amma ganinsa dauke da ledojin take away sai ta washe Baki harda cewa shiga mutuniyar taka tana ciki, ai kuwa ya wuce bedroom din Aamna,Mama sai kallo sai Harara baza su iya komai ba dama,Aamna sai soshe soshe takeyi duk ta rasa sukuni. Yana shigowa ta janye Hannunta da sauri Amma ya rigada ya gani,Dariya ce ta kwace masa yace ai sai ki fada min nazo na tayaki,Kuka ta saki masa yace yanzu zanzo na tayaki kwantar da hankalinki. Ba kinyi zaton nine ba lafiyayye ba to gashi reshe ya juye da mujiya,Kuma yau Hira zamu Sha babu soshe soshe,Aamna ta goge Hawayenta tana Dariya Tace Allah baka Isa ba ka tafi gaskiya,Amma Kuma gaskiya yasha kyau cikin wani yadi brown me azabar kyau sai kamshi yake zubawa,Tana kwance Bata tashi ba,Saman bed din ya haura tare da kwanciya shima,Tace ka rufe Kofar da key kasan Mama Kar ta shigo,ai ba Wani Abu zanyi ba Dan Kawai na kwanta mene a ciki ya furta tare da gyara kwanciyarsa. AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYATA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DAN ALLAH KARKI FITAR DA NOVEL DIN NAN,BADAN NI BA DAN GIRMAN ALLAH. IDAN BAKI BIYA BA KARKI KARANTA DAN DARAJAR ALLAH. 61-65 Official By AsmaBaffa Page naku ne AUTA ALHAMDULILLAHI AISHA Aamna kunyarsa taji ta juya Masa baya,Juyo da ita yayi suna facing juna,Hannu tasa tare da rufe idonta,Hannun ya janye yace idan fuskar Zaki rufe tashi zanyi nayi tafiyata,tsayawa tayi tana murmushi Dan Bata iya jurewa,Baki da Aiki Sai Dariya ko gajiya bakya yi,wata dariyar tayi tare da Kai Hannunta zata rufe fuskarta Hannun ya rike tare da furta kiyi dariyarki a Haka,Laaa My world har gurun wuya gareki?wanne gurun wuya kamar wata me kiba,dama Yana sani ya fada Dan Kawai ya kalli Kirjinta ne,sai yace ga shi Nan duk yayi zane,Aamna Tace Naga ta kaina ta Mike da Niyyar dakko karamin mudubi a handbag dinta ta duba,Hips dinta ya riko da Hannu biyu yace Wasa nake Miki dawo ki zauna tunda Baki da lafiya,Zama tayi a bakin bed din yace ki kwanta karki taso da kaikayinki,Dariya ya Bata ya takura Mata,yace ki dinga Jin tsoron Allah harda kaini Hospital ko Ina da cuta sai gashi ta kwaje a kanki,Mukus tayi ita duk yasa ta rude Yana kwance a gefenta. Ledojin Daya shigo da shi yace gashi Nan ki duba kici abinda kike so,Dama yunwa take ji Mama taliya ta dafa da Mai da yaji ita Kuma Bata sonta,Ledar farko tana budewa taga sabuwar waya me tsada Samsung Yar gaske,dama tana ta fama da Vivo karama,Farin ciki ne ya lullube ta,Ahmad Kuma yaga yanda take murna yaji Dadi Amma sai ya maze,Daya Ledar ta Bude taga agogo kala Uku masu tsada na Mata kamar yasan tana bukatarsu sabo da a lefenta shi aka manta ba a sa Mata ba,Daya Ledar Kuma wasu dogayen rigunane Yan Turkey kala Uku masu shegen kyau da shape,Ledar karshe itace ta shawarma katuwar gasashiyar kaza,da Icecream manyan Roba har uku,Sai wasu Snacks da lemuka, Yogourt,sai da ta Gama dubawa sannan ta juyo ta kalleshi cike da shauki da mamakin irin son da yake mata,kafeshi tayi da Ido shi kuwa wayarsa yake latsawa,Wayar ta karbe tare da fadawa jikinsa ta Rungume shi tare da kankame shi tana ta zuba godiya ba adadi tana Masa Addua,Tace gobe zanzo gidanka tun safe har Yamma zaka koya min Jullof din Nan,Allah ya kaimu ya furta tare da shafa dogon gashinta me santsi. Lips dinsa taci gaba da karewa kallo kamar tayi kissing dinsa sai Kuma ta tuna wani Abu ta fasa,junansu suke karewa kallo,Idonsa ne ya Dan canja Yana tunanin wani Abu,Fuskewa yayi yace kici Mana Kar yayi sanyi,Tace Kai fa? Bana ci Ni ki Bawa Mama Zalama Naga yau har saukata akayi anga kayana,Dariya Aamna tayi ta dauki duk abinda zata iya ci ta kaiwa Mama sauran,lokacin Baba ya dawo. Mama Tace shine sai da kika Gama kwashewa Zaki kawo mana Yar bakin Hali,Aamna tace idan Kuna so to idan Baku bukata ku bani? Baba ya Bude Baki tare da kwada Mata hularsa a kanta yace Yar Iska Mara kunya Dama badan Allah kika kawo Mana ba bakar kadara karuwar banza wacce ubanta ya gudu ya barta ba galibu,Aamna Ta musu Shuru kawai tayi tafiyarta. Aamna da Hawaye ta shigo bedroom dinta tare da fashewa da kuka,Hankalin Ahmad ya tashi yace lafiya? Aamna Tace Mama ce da Baba ta bashi labarin me Suka ce,ganin Su Baba ne yasan ba abinda zai iya musu Dole ya girmamasu komai haukarsa,Aamna ya shiga lallashi Amma Taki daina kukan,Ganin Taki dainawa ya santa da taurin Kai sai ya Mata wayo ya Mike a zuciye yace bazan dauki wannan ba akan wannan Zan Iya fatali da mutum in tattakashi ya dire kasa zai fita duk ya gigice kwaya ta motsa jikinsa har rawa yakeyi kamar gaske.. Aamna ta rikeshi da sauri tana cewa tsaya Mana su Baba ne fa,Iyayena nane fa,Suna Iyayenki zasu Miki Haka sake Ni na tafi wajensu ya fisge zai fita Aamna ta cikwikwiye shi tana rokonsa yace to kin daina kukan? Da sauri Tace ae na daina,kin tabbatar? Tace ae yace to ci abinci,Zama yayi a bakin bed din kusa da ita kafadarsu tana gugan juna,a kafadarsa ta kwantar da kanta tana shagwaba tace a ramawa Kura aniyarta ka bani a baki Nima,yace an Gama My Queen,ya Shiga Bata tana ci tana ta shagwaba sai da ta kusa cinyewa sannan Tace ta koshi. Toilet dinta ya shiga ya wanke hannunsa ita kuwa brush tayi ya kulle ta a ciki Yace Yi wanka to,Dariya tayi Kawai tayi wanka tare da gasa Hq dinta da ruwan zafi da salt sabo da Doctor ne yace tanayi Kuma sai taji Dadi sosai,ta ciki Tace Miko min lotion Dina Zan shirya,yace da kin fito ma ba abinda Zan Miki Kuma karki manta na Gama ganin komai ki daina batawa kanki lokaci,Hijab ta daura a saman towel din ta fito,kallo daya ya Mata ya dauke Kai a cikin hijab ta shafa komai,harda zabo rigar bacci me kauri ta saka,Zo na gyara Miki gashin,Ba musu ta zo ya gyara Mata kuwa ya Kama Mata,tayi kyau agogon hannunsa ya duba yace almost 10pm zo kiji me liman yace yau ya Danna mata recording,tunda Aamna taji Ana magana Akan Kara aure sabo da kin gaskiya sai Tace Ni Nace ka zauna Jin wa'azi yau ne? Harararta yayi yace maida Ni yaro yarinya ko Abu na Sha ni bana mantuwa,Aamna ta kafe Tace Ni kashe min Dan Allah ai na ranar Juma'a nace kaji,Kuma ma ai Kai Bai kamaceka ba Sam,Mata biyu baza su maka ba,ai baza ka iya da su ba,Kai da ko lafiyar Romancing baka da ita dayar ma Taya zata Kare bare biyu,Uku,hudu,ai Kai Bai halatta ba ma kayi zancen mata biyu Ina Sam,Ahmad ya kalleta Kawai yayi Murmushi yace Zaki San kin fada min Maganar nan,sai kin maimaita wannan kalaman naki,Aamna Bata Gane ba Tace au Kai da gaske yarda kayi zaka Yi auren? to Malam ku ya rufe Yana Nan da matarsa daya,ku zauna ya zuga ku,au Ashe kema a addinin zaba kikeyi Kamar a super market abinda ranki ke so shi Zaki dauka Wanda Baki so baza ki dauka, Haka ake addinin? Aamna a ranta Tace ya yarda wallahi da Wa'azin dama ance sabon musulunta akwai daukan Addini Gam,Aamna Tace kenan Mata biyun zaka Yi? Ahmad yace Ana fada Miki gaskiya kina takewa,Aamna ai sai ta birkice Tace to wallahi kaje kayi ka gani,Wayarsa ya dauka zai tafi haushi yasa ta jawo shi da karfi Tace Kai Malam ban Gane ba,ki dawo gida idan bakya so,au ta Nan ka bullo to bazan dawo ba,dama kayi Niyya zaka fake tanan,Kazo ka dameni da love love Ashe duk a Baki ne,wannan malamin shima Watarana sai an sauke shi daga limancin nasa ya daina samun Salary, Kallonta yayi duk ta tashi hankalinta kadan take jira ta tsage,Murmushi yayi yace ni nace zanyi Aure? Ke fa kika ce naji wa'azi nayi Aiki da shi Kuma Zaki zo kina damuwa,wayarsa ta fisge tare da goge recording din ta Mika Masa wayarsa,Dariya ta bashi yace Yana babban Memory na kwakwalwa tare da rungumeta tsam a jikinsa,kuncin da take ciki ne ya yaye taji wani farin ciki marar misaltuwa dalilin Kawai yayi Hugging nata. Hannaye tasa tare da zagaye shi ta Rungume shi itama,gefen Fuskarsa yasa tare da gugan Tata gefen fuskar,Aamna ji tayi kamar ta fadi wani Abu na fisgarta ta sake makale shi,jikinsa ya raba da nata ganin Yana Neman yin bacci me Dadi,Kallonsa take Yi shima haka,kunyar kanta taji ta sadda Kai kasa,yace na tafi My world Good Night,Bata so hakan ba to Kawai ta iya Furtawa,Har ya juya zai tafi sai ya dawo tare da tsayawa a gabanta kamar zai shige jikinta,Yatsansa ya daura a Dan kasan Habarta tare da dago kanta sama,Yatsansa Yana Haka a Habarta ya shiga kissing dinta cikin wani Arnen salonsa,Aamna wani nishadi ta tsinci kanta ciki,a ranta ta furta Ashe ya Iya,jinsa takeyi har tsakiyar kwanyarta Tace Allah yasa Kar ya daina da wuri,Hannayenta ta mayar saman wuyansa tana shafa Masa wuya zuwa kitson calabarsa,Aamna martani ta shiga maida Masa cikin nutsuwa Kamar zasu cinye lips dinsu su huta sabo da yanda suke kissing din ba a cewa komai,a hankali ya zare bakinsa a nata Muryarsa na rawa yace Zan wuce dare yayi Su Baba. Aamna ita da hankalinta yayi nisa hannayensa ta rirrike tana Wasa da su Tace ka kwana Mana,Dariya ta bashi yace ke ki dawo Mana Ni na kwana a Nan so kike baba ya saka speaker ya sanar layi layi,Kuma ma ai Bai kamata ba,Aamna da shagwaba Tace to Mene a ciki ai Zan dawo ne akwai shirin da nakeyi,yace to Allah ya kaimu ki Gama shirin Amma bazan kwana ba,murmushi tayi Tace to muje na rakaka,Hijab dinta ta saka har kasa Suka fito ta rike Masa Hannu suna zuwa Palo ya zame hannunsa yace Baba ko Mama,Wai Ni ba matarka bace? Yace to kinfi so na musu rashin kunya Dan kina matata,Nifa nazo har gidanku,Bayan dakinki Dana Shiga duk Bai Isa ba so kike Baba ya dinga cewa Ni Dan bariki ne kina gani yanda Suka sa min Ido Ina shaye shaye ko ya nayi Abu zasu ce ai Ni Dan kwaya ne, Kuma dai ai su suka rike ki sune Iyayenki idan da Kara,karki Yi amfani da Suna takura Miki kiga Kamar Basu da hakki a kanki idan kika musu ba dai dai ba sai Allah ya saka musu,shi Dan Adam kowa akwai halinsa na banza Dana kirki Dole ne,so Dan Adam ne zai Iya kuskure,abinda yasa ban matsa sai kin dawo ba sabo da tun farko Ni na matsu sai kin bar gidana laifi nane. Aamna ita dai mamakin Ahmad ya Gama kasheta wannan irin nisan hankali Haka Ana kallonsu a banza Ashe Dan baka zauna da su bane,gaskiya a daina zato da zargin banza tunanin da suke da shi Wanda basa Shan komai Basu Isa sunyi irinsa ba,ba kowa bane hakan, sai da suka fito zai tafi ya sake Rungume ta sannan ya hau Machine dinsa,Hannu ta sake Mika Masa Suka gaisa sannan ya tafi abinsa ya bar Aamna da sha'awarta da tunaninsa duk da cewa shima bangarensa hakan take. Washe da Yamma 5pm gaba Daya su Jibson suna gidan Mashkoor har Ahmad,Jibson ya Sha wanka cikin farar Shadda kamar wani Ango Suma ta Sha gyara harda tsira wata hula Kalar Shaddar da Takalminsa,Sumarsa gata Nan ta baya da gefe da gefe me yawa,dinkin me dogon Hannu links ya zuba Uban kyau,Bash Shima yasha wani yardi Silver ya tsula kyau Dake Dukkansu babu mummunan sai hasken fata wani yafi wani haske Haka suke,Bash shine Dan rakon zance, duk sun Sha manyan Kaya kamar ba su ba Machine Daya suka hau Suka tafi,Tawaga yace Allah ya bada sa'a,Address suka bi tiryan tiryan har zuwa Kofar gidan su Sameera,gidan da gani gida ne na rufin asiri,yaro Suka tura zuwa gidan ya Kira musu Sameera,Sameera Bata San su waye ba,tana zaune Umminta Tace Jeki ki gani mana,Sameera ta saka Hijab dinta har kasa ta fito,Daga nesa Suka Kare Mata kallo Jibson yace wannan ai yarinya ce Bata fi sa'ar Aamna ba wannan ba ita bace sai dai ko Yarta ce ta fari,karasowa tayi inda suke tare da Sallama Suka Amsa Mata,Bash ya kalleta a ransa yace wannan chocolate kyakyawar Budurwa itace Baban Brown zai aura? Kai karya ne. Kallonta yayi yace ke Mamanki Zaki Kira Mana Muka ce ba ke muke Nema ba,Sameera Tace ban Gane ba? Ai Sameera akace tazo ko? Jibson yace ae kwanon cin Abinci ba,wata bazawara wacce mijinta yayi hatsari ya mutu tana da Yara biyar,Sameera ta zaro Ido Tace to ai nice,Kuma Ni ko Yaya bani da ita sannan Ni yaro Daya na taba Haifa Kuma yau sati Uku ma da rasuwar Yaron,Jibson a ransa yace Allah raka Taki gona Daya mutu,yace malama Sameera ke wacce irin Sameera ce me Hannun karfe ce ta yayi ko kuwa me Hannun Roba ce? Matashiya Sameera ta kalle su tayi dariya da farko Bata Yi Niyyar kulasu ba Amma dariyar da Suka Bata yasa Tace Hmmm Kawai. Bash ya gyara tsaiwarsa yace da farko dai Ni Sunana Bashir shi Kuma babban me kaunarki Wanda yayi zurfi a cikin begenki sunansa Jibril abokina nane,Muna Unguwar Rigasa a Nan garin,Kamar yanda kika ganmu mu talakawa ne sai rufin asiri babu karya a tsarinmu,nasan ku Mata Kuna kaunar Mota to Allah Bai hore Mana ita ba,idan Za'a so mu a so mu Dan Allah yawwa shine magana kawai, Jibril ya Dade Yana kaunarki tun kafin kiyi auren fari cikin rashin sa'a mirgayi tsohon mijinki Allah ya Masa Rahma yayi Mana shigar sauri,Jibson yace ai shishigi ma yayi Mana da katsaladan ya aureki Ni nasan Rabo na ce ke shi yasa Allah ya karbi rayuwarsa,Sameera taji wani sanyi Haka Kawai taji sun Shiga ranta musamman Jibson,Tace Ni kaga shekarata 25,bayan na Gama Diploma aka min aure na Haihu Daya cikin hukuncin Allah Mijina yayi hatsari ya rasu,Yau kwana goma da Gama Takaba ta Kuma Yaron ya rasu shima sanadiyar cutar Malaria,Jibson Kamar mutumin kirki yace Kash banji Dadi ba Danmu ya rasu Allah yaji kansu,Kai Bash laifinka ne Kai da kake yawan zuwa Unguwar Nan ya kamata ka sanar Dani,Bash yace Nima banji ba sai yanzu,na San dai rasuwar Mijin nata. Jibson ya kalli Sameera ya furta Sannu kinyi rashi Rasuwa irin ta hatsari ai ba Dadi,Sameera Tace wallahi na Gama abincin Rana kenan naji Ringing din waya,Jibson yace Uhmm Ashe bakar waya ce,Tace Wlh sai sanar min akayi sai da hantar cikina ta kada,yace Allah ya taimakeki Bata hada da koda ba sunyi gware da shike Nan kema,Dariya ta Kama Sameera,Jibson yace ai Nigeria Sam Bata Yi ba,Bamu da hanya me kyau ga mutane suna tukin ganganci suna kashe Al'umma,mutum yasan motarsa ba lafiyayya bace sai ya lodo mutane ciki ya kashe su,Ni kwata kwata wallahi banji Dadin yancin kasar nan da amurka ta Bamu ba,gwara da ta Hana mu yanci munyi zaman mu a Hannunta da tuni munfi Haka ci gaba,Bash yace ai da Muna Hannun America da yanzu Sunana George,Jibson yace Ni kuwa bazan wuce Jack ba,Baba Kuma ko Harry kaja Jack Harry,Sameera ta dinga dariya Tace Ni Kuma fa? Jibson yace ai baza ki wuce Selena ko wata Eliza ba, Sameera Tace sai ma idan kanajin turancin Tafawa balewa ranar da aka karbi yanci Yana wani Wai the.... political.... independent.... Nigeria is Inadequate.... Su Jibson suka Kama Dariya yace lallai kin rike turancin nan,...yanzu dai Ni da gaske aurenki zanyi sonki nakeyi,kaunarki ta Gama ratsa Ni,ya kike gani? Sameera tace Uhmmm to dai zanyi tunani,Ko wani tsohon ya kasa Ni? Sameera Tace akwai dai wani Abokin Babana da Abba yake so na aura,Ni Kuma gaskiya Bai min ba,Yana Nan ance Dansa ma yayi Kamar ku Banda sauran Yara, Kuma Ni gaskiya Bai min ba,Kakar mu ta yanke saka,wannan da gaske yake a shirye yake da aurenki idan kin Amince cewar bash,Sameera Tace yanzu bazan yanke hukunci ba sai dai Nan da kwana biyu,Jibson yace ba damuwa yanzu Bamu number dinki,Nan take Sameera ta bashi number suka Yi exchange,Sameera Tace Kuma tsohon ma yaransa da matarsa sun tsaneni har karya aka fada musu Wai Haihuwata biyar Zan tafi musu da Yara gida,Jibson yace to ke kinfi karfin Babansu ma rabu dasu,Kamarki me zakiyi da tsoho,Nan suka tsaya suna ta zance Sameera Basu Dade ba ta Saba da su sannan Suka tafi. Bayan wasu kwanaki Ahmad ya fara rage shaye shaye Sam yanzu sai ya kwana biyar Bai Sha komai ba sabo da ya birge Aamna sannan Yana yawan samun Sallah a jam'i,gashi yanda yake dawainiya da Aamna kome take so zaiyi. Yau Tace zata kawo Masa Ziyara,sai murna yakeyi yasa Musa ya sake gyara ko Ina na gidan harda daukan wanka yasa wasu Riga da wando marasa nauyi rigar armless me hula,ya sauke hular a bayansa,Yana kwance a palo sai Sallamarta yaji tare da shigowa gaba daya,ta zuba kyau cikin rigunan da ya Siya Mata ta Sako Maroon Gown ta tsula kyau, Mikewa yayi tare da rungumeta tana murmushi tace muje kitchen please ka koya min Jullof din Nan,Fuska ya yatsina tare da Furta sai Sanda kika dawo gidan nan,Zama tayi a gefensa tare da kwantar da kanta a kafadarsa,Hannu yasa tare da kwantar da ita a saman cinyarsa,Kansa ya sunkuyo zuwa kumatunta Kiss ya manna Mata a kumatu a hankali ya Kira sunan My world? Na'am ta furta yace Ina so naje Lagos gida zanga Daddy da Mummy,Murna Aamna tayi sabo da ita Bata San ya rage shaye shaye ba,Sallar ma Bata san Yana zuwa Masallaci ba,Kuma gashi Wai zaije gida wajen Mummy,tunda suka dawo kasar nan Bai taba zuwa wajensu ba ,sunyi sunyi har sun gaji Wai abin mamaki yau shine zai je da Kansa,Aamna Tace wow gaishe su zakayi? Yace ae sannan Zan musu magana a kanki,Aamna Tace ya kamata ka karbi aikin da Daddy yace kaga sai ka dogara da kanka,Murmushi yayi Yana Wasa da wani botin din rigarta yace a'a Ni anan Zan bude wani Abu? To wacce sana'ar zaka Yi? Yace Resturant Zan bude,Dariya ta dinga Yi shima Haka,yace bazan Iya barin garin Nan ba sabo da abokaina,yanzu ki shirya muje Lagos tare muyi 3days,Kafada Aamna ta noke tare da furta ka fara zuwa Kai kadai Ni Nan gaba Zan bika muje,Aamna a ranta tasan ba Zama zatayi wajensa ba baza taje ba,Shi Kuma Bai kawo komai ba yace to ba damuwa zanje sai na dawo,gobe Zan bi flight,Tace Allah ya kaimu Hannunta ya rike tare da janta kitchen,Suna Shiga ya dauke ta tare da daura ta a sama kusa da Sink,hannayensa bisa cinyoyinta yace Zan fara girkin kina kallo kinji,Kallonsa takeyi ba ji ba gani Wani Farin ciki takeji,Jikinta ne taji Yana wani yam..yam,Yana magana Amma shi take kallo,a hankali ta matso da fuskarta saitin tasa da Niyyar Masa kiss har ya wani lumshe Ido da sauri ta dawo hayyacinta sai ta fara wayancewa tana dariya,Sharewa yayi shima ya fara girkin,ita Kuma tana ta faman kallonsa,Sai da Yamma ta ebi abincin a flask ta tafi da shi gida Wai yayi Dadi. Shi kuwa Karamar jaka ya dauka tare da shirya kayansa, Mashkoor ne ya kaishi Airport,sanye yake cikin wata Gezna Sea blue,Fadin kyan da yayi Bata Baki ne,kitsonsa dai Yana nan,Da Yamma 5pm Mummy tana zaune a katafaren palonta tare da Humaira sai gashi ya buga Sallama,Mummy da tsananin mamaki Tace Ahmad nake gani ko wa? Dariya ya saki ya tsaya a Gaban Mummy ya wani juya ya juyo tare da yin safa da Marwa a Gaban Mummy yace ya kika ce Mummy,Mummy Tace Wai Kaine da gaske? Shekara Nawa Muna fama da Kai kazo ma gida kaki sai yau Katsam,Yace dama surprise na muku shi yasa naki fada muku,Mummy Tace uhm Kaine kake magana Haka a nutse Kuma cikin shigar hausawa wow,Humaira sabo da murna harda tsalle ta Rungume shi tana Sannu da zuwa Yaya,Yace sis kin Kara girma fa,Mummy ya Rungume tare da aniye jakarsa a gefe,Mummy Tace Humaira sauri ki Kira Daddy kice yazo ga Ahmad yazo yaga abin mamaki,Zama Ahmad yayi kusa da Mummy. Daddy ne ya fito tare da tambaya me Zan gani Ahmad Yau Kaine a Lagos? Abin mamaki kaine,Dariya Ahmad yayi tare da mikewa ya wani sarawa Daddy Kamar Yana Gaban babban soja yace Daddy nine Mana,Sabo da farin ciki Daddy Rungume shi yayi yace Dole yau muyi Celebration yau King Guda a Nan gidan,Daddy gwada yanda suke magana ta Niggogi yayi yace Fresh Boy,the King of Guys Ahmad yace yes ooooo na me,Daddy Yace aje a shirya girki yau Ranar murna ce,a Kira Saddeeq da Mufeeda su zo,Haka aka shirya girki iri iri suka zauna a Dining Saddeeq,Mufeeda,Ahmad, Mummy,Daddy da Humaira Ana ci Ana Hira Ahmad ya fara Basu labarin Aamna,Mummy Tace dama Aamna ce? Gaskiya nayi murna. Ahmad Yana cin abinci yace Ina Baku labari da kuke gani na Haka harfa masallaci nake zuwa Sallah, Saddeeq cikin murna yace Inyeee, Mashaallah cewar Daddy,Ahmad yace Kuma shaye shayen da nake Yi duk na rage saura kadan shima Zan daina Nan gaba,Mummy Tace Alhmdllh,Ya daki kafadar Sadeeq yace ae naji Dole na fada gaskiya Daddy Yarinyar Nan Ina sonta duk ta canja Ni abinda nakeyi duk na rage Ina ta Zama mutumin kirki kullum,Humaira harda tafin Jin dadi,Daddy yace duk itace tayi aikin Nan Wanda munyi shekara da shekaru mun kasa,Ahmad yace sosai itace Kai Daddy Haka idan time din Sallah yayi zata kirani a waya,Muryarsa ya makale Wai irin muryar Aamna zai gwada musu Tace Kaje kayi Sallah a Jam'i Babyna,Ni Kuma idan banje ba sai naga Kamar ma ba sonta nakeyi ba sai na tafi,ai Sanda Sonta ya kamani Daddy na Sha fama,lokacin Baku ga danku ba,susucewa fa nayi,Dariya suka saki,Mummy tace gaskiya tayi Aiki,yace Bari na Kira muku ita kuyi Mata godiya,Nan take ya Kira Aamna ta daga yace kunji zakin muryarta ya saka Wayar a Handsfree kowa na ji Aamna Tace Babyna kaje lafiya,Mummy ya kalla yace a hankali kunji kunji ko yanda take ji dani, Saddeeq ya kalla yace ji Murya dan Allah,Dariya Saddeeq yayi yace to anji,Mummy ce ta karbi Wayar Suka gaisa da Aamna ta dinga zuba Mata godiya da Addua,Daddy ma yace bani ita nima,Haka su Humaira da Mufida tare da Saddeeq duk sun Mata godiya. Ahmad Wayar ya kashe yace Kuma k Ullum dare muke rabawa Muna waya,Babu kalmar Dake tsaya min a Rai irin idan zamuyi bacci Tace Sweet Dreams Baby har dodon kunne na sai yayi rawa Karrrrr....Dariya suke ta Sha Yana ta Basu labarin komai dama ba kunya yake ji ba,karshe yace gaskiya Maganar Serious Yarinyar Nan kuyi Mata gagarumar kyauta sannan kuje har gida ku gode Mata. Daddy Yana dariya yace zamu je ne sai Nan gaba,yanzu tunda ka gyara halinka kuje da Saddeeq wurin siyan mota ka zabi motoci ko Nawa kake so sababbi Zan siya maka,wancen Dana kwace sun tsufa latest zaka zaba,yace thanks Daddy. Tunda Ahmad yaje suke Shan labarin Aamna kullum,har kwanakin Daya kwasa Suka cika,Mota Daya tal ya zaba wata muguwar jibgegiya me tsada baka,kowa yaga motar yasan ka hau mota,kafin ya dawo an kawo motar Kd an hadata an Mata duk abinda yake bukata,Su Jibson sai murna suke Yi. Ranar da ya dawo Kd Bai je wajen Aamna ba sai washe gari ya dau uban wanka cikin wani black trouser pencil da rigarsa me dogon Hannu,Irin kyan Daya zuba ba a magana,Sabo da Iya shege su Baba suna tsakar gida sai gani sukayi Ahmad ya shigo ya Bude gate da Kansa ya koma ya shigo da wata azababbiyar mota,Dukkansu tsaye suka Mike har Aamna Dake Shanya wanki,Mama tana gefe,Idonsa ya rufe ya manta Yana Fitowa daga motar ya Rungume Aamna,itama Haka ta kankame shi suka ki sakin juna,sai da Baba yayi Gyaran Murya,Sannan Ahmad da borin kunya yace na manta ban kula ba Sannan ya rusuna ya gaisar da su,Mamaki ya Kama su Mama bayan gaisuwa harda rusunawa mutumin da ko kallo Basu ishe ba,Baki Mama ta tabe,Aamna ta kalli motar Tace wannan fa? Yace au mota? Yace dama Ina da su da yawa ma Baba ne ya kwace Dana ki shiryuwa,Murmushi Aamna tayi Tace tayi kyau,ko kina sonta ya tambaya,Tace a'a ai kayanka Kamar Nawa,idan kina so ki fada min sai na bar Miki ita,Aamna Tace na gode Baba ya galla Mata Harara Yaja kwafa ta musu asarar mota,je ki shirya muje yawo,Aamna da sauri Tace to tana murna taje ta cakare ta fito cikin Atamfa taji dinki cif ita,Da Kansa ya Bude Mata mota ta Shiga sannan ya rufe suka tafi,Wuraren hutawa sukaje suka dinga holewa Suma idan ka gansu abin sha'awa. Tunda ya dawo kusan kullum sai ya Kai Aamna Wuraren hutawa,Haka Siyayyar kayan birgewa ko yaushe Yana dawainiya da ita. Bangaren su Jibson kuwa bayan sun bar wajen Sameera sai bayan sati Daya Sameera ta Basu damar komawa,Wannan time din harda kaisu wani palon Baki,Bash ya kalli Jibson suka Yi Signa, Sameera ta dau wanka Kai sai ka rantse Bata taba aure ba,Lemo ta kawo musu da ruwa ta zauna,Jibson yace me Hannun karfe da Alama na jefa na cafke,Dariya Sameera tayi tace ae,Jibson yace to ya Maganar Dattijon naki? Sameera Tace na daga Masa red card,Jibson yace kin birge ni ai tsoho sai tsohuwa,Bash yace sai na dinga hango ku a High table Ana wedding Dinner,Cikin rashin sa'a sai ga Baban Brown yazo zance shima ya Sha shaddarsa tare da wani Dattijo abokinsa,Baban Sameera dake abokansa ne Direct palon ya shigar da su sabo da Bai San da Baki ba,ai suna shiga Suka yi Ido hudu da su Jibson suna ta Hira da Nishadi,Baban Sameera yace ai ban San da Baki ba Nan ya janye su Baban Brown suka koma dakinsa,Jibson ya kalli Bash suka kyafta ido,sai Suka Mike suka Mata Sallama suka tafi da sauri,Shima Baban Brown cike da bacin Rai ya tafi gida tare da Kiran Mubaraq yace lallai su zo tare da su Jibson,Babu Bata lokaci Brown,Jibson da Bash Suka Amsa kiransa,suna zuwa ya dinga bala'i yace Dan wulakanci Baku San bazawara ta bace? Jibson yace yo Baba Allura cikin ruwa me Rabo ka dauka,tunda Nema kakeyi muma shi Muka je. Mene zaka damu? Brown yace Baba Kamar takara ne Kuma cikinku duk Wanda ya same ta murna zanyi sabo da idan Kaine zanji Dadi tunda Baba nane,idan su ne Kuma abokai nane, ai takarace ku gwabza Kawai Wanda ya lashe zabe muje muyi Masa Allah Sanya Alkhairi,Dattijon yace okay Wato na gano ku shi yasa Yarinyar ta juya min baya,idan naje Bata saurarata Ashe kune kuke hure Mata kunne,Bash yace au Baba ta fara juya Maka baya? Baba bai San murna zasuyi ba yace ae Mana,ta daina kulani ko naje sai Harara,Ihu Bash yayi yau akwai Party za Sha Zanku dance,mun lashe zabe,Baba yace zanyi maganinku nasan me zanyi ku tafi ku bani waje mutanen banza lalatattu masu takara da ubansu,Kai kuma Mubaraq Wato abokai sunfi uba ko zaka zo ka sameni,tafiya Suka Yi suna ta dariya an Juyawa Abba baya. Ahmad kuwa yau Saturday Shiryawa yayi ya jibgowa Aamna siyayyar kayan makulashe zai je,Lokacin 5pm Zuhra ta zo da Siyama ga Mama a zaune suna Hira,Ahmad yazo Kofar palon hannunsa dauke da ledar take away,zai shiga kenan sai ya tsaya cak Jin an Kira sunansa Siyama Tace Aamna baza ki hakura da Auren mutumin Nan ba,tunda kin Gama chanjashi ki kyale shi Haka,Aamna Tace ai Bai Gama shiryuwa ba,jira nake sai na Gama canja shi gaba Daya sai na zare jiki na,Siyama Tace yanzu shine ya kamata ki zare jikinki,Zuhra Tace Aamna Baki da hankali wallahi dabba ce ke wallahi Baki San me kike Yi ba Kuma duk da kin girmeni, Ae naji Ni dama Dan na canja shi ya shiryu na Amince da soyayyarsa Kuma ai na taimaki Iyayensa,Ahmad ya Gama ji tsaf,Nan take zuciyarsa ta hau Bugawa da karfi,hankalinsa ya tashi,Idonsa ne yayi ja sosai,jijiyoyinsa Suka firfito,kasa hakura yayi gwara ta San yaji,Palon ya banko kofa da karfin ya shigo ciki, duk suka juya a tsorace suna Kallonsa. Wani haki yakeyi da huci Kamar zai mutu duk sai da suka tsorata,Aamna wacce tuni ta fara kuka sabo da ta tabbatar yaji me suke tattaunawa,Bata taba nadama irin wannan ba a rayuwa,Kallonta yayi Idonsa ya ciko da kwalla Yana Ina Ina duk ya rude yace ki fada min abinda naji kina fada yanzu karya ne,cikin karaji yace kice mafarki nakeyi,kice karya ne abinda naji....Aamna tana Rusa Kuka Tace tsaya tsaya Zan maka bayani,cikin tsantsan tashin hankali yace bayanin banza,me Zaki fada min,me Zaki fada min,Kansa ya nuna yace Ni...Ni.....Wai Ni kika yiwa Haka....kin San karya ne kika ce kina so na?...sai da kika dagani sama sannan kika sake Ni na Fado....me na Miki Haka?....Wai duk abinda nake Yi a kanki ?...kujera ya daka da karfi yace Bari kiji Ina mugun kaunar Mummy na fiye da komai a duniya Amma duk abinda Tace nayi bana Yi,Amma ke duk abinda kika ce sai nayi,sanadinki yanzu Sallah Bata wuce Ni,Shaye shaye sabo da na faranta Miki na daina.....Amma....Amma....rasa me zaice yayi Idonsa ya zubo da Hawaye yace tunda na San kaina ban taba zubar da Hawaye ba sai yau kika sani Yana magana cikin karaji duk ya girgiza su ya haukace musu gaba Daya,Mikewa Aamna tayi tana kuka Tace wall.... Cikin tsawa yace bana bukatar bayaninki Ledar Dake hannunsa ya watsa saman kujera,Laptop sabuwa me tsada ta fado daga cikin Ledar Ashe ita ya siyo Mata da kayan tande tande,Bude kofa yayi ya fice a fusace, Aamna tana kuka ta bishi da gudu tana kiransa,Siyama ta riketa Tace ki kyaleshi ke gaba ta kaiki sai ki zare kanki cikin sauki,Aamna ta fisge Hannunta Tace Ni wallahi Ina sonsa da gaske wayyo Allah na Ni na shiga Uku ta zauna ta shiga Rusa uban kuka ba ji ba gani,Zuhra Tace kinwa kanki sai ki samu Wanda ya fishi mu gani,Aikin banza tayi tafiyarta gida itama,Siyama kuwa sai murna a ranta Haka ta tafi gida abinta cike da nishadi. Mama ita kanta yau tausayin Ahmad ya kamata matuka Ashe yayi nisa a shiryuwa Aamna Bata sani ba ma,wajen Aamna Mama taje tana lallashinta,Aamna tana kuka Tace wallahi Mama Ina sonsa wallahi Allah Siyama ce kullum take zugani zuciyata ta kasa tsaiwa waje Daya,na shiga Uku na lalace Mama,Mama Tace kiyi Hakuri Inshaallah zai dawo ne. Bangaren Ahmad kuwa dama Mashkoor ne ya ajiyeshi a motar ya tafi yawo zaizo ya dauke shi,Kawai a kafa ya dinga tafiya ba tare ma da yasan Ina ya nufe ba,sai da yayi tafiya me nisa sannan ya shiga Napep direct Gidan Mashkoor aka ajiye shi,shiga yayi Yana Jan kafarsa da kyar jikinsa a sake,duk sai da suka tsorata ganinsa haka,Kansa a kasa ya nemi waje ya zauna ba tare da ya kalli kowa ba yayi Shuru,Kallon kallo su Jibson suka shiga Yi,kwalabar giya Tawaga ya Mika masa,ba musu ya karba ya kwankwada Yana goge Dan hawayen idonsa,Suna ta Kallonsa Yana Hawaye,Tawaga yace Wai me ya faru ko Mummy ce ta rasu? Shuru ya musu, Mashkoor yace bamu taba ganinka cikin wannan yanayi ba me ya faru ne King? Bama son kukanka King cewar Bash,King a hankali yace Kun san dai yanda nake son Yarinyar Nan ko? Suka ce ae,Yace Kuma kunga yanda ta nuna min kauna,Suka ce ae Mun sani,yace to Kuma dai Kun ganni kalata ba kowa ke samun Irina ba ko? Suka ce ae,yace Kuma nine King,Suka yes Mana,yace kunga irin yanda nake fama da ita ta dawo gidana Taki Amma na hakura na barta sabo da Ina jira ta Gama abinda zata Yi sai ta dawo,to Wai duk Ashe Tace ba Sona takeyi ba Kawai ta karbi soyayyata Dan ta canja Ni na shiryu na daina shaye shaye,Ihu Suka saki,Bash yace that girl?,Yace yeah,yanzu Ni kudi ne da zata canja Ni? Suka ce a'a,yace to Tace canja Ni Kawai zata Yi na dawo mutumin kirki,Tawaga yace Yarinyar da Bata da ko nonon kirki ga Yan Mata Nan suna rubibinka Amma Aunty Balaraba zata maka Haka? Jibson yace Ni dama Sam ban yarda da ita ba,Kawai ka bamu Dama mu tozartata a garin Nan, Mashkoor yace sai Dana fada maka kayi hankali da Mata yanzu ka bamu Dama muci ubanta,Ahmad yace Kuna ji na? Suka ce ae,yace ku bar min case din Ni zanyi Handling dinsa sabo da matatace baza ku Shiga zancen ba ku barni da ita,Shuru sukayi suna jimami kawai suna Kora shaye shayensu. Aamna kuwa kwana tayi tana Rusa Kuka ko gajiya Bata yi,Baba ma da yaji labarin yafi Jin tausayin Ahmad akan Aamna,lallashin duniya Aamna Taki hakura Sai Kiran Wayar Ahmad takeyi yaki dagawa,a daren ta kirashi yafi Sau dari,Daya gaji ma kashe wayar yayi gaba Daya. Sharhi sharhi fans. AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DAN GIRMAN ALLAH KARKI FITAR DA NOVEL DIN NAN. DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 66-70 Official By AsmaBaffa Page naku ne MAMU GALADIMA BESTYNBEELAT AISHA MAMAN SAMHA HAFSEE Ranar Bai iya ko gyangyadi ba bare wani bacci Yana ta tunani,saman bed dinsa Kawai ya dawo ya kwanta shi kadai yasan irin radadin da yake ji a ransa,Aamna ma tana rike da waya Haka bata Yi bacci ba Haka gari ya waye,washe gari da safe ba yanda Mama batayi da ita ba akan taci abinci Amma Taki ci ko wanka Bata Yi ba sai kuka Kawai,Hijab ta zura ta tafi gidan Zuhra,tana Shiga gidan Zuhra tana mopping Aamna ta fada jikinta tare da fashewa da sabon kuka,Zuhra taji tausayinta Tace Aamna kiyi Hakuri Kar wani ciwon ya shigeki,Aamna tana kuka Tace Ni ya dawo, Taya Zan huce ya yafe min ya dawo?, Zuhra ta kalleta yanda dare daya ta firgice,Zama sukayi a saman kujera Zuhra ta Shiga lallashin Aamna da kyar ta samu ta daina kukan Amma duk da Haka idan ta Lula tunani sai sabon kuka. Bangaren Ahmad kuwa Shaye shayen ma idan yayi baya Jin dadinsa ko kadan Haka ya hakura sannan Sallah Bai fasa zuwa masallacin ba,abokansa kuwa gaba Daya Suma sun tsaya cik sabo da halin da abokinsu ke ciki,suna ta tayashi bacin rai,barinsa suka Yi shi kadai sabo da kadaicin yake bukata,kwance yake shi kadai Yana tunanin mafita sai ga Jibson ya shigo tare da Siyama wacce taci shegen gayu,a saman kujera Suka Iske Ahmad Yana kwance Yana tunani duk ya fita a hayyacinsa,Jibson ya kalli abokinsa da tausayawa yace King gata fa Kawai ka so wannan tunda Aunty Balaraba ta ki ka,Ahmad fuskar Nan ba Rahma ya kalli Siyama yace Jibson Haka za ayi,Jibson ya fita abinsa ya rage daga Siyama sai Ahmad,tana ta faman karairaya tana fari da Ido,ta durkusa a gabansa Tace Ina sonka Ahmad,na Dade Ina kaunarka Matukar zaka so ni ba abinda bazan maka ba,har kaina Zan Iya mallaka maka,Ahmad kwata kwata hankalinsa baya jikinsa Haka Yace ba damuwa Ina sonki kinyi tashi ki tafi, gobe Jibi 10am kizo,Siyama farin ciki ya kamata harda godiya,Tsaki Yaja yace Jeki sai jibi,tashi tayi tana murna ta tafi. Kamar Yanda yace Jibi sai ga Siyama 10am ta wani dau wanka duk ta matse jikinta ta zo,Ahmad ya fito sanye da Jallabiyya Suka fita a motarsa har bakin shagon Aamna lokacin Mama sun gaji da kukan Aamna gwara ma tazo shagon ko ta rage tunani,Aamna tana bakin shagon tare da Zuhra suna magana kawai taga motar Ahmad tayi parking a Bakin wajen,Fitowa yayi sai taga Siyama ta fito tare da rike Hannun Ahmad,har Gaban Aamna suka karaso ransa a bace ya kalli Aamna Yace kalli ya kika gani Yarinyar da tasa kika wulakantani kalle ta yanzu har gida take bina tana rokata akan na so ta,har gida take zuwa lokacin kina gidana take Neman na so ta,akanta kika min Haka to gashi roko na takeyi na sota,Siyama murna ta koma ciki Bata Yi zaton tona mata asiri zaiyi ba,Tace Honey ya Haka zaka Tona min asiri,Zuhra da Aamna Suka saki Baki galalala,Tsawa Ahmad ya dakawa Siyama yace ke dalla rufe Mana Baki,Baki da hankali amfani nayi da ke sabo da tana gadara kekawarta ce ta gari,kece me Bata shawara,kallon Aamna yayi yace Dan kince Baki so na cikin minti Daya zanyi mata kala kala Wanda zasu so ni,idan nayi Niyyar saurarar Mata cikin mintuna Kamar Riga Haka Zan na canja su,ke tunaninki har mace ce,Siyama ranta ya baci ta juya cike da borin kunya ta bar wajen sum sum. Wata dalleliyar motar ce ta tsaya a jikin ta Ahmad,budurwa ce fara Yar gayu ta ko Ina tayi karshe ta karaso tare da tsayawa a Gaban Ahmad Tace Sweetheart kazo mu tafi motarka Zan Shiga kasa Musa ya maida min tawa ita a gidanka,Ahmad ya kalli Aamna yace kin gani idan kin kini cikin lokaci kankani Zan samu Wanda suka fiki komai,ya nuna Budurwar yace wannan idan Ilimi kike takama PhD ne da ita sannan me kudi ce ke gidanku ko Tyre ta mota Kuna da ita? Me kukeyi in Banda Siyar da citta,Ahmad Kamar Bai San Aamna ba Haka ya tsaya ya ci Mata mutunci tas sannan ya samu zuciyarsa tayi sanyi,Budurwar Yar gayu ita ce ta rike Hannun Ahmad suka tafi,Aamna tana tsaye sunyi mutuwar tsaye da Zuhra sai Hawaye da ya wankewa Aamna fuska,Kuka ta barke da shi me karfi lokacin da taga Ahmad sunja mota sun tafi,Zuhra Tace ya Miki kyau Aamna Kinga abinda nake fada Miki,Baki ji me yace Miki ba in a minute zai iya canja Wanda suka fiki kala kala,Mata rubibin irinsa sukeyi Kuma gaskiya ne,yanzu kalli dalleliyar Budurwar data ke like Masa,kalli kawar taki Siyama da kike takama da ita,itace ta Kai kanta tana rokonsa ya so ta,amma a gabanki me Tace? Aamna cikin kuka Tace Bazan yafewa Siyama ba,Kina gani Zuhra ya tafi gidansa da wannan kyakyawar Budurwar gidansa shike Nan kwana zasuyi tare,Zuhra Tace mene damuwarki tunda kince ba sonsa kike ba canja shi zakiyi,Aamna ta sake fashewa da sabon kuka Tace wallahi.....Zuhra....Ina sonsa......Ina....sonsa...I love him....I love him....Siyama ce take nuna min Illar auren me shaye shaye shi yasa zuciyata ta kasa tsayawa,to ai gashi ita yanzu ta nuna Miki iyakarki,tunda Dan shaye shaye ne shashasha Mene Zaki damu? Aamna da Matukar bala'i Tace Ahmad Dina ba shashasha bane ta ja tsaki tayi cikin Shagon tana ta uban kuka,Zuhra tana ta dariya ta bita ciki Tace to kiyi Hakuri Yana sonki har yanzu Bai daina ba ai kinfi ma wacce yazo da ita kyau,kin fita komai,Aamna Ido yayi jajir Tace gashi Nan ya tafi da ita gidansa,Ni wallahi komawa zanyi gidan Mijina duk Ni na cuci kaina,Zuhra tana ta dariya Tace wallahi karki koma yanzu yanda yake Fushi da ke kika je zai iya Miki Illa gwara ki Bari ya huce,Aamna Tace da abinda yake min ba gwara kullum ya dinga min Bulala Hamsim ba,Zuhra tana Dariya Tace au yanzu dukansa ma sonsa kikeyi?Aamna Tace ae dadinsa zanji Indai ya hakura to yayi ta duka na kullum har durkusawa zanyi na gode Masa. Suna zaune wata tazo siyan Citta Aamna tana ta tunanin Ahmad sai ta zuba Mata barkono,sai da ta karba Tace citta fa nace,Aamna Tace au na manta sai ta juye ta zuba mata kanunfari,Matar Tace Citta fa tunanin me kikeyi Haka ne,Sai Zuhra ce tazo ta karba ta zuba Mata,wani yazo ya siyo Wani Boxers sai Aamna ta karbi kudin dari biyar ne Kuma dari biyar din ya Bata Amma sai ta irgo dari takwas ta bashi tace ga canjinka lokacin Zuhra ta tafi shi kuwa mutumin ya sani Amma ya karbe abinsa yayi gaba. Kusan kwana Uku Aamna duk ribar Mama ta tafi Aamna tana ta yin aringizon kudi. Yau ma da safe zata hada tea a kitchen sai ta dakko gishiri ta saka a madadin sugar sai da ta kurba ta feso da shayin waje sai taga gashiri ne,gaba Daya Bata cikin hayyacinta. Ahmad Kam abokansa suna zuwa suna ebe Masa kewa,Jibson ne ya shigo ya same su tun kafin ya zauna yace ku fara Yi min jaje, Mashkoor yace na me? yace ku tausaya min suka ce Mene? Jibson yace Jiya kafin na kwanta bacci 9:30pm, Allah yaji Kan Sameera me Hannun kwano badan ta mutu ba sai Kawai na dinga ganin fatalwarta a kaina,tsorata nayi na Kira Wayarta a daren tunanina ta rasu ne an binneta tayi min fatalwa. Sai kuwa ta daga tace ita kalau take Nan na gano mayya ce zata kamani nayi Mata fata fata nace Kar ta sake na sake ganinta a Ido na,Dariya suka dinga Yi,Jibson yace Kasurgumar mayya ce ban sani ba,na Kai kaina babu dama na Dan kebe Ni kadai sai ta dinga min fatalwa, Jibson yace yanzu ma Haka Ina ganinta a idona,Bash yace ko dai so ne? Jibson yace Bazawarar Allah kiyaye,Idonsa ya Shiga murzawa yace gata tazo... tazo bazan lamunci wannan ba idan na gaji Kara Zan shigar kotu Mayya ta kamani,Tawaga yace Wai da gaske kake?yace ae Mana, Mashkoor yace kirata a waya muji,Jibson ya dakko waya tare da Kiran Sameera,bugu Daya ta daga. Yace ke Kwano Mene Haka bana son wasan da kike min,gaskiya na daina ganinki Maganar gaskiya Ina daga Miki kafa Zan kaiki Kara akan me Zan dinga ganinki,ko bacci nayi sai kizo min Mene Haka Dan Allah Ni bana so Gaskiya,Dariya Sameera tayi ya dameta da zargi Wai ita mayya ce Bayan ita Bata San komai ba,tsokanarsa tayi Tace Yau Danwake kaci ko? Tsoro ya Kama Jibson sabo da Tabbas yau Danwake kannensa suka Yi a gidan Kuma sai da yaci ya fito,da sauri ya kashe wayarsa su Tawaga Suka dinga dariya Jibson yace ba abin Dariya bane wannan wallahi Danwake naci na fito idan ba mayya ba Taya tasan naci Danwake? Gaskiya a Nemo min maganin mayu wallahi,Bari Brown yazo Dan Uwarsa ya sa munje wajen Mayya,Suna ta dariya Bash yace Ashe duk wankan da muke dauka a banza tana kallon Hanjin mu me muka ci,Jibson da sauri yace Kuma ranar tuwo naci kaga zata kalle Ni a banza Ina cin tuwo,da ace nasan Haka ne ai Kwai da nama zamu ci idan munje ta ganmu Yan gayu,yanzu ta ganmu cikinmu duk tuwo,Bash yace kyaleta anjima zamu je kaza zamu siyo muci muje Suka ce Haka za ayi su Ahmad suna jinsu suna ta dariya,Amma Ahmad duk da Haka hankalinsa Yana wani wajen. Da Yamma su Jibson kazar kuwa Suka siyo Suka ci harda Shan Yogourt,Bash yace Bari na Kara da Biscuits sabo da ta ganmu muma ba baya bane,Jibson yace Apple zanci Ni Haka Suka dinga Ciye ciye su Tawaga suna ta dariya,yau da Sameera ta shigar da su Palon Baki kallonsu tayi Tace Bari na kawo muku lemo ko da yake nasan kunyi ciye ciye da yawa,Bash da sauri ya kalli Jibson,Jibson tsoro ya kamashi yace Wai ke Kwano Taki da ita aka haife ki ko kuwa siyanta kika Yi? Sameera ta Gama Gane shi Amma sai Tace me fa? Kasa fada yayi Dan kar ya ci Mata Fuska sai yayi Shuru kawai,Sameera ta fita a ranta tana ta dariya Bash ne yace ai ance ta bangaren Uwa tafi karfi Wala Allah ita a nono ta Sha,Abban Brown ne yazo zance yau ma yaga su Jibson Ashe Basu daina zuwa ba,Takaici yasa ya shiga palon shima ya nemi wuri ya zauna sabo da shima Abban Dan rigima ne baya tsoron abin kunya gashi ya makance Akan son Sameera,Su Jibson Suma suka ki tashi mirsisi sukayi,Abban Yana ta harararsu Suka share abinsu,Sameera ta fito tare da ajiyewa su Jibson lemo ta zauna tare da maida hankalinta wajen su Jibson,Abba ko Kallonsa Bata Yi ba,kwafa ya ja ya Mike ya fice Kamar zaiyi duka. Su kuwa sai magrib sannan Suka tafi. Bayan Kwana biyu duka abokan Ahmad na kusa Mashkoor, Jibson,Bash,Tawaga da Brown wajen Ahmad Suka zo,Brown yace Ahmad ka shirya muje daurin auren Cousin Dina a Kano gobe,Ahmad yace a halin da nake ciki bazan iya binku ba ga motar Nan ku dauka kuje da ita koma Ina ne ai komai Nawa naku ne,Suka ce to ba damuwa,washe gari da Sassafe Suka shirya tare da tafiya Kano,Ahmad da Rana Yana kwance Yana ta tunani iri iri akan abinda Aamna ta Masa sai ga kiran Wayar Mashkoor sabo da shine Kawai Suka Yi waya yanzu yanzu,Yana dagawa akace masu wannan motar sunyi hatsari ayi sauri azo Kan gawarsu gaba Daya sun mutu na Daya motar ne babu Wanda ya mutu suna asibiti,Zumbur Ahmad ya mike tuni ya rasa inda zai sa Kansa,yanzu abokan nasa ne suka Suka mutu? Kayan dakinsa ya shiga watsi dasu. Kuka Kawai ya fara ya rude Kawai Iyayensu ya Kira ya sanarwa kowa hankalinsa ya tashi ko wanne danginsa Suka tafi can inda akace anyi hatsarin,Shi kuwa Ahmad a rude ya Kira Mummy ya fada mata,Yana kashe wayarsa ya fita shima ya bazama,tare da Baban Jibson Suka tafi can hanyar Kano,Suna zuwa Suka hango Yan Sanda da mutane da yawa a wajen Ana ta zaro gawarwaki,motar Ahmad gaba Daya tayi fata fata,da gani yawan gawarwakin Ahmad ya Fadi ya sume yin duniya Bai farfado ba,da shi aka hada aka tafi Asibitin da Wanda Basu mutu ba,Daya motar ita bata wani lalace sosai ba da gani kasan a motar Ahmad sune Wanda Suka mutu Kawai. Duka Emergency aka wuce da su,Mummy ce ta Kira Aamna tare da sanar Mata Tace kiyi sauri idan sun dawo ki je wajen Ahmad kar ki Bari ya koma shaye shaye,Ahmad Yana son abokansa wannan abin zai taba shi,kece kadai Zaki iya kwantar Masa da hankali,Aamna tana kuka Tace to Mummy. Ahmad da kuka ya farka Yana Kiran sunayen abokansa Muryar Mashkoor yaji yace Kai dalla mace ne ka ganmu Bamu mutu ba wallahi raunuka Muka ji na Daya motar ne Suka mutu,Zumbur Ahmad ya mike Yana bin dakin Emergency da kallo yaga dukkan abokansa suna numfashi Brown dake Jan motar ya Dan fisu Shan wahala,Farin ciki ya Kama Ahmad yace ya akayi Baku mutu ba yanda motar Nan ta dagargaje Haka? Mashkoor yace ikon Allah wallahi,ai Watarana mutuwa ba a Nan take ba sai kaga motar da Bata wani ki jiki ba an mutu wacce tayi raga raga Kuma ba a mutu ba,Jibson yaji wuya duk jikinsu raunuka yace na daina shaye shaye daga yau na jiyo kamshin mutuwa,Tawaga cikin wahala yace yan kannena marayu da tuni an musu sakiyar da ba ruwa,Ba Baba ba Ni sun Shiga Uku wayyo Allah na tuba,Ahmad yace Ni yau wacce irin godiya Zan yiwa Allah,Bash yace kaje kayi ta Sallah,Iyayen su Jibson kowa kuka ya Kare sai murna da godiya ga Allah,Ahmad ya fadawa Mummy Basu mutu ba,Itama Mummy cike da murna ta sanarwa Aamna Tace Idan an dawo dasu asibitin Kaduna taje can lallai ta kula da Ahmad. Haka kuwa Ahmad shi ya biya kudin Hospital,har Wanda Suka mutu ya Bawa Iyayensu tallafi,Transfer aka musu zuwa Kaduna private hospital Ahmad ya dau nauyin komai Dukkansu ba Wani rauni me wahalar warkewa Suka ji ba,Sameera a guje tazo Asibitin tana ta kuka a gefen bed din Jibson ita dai tana son Jibson a rayuwa,Jibson kallonta yayi kadan yanda ta tashi hankalinta a hankali ya daura hannnunsa saman nata Hannun dake saman cikinsa,Idonta da Hawaye tace ya jikin? Murmushi yayi yace da sauki Me Hannun kwano yau cuta tasa bani da kitse,namana ba maiko zaiyi ba yanzu ki tausaya karki lashi kadan,Dariya Sameera ta dinga yi,Ahmad Yana kallonsu yayi Dariya tare da zuwa gefen Jibson ya zauna yace Malam me zaka iya ci? Kannen Jibson ne Suka shigo da Abinci iri iri,Ahmad suka gaisar tare da Sameera duk da Basu San wace ba. Jibson yace kaima kasan bazan wuce farfesun hanta ba Malam,Maye Ahmad ya Furta suna Dariya yace Sameera ki taimaka a bashi,Sameera ta zuba a plate Ahmad ya tallafa Jibson ya jingina da jikin pillow,Kanwarsa Fa'iza Tace wannan Surukar mu ce ne?Ahmad yace ae Kawai,sai murna sukeyi suna kallon Sameera,Sameera harda kunya,Jibson yace me Hannun Kwano a bani Mana yunwa,Sameera kuwa Fa'iza ta mikawa Wai ta bashi ya ci,Fa'iza Tace ai mu fita zamuyi ma kiyi aikinki suka fice tare da komawa Room din Mashkoor. Sameera ta fara bashi a baki Yana ci suna kallon junansu. Mashkoor Wanda duk ya fisu Jin sauki,Ahmad ya koma Room dinsa tare da kannen Jibson gefe Kuma ga yayar Mashkoor tana zaune,wata Nurse ce Yar kyakyawa fara Amma ba can ba ta Sha fararen uniform dinta Idonta dauke da farin Glass da Alama Hutu ya ratsata kana gani kasan ba talaka bace,baza ta wuce 22yrs ba,tana kamshi ta shigo ta kalli Mashkoor Tace ranka ya Dade maganinka fa? Fuska ya Bata yace Baku da Aiki sai durawa mutum kwaya,Ahmad ya dura Masa ashar yace Amma ai kasha marar amfani Malam ka karba,ya kalli Budurwar yace idan Zaki bani a Baki da kanki Zan Sha,Dariya ya Bata tace Indai zaka Sha me zai Hana,Ahmad Baki ya tabe tare da kwadawa Mashkoor waya a Kansa kadan,Kara yayi kadan,Nurse wacce ake Kira da Nafeesat ita ce ta bashi maganin da kanta sannan ya Sha,dama Ahmad ya Dade Yana kallon Mashkoor kullum Nurse din idan ta zo sai ya wani nutsu magana ma baya Wasa ko kadan idan a gabanta ne,Kallon Nurse din yayi a nutse yace na gode ya wani gyara t-shirt dinsa,Tace juya na wanke maka raunin Dake bayanka Zan Masa dressing, Mashkoor ya cire Rigarsa tare da juya Mata baya,Nafeesat jikinsa take karewa kallo wani luwai luwai da Alama Ana kula da jikin Nan sosai dama gasu duk Yan gayu ne,Shi kuwa Mashkoor Ido ya wani lumshe da Hannunta ya sauka a gadon bayansa,Sai da abin ya bawa Ahmad Dariya ya Harare shi sannan ya fita. Room din Bash kuwa Ana gyara Masa inda kashinsa ya goce sai Ihu yake Yi,Yan Uwansa suna ta Masa dariya,Mamansa tana rike da shi.. Tawaga shima sosai yaji sauki Yan kannensa marayu sun yanyame shi wajen su goma Sha babu masaka tsinke sabo da shine jigon rayuwarsu Basu da matsala idan Yana Nan,Harda Yan Yara wasu duk sun Dane jikinsa suna ta wasa Yana ta dariya Umma tana musu fada Amma Ina,ai ko gida ya dawo da gudu zaka ga suna Fitowa ta kudu ta arewa suna Masa Oyoyo shi Kuma Yana daukansu Daya bayan Daya,Ummansa Tace Allah ya taimakemu da ace ka mutu da mun shiga uku,Dariya yayi yace ai Allah Yana Nan,Ahmad Daya shigo dakin sai da suka bashi tausayi matuka har da hawayensa ya goge kadan,Yaran suna ganinsa shima Suka dinga gudu Wajensa Suka yanyame shi suna Yaya Ahmad Ina wuni,Daukansu ya Shiga Yi Daya bayan Daya yanda suka Saba Yi musu,gaba Daya Suka taso har manyan maza da mata,Ahmad ya kalli Umman yace Umma yanzu kuka zo? Tayi murmushi Tace wallahi Kuwa Allah dai ya saka,ya muku Albarka,Allah ya baku lafiya da tsawon rai,Allah ya albarkaci rayuwarku, Inshaallah baza ku tabe ba,Ahmad yace Ameen Umma,Kanin Tawaga Yaja gefe Yace ya gidan namu akwai abinci ko? Yaron yace akwai komai wallahi,to ba Mai matsala? Yace babu komai,Yan makaranta fa? babu matsala Suma,Ahmad yace Good to yanzu ja Yaran Nan ku koma gida da Umma sai ku bar Sageer tunda shi Yana da girma Kuma Namiji ne,yace to,Umma ta ja Yaran Suka fita har Ahmad a Napep biyu ya biya kudin sannan ya bawa Umma 10k yace tayi cefane Suka tafi suna ta godiya. Brown dama suna da Dan Hali su Basu da matsala Kuma Ahmad ya biya kudin Hospital,Allah sarki shima danginsa suna tafe,Bash ma Basu da matsala komai normal. Ahmad kuwa kullum acan yake yini acan yake kwana wanka ne Kawai ke maida shi gida,Yana musu komai da kudinsa da lafiyarsa,Me Hannun kwano ma da ita ake jinya tana tafe da Abinci kullum,ko wanne room mutum Daya ne a ciki,Kuma suna ta samun lafiya kullum. Aamna Shiryawa tayi itama zata je dubiya,Mummy ce ta fada Mata Hospital din da suke,Sabo da tana sa Rai zata ga Ahmad wani Arnen wanka ta dauka cikin dankareren farin lace me tsada na lefe Wanda Bata taba sawa ba,dinkin Riga da skert komai fari ta sa har takalmi da jaka lady in white tayi ta tafi,Da Nafeesat nurse ta fara haduwa ta tambayeta,ai Kuwa duk ta nuna mata,Dakin da Tawaga ke kwance ta fara shiga Yan Yara kanana su Uku ta hango da Dan shekara bakwai,takwas,sai me biyar suna Wasa a jikin Ahmad dukansu mata,Ahmad Kuma Yana Zaune a gefen Tawaga suna ta Hira suna dariya yace ai Kai sunanka Me Marayu Allah zai dafa maka da wuri Tawaga yanda kake kula da Marayun Nan haka,Aamna tsayawa tayi tana kallonsu sun Matukar birgeta,kawarta ta tuna Siyama yanda taci amanarta ta rabata da masoyinta abin kaunarta,kafin ta Gama tunanin taga Yan Uwan Tawaga suna ta sintiri Yara da manya suna ta zuwa ana tafiya da su gaskiya suna ji da shi,Yan Yaran Dake Wasa wata Yar Budurwa ta kwashe su kaf ta bawa kannenta suka tafi da su gida,Ita Kuma ta dawo ciki,Budurwar baza ta wuce 19Yrs ba kyakyawar gaske suna Kama da Tawaga sai dai ta Dan fishi haske kadan dake mace ce,Shima Wala"Allah Dan Yana shaye shaye ne. Budurwar me suna Hafsat ta kalli Aamna wacce Taki shigowa tun dazu Tace baiwar Allah kin Dade a tsaye ba dubiya kika zo ba ne? sai lokacin Ahmad ya juyo Sabo da sun juya baya,Aamna ya gani sai da zuciyarsa ta buga,yaji wani sabon sonta ya sake shigarsa,Wutar sonta tana ruruwa a zuciyarsa,Itama Haka Aamna ji take Kamar ta kurma Ihu sabo da sonsa da Kuma yanda zuciyarta ke bugawa ba kakkautawa,Tawaga ne yace Aunty Balaraba karaso Mana,Hafsat tashi tayi Tace zauna a Nan ita Kuma ta zauna kusa da Ahmad Tace Yaya Ahmad na siyo Mana Whot kullum zamuna Yi da marasa lafiya sabo da su samu nishadi,Dariya Ahmad yayi yace kin kyauta Hafsat,Aamna ji take Kamar ta mutu sabo da murmushin da yayi ba karamin kyau yayi ba,,Hafsat Tace Yaya Ahmad give me Five ta Mika Masa Hannu zasu tafa caraf Aamna ta rike Hannunta cike da kishi Tace ba muharraminki bane Yan Mata,Tawaga yayi Dariya ya kyaftawa Hafsat Ido tace na gode da tunatarwa Aunty. Tawaga ta gaisar ta Masa ya jiki ya amsa da fara'a,Ahmad take ta faman kallo,zuciyarsa ce ta kasa Jurewa ya tashi tsam ya bar room din a fusace ya koma Room din Mashkoor Wanda daga shi sai Mashkoor,Aamna tana gamawa Tace Bari naje na duba sauran ta musu Sallama,Bayan Aamna ta fita Tawaga yace Hafsat matarsa ce fa? Dariya Hafsat tayi Tace lallai Dole ta ji haushi na,Amma fada Suka Yi? Ae Kawai Tawaga yace,Tace me ya hada su? Tawaga yace bana son gulma fa Ina ruwanki so kike naci Amanar abokina na fada Miki sirrinsa,Sorry Yaya ta furta,yace kinyi Assignment din naki? Ae ta furta yace Good so nake Yi kema ki Zama Nurse ki dinga tsira Mana tsinken bature,Dariya Hafsat tayi. Aamna dakin Mashkoor ta shiga Bata Yi zaton Ahmad Yana ciki ba, Mashkoor yace Aunty kece? Murmushi tayi tace nice ta gaisar da shi tana ya jikin? Yace da sauki,Ahmad ya Bata Rai Kamar zaiyi duka, Aamna jikinta ya sake sanyi,Aamna da kyar take danne zuciyarta Kar tayi kuka tace Mashkoor Allah ya kiyaye gab.....Hawaye ne ya zubo Mata ba tare data shirya ba,Ahmad ganin kukanta hankalinsa ya Kai Matukar tashi Amma Daya tuna kalamanta na ba sonsa nake Yi ba na karbi soyayyarsa ne sabo da na canja shi,sabo da na taimaki Iyayensa sai ransa ya sake baci,zuciyarsa tayi bakikirin, Mashkoor Kuwa tausayin Aamna ne ya kamashi da gani tana son Abokin nasu matuka Amma tuna abinda tayiwa abokinsa Tace ba sonsa takeyi ba Kawai sai ya share,yace kiyi Hakuri Aunty komai zai dawo normal,Maganar Mashkoor yasa ta danji sanyi tana shesheka Tace da gaske kake Yi? Yace Inshaallah very soon,Murmushi Aamna tayi,ganin Haka Ahmad ya fice daga dakin a fusace. Haka ta duba duka Brown,bash da Jibson ta fito zata tafi ta hango Ahmad a wajen Nafeesat Nurse suna magana tana rubutawa da Alama magunguna za a siyo,tafiya Aamna tayi abinta. Bayan Kwana biyar Aamna da Yamma Shiryawa tayi ta tafi gidan Ahmad lokacin ya shirya zai tafi hospital ya ganta ta shigo tana tafiya Sadaf Sadaf,da sauri ya koma palonsa sabo da Bai so ya ci Mata mutunci a Gaban me Gadinsa Bai Dace ba tana matarsa, palon ta shiga da masifa yace me ya kawo ki gida na? bana bukatar sake ganinki a rayuwata ki fita harkata,Aamna gwiwoyinta ta zube a kasa tare da hade Hannayenta biyu tana zubar da Hawaye tana Rusa Kuka Tace Dan Allah,Dan girman Allah ka yafe min,kayi Hakuri da abinda nayi maka wallahi Allah shine sheda Ina sonka....Ina sonka Ahmad....wallahi Kaine rayuwata,Ina sonka wallahi abinda na fada ba Haka ne a Raina ba na rantse da Allah ta karasa da kuka,Cikin hasala da karaji yace da kunne na naji, idan da wani ne ya fada min bazan yarda ba zaki Raina min hankali Get out bana kaunar sake ganinki,mayaudariya makaryaciya fitar min a gida,idan kika sake shugo min gida sai Kinga abinda Zan miki,tashi ki bar min gida,Tana durkushe tana kuka Tace Ahmad ka saurare Ni Dan Allah......Tsaki Yaja a Matukar hasale ya yo kanta ba shiri ta Mike ta fice da sauri tana ta kuka,Musa Yana kallo ta bashi tausayi,yace kayi Hakuri Oga Yarinyar ce akwai naci,Ahmad ya daka Masa Tsawa yace kai matar tawa zaka ce Mata me naci wallahi Zan sallameka a aiki,Shuru Musa yayi Ahmad ya fita Yana ta Fushi Yana Jin haushin Musa yace Aamna ce me naci,ya ja tsaki. Aamna kuwa tun kafin ta koma gida zazzabi me zafi ya lullube ta. Kwana biyu tsakani aka sallami Mashkoor da Tawaga sabo da su sun warke, Cuta ce ta Kama Aamna sabo da Bata cin abinci Kuma ga kuka kullum da take sharba,Anyi anyi taci abinci Taki ci,Zuhra ko yaushe tana Hanya tana fama da Aamna Amma Taki ci,an Bata magunguna Taki sha Tace ita gwara ta mutu ta huta da duniya,Mummy Aamna ta Kira a waya tana ta kuka Tace wallahi Mummy ina sonsa Dan Allah ki Masa magana,idan ba shi mutuwa zanyi Aamna ta sake barkewa da kuka,Mummy Tace kiyi Hakuri Aamna nasan Yana sonki zai dawo ne,Aamna tana shesheka Tace har yanzu baya ko daga wayata ko text na Masa baya Replying Ni mutuwa zanyiii.....Baba Yana Zaune tausayin Aamna ya lullube shi,yace kiyi Hakuri Aamna zai dawo Inshaallah,Mama tayi tagumi abin Nan ya isheta Allah yasa Ahmad ya dawo. Bayan Kwana biyu jikin Aamna yayi zafi sosai lokacin Kuma Brown ne kadai ya rage a Hospital Amma duk an sallami su Jibson sun warware,Shima Brown saura kadan a sallame shi. Mama ce ta shirya da kanta ta tafi gidan Ahmad,me Gadi ya Bude Mata ta shiga,Ahmad Yana garden a zaune yayi tagumi shi kadai,Jin Ana ta Sallama ya taso tare da lekowa,Mama ya gani yayi mamaki,Palo ya kaita yace shigo Mama,Zama tayi sannan ya gaishe ta harda kawo Mata lemo, Mama Tace Bazan Sha ba,Ahmad Ni ba ruwanka nazo Sha ba,Aamna tana can Bata da lafiya Kamar zata mutu akan ka,to wallahi idan Muka rasata sai munyi Sharia da Kai, Ahmad yaji wani dum a ransa Jin Aamna Bata da lafiya,a ransa yace yaushe su Baba suka fara kaunar Aamna ko da yake riko ba Wasa ba su Suka raineta akwai shakuwa Dole,a fili yace ku kaita asibiti Mana ko ku Bata magani da Abinci Ni Mene Nawa a ciki,da masifa Mama Tace Taki cin abinci Kuma maganin ma taki Sha babu yanda Bamu Yi ba,mikewa Mama tayi Tace Ina Jan kunnenka Yar mu ta mutu sai kaje kotu wallahi,Ahmad yace ku Bata magani zata tashi Ni ba abinda zanyi,Mama ta fice a fusace shi kuwa ya koma bedroom abinsa. A ranar aka sallami Brown shima,komai Normal,Iyayensu har gida Suka dinga zuwa suna yiwa Ahmad godiya. Yau Tawaga a Machine dinsa ya dauki kannensa Wanda baza su iya Kai kansu school ba yaje ya ajiye su,ya juyo zai tafi kenan Ya hango wata Matashiyar Budurwa Yar kyakyawa fara Amma Bata fiye Hanci ba,Idonta kanana idan ka ganta ka rantse ta hada jini da Yan China Amma ita doguwa ce siririya, zata Kai 18yrs, a jikin gate din makaranta ta labe Kawai take ta aikowa da Tawaga zagi da Hannunta,tana Masa dakuwa,Shi abin ma mamaki ya bashi Bai santa ba Haka Kawai,kwafa yaja a ransa yace zanzo daukan kanne na ne Bari a tashi a school yau har karkashin gadon Uwarki sai na shiga na ballaki. Kwance Aamna take a palon saman kujera ta lulluba da bargo tana ta Rawar sanyi,Kanta a saman cinyar Zuhra,Baba da Mama suna tsaye a kanta jikinta ya dau zafi ga magunguna Likita ya rubuta anyi anyi taci abinci ta Sha magani taki,Mama tace Aamna so kike ki kashe kanki,an Baki abinci kici kinki magani ma kinki Sha,gashi shi da bakar zuciya yaki hakura,kema ga taurin Kai Haba Aamna,Aamna tana kuka Tace Ni bazan ci ba gwara na mutu na huta tunda baya so na yanzu,Baba Ina sonsa Dan Allah Baba kaje Wajensa ka dawo min da shi idan ba Haka ba bazan ci komai ba. Muryar Ahmad Suka tsinta a jikin kofa daga waje yace idan Ni na Baki abincin Zaki ci? Ai Zumbur Aamna ta Mike Kamar ba ita ke kwance ranga ranga ba,bargon ta jefar sanye Take da wata Yar guntuwar rigar bacci red,Gashinta yayi buzu buzu,kofa ta Bude da sauri taga Ahmad a tsaye yaci Uwar gayu cikin wani farin yard sai sheki yake zubawa,ga wani sabon kitson calabar anyi Wato har yanzu da saura ba a Gama canjawa ba,Hannunsa dauke da ledojin take away, Murmushi ya sakar Mata ai Aamna ganin Haka tasan ya huce tuni ba ruwanta da wasu su Baba da Suka fito Suma ta fada jikin Ahmad ta Rungume shi tana ta kuka tana cewa kayi Hakuri,wallahi karya nakeyi Ina sonka bazan sake ba tana shesheka,Kankameta ya sake Yi a jikinsa Yana Jin wani farin ciki,Baba da su Zuhra kunya ta kamasu yanda idonsu ya rufe,Baba Kansa ya sadda kasa yace Ashsha....Ashsha. Ina ta godiya masu sharhi AsmaBaffa 10/26/21, 8:53 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 71-75 Official By AsmaBaffa Page naku ne BK Sweety Bella Umman Muhammad Asmau Yusuf Sa'adatu Tijjani Teema's collection Muje ciki Aamna ta furta tare da rike Hannunsa Suka Shiga Palo,Zama sukayi a saman kujera Aamna harda gyara Masa rigarsa,Su Baba da sa Ido duk sun ki tafiya suna ta faman kallonsu,Ahmad ya kalle ta yanda ta rame tausayi ta bashi ya Bude Ledar take away din ya fito da ita tare da dakko Shawarma me zafi sabo da yasan tana sonta,a kafadarsa ta kwantar da kanta tana kallon su Baba ba kunya,Mama Tace muje ciki Zuhra,Shawarmar ya shiga Bata a Baki tana ci,Mama tana mamaki yanda aka dinga yaki da Aamna taci abinci Taki ci Amma yanzu gashi tana ci,Shi Kuwa Baba tunaninsa yanda Aamna tayi ranga ranga Kamar zata mutu Wai yanzu itace ta watsake Haka lallai,Ahmad yace to ci Nan wurin yafi Nama ya Bata taci,yace da Dadi? Ya tambaya,Aamna ta daga kanta Sama sannan ta sake kwantar da kanta a kafadarsa tana murmushi,Baba yace u'uhum yace ku mu tafi Mana,sannan Suka tafi aka bawa su Aamna waje,Sai da ta cinye Shawarma ta cinye wani meat pie,ta cinye chips da wani gasashen kifi sannan ya Bata Fruits ta Sha ta Dade rabon da taci abinci Haka tunda Suka Yi fada,sai dai ta Sha tea sama sama. Sai da ta Gama yace saura wanka,ba musu ta Mike tare da cewa to tana ta wani girmamashi,Hannunsa ta rike Tace muje ciki,Kallonta yayi Yana murmushi me kayatarwa ya furta kije kiyi wanka Ina jiranki,Kuka ta saki cike da shagwaba Tace baka hakura ba kenan? Mikewa yayi yace muje,Bedroom dinta Suka Shiga ya kwanta saman bed dinta ita Kuma ta shiga wanka ta Dade kafin ta fito lokacin yayi bacci ma tuni sabo da Rashin baccin da yake samu duk dalilin Aamna,Fuskarsa ta leka tana ta wani farin ciki tana murmushi,jikinta ta goge cikin Nutsuwa ta Gama shafe shafenta ta shirya cikin wani dakakken lace Brown and dark green shima na lefe ne sabo gadagal,Yar kwalliyarta ta tsara tare da kashe dauri na zamani tana zuba kamshi ka rantse wani party zata je,Kamshinta ne ya jawo farkawarsa. Kallo ya bita da shi ji yake kamar ya hadiyeta,Hannu ya Mika Mata tare da furta taso mu wuce tafiya zanyi,Fuska ta shagwabe tare da furta Wai saurin me kake Yi Haka? Ina da abinda zanyi ne su Mummy nan da 3days zasu zo, Alright ta furta tare da Furta muje to,mikewa yayi Suka tafi tana gaba ta bude kofa kenan ya sa Hannu ya maida Kofar ya rufe ya jawo Hannunta da sauri ta juyo suna facing juna hannayensa yasa tare da riko Hips dinta ya mannata gaba Daya a jikinsa,Kirjinta Yana saman nasa,Hannayenta ta sakalo ta wuyansa suna kallon juna suna aikawa juna murmushin so da kauna,goshinta ya shiga yiwa kiss double a jere ya dire a saman labbanta. Tuni Aamna ta lumshe ido tana Jin wani taratsatsin wuta a cikin jininta,Shima bangaren Ahmad abinda yake ji ya zarta ya iya control,Aamna taji Abar tasa ta Mike sosai,kunya ce ta kamata sabo da tana jinta a jikinta,lulawa tayi tunaninta lokacin data fisge Masa towel a farkon aurensu lokacin tana gidansa suna fada,a ranta Tace wacce fa na gani a baya itace yanzu tana ta tunawa,Ahmad Kuwa yama rigata tunano Sanda yake ta Shan kallonta ba Kaya zata je wanka,Aamna Martani take maida Masa suna ta tsotse bakunansu kamar Kare ya samu kashi,a ransa Yana tuna maitar Aamna a fili kuru kuru tana bukatar Namiji Yana cin zalinta baya Mata komai sabo da kar Tace jikinta yake so ba ita ba,shima yau yanda yake ji yafi karfin zuciyarsa,jikinsa har rawa yakeyi sabo da yanda Aamna ke Masa kiss wani me zafi duk ta makalkale shi. Jikin Kofar da suke ya Kai Hannu a hankali tare da Murda key sabo da tsaro,Cike da kunya Aamna tace Allah yasa su Baba Basu ji karar key ba,Daukanta yayi cak suna karewa kansu kallo yace basa Nan ma sun fita Unguwa,Aamna tace Amma Iya Romance zamuyi ko? Abinda kike so,Tace ai Bamu koma Hospital ba an duba anga ko na warke ba,Dariya yayi shi sai yanzu ma ya tuna,Yace Ni ba ruwana da wata cutarki ai gwara ma ta kamamu tare,sai lokacin ya kwantar da ita a saman bed yabi lafiyarta ya kwanta Kara ta danyi kadan sabo da yanda ya sakar Mata nauyinsa kadan,Aamna dai tana so ayi Romancing din Nan sai ta juya Masa baya ta fake da kunya Wai take ji,a zahiri Kuma ta juyana Dan ya zuge zip din,Don gulma har da rufe Ido,Zip din rigarta ya zuge a hankali,Harda makalewa Wai Bata so,yace why? Tace su Baba nake tsoro da kunya ka Bari sai na koma gidanka idan su Mummy sunzo. Yace ba yau Zaki dawo ba? Tace Mummy ta min waya Tace na jirasu,Ahmad Yana son abinda Aamna ke so,Bai so ya Mata laifi sai yace kinfi so ayi komai idan kin koma? Aamna garin kunya tace ae harda wani Bata Rai ita bata so,yaji damuwa a ransa sai yaga Kamar Bata damu da shi ba,gashi Yana so shi ya rage zafi Amma Bata so idan yace zaiyi zai takurata ba a son ransa ba maida Mata rigarta Yana furta shike Nan,Aamna Kamar ta kurma Ihu ta cuci kanta,ta manta Ahmad Bai taba kula wata mace ba sai a kanta sannan shi baya Harkar Mata harkar gabansu sukeyi na shaye shaye Kawai. Kasa magana tayi yace ko Zaki rakani? Ina zamuje? Yace Mummy ce ta aikeni gidan Yayarta Zan Kai Sako,ba damuwa muje na rakaka ta furta,tare da mikewa ta yafa mayafinta tare da daukan hand bag da takalmi me tudu Dark green. Glass ta dakko ta saka wani light brown Nan ta sake canja dauri zuwa ture kaga tsiya,kyau Kuwa ba a magana,Fitowa sukayi ta Iske Mama a kitchen tana girki Baba Yana Zaune Yana gyara Mata wake,dama Watarana Yana Taya Mama Aiki ba sabon Abu bane Amma badan Allah yakeyi ba Wai Dan kar ayi Masa almubazzaranci sai ya zauna ya gyara da kansa,Mama ce ta juyo Tace Dan Allah Baban Zuhra ka bar wajen Nan Haka Haba me kwarin ma baza ka tsince ba sabo da tsumulmula,Baba yace naki na Bari a zubar min da dukiya a fake da kwari a dafa Mana da kwarin mu,kwarin wake ance Kara karfin gani sukeyi Ana so Dan Adam ya dinga Cinsu. Mama Tace a Ina kaji? A radio bababban Likitan kwari shi yayi bayani,shi fannin kwari ya karanta cewar Baba. Baba ganin Ahmad sai yace ki dafa waken Nan sosai sabo da bani da wadataccen jini a jikina,waccen shekarar 2020 har jini na bawa wata a asibiti Amma 2021 Ni kaina nasan bani da jini,idan aka aunani za a ga jini na Bai Kai na Bara ba sabo da yanzu ba'a cin nama da abubuwa masu inganci rayuwa ta canja kowa ya kwanta cuta sai kaji ance Karin jini,daga shinkafa da Mai da yaji sai tuwo da Dambu ba Dole a rasa jini ba Ana cin Dambu ai a ka'ida Dambu abincin agwagwi ne suyi ta tsatsatsaga. Ahmad murmushi yayi ya Gane Baba,Baba Kuwa yace tunda abin Haka ne asibiti zanje na karbo gyadar Nan ta Yara wacce ake karbo musu idan sun rame sun lalace sunki girma Nima ita Zan karbo na Sha nayi bulbul,gaba Daya na wani Zuke sai Dan ciki na kwajaja a gaba da ganin kibata an San Bata lafiya bace sai Dan ciki a gaba,Dariya Aamna Suka Yi Baba yace ba abin Dariya bane Kuna gani sai tsumburewa nakeyi bani da jini sai kace Wanda nake cin kasa Haba ya kamata a dinga kula da ni.. Ahmad yace Nima Baba Ana aunani nasan bayan rashin jinin harda shawara tana damuna Ana auna Ni za a ga shawara ta Gama dani,Nima ba ci nake Ina koshi ba,sai nayi kwanta kwanta ake bani kudin,Baba yace Kai kana Dan gidan Ajebo inji Yan Birni Dole fa ka siyo Mana Nama a gidan Nan duk wata shawararka karya kakeyi,Dariya Ahmad yayi yace to Kawai,Aamna Tace mun tafi Unguwa,Baba yace Halina da ke Aamna kin kasa wayewa wata kidahuma ce ke ace shekara kusan biyar a birni Amma har yanzu sai halin banzan ki na kunbiya kunbiya baza ki fito ki dinga fadan gaskiya ba yanzu idan gidansa zaku tafi Zan hanaki ne? Idan ma Hotel Zaki tafi me zamu ce tunda mijinki ne,Aamna ta bude Baki daga ji tasan Gulmar Baba ce Kawai so yake yaji inda zasu tafi Yana zarginsu,Mama Tace a dawo lafiya,Ahmad Yana gefe Yana jinsu saura shima ki ta Masa halinki na munafunci baza ki dinga Fitowa ki nuna kina son Abu ba,idan Kifi kike so kice ya dinga siyo miki,idan nama ne ko Madara ki fada Masa,Dariya ce ta kwacewa Ahmad su Wato Dole sai sunci kudinsa kenan shi yasa suke ta wannan abin,Baba da sigar lallami yace Yaron Nan idan mota kika ce kina so ya Siya Mana tsaf Zaki ga Allah ya azurta mu. Ahmad Palo ya tsaya yace Ina jiranki,Ahmad Yana Jin Mama Wai tana sirri da Aamna tace to ke Soyayyar zamani ma ba iyata kika yi ba,Dan ubanki idan baki dage ba yanzu Mata sun dage kwacen maza sukeyi wata idan taga wannan zukeken ga kudi ai wallahi ke da kwanciyar hankali a duniya sai dai kiji a makwafta,da asiri za a rabaki da shi ko idan Suka fiki iya tarairayar Namiji shike Nan,Baba harda zaro Ido yace Sorrynki Aamna inji bature,kije Zuhra ta koya Miki zaman duniya,gata can da Adamun ta kullum mashaallah,bakiji sunan da take Kiran Adamun ba? Me lobuli,Dariya Aamna tayi Wai Baba (My Lovely ) yake nufi shine Me lobuli. Aamna tafiya tayi tana cewa Nima na iya ai ban fara bane,sabo da ke ga Yar me taurin Kai ko? Cewar Mama,Aamna King ta samu Tace let's go,Suna tafiya Baba yace ai yanzu tunda auren Nan na Aamna ya koma mutu ka raba to dagewa zakiyi ki Mata gyara irin na Iyaye sannan ki koya Mata salo da dabarun kauna sabo da ta Haka ne kadai zamu samu harka,idan Yana Jin dadinta babu abinda bazai Mana ba a duniya,Duk da kema wata kidahumar ce baki iya komai ba Nima maleji nakeyi Amma ki koya Mata dai Kamar yanda kika yiwa Zuhra,Mama Tace au ci min mutunci zakayi? Da me kika iya? Karya nayi? In Banda ta'adin Omo da Ashana me kika kware? Mama Tace to Kai din wanne Jin dadin ka nuna min abinda Hakuri nakeyi da Kai. Amma ke dai Butulu ce Aishatu wanne tsoho kika taba gani kamata me koyi da Sunnar Annabi Irina? Da girmana Amma idan Ina gida sai na tayaki girki,yanzu ke kika sani? Amma na zauna Ina gyara Miki wake,sannan nine yanka Miki Albasa,Alayyahu,fere Miki dankali da doya,har kabewa nake fere Miki duk Baki gani ba,Mama ta dauke Kai Tace ai Dan kar a maka barna ne,. yace raguwar Banza raguwar wofi yarinya Daya kika iya haifar min,tun da kuruciyarki kina shekara14 aka aura min ke Amma da an tabaki sai kuka wayyo...wayyo...ki bare Baki Kamar Ramin kurege,Duk nayi zaton kuruciya ce Ashe Kya ce kaci Ubanka Husaini har girmana Haka aka halicce Ni. Mama Dariya tayi Tace to babana ne ya jawo da aka haife Ni wanzami aka bashi Ni ya yanke min beli,Ashe Bai iya ba,ance Dan redar kadan akeyi shi ya yanke da yawa,Da sauri Baba yace wanne Ya yanke da yawa ai gaba Daya ya jijjige shi ai Allah ya tsinewa wannan Wanzami wallahi tallahi bazai ga Annabi ba. Ya rasu fa cewar Mama,Baba yace ina ruwana da mutuwarsa Nima Nan gaba mutuwa zanyi kowa ma Haka Kawai ya cuceni,Hannu Baba ya daga Yana rokon Allah yace Allah kasa walakiri ya ta jibgar Salele Sarkin aska har tashin kiyama sanadiyar abinda yayi min,gashi Haka na hakura ban Kara aure ba babu Yara da yawa ga ba Wani dadin aure nake ji ba,Mama ya nuna da yatsa yace asiri kika min muguwa shi yasa na makale sai ke kadai,Mama Tace Hakuri ne Kawai irin namu na mutanen da,zaka ga ba'a Jin dadin rayuwar aure da komai Amma anyi Hakuri an zauna mutu ka Raba. Baba yace Haba ai na ciji yatsa da ba Dan zamanin yanzu bane ni gashi sai yanzu ake ta santalo Mata zalla zalla gasu Nan suyi ta giftawa sai hange daga nesa,Mama ya gallawa Harara yace ku Kuwa daga me Hanci a karkace sai baka wuluk,sai me katon goshi,sai me Kai kamar kwallon goruba,fata kamar Bayan Bishiya duk gaku Nan taron tsintsiya ba shara,yanzu Kuwa kaga Iyaye munana Amma sun Haifo kyawawa da naga wata Rannan tazo da Yarta shago na sai da na rantse Sato Yarinyar tayi Ashe Wai Tata ce,da har Zan kurma Ihu nace jama'a barauniyar yara. Ni gaba Daya na tsani kaina ma sabo da banzo a yanzu ba,Mama tana Dariya Tace to ya zakayi aikin Gama ya Gama gani auren zumunci ko ka koreni sai an sasanta,Baba yace ai ni duniya na hakura da Jin dadinta naji a lahira Allah yasa mu Dace. Aamna Kuwa fitowarsu kenan Kofar gidan taga wata sabuwar motar galleliyar gaske tafi wacce akayi hatsari da ita komai da komai ruwan toka,a baya Ahmad da Kansa yake Bude Mata kofa sai ta Shiga zai rufe ya dawo shi ya shiga Amma wannan lokacin sai taga ya shige mazaunin Driver ya barta,taji ba Dadi a ranta tunda ta Saba da yanda yake ji da ita Yana Nuna Mata tattali,Shiga Kawai tayi itama ta rufe,Motar ya ma key ya fara Driving cikin nutsuwa,Kallonsa takeyi jefe jefi Wanda da abaya ne shine zai ta kallonta Yana Driving har sai ta Masa magana ya kula da Driving sabanin yanzu taga ya wani dawo da takamarsa da izzarsa sai wani basarwa yakeyi,Bata ga laifinsa ba tasan ita ta jawowa kanta,a nutse yake Driving Yana satar kallonta ba tare data lura ba,ganin ta Lula tunani tayi Shuru kamar ba ita ce ba, Murmushi yayi a ransa kawai. Masu siyar da Apple na Kan danja da masu popcorn etc sune suke daga musu Abu ko zasu siya,Ganin tayi Shuru yace ko Zaki ci wani Abu? ba tare da ta kalle shi ba Tace a'a Kawai ta kalli window,sunyi tafiya me nisa wani gida me kyau taga an Bude Masa gate ya Shiga,gidan ya hadu shima,Yan Yara ta hango su Uku zasu Kai 5-7yrs suna Wasa a wajen flowers,Ganin Ahmad ya fito Suka bisu da kallo Basu San waye ba da Alama,Wata bakar Budurwa ce ta fito sanye cikin Uniform da Alama Islamiyya zata tafi,tana ganin Ahmad ta furta laaaa Yaya Ahmad lallai Kaine yau a gidan mu,tab Dariya tayi Tace Yaya Ahmad Wai Kaine da kayan hausawa lallai ta tabbata Ashe da gaske Mummy take da Tace Aure ya gyara ka,Aamna ta kalla Tace ga Auntyn mu ma nasan ita ce,Ina yini? Aamna tayi murmushi ta amsa,Ahmad Kuwa dama miskili ne,Fuska ya Bata da yaji tace wani Wai aure ya gyarashi ta Raina Masa hankali,a ransa yace matsalar Yara Basu iya magana ba,Ko gaisuwarta Bai amsa ba yayi gaba abinsa,Ita kanta Yarinyar mantashi tayi shi yasa ta iya fada Masa Haka,tasan da a baya ne da tuni ta Sha Mari,Sum sum ta tafi makarantarta. Suna Shiga suka Iske wata Mata Babba me Kama da Mummy da Alama ta girmi Mummy sosai sai dai ita baka ce Mummy Kuwa fara ce Amma suna Kama da Mummy sosai,Aamna kallo Daya ta Mata ta Gane ta lokacin da aka kawo lefenta harda matar, Matar da fara'a Tace ikon Allah yau Ahmad a gidana? Muna gari Daya Dan Iskanci sai na shekara biyar ban ganka ba sabo da kar na maka fada,sai yau lallai Aamna tayi kokari da gani ba sai an fada ba,jajayen Lips dinsa ya turo gaba yace nazo na gaida ki shine Zaki ce Haka gobe bazan dawo ba,Dariya tayi Tace na daina Barka da zuwa,Zama sukayi Aamna ta rusuna tare da gaisar da ita,cike da fara'a ta amsa,Tace Sannu da zuwa Aamna,yawwa ta furta,Ahmad yace Amma dama Mummy ce Tace nazo na gaisar dake,au Dan Iskanci ma ba Ganin damarka bace? Anya Kuwa zakuyi zumunci Nan gaba Bayan Bama raye, shine Ina Hospital da dumbun patient ka min waya kace lallai na dawo Sako zaka bani Ashe wannan ne sakon,Murmushi yayi har Aamna ya kalli Aamna yace Yayar Mummy ce Uwa Daya uba Daya,Aamna Tace Naga sunyi Kama ai Kuma na ganeta,Amma tace kwarai Kuwa da Ni aka Kai lefenki. Bayan an tashi Yan makaranta Tawaga yaje dakko kannensa Yana zuwa ya dauke su ya fyalla da gudu kamar zai tashi sama,Yaran ya Kai gida yayi sauri ya dawo school din lokacin Yan Ss3 Basu tashi ba Ana musu lesson sabo da sun kusa Zana Waec,Jira yayi tunda yaga Yarinyar da Alama a Ss3 take,Sai da yayi 30mnt a Bayan wani gida Yana lekowa ai Kuwa ya hango me Kama da Yan China ta fito tana tafiya tana ta dukan wasu classmates dinta tana guduwa,suna cewa wallhi Yar China gobe sai mun Rama Zaki zo ne, Wasu duk an dauke su a mota sun tafi gida ita Kuwa ita kadai tabi ta wani lungu,tana ta gantali a hanya tana bin ta cikin Unguwanni. Tawaga ya kunna machine dinsa ya bita a hankali Bata sani ba,Jin karar machine Taki karewa yasa ta juyo tayi Ido biyu da Tawaga Nan take ta Gane shi ta tsorata,takalmanta ta cire ta kwashe da gudu,Tawaga a nutse yake ta Binta har zuwa wani gida Haka na Bulon Siminti me Dan kyau dai na rufin asiri,Gidan ta fada da gudu Tawaga yaci birki ya sakko,Kawai gidan ya Bude shima ya shiga,wata tsohuwa ya gani tukuf tana zaune Yarinyar ganin Tawaga ya shigo har gidan ta Mike da gudu Tace Iyalle barawo tabi ta Kan tsohuwar ta fada daki tare da fatalar da kwanon abincin da Iyalle take ci,Tawaga ba ruwansa da wani gidan mutane a Haka ma sabo da ya dan shiryu Kawai yace Salamaualaykum Tsohuwa gyara kafarki Kar na karasa gawar da Bata tawa ba,Iyalle Tace Kai Malam barawo ne Kai? Tawaga yace duk abinda kika Yi tunani a ranki Haka nake,Iyalle Tace to Kai Dan shaye shaye ne naga Alama,Iya Lallai kina da kwanya gyara kafarki cewar Tawaga,Kai yaro ko gidan Ubanka ne ai sai Haka,Shege ne ni bani da uba Tawaga ya furta tare da tsallake Iyalle yayi cikin dakin ya nemi Yar China ya rasa. Cikin wani karamin Sip irin na da ya Bude sai ga Yar China bul a ciki tayi zuru zuru ta hada zufa,Iyalle Tace Dan Allah yaro karka Dakar min jika Yar China marainiya ce Bata da Uwa Bata da uba,nice nake rike da ita sai kanina da yake kula da yake Dan kula da mu sama sama,shi Kansa ba karfi ne da shi ba,abinci ma wallahi da kyar muke samun sau daya ko sau biyu a Rana,Yar China tsokana ce da ita Amma tana da saukin Kai kayi Hakuri Dan Allah,sakaki nane yasa take da Rashin kunya nice sangartata,Tawaga yace ban Santa ba ta zageni dama nace har karkashin gadon uwarta sai na bita Ni ba ruwana da wani gidan matan Aure ba Wani ganin darajarsu nakeyi ba,Iyalle ta Bude Baki Tace matan auren? Tawaga yace Ina ruwana da Iyalin wani bani da mutunci ya Furta Yana zarowa Iyalle kyawawan idanuwansa. Ya sake cewa Iya Dan fa Baki Sanni bane da a wata Daya Baya ne da na amsa Sunana na Tawaga Dake da Yar Chinan Zan hada na zubar muku da hakora,Iyalle Tace yaro Ina Naga hakoran da zaka zubar Dan Ubanka kalli Baki na Iyalle ta wangalewa Tawaga bakinta yaga ba hakora duk sun zube,Iyalle da lallashi Tace Yi Hakuri Dan jikana Ni yanzu da zaka Bamu na kokon safe ma da ka kyauta,dama Ina ganinka na Gane addu'ata kanka ta fada Allah ne ya turoka ka Bamu na Shan Koko da safe,Kuma jikata kagani wallahi an kusa rufe musu jarabawa zasu Zana ta fita mun rasa yanda zamuyi mu biya Mata tayi kuka har ta gaji. Yar China ce ta fito Sadaf Sadaf ta fada jikin Iyalle tare da fashewa da kuka tana Iyalle kudin Waec wallahi jibi Za'a rufe,na shiga Uku na lalace,Baki Tawaga ya Bude Kiri Kiri sun Raina Masa hankali,Kallon Yar China yayi tana faman kuka har wutsil wutsil tana cewa Babana ya mutu tun Ina karama,Babata ma ta mutu duk bani da wayo Suka mutu shi yasa bazan samu Ilimi ba ni bani da gata,Tawaga a ransa yace kaji mutane sun bige da maula, kallon Yar China ya sakeyi a ransa yace shegiyar yarinya sai farin fatar tsiya ita ba Wani kyau ba,Harara ya galla Mata tare da daka Mata Tsawa ya fara Mata magana Wai da yaren Yan China tunda ance sunanta Yar China Kuma da su tayi kama,Yace Chan chan hu whaaaa? Harda gwadawa da Hannu Yana ci gaba da cewa Jiji chan huuuaaaa? Yar China ta kyalkyale da dariya harda rike ciki Bata San shima haukarsa ya hada ba Tace Kai bana Jin Yarensu wallahi Kawai Allah ne ya halicce ni nake Kama da su tsaya kaga hoton Babata da Baba na, Daki ta fada da gudu ta dakko hoton Babanta da babarta ta nuna Masa ka gansu,Lekawa yayi yaga Babarta wankan tarwada ce,Babanta ne fari Amma danfulani ne usul Bai Kama da ita ba Sam,Tace mu yan Kebbi ne asalinmu. Tawaga yace to Ina ruwana da Kebbinku Allah yasa a Minner kuke karewa Yaja Tsaki ya juya zai tafi sai ya fasa ya dawo ya zubawa Yar China Rankwashi ta kwalla ihu,Iyalle Tace Yi Hakuri jikana,Hannu yasa a aljihun Jean dinsa ya zaro Dubu biyu ya damkawa Iyalle a Hannu yayi tafiyarsa,Ai Yana tafiya Iyalle harda rawa Tace wallahi yau sai na raba dare Ina Nafeela Ina godewa Allah mun samu kudin Abinci na kwana Biyar,ko matar Yaron Nan kanina Bata kawo Mana ba sai mu siya muci,idan Kuma ta kawo Wanda bazai ishe mu ba sai mu Kara da ko garin kwakwi ne,Yar China sai murna takeyi Tace Alhmdllh zamu dinga cin abinci sau uku a Rana,kwana Nan Zan murza kiba,Kuma Iyalle nasan zanyi kwana Uku ko biyu kina bani ashirin kudin makaranta,dama na dade banci ko Aya ba a makaranta. Tawaga yana jinsu sabo da a soro ya labe yaji me zasu ce,sai Suka bashi tausayi duk irin kallon gidansu da yakeyi sai yaga ashe su a Rahma suke,Tafiya yayi abinsa. Mashkoor Kuwa ya makalewa nurse Nafeesat tun Bata wani kulashi har ta dawo Yana birgeta Kuma a cikin kankanin lokaci Suka Shaku sosai har Tace ya kamata yazo gidansu,Ranar Bai fadawa abokansa ba ya shirya shi kadai cikin Shadda milk ya wani coka hula Malam ya wuce gidan su Nafeesat, Mashkoor yayi tunanin dama su Nafeesat masu kudi ne Amma baiyi zaton kudinsu ya Kai Haka ba,gidansu ko Ina Securities ne, sannan Unguwar da suke ta masu Hannu da shuni ce sai ka shahara kake Zama a Nan. Mashkoor tsoro ne ya kamashi Allah yasa a motar Babansa yaje, sabo da an San da zuwansa Kawai Yana cewa shine Mashkoor aka Masa Iso har wani katafaren Palo na Alfarma,Nafeesat ce ta fito sanye cikin wata Arabian gown da gani kasan an kashe kudi wajen siyanta,wata maroon,takalmi me tsini ta saka ta zuba kyau,sai kallonta yakeyi sabo da shi a uniform ya santa,Duk wani susucewa yayi shima irin ta Ahmad yayi yaji ya kasa magana,a ransa yace Allah sarki King Ashe Haka yaji,duk yanda Namiji ya Kai macece maganinsa,hayyacinsa ya dawo ya Dan sake kallonta maimakon ta Masa fari Wai shine ya mata wani Wal Wal da Ido,Nafeesat ta fara Dariya ita dai abin dariyarsu ke birgeta,Dariya shima yayi yace kinyi kyau My Heart,thanks ta furta tana Masa wani kallon so ta dawo gefensa ta zauna kamshinsu ya hadu waje Daya,Nafeesat ta Mika Masa Hannayenta,ya kalla ta janye,kafafunta ta nuna Masa masu kyau yace ae na gani Kuma na tabbatar ba gurguwa Zan aura ba,Dariya tayi yace saura Mayafi a cire na gani,Dariya tayi Sharewa tayi ta gaisar da shi,kayan ciye ciye aka kawo Masa yaci abinda zai iya sannan Tace Abbi Yana son ganinka, Mashkoor ya zaro Ido,Tace karka damu Abbinmu Bai da matsala,idan ka sake dawowa sai ka gaisa da kanne na da yayye na maza,Ba damuwa Mashkoor ya Furta. Hannu Nafeesat ta rike sai da zasu fita ta saki. Iso ta Masa har part din Abbinsu Yana shiga a nutse,Ammin Nafeesat da fara'a Tace karaso Sannu da zuwa, Mashkoor da kunya ya karasa shiga ciki Yana wani kasa da Kai,Dagowar da zaiyi kenan sai yayi arba da Limamin masallacin kusa da gidan Ahmad Wanda ya biyosu har ya musu kyauta Kuma yace Mashkoor yaje cikin yayansa ya zaba zai bashi yace baya so yafi son jahila,ikon Allah gashi ya Kawo Kansa,shi Kansa Limamin Nafeesat ta fada Masa Amma baiyi zaton Mashkoor din bane,Murmushi yayi, Mashkoor a ransa ya tuno Nafeesat ta rike Masa Hannu Kuma gashi Babanta babban malami ne Amma ta rike shi ba aure,Kuma shigarta ma Bai nuna ta Yar Malam ba ce,Malamin murmushi yayi tare da mikawa Mashkoor Hannu Suka gaisa yace Ikon Allah abokina ne ai Nafeesat, Mashkoor kunya ta kamashi,Malam yace ai kaci Screening Ina bibiyar komai naku nasan komai da kuke ciki,tashi kaje Allah ya tabbatar da Alkhairi, Mashkoor farin ciki ya kamashi a ransa haka Suka fito Yana ta murna. Palon Suka koma ya kalli Nafeesat yace Ashe abin naku duk buge ne? Nafeesat Tace Kamar ya? Yace ai Ni nayi tunani yayan malamai da hijab da Nikaf Zan gansu sai gaki har da rike min Hannu Ashe duk abin naki buge ne,Dariya Nafeesat tayi Tace wallahi ba Haka bane ai to malamai ba mutane bane? Ai kowa Yana kuskure,Kuma ma ai Dan Ina sonka ne Kuma ya kamata kaga wacce zaka aura sosai wannan ba laifi bane, Mashkoor yace hakane Kam to Ni dai na tsallake rijiya da baya Abbi ya bani ke,sai da suka Gama hirarsu cike da so sannan ya Mike zai tafi,Kallon Nafeesat yayi yace kiyi Hakuri Yar gidan Malam ya rungumeta a jikinsa,Nafeesat Tace Yar Malam ce Amma ba malama bace ta dago a hankali ta Masa light kiss a lips, Mashkoor ya wani Zama dolo yaji abinda Bai taba ji ba,kunshe murnarsa yayi har ya dawo gidan King yasan su Jibson suna gidan. Bayan ya fito daga motarsa a tsakiyar Compound din ya tsaya ya Buda hannaye sama kamar me Addua ya dage ya saki Ihu,Wai murnar kiss ce Daya kunso abarsa ya adanata sai da ya dawo gida zaiyi abarsa,Su Tawaga suka fito gaba Daya dama Ahmad baya Nan Yana can tare da Aamna gidan Amma. Tawaga yace Kai dalla Mene Haka ka tsorata mu, Mashkoor ya dinga kyalkyala Dariya shi kadai Yana tangal tangal a tsakar gida kamar ya Sha kwaya,Jibson yace Kai wlh dakiki ne,Bash da Brown suna ta dariya suna tambaya lafiya, Mashkoor yace Kutmar idan ba Nafeesat ba na mutu kawai,ku matsa nan,Brown yace na Nafeesat ikon Allah,ai da sauri Mashkoor ya zaro dari biyar a aljihunsa yace ungo karbi na baka,Brown ya karbe kuwa,Tawaga ya tabe Baki yace kaima ka Zama King suna ta Masa dariya. Bangaren Ahmad Kuwa sai da suka Dan Jima suna Hira sannan yace da Aamna ta tashi su tafi,Amma ta bawa Aamna Magungunan Mata iri iri da yawa a Leda ko wanne da yanda ake amfani da shi a jiki,Ko da suka fito Ahmad ba yanda baiyi ba Aamna ta nuna Masa me aka Bata Taki yarda shi Kuma baiyi rayuwa da Mata ba Sam bare ya gano,shi da Abokansa maza yayi rayuwa ko Yan Uwansa Bai zauna da su ba bare ya San Kan abin,Aamna dai duk fitsara an ajiyeta gefe ta koma salihar Dole sabo da yanda Ahmad ya wani canja Mata ba irin a baya ba yanda yake cusa Kansa gareta tana Masa abinda taga Dama. Hanyar gidansu taga ya dauka sabo da lallabashi takeyi tana tsoron sa Tace Ni yau a gidanka Zan kwana,yace gobe Kuma fa? Tace sai na koma gida,a ransa yace Yarinyar Nan tana Raina min hankali Ina Aurenta baza ta dawo ba Wai ma Sai Mummy ta zo, Dole na gyara ta,Bai magana ba sai gani tayi ya ajiyeta a gidan Baba Kuma baya nuna bacin ransa ko kadan hakan da yake Yi gasa ta yake Yi gaba Daya Bata Jin Dadi Amma a hakan ma ta gode tunda ya hakura,Yana yin parking ya zuge handbag dinta tare da zuba Mata kudade a ciki yace Goodnight Kawai,tasan da Dane sai yayi hugging nata sunyi kiss,Idonta ne ya ciko da kwalla ta shanye abarta ta fita Kawai ta tafi ciki. Ko da ya taho Hanya masifa yayi ta Yi shi kadai yace yarinya karama ta dinga buga min Kai Dan Iskanci Mummy ce ke Aurenta ko ni,na Dade Ina Binta ta dawo Ina ta lallabata,kitsonsa ya shafa yace an fada Mata Ni katako ne ko dutse,kullum Hakuri nakeyi Ina danne sha'awata sabo da ta Gane ita nake so ba jikinta ba Amma Sam Taki fahimta,Tsaki Yaja duk cikin matsananciyar sha'awa yake,zafin sha'awa yasa yace idan na mutu ai ta huta,da nasan a lahira Zan Dace na shiga Aljanna da nace na mutu ma ta huta gaba daya,aikin banza yarinya sai jarabar yanga take min,Ina magana ta Kama min kuka,Wai Ni karfe ne Bata dubawa, Maganar Aamna ya gwada yanda take makale Murya Wai a gidanka Zan kwana yau,sai kace idan ta kwana wani abin zata bani,maybe ma dakinta zata kwana ta barni,Kwafa Yaja yace duk Randa na samu yanci Zaki Gane shayi ruwana, bazan tausaya Mata ba ko kadan saina huce takaicina pieces Zan mata,sabo da rowar masifa ko Nonon din ma Bata Bari naji kamshinsa ma bare na taba,Idan nayi zuciya na Saniya zanje na cakuma kowa ya huta,a fili yace to idan Saniyar ta Haihu fa? Ya ba Kansa amsa da sai nayi fatali da Dan nata Ni na Maye gurbi,Dariya yayiwa Kansa yace Kai lallai na zare da yawa. Ko da ya Shiga ya Iske su Mashkoor suna ta kallo abinsu yanzu an daina shaye shaye saura kadan,da Tsaki ya shugo ya zauna shima tare da nutsewa a cikin kujera Yana ta Jan kwafa Yana karkada kafa,Jibson ne ya dinga dariya Yana kallon Ahmad,har Ahmad ya gaji da dariyar da yake Masa ya Shiga dura Masa ashar,Tawaga ma ya gano sabo da kafin ya tafi sai da ya Gama zumudinsa sun San Kuma a matse yake Kawai dai bazai fada ba ne sabo da su sun San junansu sosai,ko baka fada ba suna ganewa,Jibson yace wallahi tun kafin cuta ta Kamaka kaje ka dakkota ko Bata so,King Ku fa Baku San Mata ba,Ni Kuwa kaga nayi Muamula da su,gashi Ina da kanne da yawa,King yace Can you Imagine Tace sai Mummy tazo zata dawo,kalle Ni Dan Allah Yarinyar Nan fa hallakani take so tayi Wai har Nan da 3days,nufinta in tsaya Ina jiranta? Tawaga ya dinga dariya harda buga kafa,yace to da ba'a maka auren ba fa? Da sauri Ahmad yace fine dama ban sa Rai ba,Amma wannan matar tawa One in town sannan Ina tsananin sonta,Nifa ko kwalla tayi a cikin zuciyata nake Jin hawayen Yana zuba da sharara,Brown yayi tafi Yana dariya yace Allah ya Biya lover boy, Ahmad yaci gaba da cewa Wai yau anan zata kwana,nace gobe fa Wai tafiya zata Yi sai Mummy ta dawo,Ni Kuwa naji haushi na ajiyeta a gida Wai Kuma ta fara min kuka,da kyar fa na danne zuciyata na kyaleta har zuciyata ta karye na danne. Jibson Yana dariya yace wlh baka San Mata bane shi yasa kake ganin laifi ta maka,da ta hanaka kunya ce fa ta sa,kana Dan lallabata zata bada Kai,Kai banza ne da ace ka taho da ita yau da ka Shana ka cuci kanka. Ahmad zagin Jibson yayi yace da can kasan wannan baza ka fada min ba,naje can zata kalleni a gara ma Ashe,Zumbur ya Mike yace Bari naje na taho da ita ko na samu salama idan ma ta hanani babban Gwaskan a bani kaninsa,Tawaga yace Kwarton banza,dama Ina so Zan fada maka wasu suna bukatar tallafi wallahi yarinya ce suke Neman tallafin kudin Waec ka biya Mata ka samu lada,Wacce Yarinya Kuma? Tawaga yace wata ce Wai sunanta Yar China,Ka Bari Nima naje a bani Nawa taffin tukun,Ni yanzu bana hayyaci na,kuje da Mashkoor ya Bata Ni na Masa transfer idan na samu nutsuwa,Yana magana ya fita Yaja motarsa,lokacin Aamna Kuwa Sallar Isha tayi ta kwanta tana tunanin mijinta,sonsa da sha'awarsa sun addabeta,Hawaye ne ya gangaro Mata ita ya daina sonta irin da,Sam yanzu baya ji da ita tasan ma Bai hakura ba da laifin da ta Masa,Sallamarsa taji a gidan,mamaki da farin ciki ya kamata. Baba rada yayiwa Mama yace munfa Shiga Uku da naci,gobe Zan Kori Aamna ta koma can. Aamna tashi tayi tazo bakin kofarta Dan ta tabbatar,Dan ta sake birgeshi sai tayi sauri ta fada toilet Wai wanka zata sake Yi,Ahmad Kuma Yana zuwa yace Mantuwa nayi dazu Zan karba na tafi,Baba ya Gane Sarai yace ae ai da gani Babbar mantuwa ce idan ba Abu me muhimmanci ba yaushe za a tafi yanzu a dawo Suka tashi shi da Mama sukayi dakinsu,Har ga Allah Aamna kuwa Mummy ce ta hanata komawa gidan Ahmad,Tace lallai ta Bari sai ta zo. Masoyana Ina Alfahari da ku wallah masamman masu sharhi . AsmaBaffa 10/26/21, 8:54 AM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 76-80 Official By AsmaBaffa Page naku ne MRS MUKHTAR PHATMAH UMMY MANGA MUMMY SANI LEEMAT Ahmad bedroom dinta ya shiga ya Iske Bata ciki,karar ruwa yaji,Zama yayi Yana jiranta Bata Dade ba ta fito daure da guntun towel na Jan hankali,Ahmad ya bita da kallo,murmushi tayi Tace ya na ganka? Ido ya lumshe yace ba kince a can gidana Zaki kwana ba? Aamna taji Dadi Tace ae Amma ji nake baka so,wayo ya Mata ya Furta Ni Nace Miki bana so ai ban Baki amsa ba ai nufi na zanje na dawo na daukeki Baki fahimci yaren Nawa ba?,Aamna Tace ohh, a ranta taji haushin kanta da ta dinga tunanin Iska,ganin tana da Kaya a gidansa Kawai cewa yayi da rigar bacci ki saka wannan Hijab din mu tafi,Aamna ta saka Rigar baccin me Dan tsayi Arsh Hijab kato har kasa ta saka, Wayarta ta dauka,Tace sai dai fa mu lallaba Kar su Baba su ganni akwai kunya. Lekowa yayi yaga ba kowa key din motar ya Mika Mata yace sauri kije ki Shiga gani Nan,Karba tayi ta fice a hankali,zata fita kenan Baba yace keee....ina Zaki? Juyowa tayi taga Baba ya fito daga daki yace Ina kallonki munafukai,Ahmad Yana boye Dariyarsa ya fito yace gidana zamuje zata gyara shi yayi kazanta da yawa,Baba ya Gane karya yace da Daren Nan bakwa tsoron aljanu?Ahmad yace ko Daya ai Ina da kyakyawar alaka da su,Sannu Bokan Kan dutse dan Allah ku tafi ku bani waje na rufe gidana,Kai kullum baka da gaskiya,bayan satar min radio da Startime da kayi Bai isheka ba,wallahi sai ka biyani radio ta,Ahmad Yana dariya ya fice abinsa. Gate ta Bude a hankali ta fita tare da Bude Kofar motar ta shige,Sai daga baya shima ya fito ya tuka Suka wuce,Yana Driving ya Kira Jibson yace Kun tafi?Jibson tsokanarsa yayi yace Muna Nan,King ya furta to ku bar min gida tare da kashe wayarsa,a gidan yayi parking ya Iske ba kowa ,da Kansa ya fita tare da Bude Mata harda rike Hannunta ta fito Yana cewa takawarki lafiya Gimbiyata,a ranta Tace me zai Hana tunda za a min wayo, tunawa yayi Bai siyo musu komai na ci ba,Wayarsa ya dauka ya Kira Brown ya lissafa Masa kayan makulashen da zai kawo Masa,Hips din Aamna ya tallafo suka Shiga ciki har Bedroom dinsa Yana cewa Kaya...kaya Yana shafa mazaunanta sai kace Dan iska,Bedroom dinsa suka wuce,zaunar da ita yayi Yace zauna nayi wanka,Toilet ya Shiga kafin ya fito Brown ya Danna Door bell,Aamna ce ta Bude tare da karbar ledojin shi Kuma ya juya ya tafi abinsa Yana cewa Asuba ta gari Aunty Balaraba. Yana goge jikinsa ya tafi ruwa Yana Dan digowa ta saman tsinin hancinsa, Kallonsa take faman yayi sabo da kyawunsa da Kyawun surarsa,Murmushi ya sakar mata tare da jefar da guntun towel din Dake hannunsa ya nufo inda take,Aamna tun kafin ya karaso Tace amma ba abin zamuyi ba yau ko? Haramun ne?Tace no Mummy ce tace akwai abinda ta shirya sai tazo yace Wai Mummy ke aurenki ko Ni? Amma ai itace Sila,ganin ta shagwabe yace Alright amma kin San idan ta zo ba mutunci ko? Dariya tayi Tace ae na yarda,ya ja kwafa yace Allah ya kawota lafiya wallahi sai na sissikeki tas ,Ledar da aka kawo ta jawo tare da budewa taga su nama da sauransu,Ci ta fara Yi Kawai tana cewa kaje ka shirya,yace ai na Gama shirin,a Haka daure da towel? ae ya furta kawai,mikewa tayi ta dakko Masa Boxers cikin kayansa Tace sa wannan,sai dai ki saka min ya furta tare da mikewa tsaye,a kasa ta duka Tace to saka,Kamar ya yaro harda dafa kanta sannan ya zura kafa daya,Dayar ma ya saka ta ja sama ta saka Masa sosai ta kasan towel din,sai data saka Masa sannan ta cire Towel din ta maida su Toilet. Zama sukayi suka ci Suka Sha sannan Suka Yi brush suka fito,kulle ko Ina yayi tare da kashe musu light,a gabanta ya ya tsaya harda daga hannaye sama yayi Mika tare da yun jumping sau biyu Kamar Wanda zai buga kwallon kafa,Yatsunsa ya lankwasa sukayi Kara kas kas yace madalla,Aamna ta kyalkyale da dariya,harda wani lankwasa wuyansa gefe da gefe, Daukanta yayi tare da daura ta saman bed ta zauna daram a tsakiya,ta Bayanta ya koma ya zauna,juyowa Aamna tayi suna facing juna a zaune saman tsakiyar bed,Ahmad a ransa yace ta Ina Zan fara ne? Kallonta yake ta faman Yi yace in fara ta kafa? Kai ya girgiza yace nooo...ai ko wanka ta sama ake farawa,Yace Bari na Mata kamar wankan tsarki na faro ta gashinta sannan tsagin dama sannan tsagin hagu,Nan yace Haka Za'a ayi. Hannunsa ya daura saman gashinta tare da janye Ribbon din nata,gashinta ya watsu a gadon Bayanta, My world kina da gashi,Murmushi tayi tare da matsawa ta kwanta a saman kirjinsa suna shakar kamshin juna,gashin ya shiga shafawa Yana shakar kamshinsa,dagowa tayi tana kallonsa cikin Dan hasken Daya bari Dan kadan wani Blue,Aamna a hankali ta furta I love you,Hannunsa Daya ya sarkafo ta Bayan wuyanta tare da matso da fuskarta gareshi ya shiga kissing nata Yana cewa love you too My world,ko Ina na fuskarta yake bi da kiss Wai irin wankan tsarki zai Mata, Aamna wani Nishi tayi tare da sake matsawo jikinsa sosai jikinsu Yana rawa ya shigar da bakinsa cikin nata Yana tsotsa cike da salo, Wuyanta ya gangaro yana kissing din lips dinta,maida Masa martani takeyi tana sake makale shi. Wata tsuma yakeyi tare da sabule Dan siririn Hannun rigar tata,nonuwanta manya masu laushi da santsi da sheki sune Suka bayyana,sake rudewa yayi hannayensa biyu daura samansu Yana shafasu cike da nutsuwa ba Wani shirme,Irin na wayayyu yake mata,Wani Nishi takeyi me Jan hankali Wanda yake Kara tayar Masa da hankali,Fuskarsa ta tallafe sosai tana ta kissing nasa da sauri da sauri,Dan tsayawa tayi kadan tare da wani lumshe Ido sanadin Nipples dinta Daya Kama Yana murza su a hankali,Muryarsa na rawa yace ya akayi My world? a hankali Tace Dadi nake ta ji....wash....shuuuu....ahhh....takeyi,Yana Wasa da dukiyarta ya maida harshensa samansu Yana lasar mata su Yana tsotsa Yana ohhsh....ba adadi,Ita Kuwa shafa shi takeyi ta ko Ina tana sake mannewa,Rigar ya karasa zare mata,shima ya cire short din nasa,Aamna Yar kunyar ma ta Kare tana gani ya kunna light gal a kansu fuskarta Kawai yake kallo Yana Sarrafata,Cibiyarta ya karasa Yana Mata kiss Yana lasa har zuwa kasanta hannayensa Yana saman Kirjinta Yana matsa mata su,Gaba Daya gani yayi ta jike sosai da Niima,Kwantar da ita yayi a hankali tana lumshe Ido,Yana Dora harshensa a pussy dinta ta ja Ajiyar zuciys,wow ya furta gani Niimar Aamna tana zubowa,bakinsa yasa Yana Mata wani irin Wasa Aamna ta dinga ihun dadi,Bata ma San tana cewa aci gaba ba,Yana Kara kaimi,ka rike Ni Zan mutu.....cewar Aamna,Cinyoyinta ya rike Kam tare da sake bargaje su,Aamna tana ta faman ihu jikinta Yana wani rawa,Sai da ya tabbatar taji dadinta sannan ya fara shafa Mata hq din da hannunsa a hankali,Jikin ta Kamar an jona mata Wutar lantarki Haka yake rawa, Yatsansa ya sa Mata a bakinta tana tsotsa tana nishinta Uhmmm....tana ci gaba...Yatsansa ya gwada Dan sa Mata a cikin hq din yaji a matse wajen cik,Wai a hakan ma duk ta Bude,a hankali yake Mata da yatsa Yana Dan turawa Yana zarewa har ya Dan shige,Aamna tayi zullo tare da daga Kai sama ta kalli saman pop, Idonta Yana Rufewa Yana budewa,Haka Baby?ya tambaya Tace Yes....yes....ci gaba Dan Allah....Ahmad a ransa yace na dauki hakkin Yarinyar Nan Ashe tana so Allah sarki My world, jikin katifar take bugawa da Hannunta tana kukan Dadi....ashhhj....Uhmmm.....shima Kansa Wanda ke matan Dadi yake ji a jikinsa,Idonsa ya canja,sai yabonta yakeyi Yana nishi. Da kyar Aamna ta iya cewa ka sake shanye min ruwan Baby... Really? Ya tambaya da sauri Tace yes ka cinye min shi please...,Komawa yayi tare da gyara Mata kwanciya,yatsansa ya sake shigarwa cikin pussy dinta tare da sa harshensa a clit dinta Yana karkada Mata Yana Wasa da shi,Ihu takeyi Wanda yafi na Baya tana shafa Kansa shi Kuwa ya sake dagewa ba sanya,Rudewa Aamna tayi ta saki wani gurnani Kawai sai ruwa ya shiga fesowa faaaaa.....kamar an Balle tap,jikinta na tsuma tana Oh...My...God Baby....fuskar Ahmad ta wanke fess shi kuma harda Bude Baki Yana ta Shiga suna faman ihunsu,Sai da ta Gama fitarwa jikinta ya saki,Wani nishadi da farin ciki ya lullubeta,Kunya ta kamata tana tuna abinda tayi,Ahmad yace Ni ya Zaki min Haka Ni wallahi Baki Isa ba,Haka nace ki kawo?Taya Zaki min haka? banyi Niyyar kyaleki ba yau Kawai sai ki kawo. Ahmad shi Baiyi maintaining ba ya dinga mata dan ganin tana Jin dadi,sai da ta gamsu kuma a zahiri yau bazai kyaleta ba wayo yayi Niyyar Yi Mata ya samu abinda yake so,Dariya ta dingayi Tace taho kaima na maka. Baki ya turo yace Ni baza ki fada min ba sai Kawai ki Tara abu haka,Dariya ce ta kamashi Kuma shi wallahi Bai San a gaske Mata na Haka ba tunaninsa Kawai karyar su Jibson ne,a fili yace idan Kuwa Haka ne kullum na samu abin kallo,sai nayi ta Mata Ina gani,ya kalleta yace ahhh Ashe kema Haka kike to idan Haka ne wallahi sai na Kara Miki Sadaki,sadakin aurenki yayi kadan Ina Sam Dole nayi wani Abu a Kai, Aamna ta dinga dariya. Yana cikin jarabarsa Aamna ta Rungume shi ta baya gashi ba komai a jikinsu,wani Niima yaji,Nonuwanta ta Shiga goga masa tana laiyasu a jikinsa,Layi ya fara saki....Yana Nishi Yana furta kalamai masu nauyi, tana goga masa Boobs dinta suna tsotsar bakin juna da sauri yakeyi kamar zai cinyeta,Aamna ta kalle shi Tace Gwaskar taka Mike jira take,Bai iya magana ba, Gwaskar tasa ta Kama da Hannunta tana Wasa da ita tare da karkada ta,shi Kansa shima Niima Fitowa takeyi,yanda zaiji Dadi take Masa kafin ta shigar da ita bakinta tana tsotsa,Hankalinsa ne ya gushe yana Furta Yeah...Fuck me....Fuck me.....Dadi...ahhhshh....Gaba Daya Aamna ta shigar da ita bakinta tana Shiga tana fitar da ita a hankali Kamar a cikin down dinta Yana Sex Haka yake ji,Ya dinga gurnani Yana maida Mata gashinta baya Yana Kuma Dan sake Danna kanta Yana dagawa,babu wani dogon lokaci Ya kawo Aamna sai ji tayi ya rike kanta da karfi ya kankame kanta sosai ya gigice sai da ya Gama fitarwa sannan ta janye tare da fadawa Kansa ya rungumeta suna kissing din juna a hankali a hankali tare da maida numfashi. Siyama a zaune take a dakinta tayi tagumi tana tunani,a fili tace Wai Ni Faisal zai gani a hanya ya shareni kamar Bai ganni ba sabo da ya siyi mota ko me? tunani ta sakeyi Tace ga dan aikin da nakeyi a Resturant ya Kare matar ta daina ta ma siyar da Resturant din wani ya rushe ya fara gini,ga talauci Ina fama,da ace muna tare da Aamna nasan bani da matsalar kudi Amma yanzu nasan baza ta kulani ba sam,yanzu ya zanyi? Shuru tayi tare da sake kwanciya a katifarta tayi lambo kamar wacce tayi bacci Amma a zahiri ba bacci takeyi ba,ita kadai Tace to ko wainar flour Zan koma yiwa Yan primary Ina bawa Almajiri yana siyar min ko Yar dari da Kobo na samu,Haka za ayi motsi yafi labewa,Nan take ta Mike ta dakko wata tsohuwar dubu dayanta wacce sai da ta sake liketa da gum sannan ta fita kanti tare da auno Flour da kayan aiki,Amma da Yar kadan zata fara Nan gaba idan ta samu riba sai ta Kara jarinta. Bangaren Baba Kuwa Shuru sukaji Aamna Bata dawo ba,dakinta Suka duba Aamna ba ita ba alamarta Basu ce komai ba tunda sun San Ina ta tafi,Mama tace uhm Dadi Miji an tafi,ta birgeni Haka ake son Mata wayayyu ba irinki ba,Mama tace to ka godewa Allah da ya kawo baban Ahmad gashi mun washe da baka taho birni ba da yanzu Muna can,Baba yace gashi mun Raba Hanya da tuwo sai dai da marmari Amma a can kullum sai mutum ya narki tuwo kana tashi da safe sai toilet,Kema da yanzu kina can kina aikin wahala damatsanki duk sun murde sun dawo na maza,ayi magana kice mace ce kema,kawo min fura ta da fatan dai ta dauki Raba a cikin fris (fridge)? Mama tace to baka iya ba Frich(fridge) ake cewa,tunda kin gane me nake nufi ai ba komai,ki hado min da lemon Nan na gwangawani Ina so In Sha inji bakina Kamar kiyashi ne a ciki Yana min mutsu mutsu,Mama ta tafi yace da ragowar Dambun Naman nan. Mama ce ta kawo duk abinda Baba ya bukata ta ajiyewa tace Dambun nama ya Kare sai ragowar Naman Nan na Aamna da tazo da shi na Rasturat(Resturant) Baba Yana dariya yace to ba Haka bane restoras ake cewa,Naman ya gutsira ya ajiye tare da cewa dauke wannan laushinsa yayi yawa daga ji Naman jaririyar akuya ce,kin San idan aka yanka akuya ko tinkiya me ciki jaririn cikin masu restoras ne suke zuwa su siyo a Araha su dafa,Mama Tace shi yasa zaka ji namansu laushin yayi yawa har yauki yauki,Af jaririn akuya ne cewar Baba,Yana Shan furarsa yace Dan Allah Aishatu ki dauki ciki Mana ace 'ya daya tal,me yasa ne ke Sam Baki da karsashi? to Wai Ni Zan bawa kaina cikin ne? Kuma da tsufa na Zan haihu baka ga na Daina Jinin Haila ba tun shekaru Uku da Suka wuce,Baba kunnensa ya karkade da Hannu yace me nake ji haka? Kin daina me? jini ta bashi amsa,au yanzu da gaske kin daina? ai na zaci karya kikeyi,Amma na zauna ban fara Neman bazawara ba,Mama Tace wallahi baka Isa ka min kishiya ba,Kiyi Hakuri tunda Kinga ke kinyi Kwandam(condem) alamun tsufa sun Gama bayyana a jikinki,ki Bari ko Aiki ta dinga tayaki bibiyu tafi Dadi Aishatu,Zan dinga siyo Miki Omo da yawa da Ashana da sauran kayan aiki kiyi ta barnarki,Har Flask din shayi Zan siya miki,Mama Tace bana so ta Mike tayi tafiyarta tana Fushi, Baba yace ai wlh sai na Kara aure dama akwai Kanwar abokina a kasuwarmu Aurenta ya mutu kwana Nan zanje na Shiga cikin Yan takara. Washe gari Tawaga tare da Mashkoor Suka tafi gidan Yar China da Yamma,ta fito zata tafi Islamiyya ta gansu,ta Gane Tawaga Yana ta waya ya juya baya, Mashkoor ta kalla tana daga jikin Kofar su,Ido Suka hada kayanta sunsha wanki da guga Tace hum...hum....ganin Bai kulata ba ta saci kallon Tawaga taga waya ma yakeyi tafi tayi ta farrrrr da Ido ta jujjuya Idonta Tace Nan gani na bari ehe,Dariya ta Bawa Mashkoor yanda take ta tsokana,bakinta ta tamke tare da Murguda Habarta ta sake yin tafi tare da Furta chas...chas...chachas.....Tawaga Yana juyowa yaga Abinda take yi,Shareta yayi Suka nufi Kofar Shiga yar China ta tare hanyar shigar tasa Hannu biyu tare da tala kafafunta,Tawaga tafiyar ruwa yayi da ita Suka Shiga,ita Kuwa Bata da karfi ta Fadi,da sauri ta tashi ta ruga gidan da gudu,wani kwano a Gaban Iyalle ta dauke tayi cikin daki da abinta,Ita Yar China yau shinkafa da Miya aka kawo musu a makwafta har da yankan Namanta biyu shine take tsoro Kar Iyalle tayiwa su Tawaga tayin abincinta Wanda take cancanawa sai dare zata ci abinta. Tawaga Yana shiga Iyalle ta dinga Masa Sannu da zuwa harda shimfida musu sabuwar Tabarma,Bayan sun gaisa yace Iya Nawa ne kudin Waec din Yarinyar can? Iyalle Tace dubu goma Sha Tara kasan wani makwafcinmu ne ya sakata a makarantar kudi Kuma daf da zasu fita Allah ya Masa Rasuwa,Nan take Tawaga ya irga kudin ya Basu tare da karawa Iyalle dubu biyar na cefane,Yar China ta fito tana tafi harda yin Enter....Enter a tsakar Gidan sabo da Murna Tace Iyalle na fasa zuwa Islamiyyar yau murna Zan tayi,Su dai su Tawaga tafiya sukayi abinsu,Iyalle sai murna da godiya,Yar china da sauri ta fito ta Iske har zasu shiga motarsu da karfi Tace mun gode Allah Kara arziki gobe ka siyo min Icecream na Dade ban Sha ba tun Watarana da naje gidan kawata babanta me kudi ne shine Yayanta ya siyo mana,Kuma daga Shan Icecream dinsa yace Yana Sona Wai na aure shiii......Yar China ta fashe da Kuka tana wallahi bazan yafe masa ba kamata yarinya a min aure, Mashkoor Yana ta dariya a boye yace wannan yarinya ce ta gaske,gata kamar Yar fari,Tawaga yace Dan Allah muje wanda zai so wannan ai yayi asara. Bash ne ya nemi Brown Suka tafi wajen Bazawarar da Suka samowa Baban Jibson,wata Dattijuwa ce kyakyawa amma juya ce Bata taba Haihuwa ba,tayi aure sau Uku gata Yar gayu sabo da ma'aikaciya ce tana Aiki a ministry of education,Wani Abokin Bash shine Dan Uwan matar Safiyya,Bash,Brown,Tawaga da Mashkoor har gidan su Jibson suka Iske Baban Jibson Yana Zaune a Kofar gidansa yayi zuruu da Alama tunani yakeyi,Sallama Suka Masa tare da zama,da fara'a yace Ina zakuje Haka ne? abokiin naku ya fita yanzu,Bash yace Baba ai wajenka muka zo,Baba Zama ya gyara,Tawaga yace dama wata Bazawara ce me hankali Muka ga ya Dace kaje ka ganta in tayi ka aure ta,komai zamuyi na auren ko sisi baza ma ka kashe ba,Brown yace Zaka so ta Wlh Abba,baka ganta ba suna Kama da Ummati ma,Sannan gata juya,duk wani Qualities na aure tana da su,Abba yayi Dariya yace kuka Ce bazan sake aure ba? Brown yace ai Abba munce sai dai juya Kuma mun samo maka,Abba dai da kunyar yaransa Yana wayancewa yace to ayi Haka Kuwa? Dariya Suka kunshe Suka ce Abba hakan ma za ayi,Kuma Yar Boko ce ma'aikaciyar Gomnati ,Abba yaji Dadi a ransa,a fili yace dama irinta nake Nema wacce baza tazo ta Dora min nauyinta gaba Daya ba,wannan Kuwa sai dai ta rage min nauyi,Brown yace Abba gata Yar gayu,Abba yace irin dai Ummati ce Kawai kuce? Suka ce ae,Abba harda kuri yace a jini nane,ai Ni duk matar da Zan Nema to zaka ganta haka Haka Allah yayi Ni da samun me kyau da gayu,har so nake nayi mace mummuna amma Ina Sam Allah baya bani,Dariya Suka dinga Yi, Tawaga ya Mika Masa takarda da address din gidan da komai,Yace Abba mun Gama komai Kawai zuwa zakayi ta ganka. Bash ya Mika Masa Leda Viva dauke da sababbin kaya Shadda taji dinki kala biyu da takalmi da hula dai dai shi,sabo da telan Abban ne ya dinka Masa, Envelope Suka Mika Masa Abba ga kudin zancenta,Kai kaniyarku Abba ya Furta yace ku tashi ku tafi tunda Kun bani Address Ina ruwanku sauran yaki ya rage Nawa,Ajiyewa sukayi Suka tafi suna Dariya,Abba Yana ta musu masifa,Yana so Yana boyewa sabo da kunya. Bangaren Jibson Kuwa soyayya ce suke ta zubawa da Sameera Abu kamar Wasa Yana ganin bazai so ta ba sai gashi Bai ma San Sanda ya fada sonta ba,ko yaushe cikin waya da chat suke. Aamna kwance take a jikinsa sai da suka huta sosai sannan ya dauketa suka Yi wanka tare da tsarkake jikinsu, bedsheet ta canja tare da gyara dakin Yana kamshi,Abin makulashe ya shiga Bata a baki Suka sake ci,sannan Suka kwanta,Cikin Bargo Suka Shiga tana kwance a jikinsa suna Hira cike da so,Gemunsa take shafawa tana Masa magana cikin wani kisisina,dake Basu kashe light ba tana Maganar Yana kallonta hannunsa Yana saman Nonuwanta Yana shafawa,yace fada min sau Nawa kika Yi kuka Sanda Muka Yi fada? Murmushin da tasan Yana Mata kyau tayi cike da shagwaba Tace bazan fada ba,Dariya yayi yace to Ni kullum sai nayi kuka,Tace ban yarda ba abinda ka manta Dani kaci gaba da harkarka,kumatunta ya taba da yatsa Yana gyara kwanciyarta a jikinsa tare da sake shigar da ita jikinsa,yace to kece kin fiye taurin Kai bakya Jin Magana My World,yatsunta ta sarkafo da nata Tace ai na daina Amma ai Kaine da saurin Fushi ka sa Yan hassada suna ta min Dariya. Wata kawar mu Hauwa'u harda kirana a waya Wai taji ance ka sakeni Ina gida tana min jaje,Ahmad yace kaji Munafuka ko,Dariya Aamna tayi Tace Kuma tace Kar na dawo gidanka sai na baka wahala tunda baka da mutunci,Inji ita Hauwa din? Kamar ya santa Haka ya tambaya,Aamna ta daga Kai Wai ae,yace to Allah yasa Watarana tayi gangancin zuwa gidan Nan,Aamna Tace Kuma Tace dama da ganinka ba mutunci zaka Yi ba,ke Kuma kika kyaleta ta zagar Miki Miji maimakon naji an Kamaki a police station kin yanke ta da wuka na tafi Bailing naki shine kika kyaleta? Aamna Tace ai munyi fada na zazzage ta,a banza ai tunda a iya zagi kika tsaya ke da zanjiki a police station kin Mata barna,Dariya Aamna takeyi,Yace yanzu da gaske baza ki Bari nayi ba sai Mummy tazo? Aamna Tace ae sai na tanadi kayan gashi sabo da Zuhra Tace Sanda tayi na farko Kamar anyi Accident a wajen Haka taji,a kunne ya rada Mata please ki bani Nima nayi Hatsarin a ciki,Kafada ta makale yace Ni fa yau ba Wani Mummy da Zan jira gaskiya ya Furta tare da gyara musu bargon ya Haye saman Aamna tana ta Ihu da dariya a ciki tana so ta ture shi Amma ta kasa shima dariyar yakeyi kasa kasa suna wutsil wutsil a bargo. Ina godiya masu sharhi AsmaBaffa 10/26/21, 8:55 AM - A Maryam: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 81-85 Official By AsmaBaffa Page naku ne Maman Murtala Maryam Hafsee Cikin bargonsu suke Wasa da dariya,a Haka barawon ya sace su ba tare da sun shirya ba,da asubar fari ya farka ,Ahmad an shiryu harda Adduar tashi daga bacci tunda yaji Malam yayi wa'azi akan adduoi,Aamna ya kalla wacce ke sharar baccinta gaba Daya Rabin jikinta Yana jikinsa,Kallo ya Kare Mata tare da murmusawa ya sake rungumeta tsam yace kamar Kar na tashi,Hancinta ya taba a hankali ya Furta ji Hanci Dan Allah,a hankali ya tashi ya bar saman bed din zuwa toilet,Brush ya fara Yi sannan yayi Alwala ya fito tare da saka Jallabiyya harda fesa turare ya dauki carbinsa fari Kalar rigar yazo tashin Aamna,Harshensa ya saka cikin kunnenta,tayi motsi kadan,sake hura Mata Iska yayi a ciki Wanda ba shiri ta Bude idonta a hankali, ganinsa tayi da Alama masallaci zai tafi taji Dadi a ranta gaskiya ya shiryu sosai ma,Kije kiyi Alwala da Sallah Yana fadin Haka ya fita abinsa,Aamna ta dinga mamaki tare da godewa Allah itama ta shiga toilet tare da Yin brush da Alwala. Raka'atanil fijr ta Gabatar tare da Sallar Asuba ta zauna tana Azkhar ya shigo,ta ganshi dauke da glass cup Guda biyu a hannunsa,Warm water ne Wanda ya zuba Zuma lafiyayya cokali biyu,Aamna ya mikawa shi ma ya shanye nasa,yace ki Sha Yana Kara lafiya sosai matuka,Indai mutum zai jure da Asuba ya fara Shan ruwa me dumi da Zuma ciki to Kuwa Yana maganin cututtuka iri iri,Aamna ta shanye itama Tace to ai gwara daka fada min,a gefen bed ya zauna Yana Jan carbi,Aamna Tace wannan kitson calabar naka baza a canja bane? Yana maka kyau sosai Amma a canja min style Mana,Murmushi yayi yace Ni Zaki yiwa wayo Wai na canja Miki Kinga sai nace Wato sabo da ke Zan canja,to Baki Isa ba sai end of this year Zan canja style gaba Daya,duk sati ake canja min calaba sabuwa,mu duk shekara ki tambayi abokaina duk shekara muke canja gyaran gashi,ko wacce shekara da salon tsarin askin da kowa ke zaba ya canja,sai dai muyi ta sabunta shi duk week har karshen shekara,Aamna tace Wato Ni ban Isa a min abu ba,Ahmad yace ae Haka Kawai ki rainani ke ki koma Mijin ni matar,idan time yayi Zan sake zamu je ki zabi Wanda ya Miki sai nayi Miki Wanda kike so Amma Indai kika zabi bana yan gayu ba kin San bazanyi ba,Haka Kawai baza ki maidani tsoho ba,Dariya Aamna tayi Tace Allah ya kaimu. Ki Gama bacci nake ji ni,Addua ta Gama sannan Suka sake kwanciya bacci. Sai wurin 10am Aamna ta farka tashi tayi ta fito gidan ta kalla taga ba Wani dirty ko Ina fes,gidan ta fara gyarawa tana babu Bata lokaci ta gyara duk inda Musa Bai shiga,dakinsa ma Bed ne Kawai bata gyara ba kasancewar bacci yakeyi,Kitchen ta shiga ta soya dankali da kwai,Naman jiya da suka rage tayi warming nasa ta shirya komai a dining sannan ta koma Bedroom dinta a can tayi wanka ta shirya cikin wani Bumshort pink me aljijuna ko Ina,Yar Riga me gajeren hannu ta saka wata fara me adon pink,gashinta ta gyara sosai Yana sheki da kamshi ta Kama da Ribbom pink and white,jelar gashin tana Lilo a Bayanta me tsayi,Pcap ta saka kace wata baturiya ce,Wayarta ta dauka ta fara yiwa kanta Selfie kenan ya shigo sanye cikin wata jallabiyar ta daban silver color ta tsangale itama,Takalminsa flat shima silver,Yana ta walwali yayi wani kyau na musamman,Mata da pic basa gajiya ya Furta tare da zuwa ya rungumeta ta baya ya leko da Kansa ta saman kafadarta ya kwanta yace ayi dani Nima,Dariya sukeyi tana ta dauka kala kala suna canja style,Sai da suka Gama yace ki saka security fa Kar wani ya karbi wayarki ya kalle min ke a haka Zan Iya sheke mutum ba ruwana, Daukanta yayi Suka wuce Dining Yana yabon kwalliyarta. Serving nasu tayi a plate Daya komai a Abu daya spoon ma Daya,suna Hira suna ci Aamna tana ta bashi a Baki,kallonta yakeyi yace dama kin kware wajen iya bada abinci a baki,Amma wajen dadin kin Hana kina jiran Mummy,Dariya tayi tare da furta ae,yace ai Baki hadu ba yarinya,ita Mummy na rasa Hujjarta,Kiran Mummy ne ya shigo Wayar Aamna,Tace ka gani ta Kira,Nutsuwa Aamna tayi tare da dagawa da ladabi Suka gaisa,Mummy tace fatan dai Baki koma ba ko? Aamna ta kalli Ahmad suka Yi murmushi Tace ae Ina gida ma ai bazan koma ba sai kin dawo,yazo yace mu tafi nace Nan da kwana Uku,Mummy Tace yawwa akwai shiryen shiryen da nakeyi ne karki koma sai na zo da kaina Zan kaiki,Aamna Tace Inshaallah... Inshaallah Mummy,ban so yanzu kije nafi so ya Sha wahala zai fi ganin kimarki,Aamna Tace hakan yayi sosai ma,Ahmad Yana ji ya girgiza Kai Yana ta dariya kasa kasa tare da riko Aamna ta dawo saman cinyarsa da rada yace Mummy kin ganmu ma Aamna ta Duke shi a kafada tare da Harararsa da wasa,Mummy taci gaba da cewa gyara Za'a Miki Aamna ki San yanda zakiyi karki koma Muna tafe Inshaallah,Aamna Tace to Mummy bayan Sun Gama Ahmad Yana dariya yace to kafin tazo ma Ni na Miki babban gyaran,da kaina zanyi gyaran,Wato shi yasa kika dinga Raina min hankali,Bayan sun Gama cin abincin tare da shi suka Yi wanke wanken Suka gyara kitchen. Kallo ta kunna Tace Dan Allah Zan kalli wannan Series din na Yan India Ina bibiyarsa bana so ya wuce Ni,Baki ya tabe yace wannan shirmen kike bibiya? Aamna Tace mugun kyau ne da shi guda biyu nake bi yanzu daya Chanel din zasu fara haska Dayan,to yanzu wanne Zaki kalla wanne Zaki Bari? Aamna Tace duka ai bazan Bari ko wanne ya wuce Ni ba,tv sama Zan kunna idan na kalli wannan na minti biyu sai na dawo kasa na kalli wannan shima na minti biyu,Yace to ni Kuma fa na minti Nawa Zaki kalle Ni? Kaima na minti biyu Yace to Bismillah,Yana Zaune a Palo taje ta kunna tv sama Suma sun fara ta zauna ta kalla ta kalla sannan ta sakko kasa da gudu ta zauna ta kalla ta kalla sannan ta juya Kan Ahmad ta kalle shi ta kalle shi ta Mike tayi sama,Dariya ce tayi mugun kamashi yace wallahi bazan yarda 25years Aamna take ba ai ko Yar 14yrs baza tayi wannan ba,Dan hauka daga cewa shi na minti Nawa zata kalle shi sai ta maida shi tv tana kallonsa tana murmushi kamar me kallon Film. Tana minti biyu a sama ta sakko da gudu,yace wallahi idan kika karye kika jawo min asara sai kin sani,mene Haka so kike ki jawo min masifa Zan fara amarci da karyayyar Amarya,Idan kika karye Allah a Haka zanyi ba abinda ya dameni Kuma bazan tausaya Miki ba,Aamna ko a jikinta ita ta film dinta takeyi Kar ya wuce ta,shi Bai taba sanin tana kallo ba Haka,yasan dai farkon kawota gidansa kullum Yana ganinta tana kallo Bai San masifar ta Kai Haka ba,kalla ta sakeyi yaji tayi Kara Tace an caka Masa wuka wayyooo....bawan Allah za a kashe Fairus shike nan tayi tagumi,Tv din ya kashe duf kamar Wanda ke gani yace tunda an kashe shi ai film ya Kare an lalata film an daina kallo,ai sai su sa zuciyar mutum ta buga,Gabansa Aamna ta dawo tana kukan shagwaba tana cewa Dan Allah ka kunna min,yace an kashe Star film ya Kare,Aamna Tace ai ba shine star din ba shi ai Kanin star ne,to ai Nan gaba shine zai dawo star din Kuma an kashe shi kallo ya Kare,Aamna Tace Allah dama Fairus ne zai auri Abhi? Ahmad yace kwarai ai Ni downloading nayi na Gama kalla,ita kanta Abhi din ai gobara ce take tashi a dakinta ta mutu gaba Daya,Aamna ta goge kwallarta Tace Allah sarki Abhi Allah ya tsinewa Wanda yake sa Miki wuta ya kone ki,nasan bazai wuce Arjun mugu ba,Ahmad yace kamar kin Sani shine Kuma guduwa yakeyi da kyar Yan Sanda Suka Kama shi,to Yar Abhi data haifa ya akeyi da ita? Ahmad yace ai Baki sani ba? Arjun ne ya jefata a katon ruwan bautarsu sai ta mutu,Wayyo Amma gunki lakshimi Bata musu Adalci ba,ai sune sunki su Gane gaskiya Allah Daya ne sai Gunki Lakshimi cewar Aamna. Ahmad yace ai duniya sai da ta tsinewa Director din wannan film din. Aamna Tace na daina kallon wannan jakin film din Bari naje na kalli wancan na Aryan,Ahmad ya zaro Ido a ransa yace Ina ruwa,a fili yace ai wannan film din Baki San Wanda ya shirya film din an kamashi ba? Aamna Tace akan me? Yace ke yanzu duk yanda duniya ke zancen Baki sani ba? Aamna Tace me yayi? Yace Ana Nan Zaki gani a Nan gaba yaci mutuncin Musulmai da musulunci yanzu Saudiya tana can tana nemansa zasu kamashi,ta sanar Kuma duk me kaunar musulunci Kar ya sake kallon wannan tashar,Aamna ta zaro Ido Tace mutanen fa basa kaunar mu da gaske,yace ai fa,fasa kallon tayi ta dawo jikinsa ta zauna,Tace Idan sun fara sabo na dinga kalla,a ransa Yace ai wannan haukar kallon bada Ni ba,kizo kina girki kina kallo ki jawo wuta ta tashi ta kone min ke na Shiga Uku Akan kallo,ayi kallo kadan kadan ba na hauka ba. Kwanciya tayi tare da daura kanta saman cinyarsa suna kallon juna tabe tabensa yakeyi a jikinta Kawai har 11:30am,kitchen Suka Shiga tana girki, baya ta juya tana yanka tumatur,ta baya ya rungumeta tare da zura hannayensa ta cikinta ya karbi wukar a Haka yaci gaba da yankawa Kansa Yana saman kafadarta,a Haka suka Gama girkin,da Yamma Kuwa wanka suka dauka zai kaita yawo,yasha wata Shadda milk tana kyalli,Ita Kuma wata English gown ta saka Golden and milk,sunyi kyau,Musa ya hango su sun fito shi kadai ya dinga murmushi Yana tayasu murna Yana kallonsu da Sha'awa,Aamna ya gaisar ta amsa da fara'a,Ahmad yace Musa yanzu na gane me kake nufi lokacin da kake waya da matarka yanzu sai dai muyi kokawar daukan duniyar Nan tare domin Nima Zan mikawa tawa gwanar kyautarta, Oga sai dai kowa ya dauki bangarensa cewar Musa,Dariya Musa ya dinga yi suka shiga motar su,Yana lailaya Kan motar cikin kwarewa Suka fita,Wani wurin huwata suka Shiga me dauke da Swimming pool kala kala,wani bangaren me dauke da pool Ahmad ya biya kudin na daban Wanda daga shi sai Aamna ba Wanda zai leko wajen,special ne na masu Neman privacy,Ba Wanda ya Isa yazo wajen ko ma'aikatan ciki babu me shigowa,Abinda zasu ci yasa aka kawo musu tare da rufe musu wajen ba me shiga. Kayan wankan Daya siyo musu a wani super market ya saka Boxers Kawai,Aamna kuwa wata bra ce da pant na wanka Tace karfa wani ya shigo,yace na fiki kishin jikinki Wifey ki saka abinki,Aamna ta saka Yana ta kallonta Yana Shan lemo tayi kyau sura gata Nan gwanin sha'awa,ga wani uban kida kamar zai fasa maka kunne na wakokin Yan Nja,Kamar karka fito Haka zaka ji,Aamna ita kanta tasan tayi kyau. Shiga yayi cikin ruwan,Aamna Bata iya ruwa ba amma Bata tsoronsa,lallabawa tayi ta shiga dake pool ne kowa zai Iya shiga ma,a hankali take tafiya a ciki tana dariya har ta karaso inda yake,suna facing juna ya rungumeta suna tafiya a haka,Kasa yayi da ita suka taso tana shidewa,Ruwan ta watsa Masa a fuska Tace zaka sa na mutu,Bayansa ta koma ya goyata tasa hannayenta ta wuyansa Yana tafiya da ita sannan Yana nutso da ita suna dagowa sai Dariya sukeyi,Gabansa ta dawo tare da rike hannayensa ta cikin ruwan,Bakinsa ya matsar saitin nata a hankali Suka Rungume juna suna zuba kiss a Haka Suka Yi nutso ya Dannata ta dago da sauri tana shakar numfashi ta Harare shi Yana ta mata dariya ta Shiga watsa Masa ruwan a Fuska tana watsal watsal,bayansa ya juya yace hau,Bayansa ta sake danewa sun Dade a Haka suna wanka kafin ya koma wasa da Albarkatun Kirjinta, sai da suka Dade suna soyewa sannan Suka fito zasu huta,kujerar hutawa ta zauna ta Bayanta ya koma tare da Zama tana a tsakanin kafafuwansa suna cin kayan makulashe suna Hira da wasanni irin na masoya. Abban Brown ne tare da abokinsa a shagon siyar da shaddojinsa yace Yaran Nan fa sun kasa Ni kaji ma an Kai kudin auren Sameera Jibson tuni ya Kai kudi Kuma an karba sabo da ta nace sai shi,Abokin Abba ya dinga dariya,Abba yace yanzu Abinda nake so Zan nuna musu na fisu, jiya ba yau ba,Yarinya Danya sharaf nake so ka samo min Budurwa wacce Bata da gata yanda ko yaya na Dan kashe kudi za a aura min ita,Abokin yace akwai wata kuwa makwaftanmu ce tana Nan duk inda kake neman rashin gata ya Kare a kanta,Bata da Uwa ba Uba a Hannun kakarta ta girma,wahala suke Sha matuka,wannan da wuri za a baka Aurenta Kuma gata fara kyakyawa,Abba yace ai ranar Suit Dina Zan sa Wanda Muka je Abuja da su taro,Abokin yace kaga Kuwa wani saurayi saurayi zaka dawo zata fi yarda,Yar China ake ce Mata sabo da tana Kama da su,Abba yace yau da Yamma zan je kaga dama motata tana wajen wanki sai naje da ita,ka min kwatancen gidan,Kana zuwa gidana kace a nuna maka gidan su Yar China kowa ya santa,Abba yace an Gama. Da Yamma Abba yasha Suit dinsa baka ya Shiga motarsa wacce ta Sha wanki tana kyalli. Bai Sha wahala ba Yana tambaya aka nuna Masa gidan,ya ja motarsa zai karasa gidan Yana cikin mota ya hango wata galleliyar mota a Kofar gidan,Tawaga ya hango da Brown dinsa suna ta fito da Taliya da macaroni da sauran kayan Abinci,ga Budurwar Yar China tana ta murna tana tayasu dauka suna shigarwa ciki,Abba ya dafe kirji yace duk sunbi sun kankane matan duniyan ko Ina da su,gaba Daya sun tare min ko Ina,Abba yace nazo da dubu biyu Zan ba yarinyar nan gashi su kayan abinci suke saukewa kaga baza ta ssurareni ba,a hankali yace zaka ci Ubanka Mubaraq zaka dawo ne gidan ya juya da motarsa ya koma inda ya fito. Sai bayan Magriba Mubaraq ya koma gida ai Kuwa Abba ya rike Hannun Mubarak carab ya murde shi yace Yan Iska Baku da Aiki sai yawon bin Yan Mata,ko Ina Kuna can duk Kun kankane matan duniya ku kadai,a gindinku za a Kare Wai? Ko Ina Kuna can wallahi Allah yasa Naga wata kuje wajen kaga Ni korarka zanyi daga gidana kwanan nan,Brown Bai San Kan zancen ba shi dai ya shiga bawa Abba Hakuri Yana dariya,Sakinsa Abba yayi tare da tallafe Masa keya. Daddy ne zaune a palonsa na Alfarma Yana ta fada kasancewar yasan Aamna da Ahmad sun dade da fara son juna Amma shi yaji Shuru baiji ance tana da ciki ba,Mummy ce tasan komai ita Kuma ba fada Masa takeyi ba,Daddy yace Haka muka Yi mu Sanda Mukayi aure? Sam Ahmad Bai gado Ni ba,Sanda Muna game din first score Dina cikinsa aka samu,second score kika samu Saddeeq sai Humaira Amma shi shuru,Mummy tana Dariya Tace lokaci ne baiyi ba,ka godewa Allah ma da aka samu ya shiryu,wannan tafiyar da Ni za a je can na tambaye shi Ni da shi naji dalilin me yasa matarsa banji ta samu ciki ba. Mummy tace Danka ne dai Ina ruwanka da aurensu zata samu ne very soon,Tsaki ya ja yaci gaba da Shan tea dinsa. Abba ne ya shigo hannunsa rike da bakar leda,Kansa Kuma buhun Omo ne ya shigo da shi tare da direwa a Gaban Mama Yana murmushi yace gashi kiyi ta wanke wanke kumfa tayi ta tashi cikin kwata ba ruwana na daina Miki fada,ga Ashana ma kiyi ta kyastata,Harara Mama ta balla Masa Wai Nan Baki zai toshe Mata sabo da zaiyi aure, kafa Mama tasa tare da yin ball da Omon da Ashanar gaba Daya,Baba Baki ya tabe ya gyara Zama a Palo Yana kallon tv Ana haska wani Indian Film Madhubala,Madhubala ya kalla yace Wohoho wallahi da Zanga wannan zuwa zanyi na durkusa a gabanta na Bata Wayar hannuna kyauta Ni na zauna zero, Dariya ya bawa Mama,dubu Daya ya zaro ya mikata jikin screen din tv yace ungo na Baki Alqur'an,Wani murmushi Yar Indian ta sakeyi Baba yace kin Gama Dani wallahi na Kara Miki dubu,Mama Tace kana abin kunya ko yaro Dan 20yrs bazai yi abinda kakeyi ba,sannan idan ka Bata wata wayarka ai ta fika kudi. Ai ko zata karba ta bawa Almajiri na gode Mata,Dan Kawai naji Dadi a raina Zan Bata ni,Zan Iya Bata jarin shago na gaba Daya,tunda na ganta sau Daya da ita nake kwana nake tashi kullum,Mama ta tabe Baki Tace kaji kunya tsofai tsofai da kai, kawo min abinci na,ki hado min da Madara ko na samu furfurata ta tsaya iya Haka,ko wata rana Allah zai hada Ni da Madhubala ta kyasa Ni itama, Mama Tace sai kaje Madhu din ta baka abincin,Baba ya kalleta yace Ina yo Amarya zata koreki daga gidan nan tunda Baki da hakurin rayuwa,irinku Amarya ke shigowa ta fitar da ku daga gidan miji,ki taka a sannu,ke ba wata macen kirki ba wanzami ya Gama dake,Mama Tace kaji da shi dai tsohon ala gwan gwan. Mashkoor da Jibson duk an Kai kudin aurensu saura da biki ya rage,Siya ma ce a kitchen hayaki ya turnuketa tana ta fifita wuta tana soya Wainar Flour ga Yara sunyi layi suna jira zasu siya Yaran makwafta,Babar Siyama ce Tace Wai Siyama Ni Ina kawarki Aamna ne?naga Bata zuwa gidan Nan,ko waya bakwa Yi,sannan Ni fa ban Gane Miki ba mene dalilinki na korar Faisal? Ko dai fada kuka Yi da Aamnan Taki? Siyama karya ta shirya Tace Mama Aamna tunda ta auri me kudi take wulakantani tana min kallon banza,ko na kulata Bata saurarata Ni Kuma Kawai Naja mutunci na,Babar Siyama tace Allah ya kyauta amma Siyama ban yarda dake ba nasan fa bakin halinki Amma ko Mene Zan Kira Aamna a waya naji,Siyama fuska ta kumbura Tace to ki kirata Mana,dama Siyama Sam Bata yiwa Iyayenta biyayya rashin kunya take musu,Kwafa Kawai Mahaifiyar Tata tayi ta tafi. Ahmad Basu dawo ba sai dare gaba Daya hankalinsa a tashe yake,cikin maitarsa yake ya rasa dalili a baya ba ruwansa da wannan jarabar Amma yanzu tunda ya fara kaunar Aamna yake fama da Jarabar maitarta ya rigada ya tabbatar yau Aamna Bata Isa ya kyaleta ba,Sabo da Haka ma Sai ya tsiri Fushi da ita,Aamna ta kasa Gane Kansa da Suka dawo daga yawon shakatawa,Wanka Aamna tayi ta sa wata yar guntuwar English gown me gajeren Hannu iya cinya ta tsaya Mata,Kayan wankansu ta wanke ta Shanya sannan ta dawo bedroom dinsa dauke da coffee ta Ajiye a gefensa inda yayi wanka Yana sa Kaya,Zama tayi Tace ga Coffee nan,Na koshi ya furta kawai,Tace Wai me ya faru ne Naga muna hanyar dawowa kana ta Fushi ko laifi na maka? Ahmad yace laifin me Zaki min Ni? ya fuske,tashi na maida ki gida Kawai,Aamna Baki Bude Tace lafiya? akan me? Sabo da Ni tayar min da hankali kikeyi Bayan baza ki Bani hakki na ba,na gaji kin San irin halin da nake ciki? Kawai tashi na maida ki gida,Hawaye Aamna ta fara tace to Kuma sai ka fara Fushi da Ni? Ya bazanyi Fushi ba,Wai bakya tausaya min? Maza fa ba irin Mata bane,tashi Kawai mu tafi gidanku,Aamna cike da shagwaba tace to ai ba Fushi zaka Yi Dani ba sai ka fada min abinda kake so,Zan hanaka ne kayi tunda Haka kake so,Fuskarsa ya dauke daga kallonta ya kyalkyale da dariya cikin sirri sannan ya juyo yace idan da gaske kike tashi muyi Sallar Nafeela, Aamna ta Mike tana shagwaba ta tsaya sukayi nafila sannan ya musu Addua,Zaki ci wani Abu? Aamna Tace cikina ya cika fa da za a rage min abincin ciki ma so nakeyi. Alright ya Furta tare da daukan coffee din da yace bazai Sha ba ya shanye duka sannan ya kashe light,Aamna Tace yanzu fa 8pm tun yanzu zamu kwanta ka Bari Mana sai 10pm,Ahmad Yana dariya yace bazan iya jira ba,bafa hanaka zanyi ba Ni ka Bari na kalli film din Nan da na fara kallo jiya,Nima Nawa Film din Zan fara Shiryawa yanzu ya furta tare da cewa My world ya janyo ta tsakiyar Bed,Aamna Kirjinta sai dukan Tara Tara yakeyi,Tace Dan Allah karka min da zafi a hankali,yace ai a hankali zaki dauki darasin ki dage kiji Dadi yanda baza ki Sha wahala ba,ba mutunci Zan Miki ba yau,Aamna ta fashe da kuka,yace ai sai dai ki tsage My World ai yau na Zama nasara tuba babu,jikinsa ya jawota Yana shafa Kirjinta a hankali ya zare Mata rigar ya Shiga kissing dinta ta ko Ina,a kunne ya rada Mata ki daina kukan Nan ki min abinda nake bukata ko azabarki ta karu,Banza ta Masa Taki tayashi Wai Dan kar yaji Dadi,Ya rigada ya Gama Gane inda idan ya taba Mata Dole ta kawo wuta itama,sabo Haka Kissing dinta yakeyi Yana tsotse harshenta tare da karkada Mata nasa Harshen a Kan nata cikin nutsuwa,hakoransu Yana haduwa Dana juna,Hannayensa Yana Wasa da Boobs dinta yanda yake so,Harshensa ya maida cikin kunnenta Yana Wasa da shi ciki,Ido ta lumshe tare da shidewa,jikinsa ta sake shigewa tare da sa Hannu ta cire Masa rigarsa Armless,jikinsa take shafawa zuwa kirjinsa tana Wasa da Dan nipples dinsa, Hankalin King ya sake tashi ya kwantar da ita hannayensa ta riko tare da daura su saman manyan Albarkatun Kirjinta Yana Mata wani Kalar wasa na musamman Wanda ba irin na Jiya bane,yau salon na daban ne,Jikinta yake bi Yana lashewa inda yasan zata ji a jikinta,tun tana Dan Fuskewa har ta Gaza ta fara ihun Dadi tana sambatu, yace My world kina Jin dadin Nan Kuwa? Aamna Tace na karshe ma,sai kace zai Mata massage Haka yake Binta gaba gaba,cinyoyinta ya fara Dan lasa kadan Yana musu kiss,Aamna ta shafa kanta tare da Sosa gashinta duk sabo da abinda takeji,tana Nishi a hankali da wani slow,tana lumshe Ido sai lashe lips dinta takeyi kamar mayya,shima kalaman da yasan zai sake rudata dirty words su yake Furta Mata Kuma babu wani sakayawa Wai wani da turanci da hausa yake fada sabo da yafi shigarta,Itama a Wajensa ta koya tana sakin layi,Yana daura harshensa a pussy nata ta haukace ta fara sambatu da ihu,Tsoro yaji Kar ta kawo irin jiya ganin yanda take tsiyaya duk ta Zama wet sosai,Kasancewar cikin duhu suke yau Bata Gane me zaiyi ba,Sai ji tayi Yana neman shigarta,Tace ka tsaya ba yanzu ba Kai fa banyi Romancing naka ba,yace ai hakan ma Alhmdllh na Gama kaiwa karshe yayi Haka Nan gaba Kya min idan zanyi second round,Aamna zata sake magana yace Allah Miki Albarka Ni hakan ma yayi. Gyara ta yayi sosai Aamna Tace to Ni gaskiya ka Kara min me dadin ban Gama ba,yace you are not Serious My world,gani yayi tana Neman zukewa,ya kamata yana Furta karfi kike so na gwada Miki naga alama? lallashinta ya Shiga yi Bai son Mata dole,Aamna fafur ta dinga cewa ita Bata so,Yasan Bata son ganin bacin ransa kawai sai fara kukan karya. Ka rantse da gaske yake yin kukan,Aamna ta tsorata tace My King Mene Haka? Ko kulata baiyi ba harda yin tagumi ya Kara volume din kukansa harda tari uho..uho...Yana bugar kirjinsa,Aamna kafadarsa ta jijjiga hankali tashe Tace kuka fa kake Yi? Cikin kuka yace ba Dole nayi kuka ba an hanani hakki na,Ni mutuwa zanyi ki huta,Aamna taji ance mutuwa ta tsorata Tace haba Babyna Dan Allah ka daina kukan Nan Wai Mene Haka, Alright I'm sorry na yarda wallahi kayi ko mene,Ahmad da kukansa Yana tari yace Ni na hakura...gwara na mutu kawai.....Haba My King Yi Hakuri gani fa Allah kazo kayi ko Hawaye bazanyi ba,ko naji zafi Zan jure Haba Dan Lelena,Ahmad yace Kawai ki bar abinki Ni Bari na Daura igiya na kashe kaina,Ido Aamna ta zaro,Yaci gaba da barin wasiya wai,yace kudin Dake accnt Dina na bar Miki duka kiyi business,da Motata,Aamna ce ta rufe Masa Baki da nata ta hanyar hade su waje Daya tana tsotsa,Yayi shuruu....taci gaba murza shi tana sarrafa shi tare da Furta I'm sorry my king,Shagwaba ya dinga Yi tana ta biye Masa tana Masa abubuwa masu rikitarwa,kwantar da shi tayi sosai tare da komawa samansa tana murza Masa Boobs dinta manya masu laushi a kirjinsa tare da daura cinyoyinta a tsakankanin cinyoyinsa a hankali cike da salo take murza Gwaskar tasa cewar Aamna, tana kissing din wuyansa,Ahmad tuni ya saki layi jikinsa Yana wani mugun rawa Kamar mazari mussaman yanda yake jin Aamna na tsiyayar da Niima a jikinsa,Birkitota yayi ya maidata kasansa tare da gyara ta yanda zai ji dadin Harkar,Muryarsa da kyar take fita ya nemi hanyar shigarsa. A hankali yake kokarin Shiga Amma Ina sai da ya dage wannan abinda yake ji a jikinsa shi yasa ya kasa bi a hankali ya Shiga da karfi,Aamna ta kwalla Kara kadan,kasa kasa take cewa zafi ka rage sauri,shi ko sauraronta ma baiyi,ihunsa da gurnani yakeyi Yana furta you are so sweet My world,Ya fara cewa kinfi Zuma tafi sau Hamsim,I love you Kuwa ya furta tafi cikin kwando,Bai taba Jin dadi irin wannan ba a duniya ji yake kamar zai mutu sabo da Dadi,Aamna ta daure Kuwa Bata Yi kuka ba duk da ta Sha wahala Kuma taji zafi,gaba Daya ji tayi jikinta Kamar ba nata ba. Hannayensa yasa ta gadon Bayanta ya dago ta tare da Kankameta a kirjinsa Yana wani nishi taji wani ruwa me dumi Yana Shiga jikinta,kamar Kashinta zai tsage Haka ya matseta a jikinsa Yana wani Nishi na daban,Idonsa ya ciko da ruwan kwalla sabo da Dadi,Aamna ta saduda duf tayi sai da ya Gama fitarwa ya gamsu matuka sannan ya sassauta rungumar da ya Mata, Muryarsa na rawa yace Al...Allah...yasa...mu...jone...a haka...a...gidan...Aljanna.... tare da gyara Mata kwanciyar ta,Sannan ya zare jikinsa ya koma gefenta Yana sauke numfashi Yana Jin dadi,sai da ya huta sannan ya juyo da Kansa Yana kallon Aamna Yana ta dariya Dariya murmushi murmushi,yanzu da wannan Abu me Dadi kuka barni kuna kallo Ina Shan kwaya da giya aikin banza abin Dadi a Nan aci asha ayi hani'an. Aamna Baki ta turo gaba zata Yi kuka,Ahmad harda tashi yace ko goyaki zanyi ne? Harara ta watsa Masa,yace sai nasa zani na goyaki,ko gidan Baba sai na kaiki a bayana ba gajiya zanyi ba,yau kin min Allura ai,Fuskar Aamna ba Rahma Ahmad ya kwaikwayi Baba yanda Baba yakeyi idan yaji dadin kyauta ya rike Hanci ya Kama Ayyiriririri yace yes yau nake Ango, light Aamna ta kashe tana Jin haushi,Kunnawa yayi tare da sauka a kasa ,Yace sai wanka anjima da Asuba akwai Breakfast,nan fa Aamna Tace wlh bazan yarda ba,zanyi kuka ya Furta Yana kwabe Fuska da shagwaba,Aamna Tace Kayi kukan jini ma. Daukanta yayi Yana dariya suka Shiga toilet. Ruwan zafi ya hada ya gasa ta sosai taji dadin jikinta da kanta ma ta fito,Door bell Suka ji Ana dannawa ba adadi,Ahmad ne ya zura jallabiya jikinsa duk ruwa ya fito daga wanka Yana budewa yaga Mummy da Humaira,yace Mummy ya na ganku yau da Daren Nan Haka?,kana Ina Ina ta Kiran wayarka Dan Iskanci baza ma daga ba,Daddy Dinku ya Kira shima Shuru Yana Hotel shi a can ya sauka,to matsa mu shiga Mana ko baza mu shiga bane? Ahmad a ransa yace tab Mummy zata kure Aamna gashi ta Mata karya dazu da safe,Bangaje shi Mummy tayi ta shiga tana Dan Iskanci ka tare hanyar,Humaira tana Yaya Amma Ina da sauri yayi sama ya barsu,Aamna taga ya Fado da sauri yace Mummy ce da Humaira Kuma direct take shigowa dakin nan,Ido Aamna ta zaro Tace wayyo kulle Ni a toilet ka kwashe duk wani Abu da yake nawa. Masu sharhi Ina godiya sosai. Ayi min afwa banyi posting da wuri ba,naje Unguwa ne. AsmaBaffa 10/26/21, 8:55 AM - A Maryam: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 86-90 NAFEE TA INA GAISUWA PAGE NAKI NE KHADIJA ABUBAKAR HAMZA DZ Dariya Aamna ta bashi yanda ta tashi hankalinta sai kace ba mijinta bane,Hey Baby relax me zata Miki Mene Dan ta ganmu? karya fa nayi yau da safe Ni gaskiya buya zanyi Aamna ta Mike tare da fadawa toilet,tana Shiga toilet Tana cewa kwashe komai belong to me,Dariya Ahmad yake Mata ya shiga tsince kayanta Yana adanawa,Yana gamawa Mummy ta shigo tare da furta Ahmad wancen uban kayan abincin duk Kaine ka zuba? Naga abubuwan girki sosai ga abinci me Dadi duk Kai kayi? Ahmad da sauri yace ae Mana ah Mummy kinfa Sanni da Harkar girki ba sauki,Dakin Mummy ta bi da kallo karaf ta hango pant da dankunne a kasa kusa da jikin bed,kallon tuhuma ta fara bin Ahmad da shi Tace Ni fa ban yarda da Kai ba Ahmad Yau Sam,Dariya ya sakeyi tare da Rungume Mummy yana Me kika gani? Mummy Tace wancan pant din na Mata fa? anya Ahmad ba Mata kake bi Kuwa? Idan Mata kake bi kayi Hakuri ka daina Nan da sati Daya matarka zata tare a sabon gidanka da Daddynka ya kera maka,Ahmad yace oh har gida aka min sabo? Mummy da murmushi Tace sosai ma gobe zamuje ka gani,Ahmad ya dinga Murna,Mummy ce ta fara latsa Wayarta zata Kira Aamna ta sanar Mata gobe zata Zo gidan,tana Kiran waya ta Kara a kunne tana fara ringing sai Kuma karar Wayar Aamna a saman bed din Ahmad,Ido ya zaro Mummy Bata kawo a ranta ba Tace sai kace wayarka na Kira gashi Nan tana ringing itama,Ahmad da sauri ya dauki Wayar yace Bari nayi waya sai ya saka Wayar a silent a dalilin Wai ya daga wayar ita Kuma Mummy tana ta zabga Kira ta Gama ringing ba'a daga ba,Tace maybe tayi bacci,ta juya zata fita tana cewa Ahmad ku Yaran yanzu sai kuyi ta siyen wayoyi ku tarasu yanzu ga wayarka ka Karo wata kusan wayarka Uku ko hudu ta fice tana fita ya Danna key a kofarsa sannan ya Bude toilet yace fito ta tafi,kasa key? Yace ae,sai lokacin Aamna ta fito. Yanzu King Taya Zan fita gobe daga gidan Nan gobe Mummy zata je gidanmu fa,Zaki fita ne Inshaallah duk kinbi kin damu Haka,zata kwanta yace tsaya a cire rigar baccin Nan,Bata hanashi ba ya Kara figeta ya ajiye dama shi Dan short ne a jikinsa a Haka suka kwanta,suna baccinsu me Dadi karshen dare ya farka Aamna tana ta sheka baccinta ya kunna light ya shiga karewa surarta kallo,wata sabuwar sha'awarsa ce ta taso ya Rungume ta sosai Yana shafa Nonuwanta,Aamna ta farka tana kwacewa suka fara kokawa tukuru da Hayaniya Yace kiyi a hankali Mummy zata ji fa,Mikewa Aamna tayi tana tafiya da kyar tana tattalewa,Ahmad yace ki hakura My world kizo idan na kamoki wahala Zan baki,Kai wallahi baka da tausayi kana kallon halin da nake ci baza ka tausaya min ba,tausayi Kuma? Mene shi? Menene tausayi? Ahmad Kiri Kiri ya nuna Bai San ma mene tausayi ba,Aamna tace au tausayin ma baka sanshi ba?waye Wai? Yace mutum ne? a wanne garin yake?Aamna taga fa ya Gama Raina Mata hankali Tace Imani ko Imanin ma baka sani ba?Kansa ya daga sama Yana tunani Yana furta Imaniiiii.....I.....Mani.....mene ma?....oh na tuna Ina da Imani Mana Amma sai Raina ya baci Imani na yake tashi inyi ta yinsa Kamar me ai bani da sauki Nima bani da mutunci shi yasa Idan Imanina ya motsa sai na samu abinda nake so ai Ni masifaffe ne sosai,Aamna tayi Dariya tare da jinjina Kai tace okay masifa shine Imani nufinka? Yace to ba shi bane? Pillow ta dauka tare da kwada Masa a kirji,Binta yayi da Niyyar kamata ta bigi jikin Mirror wasu lotion suka zubo kasa,Mummy tana bedroom ita da Humaira dake Suma suna saman sukaji karar faduwar Abu,Rike Aamna yayi suna kokawa tana Hawaye tana rokonsa da taga lallai bazai kyaleta ba ta Shiga daukan su Hand lotion da sauransu tana ta jifansa suna faduwa kasa,ta baya ya rike Hips dinta kam da Hannu biyyu tana wutsil wutsil ga ba damar kuka Kar Mummy taji,zanyi Ihu Allah,yace kanki kika tonawa asiri na fada Miki ki hakura nayi Ni sauri nakeyi na gyara hanyar Nan na zuba mata kwalta ta Mike dodar,na matsu ki Saba mu dinga Jin dadin tare ke ba Kya ganewa,hanyar tayi kadan babu Fadi wahala Zan Sha. Aamna tace to da Haka ake sabawa da gaggagwa ai sai a hankali,a'a Ni wlh bazan jira ba sai wani a hankali bazan iya ba,Yanzu idan ka min Illa fa? Sai muje asibiti, ba komai Indai Munga Likita ai Zaki warke ne ko na Miki Illar, Ki hakura Kawai.....muryar Mummy Suka ji Tace lafiya Ahmad naji Kamar Ana ta jifa da Abubuwa? Duf sukayi yace ba kowa Mummy wata Mage na kawo Ina kiwonta shine take ta tsalle sai ta fita,Tsaki Mummy ta ja tare da komawa bedroom dinta,Ahmad yace zanyi da karfi na tunda kinki yarda. Gajiya Aamna tayi Tace Maye Kawai Yana dariya yace naji,Kura Kya ci da gashi yace nine nan,Tace garuje,ya dauketa Yana cewa nice name,Yau kwalta Zan zuba me kyau a hanyar Nan yanda kullum nazo ba gargada,kin kulashi Aamna tayi tana ji ya fara Sarrafata,ita Kuma ga jaraba itama Ana fara murzata sai ta birkice ko Bata Yi Niyya ba sai ta tayashi Dole,Down din ne yau ko wajen ya nufa sai kuka,Amma ko tausayi babu ya shigeta Yana cewa ki nutsu a hankali Zan Miki,Aamna ta fashe da kuka ko a gefen rigarsa shi dadin kukan ma yake ji sai yaji kamar kukan Dadi takeyi wani kaimi ta Kara Masa gashi ya Kawo tun dazu a second round Dole ya dauki dogon lokaci,Aamna tana kuka Tace to ya Isa Haka ai,Ni dadina nake ji cewar Ahmad ya Furta da kyar Yana jagalin dinsa,Aamna Tace Idan nasan Haka zaka min in nazo Allah ya tsine min bazan biyoka ba,daga baya kenan My World Ni ki min kukan Nan yafi birgeni,Kafarta Daya ya dago yayi sama da ita sosai ya riketa Kam Yana Bental ubansa Kawai 😂Ihu Aamna ta kurma sai karaf a kunnen Mummy lokacin tana Sallar Nafeela,Mama Tace Kai gidan Nan ko malamai za a kawo ayi Masa karatun Qur'ani ko sauka Uku ne,Ahmad tuni ma ya fita a hayyacinsa Maganar ma ta gagara sai ihun dadinsa yakeyi ya hada zufa Yana ta uuuhhhhh....Ahhhh....kalaman kauna da Dirty words yake furtawa,Sai da ya dauki 30mt Yana gwangwajewa sannan ya gamsu ya fitar da abinda ya dame shi,Aamna kuka takeyi ta daina Yi kasa kasa ma,Da kyar ya lallasheta ta rage kukan,Mazaunanta yake shafawa Yana ta latse su,Kansa ya maida samansu Wai a Nan zaiyi bacci kafafunsa suna saitin kanta Aamna ta kwada Masa duka a kafar daya dorata a kanta Wai da ita yake shafa gashinta, yaki tashi kuwa,Yace wannan kafi katifar Zan kyale a banza kiyi Hakuri My world Dole na Kara Miki sadaki,Bana so Aamna ta Furta da karaji,Dariya yayi yace na daina bazan sake Yi Miki ba My world sai kin huta sosai da sosai zanyi Hakuri na danne zuciyata zuwa gobe da daddare nasan lokacin kin warke sumul,Ido Aamna ta zaro tare da daina kukan Tace yanzu gobe da dare shine kayi Hakuri? Yaushe na warke ma to? Yan fa Hours ne suka rage a Haka Zan warke?,Aamna da an baza kunne tana jira taji yace sati daya zai barta,sai taji Yan wasu Hours ne kawai. Yace au hakan ma ban birge ki ba?banza ta Masa. Magani ya Bata ta Sha Wanda zai rage Mata raunin,da Asuba ko Sallah ba ayi ba Aamna ta saki kuka Tace ita yunwa take ji,Haka baije masallaci ba ya Shiga kitchen ya fara dafa Mata Indomie da tea,Mummy taji karar kwanika a kitchen ta fito tana dubawa taga Ahmad Tace Kai Kuwa sai kace Aljani Ahmad bakayi fa Sallah ba gashi ma yanzu aka Yi Kiran Sallah Amma kana girki Ni Naga ka Canja ne Wai lafiya Kuwa kamar kana boye min wani Abu,Ahmad yace Wai Mummy Dan Allah Nan ba gidana bane kije kiyi sallarki Zan tafi masallaci yanzu abincin Zan dafa idan na dawo zanci abuna,Baki ta tabe tare da juyawa tayi tafiyarta,Shi Kuwa sai da ya hada komai ya kaiwa Aamna,Toilet ya kaita tayi wanka tare da gasa jikinta sosai shima Haka tare sukayi har brush da Alwala suka fito,Shi ya jasu Sallah suna idarwa Bata kulashi ba ta fara cin abincinta Hannu baka Hannu kwarya,Yace Sannu.....duk kin fada dare daya My World,Harara ta balla Masa tana cewa me zai Hana tunda ka Gama cinye Ni har hanji na,Dariya yayi tare da cewa kawo na Baki a baki,Aamna Tace ban so kaje kayi rayuwarka nayi tawa kuma Allah gobe Zan tafi Kar Mummy ta kure Ni,to sai me Wai kina matata basai Naga dama ba Zan barki ki tafi,Indomie din ta tura a bakinta da yawa tana Shan yaji Tace bani tea din Yi sauri ko wallahi ka Gane kurenka Nan gaba,Tea din ya dauka Yana dariya ya fara Bata a Baki tana kurba,idan ta zuba Indomie da kanta a bakinta shi Kuma ya Bata tea,a Haka ta koshi ya cinye ragowar har tea din sannan Suka koma baccinsu,10am suka tashi lokacin tuni har Mummy ta shirya ita da Humaira Driver ya dauke su suka fita ba tare da Ahmad ya sani ba,sai da suka tashi Aamna dakinta ta tafi da sauri ta zuba tarkacenta na bukata a handbag na Shirin tafiya sannan tayi gashi da ruwa sosai tare da wanka ta dauki wanka cikin wani shegen Idian Sari amma Riga da skert,Bayan rigar igiyoyine aka harde Bayan dasu akayi wani raga mayafinsa me Dan kauri ta yafa ta fito da Niyyar tafiya gida,Ahmad yasha wanka cikin wata Shadda Malam sky ta hadu wani sheki yakeyi kana ganinsa kasan Yana cikin nutsuwa. Hangota yayi tana cewa King kaga Musa yace su Mummy sun fita tafiya zanyi,Ahmad riketa yayi Yana binta da mayen kallo ta Masa kyau matuka,yace My world ko zamu koma bedroom? Allah kiyaye ta hayayyako Masa da masifa,ba shiri yace Yi Hakuri Mummy,Tace kashe Ni zaka Yi daga zuwa Dan Ina ma Biyayya sai kayi ta kwakwuleni Ni Kamar bani da jini,Baki ya Bude Yana dariya Yana kallonta tana dingishi tana tafiya tana masifa,Riketa yayi yace to banyi niyyar barinki ki tafi yanzu ba idan Kuma kece da kanki to ki tafi na gani,Mukus Aamna tayi tare da tsayawa,a palon ya zauna saman kujera Yana kallon yanda tayi kyau,Yace Kuma baza ki fita da kayan Nan ba gwara ma ki canja wasu wannan Ni kadai Zan na ganinki cikinsu,Kuma daga yau duk inda Zaki ko gidanku kike to sai kin nemi izinina,kika fita ban sani ba bada Yawu na ba,sannan wani zuwa Shagon Mama as from today nayi cancel, Aamna Tace ai dama na sani ko baka fada ba ai Dole na tambayeka,Yace to dawo ki zauna kafin Mummy ta dawo sai na kaiki gida,komawa tayi ta zauna kusa da shi yace Haka ake Zama kusa da Miji? Kanta ta kwantar a cinyarsa ta Mike kafafu Wai duk Dan yayi sauri ya ajiyeta a gida,Kar Mummy ta dawo,Yace yanzu idan Mummy ta shigo fa? Aamna Tace ai Kawai juyin duniya kace yanzu nazo gidan cuta kakeyi nazo jinyarka kaw.....kafin Aamna ta rufe Baki Mummy da Humaira sun shigo palon da ledoji a Hannunsu,ai Kamar walkiya Haka Aamna ta Mike ta yo kasan kujera tana cewa Ahmad Sannu ya jikin kasha maganin Nan tafiya zanyi dama biyowa nayi na dubaka,Ahmad ya rike cikinsa Yana Kara Ohhh.....my Internal Organ woooooo..... My Abdomen wooo......pain......Ahhhh.....pain in the lower part of my Abdomen wooooo......Mummy da Humaira kallonsu Kawai sukeyi,Humaira rada tayiwa Mummy tace na rantse Mummy a Nan gidan Aunty Aamna take dama, babu wani wayo da zasu mana,Kuma jiya Ihunta Muka ji da dare. Kallonsu Mummy tayi a ranta tace uhm Yaran yanzu da karya suke Allah kawo min jikoki na gari lafiyayyu Kawai da gani Ahmad bazai jirani ba,Fuska Mummy ta Bata a fili Tace me nace Dake Aamna? Kanta Aamna ta Sosa tana murmushin yake duk ta rude Tace Sannu da zuwa Mummy,Humaira dake aka zo? sannunku da Hanya,yaushe kuka zo?ai nayi zaton sai jibi Zaku zo,ya su Saddeeq? Mummy a ranta tayi Dariya yanda taga Aamna ta gigice ita kadai,Aamna ci gaba tayi da cewa yanzu nazo Nima gidan Zan duba shi baya Jin dadi maganinsa nazo ba shi shiya sa ma kuka ganni,Mummy Tace Naga Alama ai,Ahmad harda Kara Yana rike ciki. Da sauri Aamna Tace Zan tafi gida,a kunne Kuma ta radawa Ahmad Ina jiranka a waje, a fili Kuma yace da kin iya mota da kin dauki motata kin tafi da ita,Aamna tace Asibitin fa ka fasa zuwa Likita yace yau za a maka test,Ahmad yace Haka ne zanje anjima,Aamna ta Mike tare da dakko Hijab me Hannu ta Dora a saman kayanta ta dauki Jakarta ta fice fit,Mummy tana kallon rainin wayon su Ahmad ta kada Kai kawai Suka Yi sama da Humaira,suna tafiya ya Mike da sauri ya dauki key din motarsa da sauri Yaja motarsa ya bar gidan,Yana fita a mota ya hango Aamna tana jiransa a gefen Titi. A gabanta yayi parking Yana dariya ya sauke glass yace Yar gurguwata let's go,Harararsa tayi tana dingishi ta shiga motar da kyar tana cijewa sabo da wahalar da ta Sha a hannunsa,Yace da dare zanzo na daukeki,Aamna Tace wlh Kar ma kazo bazan dawo ba kunyar Mummy nake ji,Nufinki na kwana Ni Daya bazan iya ba,banza ta Masa ya ajiyeta a gida ya wuce gidan su Jibson. Aamna Kuwa tana Shiga taji Mama da Baba suna ta fada yace Aure ba fashi sai nayi,Mama tana baka Isa ba,Butulu Maci amana Nan na biye maka Ina Goya maka baya Muna hadawa Aamna gadar zare akan son zuciya Muka dinga zalintarta,Baba yace munafuka me bin bokaye ke da kika Nemo Laya da guru akan ke lallai sai kin maida ta me bin malamai Dan kar mijinta ya sota,Mama Tace ai da hadin bakinka dan kaci kudin mijinta,Aamna ta labe tana jinsu Suka Gama tonawa kansu asiri,batayi mamaki ba sabo da ta Dade da gano hakan,Amma duk da Haka sun riketa sun Bata Ilimi da tarbiyya Bata da damuwa,Yi tayi kamar Bata ji su ba Tace Mama Ina ta Sallama na dawo,Mama harda kuka ta rike Aamna tana cewa ki yafe Ni Aamna Namiji ba Dan goyo bane,Aamna Tace ba komai Ni koma Mene na yafewa kowa,Baba yace akan zanyi kishiya shike Nan ba zaman lafiya,Aamna Tace kiyi Hakuri Mama,Mama Tace kyale shi ya auro din,Baba yace shike Nan yafiye Miki da kika hakura,Aamna taga sabon kauna wajen Mama sabo da Mijin data dogara da shi suke kashewa su rufe ya juya Mata baya. Mummy a ranar tazo gidan su Aamna tare da wata Mata Yar gayun gaske me suna Maman Haneef wacce ke karanta novels tana maida su audio,har Chanel gareta Maman Haneef Chanel kana bude link dinta zai kaika Chanel din,itace me gyaran Amare,sai ka Isa ake dakko ta,da kayan tarkace na gyara tazo,Mama da Aamna Suka tarbesu,Bayan sunci sunsha Mummy ta Gabatar da ita tace Aamna ga Maman Haneef nan kafin ki tare zata Miki gyaran da akewa Amare na biya komai har gida zata na zuwa kullum tana Miki gyaran da ya Dace. Mummy Tace Nan da sati Daya zaki tare a gidan Ahmad an Gama komai,Mama da Aamna Suka dinga godiya sai da Mummy ta Gama bayanin komai sannan ta tafi ta bar Maman Haneef da Aamna tana koya Mata yanda ake Zama da Miji,Jan Hankalin me gida da sauransu,daga Nan a ranar ta fara gyarata da wasu magunguna na Sha Dana tsarki sai Kuma gyaran skin dinta yanda zata Yi laushi da santsi,sai Harkar kamshi da sauran su,Aamna sai tambayoyi takeyi tana Wayar Mata da Kai. Mama Kuwa Kwana biyu watsi tayi da Baba Sam ta daina kulashi,ya kasa Gane kanta,abinci ma Kawai ajiye Masa takeyi ta juya abinta,Baba ya Shiga damuwa yanda Mama ke share shi Bai jin Dadi Sam,Baba ya rasa inda zai sa Kansa ya zauna a Palo yayi tagumi,Mama tana ta harkokinta tana cin magani,Gajiya yayi yace Wai Ni me nayi ne duk anbi an tsane Ni a gidan Nan ba a kaunata,banza Mama ta Masa Aamna ma Bata ce komai ba,Baba yace tunda ba'a kauna ta shike Nan Allah yasa ma ayi kidnapping Dina kowa ya huta Kuma wallahi sai dai su hallaka Ni sabo da bani da dukiyar da za a fanso ni,Mama ta Harare shi,Baba yace Nima katanga ne a gidan da ake ganin Kamar bani da amfani idan na mutu ai Za'a ga amfani na,daga mutum yace zaiyi aure,ko zance ban fara zuwa,to jaraba nayi bakin jini ma Tace Bata so na Bazawarar na hakura na ci gaba da Hakuri dake Allah yasa sakamakon zaman hakurin da nakeyi Dake na shiga Aljanna a lahira,Mama ta Masa banza ya gaji ya koma daki ya kwanta Kamar maraya,Aamna ce ta kalli Mama Tace Dan Allah Mama kiyi Hakuri ki kyale Baba Haka yasha wahala,Mama Tace ai na hakura na kyale shi,to kije Wajensa Mana,Mikewa Mama tayi tare da shigewa wurin Baba,Yana ganinta ya Mike zaune a saman bed Yana tafi da Hannu kamar yaro harda Waka kaga ta Baban Zuhra....kaga ta Baban Aamna.....me takalmin karfe,Dariya Mama tayi ta zauna yace Haba har naji wani sanyi Amma da Kuwa sai dai naji wani zummmm.....a jikina. Mummy gaba Daya ta Hana Ahmad Zama Kawai abubuwa take sa shi,ko Daddy sau daya yaga Ahmad suna tare da Mummy suna shirye shiryensu shine dalilin da yasa Aamna taga Shuru sai dai suyi waya sau Daya kullum,hankalinsa gaba Daya Yana Kan Aamna amma Mummy da Daddy sun Hana suna can suna shirya Masa abubuwa,Kuma har su Jibson ake komai,koma Mene oho. Ahmad ya gaji kullum Suka fita sai dare suke dawowa ranar da Suka cika 3days Ahmad da safe ya Iske Mummy a bedroom ta shirya tana jiransa zasu fita cike da shagwaba ya sameta Yana cewa Mummy Dan Allah yau ki barni naje wajen Aamna pls ko 5mnt ne,murmushi Mummy tayi Tace baza kaje ba sai ranar data tare idan Kuma ban Isa da Kai ba to,Fushi yayi ya zauna Yana jiranta ta Gama shiryawa Suka fita Mummy na cewa Dan iskanci Ana shirya muku rayuwa me kyau Kuna Iskanci kafi so a dinga baka kana kashewa kawai. Daddy da shi aka je tsaida ranar Auren Jibson da Mashkoor,Shi Kuwa Brown tunda yaga Humaira Kanwar Ahmad ya nace Mata itama Humaira mugun sonsa takeyi dama ita Yana birgeta shima akwai Izza ga daukan wanka,Ahmad ne ya dinga Murna,Harda Kiran Humaira gefe zasuyi sirri. Yace ke Dan na bawa Brown ke Kuma wallahi kika ce bakya sonsa sai na tattaka ki,sabo da Haka an kusa bikinki Kawai nine waliyinki,Humaira tana Dariya Tace Yaya Ina sonsa fa dama Kawai aji nake ja,Ajin banza mu mun fiki aji yarinya cewar Ahmad ki godewa Allah Zaki samu irin mu,Humaira tana ta dariya yace Kinga tuwona maina Kinga sai a kawo ki Nan Muna tare abinmu a kd, Humaira tana Dariya Tace ae. Abban Jibson tunda yaga bazawararsa ya gigice duk kyan Ummati wannan ta fita ga daukan wanka ai itama matar Hajiya Rahinatu tuni Abban ya Mata abinka da Auren Manya ko sati ba ayi ba aka Daura Aure,tariya kuma sai ranar da Za'a kaiwa Jibson Amarya itama sai ta tare. Shi Kuwa Abban Brown abokinsa ya samu a kasuwa ya fada Masa komai tsakaninsa da Yar China,shima ya dinga dariya,Abba Yaja kwafa yace Allah ka are min Rana na samu wasu makafin kudi Yaran Nan na nuna musu ruwa ba sa'an kwando bane naje Saudiya na auro balarabiya,Kuma a ka'aba za a daura auren,tunda sun tare matan kasar nan ko wacce sai su shike Nan suje da na Nan Ni Kuma Zan fashe haushi na da Balarabiya. Mashkoor ma Ana ta shirye shirye da Nafeesat ma, Kamar yanda Malam yayi Alkawarin yiwa Jibson komai Haka yayi ya bawa Jibson kudade masu nauyi sannan ya bashi gida Kato kyauta me gate part biyu ne a gidan,Ahmad yace wannan gidan Jibson ya Bawa Abbansa su koma ciki tunda gidan su Jibson na Haya ne Kuma Bai da kyau ga yara,Jibson yace to tunda yasan Ahmad yace Haka to akwai shirinsa na daban,Haka ya fadawa Malamin surikin Mashkoor,Malamin yace duk yanda sukayi dai dai ne shi dai ya bashi kyauta,Haka Abba ya dinga Murna Yana sawa su Jibson Albarka,kannen Jibson murna Kamar zasuyi hauka,babu Bata lokaci Suka fara Kai Kaya sabon gida Ana tsara shi gashi Jibson da kudinsa ya zuba musu furniture masu kyau komai Shar shar cikin rufin asiri. Tawaga Kuwa Son Yar China ne ya kamashi a hankali,gajiya yayi ya tafi fada Mata,Bayan yasha wanka yaje gidan,tana Jin karar machine Yar China ta fito da gudu tana Masa Sannu da zuwa sabo da gaba Daya sun Saba, ta daina Masa tsokana sai rashin ji sabo da yarinya ce,Tawaga Bai taba kula mace da sunan so ba,Kawai Yar China tana gabansa ya kalle ta yayi Mata irin ta Yan shaye shaye yace Kee....to ya akayi ne.....Yar China tayi Dariya tare da furta ya akayi Kuwa,Yace... to... ya ake ciki ne aehhh..... ko Baki gane bane aeee? Yar China Tace me Zan Gane? da masifa yace ke karki Raina min hankali mana ya Zaki min wani ae yane?.....Haba dalla yawa kike....Yar China ta sake tuntsurewa da dariya sai ya fusata tana Masa dariya Kawai sai Mari taji feesssss....ya fesa mata Mari,kumatu ta dafe tana kuka,a fusace yace Ni Zaki rainawa hankali kice Baki Gane me nake nufi ba ke dalla Ware ko na farfasa Miki jiki,Yar China da gudu tayi gida tana kuka shi Kuma a Nan ya tuna Bai kyauta ba,a fili yace me yasa Zan mare ta,can Kuma yace to Dan uwarta ya zata ce Bata Gane sonta nakeyi ba,machine dinsa ya buga ya tafi Yana ta masifa a hanya. Ko da ya hau titin kwalta ma ko ya wani ya Masa overtaking sai zagi ya fara dura Masa ashariya yau Yar China ta Bata Masa Rai,Ko da ya koma wajen su Jibson yaje ya Basu labari yace Dan iskanci wai Tace Bata Gane ae yane ba,Yawa ta min Ni Kuma na kwashe ta da Mari,ya dan rainin hankali Ina Mata maganar ya ake ciki tana wani sharewa,su Jibson Suka dinga dariya Kamar me,Nan ma yaji Haushi. Washe gari Haka ya koma da Yamma horn din duniya Yar China tana jinsa Taki Fitowa, Iyalle tana ta Mata fada taje Amma taki,gashi Tawaga son Yar China ya dame shi ai ya sake Danna horn sannan Yar China ta fito tana Fitowa ya kwada Mata Mari tare da nuna ta da Yatsa ke Dan kutmar....kina jina Ina kiranki tun dazu amma kika Shanya Ni? ai Yar China takawa tayi zata koma gida da kuka ya riketa caraf,juyowa tayi tana kuka ya kalle ta Itama Idonta cikin nasa da masifa yace kalli cikin kwayar Ido na...Yar China ta kalla sosai yace Baki ga wani Abu ba? Yar China tana shesheka Tace Naga kwayar idonka baka wuluk idonka fari tas,Ran Tawaga ya sake baci yace kalleni sosai Baki ga wani ae yane ba? Yar China Tace ban gani ba zata Yi Dariya yace Zan mareki wlh,Hannunta ya Kama tare da dorawa a kirjinsa yace Baki ji wasu kalmo mi na tashi ba? Yar China ta Kara sakin Dariya ya hade Rai sai tayi Shuru ya sake danne Hannunta a kirjinsa yace tun ranar da kika taba zagina a gate din makarantarku zuciyata take bugawa Haka,tana furta Miki kalamai,Yar China Bata kawo komai ba Tace Tsoro na kaji Kawai,ai idan aka ji tsoron mutum shine zuciya ke wannan bugawar,Yace na mareki ba Haka take nufi ba,wasu kalmomi take ta fada Miki tun ranar Amma bakya ganewa ke, Yar China Tace to me take cewa? Tace ki gano mana da kanki Yace cewa fa takeyi Ina sonki...Ina sonki..... Yar China da yarinya ce sai ta dinga dariya Tace me zanci da ita Ina da tawa zuciyar Nima Allah ya min,Ran Tawaga ya sake baci kamar yayi me,Yar China Tace Ni wallahi Ina da tawa ta isheni rayuwa,Tawaga tafiya ya sake Yi ransa a bace. Yar China ta shige gida tana ta dariya tana bawa Iyalle labari,Iyalle Tace ke shashasha ce Yar China ai nufinsa sonki yake yi,Kuma aurenki zaiyi Alhmdllh kinyi Dace jikata,Yar China ai sai ta tashi ta Kama rawa tana murgude murgude,Yatsa tasa a bakinta tana rausaya kanta Tace dama Allah Iyalle Ina sonsa gashi Dan gayu Iyalle kullum kamshi yakeyi,Iyalle Tace ai fa gashi kyakyawa,idan ya dawo kice kin Gane nufinsa kema kina sonsa,Yar China Tace Ni kunya nakeji wallahi Ina fada Masa Zan gudo gida abina,bangaren Tawaga ko da ya tafi gida da dare sake dawowa yayi zai fadawa Yar China Kawai Yana Sonta,Yana zuwa ta fito da gudu,yace bana hanaki gudu ba? Yi Hakuri Yaya,murmushin Jin Dadi yayi yace dazu Baki Gane nufina ba sonake na fada miki,Idonsa Tawaga ya rufe Kam tare da maida Kansa gefe ya karasa da cewa so nake nace Miki Ina sonki Ina kaunarki Zan aureki idan kin Aminc....kafin ya karasa ya buga machine dinsa ya Sha kwana,Yar China da mamaki ta daga Murya da karfi yanda zai ji ta Tace Ina sonka Nima Yaya,I love you Haka wata kawar mu take fadawa saurayinta Nima I love You....Baki ta cuno yanda ta tuno kawarta tana yiwa saurayinta a waya Wai kiss Tace Yaya Muahhhhh ...Tawaga Yana dariya da karfi shima ya Furta Yar China Nima Muahhhh..... Yau Tawaga yayi kwanan farinciki su Jibson sun Sha labari,cikinsu Bash ne Kawai Bai da wacce zai aura,Brown yace Bash yayi kwantai jama'a a samo Masa tasa Bai kamata mu angwance ba shi ba,Tawaga yace tun yaushe ya likewa Kanwata Hafsat kullum suna tare ya hanata karatun kirki,da Hafsat a class itace ke daukan na Daya Amma tunda Dan Iskan Yaron Nan ya fara zuwa wajenta na Uku take zuwa yanzu,Bash Dake zaune ya dinga dariya yace ai kyaleku nayi ku Gama haukar ku Ina da gwana ta Nima. Mummy fafur ta Hana Ahmad ganin Aamna,ganin ma zai iya zuwa a boye sai tasa Suka koma gidan Amma,itama Aamna sabo da tana so ta huta ta warke daga raunin da Ahmad ya ji mata sai Taki fada Masa inda take har yayi Fushi ya daina Kiranta,Ana saura kwana daya Aamna ta tare gaba Daya su Mashkoor suna tare Wai sai sun raka Ahmad dakin Amarya sunyi Addua duk da an daina yanzu su sunce sai sunyi sai kowa ya raka kowa anyi Addua,Ahmad sai zumudi yakeyi ya wani kwana a kujera ga Hajiya Babba ta Mike sosai sai Dariya su Mashkoor suke Masa,Ahmad yace zaizo kanku ne Dan Uwarku,Iya azaba Mummy ta Gama gana min,Kawai mutuwa ne banyi ba,Wai King baza ka bari yarinya ta huta ba wannan jaraba Haka cewar Brown,Ahmad yace Ina Baku shawara wallahi ranar da aka Kai muku Amarya karku sake ku barta ta kwana lafiya,ko Bata da Niima ku shafa Vaseline ku tura da kyar karku Bari Daren Nan Dadi gareshi,Suna ta dariya Ahmad yace duk Wanda ya dandana abin Nan Matukar Bai daina shaye shaye ba to Allah ya tsine Masa Albarka duniya da lahira,sabo da yaci zarafin abin Dadi,ga abinda ya Dace aci an zauna shaye shaye Kawai ayi aure Malam,Kuma idan matarka ce hankali kwance Malam,ba tsoro ba fargaba,ba Wani gate naka ne kayi abinda kaga dama,Noma zakayi ta inda kaga dama,suna ta dariya King dinsu ya haukace,Tawaga yace tawa fa Yar shila ce King? King yace karka sake ka daga Mata kafa ko yau uwarta ta Haifo ta idan ka barta ta kwana lafiya sai kaci Ubanka wallahi,Suka dinga dariya Brown yace Ni me kanwarka fa? Yace ai Kai baka da matsala mutumina Mummy zata gyara ma ita sosai itama Kar aji tausayinta kowa Muka raka dakin Amarya washe gari ya kawo min report me kyau,Brown yace Humairanka fa? Ahmad yace ban son Iskanci fa Ina surukinka kana min Iskanci,Dariya sukayi yace Ni wallahi matata nake so a bani na gaji da Dan Iskan gyaran nan,Tagawa yace gobe Zan siyowa Yar Chinata waya me kyau tana Gama Zana Waec Iyalle Tace za ayi bikinmu ita Kuma Iyalle zata koma gidan kaninta da Zama su zuba Yan haya a gidansu,Bash ya kalli Tawaga yace Ni Kuma fa Hafsat din taka sai yaushe? Ga waliyinta Nan ka tambaye shi ya Nuna King,King Yana dariya yace tare zamu hada bikin ma,Bari mu zauna da Daddy gobe kafin ya tafi sai ayi Maganar idan da Hali duka a daura dasu Mashkoor. Aamna Kuwa Ana ta gyara tayi wani uban kyau ta sake haske sai sheki da kyalli takeyi,fatarta tayi wani Irin smooth ko Ina ta zauna ta tashi Kamshinta sai yayi kwana Uku Bai bar wajen ba,turaruka ne masu tsada da dadin kamshi,kayan maganin Mata Kuwa ba a magana an Gama hada Aamna,washe gari ranar da za a Kai Aamna gidanta na aure Suna zaune da Maman Haneef tana koya Mata tarairayar Mai gida kissa da kisisina,shagwaba da sauransu Ahmad ya Kira waya,Maman Haneef tace to a fara gwada shagwabar Ina kallo,Aamna aka makale Murya Tace Hello ranka ya Dade,Ahmad yace My world I miss you so much,Cike da shagwaba kamar zata Yi kuka ta Furta me to My life,Zuciyarsa ce ta wani karbi sabon son Aamna yace karfe Nawa zanzo gidan to idan an kawo min ke? Aamna Tace wannan zumudi Haka ka Bari Mana sai an kawo Ni,a'a Ni gwara na sani tun yanzu sai nayi shiri,Murmushi tayi Tace Mummy Tace 8pm zamu tafi,Har 8pm yanzu wa yake wani Kai Amarya 8pm ai 3-4pm ake Kai Amarya 6-7pm ango ya shigo ya tarbi abarsa,Amma za ace wani sai 8pm nufinta sai 9-10pm Zan shigo,Tsaki Yaja ya kashe wayarsa Yana ta masifa a Gaban su Jibson suna ta dariya. Aamna Bata taba zaton sabon gida za a kaita ba,Bata san komai ba Kawai dai Maman Haneef ta sata ta fesa wanka ta shiryata cikin wani lace black and pink me shegen kyau,ta Mata dauri me kyau da kwalliya ta hankali me kyan gaske,Aamna kamshi da sheki Kawai take Yi,Maman Haneef ta gama aikinta ta tafi abinta, Mummy da Daddy tare da Amma sai Humaira sune Suka zo daukan Amarya,Mama Tace muma baza a barmu a baya ba,Haka Baba ma da Zuhra Suka shirya suka tafi gaba Daya Kai Aamna dakin Miji,Lokacin Su Ahmad sun Sha wanka gaba dayansu kowa da Kalar shaddarsa irin kyan da sukayi ba a cewa komai,ranar wani Dan biki sukayi domin abinci ma order King yayi musu suka ci suka Sha ga kida na tashi,da dare Kuma suka dauki sabon wanka sabo da Daddy yace Yana son magana da su gaba Daya su hadu a gidan Amarya. Siyama Kuwa kaskon ta yasha wanki da Omo da soson karfe,ko da tazo soya Wainar sai ya fara Kama Wainar tana yagalgalewa duk ta kwabe ,Hayaki ne ya turnuke ta a kitchen ga Yara sunyi Layi Kamar yanda Suka Saba suna siya musamman Almajirai sunfi yawa,wani yaro ya Bata kudi dari biyu ya siyi ta dari zata bashi dari canji ai Siyama Tace Sam yaro Bai Bata bata ko sisi ba,Almajiri yace Allah ya Isa wallahi dari biyu na baki,Siyama cafko Yaron tayi ta Mike tsaye tare da danne Kan Yaron ta dinga dirka Masa duka a gadon baya ji kake Dimm....dimmm...Dimm....Yaron Yana ihu da kuka Kuma Bai fasa Zaginta ba,dama Siyama ta Saba mugunta sai taci kudin yaro idan yayi magana ta Masa dukan tsiya Haka take musu,Almajiri yana kwacewa ya fita da gudu Yana kutuntuma Mata ashar me yaji. Tana masifa ta gyara daurin zaninta ta zauna taci gaba Yara suna na Baki kudi na a bani,Nima a bani,nine a layi,Wata yarinya an zuba Mata ta tsuguna tana zuba yaji Siyama ta dinga dura Mata ashar tana kaga Yar Iska Zaki karar min da yaji Ubanki ne ya bani jarin,Yarinya sai tayi gaba tare da cewa bazan sake dawowa ba shegiya,Zan Kamaki ne Islaha na ganeki Zan Kamaki a hanya cewar Siyama. Shima wani Yaron daga yace tun dazu nake zaune kin hanani Ina ta jira,ai Siyama Tace zanci uwarka wallahi,Yaron yace sai dai Uwarki,Siyama ga Waina Taki yin kyau ga itace yaki ci ta cafko Yaron tana daga zaune ta tsugunar da shi a gabanta shima ta dinga dirka Masa duka a baya,yace kinci Uwarki,Siyama ta Mike tsaye tare da jawo shi tsakar gida zata dake shi ya fisge zaninta ya Fadi kasa sai ga Siyama cinyoyinta a waje Siri Siri da su sai pant kawai a jikinta rigar atamfar gata Yar ficika Yara suka saki ihu,Babarta Tace kinwa kanki dabba marar tunani ,Siyama ta duka ta re da dakko zaninta ta daura da sauri,ai kullin Wainar flour tayi fatali da shi Tace an daina sana'ar kowa ya tafi gidan ubansa Shegu Kuma Wanda na karbi kudinsa asara ta hau shi a bakacin ihunku da kuka min matsiyata ku tashi ta kifo su waje Suka fito da gudu. AsmaBaffa 10/26/21, 2:11 PM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY 91-95 Official By AsmaBaffa Ina miko gaisuwa ta musamman NAFEE AUTA UMMI DEEJAT ~- MAMAN MURTALAH Page naku ne Ya Hajja kamshi Mom Abdallah Pretty Deejarth M Dewu Mama Fati Mai kubewa da kuka Babar Siyama Tace kinwa kanki Siyama wallahi nasan karya kike Aamna ba abinda ta Miki kece kika Mata laifi Zan kirata awaya jibi Inshaallah na ji,yanzu kin Kori Faisal sai ki fara son Hasheem Dan gidan kanina Dama ya Dade Yana sonki Alhmdllh ya samu sana'a Yana aikin buga bulo a gidan Bulo sai ya Kama Miki gidan haya ku zauna Kamar yanda kanina yayi maganar,Siyama Tace Ni Allah bana sonsa Abu Baki da shi Haka Kuma,to kyau kika fishi Kuma ai Hasheem ba Baki bane Wuluk Dan baki baki ne Haka, ya Gama diploma dinsa Aiki ne Bai samu ba,Hasheem Dan gayu ma irinsa yaro me hankali ai Hasheem din da kike rainawa yafi karfinki Siyama shine zai rufa Miki asiri Kuma wallahi sai kin aure shi sabo da idan Baki sani ba Faisal din da kike so ya dawo wajenki an sa ranar Aurensa,gashi ya dankara gida me kyau da katon gate ga mota dalleliya, kuma kwana Nan ya biyawa Iyayensa Makkah,ai Siyama sai ta fashe da kuka Jin Faisal zaiyi aure ya manta da ita,Tace na cuci kaina wallahi sai naje na roke shi ya dawo ai nasan Yana so na,Kuma sai naje gidan wacce zai aura na hada mata jini da majina,Kina da Aiki Allah bada sa'a cewar Maman Siyama. Wata Unguwar masu Hannu da shuni aka wuce da Aamna sai kallo sukeyi gidaje galla galla sai Wanda ka gani a layin,Wani shegen Estate aka Shiga da Motocin Guda biyu na Amarya,gidaje ne masu zaman kansu Guda shida,ko Ina yasha bishiyu da shuke shuke sai kace a turai,ko wanne gidan daban yake a ciki da komai nasa Guda biyar sune a farko a jere Hannun dama da hagu,kowa ya kalli wannan building din yasan Naira taci ubanta,ko wanne gida Dake Estate din sama da kasa ne, ciki aka Shiga da da motocin sosai Suka bi kwaltar dake a tsakiyar tsakanin gidajen gefe Kuma grass carpet ne da flowers,Garden ma da wajen kiwon tsuntsaye daban yake a ciki,Haka ga wajen wasannin Yara Nan abubuwa daban daban,sai da akayi tafiya me nisa sannan aka zo wani katafaren gidan Wanda shi na musamman ne kalarsa ma daban ne,yanda aka tsara ginin shi zai ja Hankalin mutum,iya tsaruwa ya tsaru gashi shi a Haka ma ta ciki idan ka shiga part biyu ne,bangaren garden dinsa daban a Nan akayi katon pool,komai na hutawa da Jin dadi ya tare a wannan gidan Wanda da Alama shine na king,motoci a parking space sun Kai hudu,sabanin wacen gidajen da kowanne gida mota Daya ce me kyau,wani baka,wani fara,wani red,wani arsh wani black. Iya gidan Ahmad shi kadai ma'aikata maza mutum Uku ne kowa da inda yake kula da shi,Mata masu Aiki sai nan gaba zasu dakko da kansu idan sunga dama. a bakin gate na shigowa Estate din masu Gadi ne mutum biyu sai masu kula da Compound da garden na sauran gidajen Guda biyar mutum biyu ne. Su Mama Basu Gama Kai karshen kallo ba sai da suka Shiga cikin gidan Ahmad La'ilaaaaah tsayawa lissafi Bata Baki ne an narkar da dukiya wajen kera gidan da furniture abin ba a cewa komai,kitchen Kuwa wani mugun katon gaske har Guda biyu ne shi ma,kayan da suke ciki sai wane da wane,gaba Daya color din gidan Milk and Golden ne,komai Yana daukan Ido Yana sheki,shi kanshi tsarin steps din da zaka hau sama abin birgewa ne,gadaje na alatu,kujeru na nunawa sa'a,toilet Kam sai dai a rufe Baki,bangaren sauran gidajen Kuwa milk and Brown ne sannan furniture da komai iri Daya ne,Aamna ta Zama Yar kallo. A Palo aka ajiye Amarya ba a Dade ba sai ga su Ahmad sun shigo su shidan cif,Zama sukayi Suma a kasa su Daddy suna kujera,Humaira tana ta yiwa Brown signa suna kallon juna,Daddy ne ya kalle su gaba Daya yace Bismillah samari a bude taro da Addua,sun fara kenan sai ga Saddeeq da mufeedansa Suma sun shigo da Sallama,Addua akayi aka shafa. Daddy yace Alhmdllh mun godewa Allah daya nuna Mana wannan Rana da ranmu gamu mun gani Ahmad Guda king yau an wayi gari ya shiryu tare da guys din nasa gaba Daya,an samu yau kowanne cikinku ya daina Shan komai Wanda Ahmad silarsa Matarsa Aamna ko ta Nan mun Kara tabbatarwa aure Rahma ne,aure Yana gyara mutum daga mutumin banza ya koma mutumin kwarai,sannan ku Kuma shiriyarku ta hanyar hatsari kunga mutuwa kuka saduda dama wani baya tuba sai yaji wuya mun godewa Allah. Abinda yake Kara birgeni da ku tun a baya gaku Kuna shaye shaye Amma Allah ya baku hankali da basira,Allah ya baku zuciyar Imani da tausayi,biyayyar Iyaye,kula da Iyaye da yan uwa marayu wannan kadai Allah bazai Bari ku tabe ba,ga rikon Amana a tsakaninku Wanda yanzu itace tayi karanci,Wanda basa shaye shayen sai kaga suna tafka haukar da sunfi me shaye shaye rashin hankali,akanku na Gane cewar Dan kaga mutum a wani Hali karka dauke shi a banza sabo da Allah Bai halicci banza ko dolo marar amfani ba,duk lalacewar mutum Allah ya bashi baiwarsa ta daban,Yanzu mu dauki gidan Kai Tawaga ba karamin darasi bane,Babanku yayi Aure aure tun Yana da Rai Kaine jigon gidan,yazo ya rasu ya bar maka dunbun marayu Amma baka Gaza ba tare da taimakon abokanka kuka rike su kuka yiwa rayuwarsu gata,iya Maraya Daya ka dauki nauyinsa Allah ne kadai yasan iya adadin ladanka bare marayu Haka Yan uwanka,Kuma a Haka ka hadu da Budurwa itama ka daura nauyinta a kanka ka tallafeta baka ce kaima naka sun ishe ka ba,Haka kake kula da ita gashi babban taimako zaka aureta,iya gidanku Tawaga yakan sani zub da Hawaye musamman idan Naga kannenka idan ka dawo gida yanda suke turuwar fitowa taronka Ana maka Oyoyo ta kudu ta arewa kowanne yana rige rigen ka dauke shi,Iyayenka sunyi farar haihuwa,na jinjina maka kwarai dalilin wannan gidan Ahmad da yake damuna cewar gidansa ne a Nan zai mutu na baka gidan Nan halak malak ka kwashe marayu da mahaifiyarka su koma wancen gida zai ishe su zasu sake a ciki sabo da Babba ne,Komai ya koma mallakinka ka saka kannenka da mahaifiyarka. Na dawo kanka Jibson kaima mahaifinka na raye da mahaifiyarka Amma Kai kake komai na gidan ka dauke musu nauyi da taimakon abokanka,Mahaifiyarka ta rasu tana sa maka Albarka Kai Kam ka Dace sannan mahaifinka yayi Rashi ka tausaya Masa Zama shi kadai kuka samo Masa Mata daidai shi kuka Yi komai na auren aka daura,an baka gida ka sadaukarwa mahaifinka Kai ka hakura Zaka nemi naka gidan daban,ka samu mace Amma bazawara Kuma sabo da Allah ka so ta kana saurayi zaka aureta ba kowa zai iya wannan ba a Yaran zamani, weldone Jibril,gashi tun da wuri Allah ya Buda ma limaminku ya baka gida da komai na auren wannan falalar Allah ce ya fara saka muku tun a gidan duniya. Bashir,Mashkoor da Mubaraq ku Kuma Kuna da rufin asiri da iyayenku Baku da matsala babba amma rikon Amana da sanin darajar abokantaka da lafiyarku da dukiyarku Kun tsayawa abokanku Kun bada gudun muwa wajen shuka abin Alkhairi ,Ana samun Haka da yawa mutane suna kallon masu shaye shaye a banza wallahi mafi yawa sunfi Wanda basa Shan komai Hali me kyau da sauran dabiu masu kyau,ga taimako,ga rikon Amana,da kaunar junansu Amma mu mutane maimakon a jasu a jiki masu karfi su tallafa musu Wanda ke Neman agaji da sauransu sai dai mu zage su,mu tsine musu sannan mu kyamace su,aure ma baza a Basu ba sai marar galibu Bayan da yawa in sukayi aure shiryuwa sukeyi musamman idan Suka fara Tara iyali,ya kamata mu gyara muma karka tsinewa wani Dan Yana Abu ba daidai ba,Kamar yanda surukin Mashkoor yayi Haka ake so a kasance,yasan kana shaye shaye Amma yace ka nemi yarsa,yasan kuna shaye shaye ya Baku kudi ya tallafi wani da kudin aure da gidan Zama,Rashin wannan shi ya kawo yanzu muke wannan halin na sama basa taimakon na kasa,sai zagin juna da aibata juna tare da hassada iri iri,Wannan Hali naku yayi kuci gaba da taimakon na kasa Haka ake so sai rayuwa ta inganta. Daddy Kuwa Ahmad ya kalla yace My son Ban taba tunani kana da hankali da tausayi Haka ba,Ban taba ganewa kana da wannan halin ba sai daga baya,Ashe Kai gaba Daya mutumin kirki ne fahimta ne bamuyi ba,sa'ar Haihuwa yanzu mun San munyi sa'ar Haihuwa Kuma Allah ya muku Albarka ya sake hada kawunanku Amanar Nan Taku ta dore har abada,Ameen kowa ya Furta,Daddy yaci gaba da cewa Wannan gidan da kuka gani Estate Guda naku ne, Mashkoor ga naku can guba biyar kowanne da motarsa Kuma an saka komai na bukata a cikin gidan,duk Wanda aka tashi kawo Masa Amarya Nan za a kawota kowa ya zabi bangarensa gashi ga keys Daddy ya basu har da key din mota kowa da nasa,yace naga Kuna kaunar juna,idan na dauke Ahmad na raba Abota Allah ne ya hadaku,shi yasa na muku gida Haka sabo da ku zauna kusa da juna. Mummy Tace Kuma yanzu Daddy zai na Dan hutawa kamar yanda kuka gani munje daku katafaren building dinsa Wanda kuke masu kula da komai na dunkiyar Daddy, Saddeeq an bashi kasonsa kaima Ahmad gashi Nan an Gina muku Naku Office din Rabin harkokin Business na Daddy ya dawo hannunka abokanka zasu taimaka maka zaku kula da shi,Gaku Nan office Dinku ma a building daya kuke kowa da Office dinsa sai ku ragewa Daddy aiki kuma,masu aikin Gomnati Kuma nasan da kanku zaku ajiye aikin Gomnati sabo da yawan abinda zaku samu,kanfanonuwa ne da dama a karkashiinku yanzu,Amma sai Bayan 4months za a karasa hada komai kunga lokacin Kun Gama Amarci dunmkda biki ya matso,Godiya mukeyi sosai. Daddy dai Aamna ya kalla ya fara Mata nasihar zaman aure tare da Angon, yace har ku ma su Jibson a karshe ya rufe da Addua tare da furta game da aikinku da zaku fara da kaina Zan dinga Guiding Dinku komai,Godiya Suka dinga zubawa,Mummy itama tata nasihar tayi Haka Amma ma,sai Baba yace Gaskiya Naga darasi a rayuwa Nima nayi hankali yanzu shekarata Kusan sittin Amma sai yau na Gama hada hankalina cif,na nutsu Nima Kuma Zan koma gefe nayi shuru abina... Dariya akayi Mama tace Nima sai kwana Nan na hada Nawa hankalin ta kalli Ahmad tace Dan Nan Muna kallonku Baku da hankali Ashe kunfi kowa hankali,Ahmad yace ai Kuma Kuna da naku kalar, Baba da sauri yace Kai yaro Bari Ina wani hankali a wajen mu,da Muna da shi ma aikata abinda muka aikata a baya? Su Jibson suna ta dariyar Baba,yace ke Aamna Allah yasa dai kema kin waye kin iya magana nasan halinki abinda kika ga dama fadawa mutum kikeyi to ki kula wannan samarin ba irinmu bane kishiya sukeyi da wuri,Aamna kunya ta kamata ta boye Fuska Baba yace daga baya kenan Allah ya dawo da Babanki shima wani bakin Dan Iskan gantalalle ace shekara ashirin da wani Abu kaki waiwayar jininka,Dariya Baba yake ta Basu wannan zagi Haka cewar Daddy,Baba yace Allah ya kawo shi kasar nan duk Randa ya kuskura yazo zai ci ubansa a wajena,bushashen banza Yana tafiya Kamar Iska zata dauke shi wuya kamar sillen karan dawa,Shi Sam baiyi Kama da Yan Sudan din Bama Allah Kalar bakin fatarsa irin na Yan Kenya ne karya ne ruwa biyu ne Babarsa ko babansa ciki Daya bazai wuce Fulanin Kenya ko Senegal ba,sai tsayi Kamar rakumin dawa,aka dinga dariya har Aamna Ana ta kashe tsohonta da ba'a ita Bata sanshi ba ma,Baba yace ai ke Kam Aamna bangaren Sumayya kika gado su Daddy amma da kin gado bangaren Ubanki babu ta yanda za ayi kiyi kyau,sabo da kaf dinsu babu me kyau ga Baki, Hanci kwabal,ai wallahi an cuci larabci cewar Mama. Baba yace Haba ke dai Bari Aishatu idan naji Baban Aamna Yana larabci lokacin Nan inda kisan na sa Sanda na sheme shi Haka nake Jin haushi Wai Balarabe ta gidan uban wa? ba gwara ace nine Dan Sudan din ba ya kika ce? Mama tace tuni ma labanil mara'i kullum babu Yankewa Madara me Dadi,Almara'i ga tuffa Yar kasar madina. Ana ta dariyar su Baba Jibson yace kace shishigi Suka yiwa Larabawa Baba? da sauri Baba yace da gani ba tambaya cirani Iyayensu Suka je kasar Suka hayayyafa a can har yayansu sune irin su Baban Aamna suka girma a can suka ji larabci,bazai wuce Kakannin Aamna Bayi bane a can suka Tara zuriya zasu ce Wani Yan Sudan ne su harda zuwa kasar mu a Raina Mana wayo mutumin da na ninka shi Fari sau goma Amma Ni bana Jin larabci sai shi,Ni abin haushin ma ya dameni da wani ta'alli ta'alli Yalla yalla,aka dinga dariya Tawaga yace Surukin mu ne fa Baba,Baba yace kaji kalen dangi a Ina ka ganshi ma in ba mu ba Kuna da wani suruki ne?,Mama tace yo ai da ganin irin salon iskancinsa na guduwa a bar Iyali ai na Yan Nan yankin ne, sune Suka kware wajen zalunci,tsayinsa ai da gani Dan Kenya ne,ke Aamna ba Wani Yar Sudan Yar Kenya ce ke ko Senegal cewar Baba,Daddy Yana dariya yace to shike Nan a daina yiwa Yata tsiya haka,Baba yace ai da ace balaraben gaske ne da yanzu Aamna ta kamo Ahmad a hasken fata,Amma Babanta ya cuceta ta sirka da duhu kadan shi yasa Bata Kai Ahmad ba. Baba ya kalli Ahmad yace Dan Nan wani satin zamu rangado muku kayan gara,Ido ya zaro yace No Baba Ni bana son gara kana gani an zuba komai Bamu da bukata,sannan ma ai mu Bama cin alkaki da wani tarkace,Baba dama Yana sani ya fada tayin marowata yayi Dan suce sun yafe yace zai kawo yasan baza su karbi wata Gara ba,inda ake arziki ba'a tsiya,tunda ba Addini bace duk me sa Ido Akan gara to dama zuciyarsa a mace take. Baba yace abin al'ada Dan Nan kuce ku bakwa so Haka akeyi sabo da Allah? Daddy yace ai na dauke muku komai,Baba ya dage Kamar gaske harda cewa 'yata Guda na raineta ace ba kayan daki an hanani Yi Kuma garar ma baza a barni nayi ba ai dadin sai yayi min yawa Haka,Mummy Tace ba komai wlh,Zai sake magana Mama Tace to Husaini kalata ka hakura kayi godiya Haba. Ahmad shi duk ya gaji da surutun Nan yace Shikenan Alhmdllh komai ya kammala,Mummy ta galla Masa Harara,Shuru yayi Yana Sosa kai,Daya Hannun Kuma Yana cikin gyalen Aamna ya rike Hannunta. Daddy ne yace Baba Nan gaba kadan Zan maka magana Akan wani tsarin Inshaallah...kafin ya karasa Baba yace Allah ya kaimu Ameen,Ahmad ya sake cewa to shike nan an gama,Mummy ta kalle shi Suka hada Ido yayiwa Mummy signa Wai Tace su tafi,kanta ta dauke,abokansa ya turawa text duk suka zaro waya a tare Suka duba me ya tura musu,Wai Kar kowa ya sake Jan Hirar nan,duk abinda akace kuce Uhmm kawai,Dariya sukayi Tawaga yace zaka ci Ubanka tunda baka da kara. Ai Daddy suka kalla tare da Baba Suka dasa sabuwar hira,Baba dama kadan yake jira sai surutu suna ta dariya,Ahmad Yana ta duba agogo. Mika yayi da hamma tare da mikewa tsaye ya koma ya zauna Yana cewa na gaji da yawa,ba Wanda ya kula shi,Aamna tana ta dariya a ranta harda cewa Zuhra da Humaira ku kunyi Shuru ya kamata ko lemo ku kawo a Sha akwai a kitchen,Ahmad ya harari Aamna yace ke kika zuba lemon yau? Ni gidana ba komai a ciki na ci,Zuhra tayi Dariya ta shige kitchen ba abinda babu ta Bude fridge ta ebo masu sanyi ta dinga kawo musu,Saura cups cewar Bash,Brown yace na gwangwani Zaki kawo Mana Ni da Mashkoor,Jibson ma yace Tawaga Miko min wancen juice din,Ahmad yace kamar zaiyi kuka yace Dan Allah karku Bata Mana gida mu Bamu kawo yar aiki mace ba tukun,Amma tace Kai kaci uwarka Ahmad Dan Iskan yaro anzo tayaka murna sai korar mutane kakeyi tun dazu fa Muna jinka ko kunya baka ji Wai? Baki ya turo ya kalli arewa da Kansa,Daddy Dariya yayi kawai,Yace ku tashi mu tafi Dan Allah,Mummy Tace sai mun Sha wlh sai dai ya mutu,Baba yace yaro daga cin arziki Anya Kuwa ka gaji halin Babanka dama fa na Gama ganeka Dan tsumulmula ne Kai Haka Rannan ma Ina son Nama kaki siya min Kai sai dai matarka ta moreka Banda danginta wallahi ka canja Hali fitsararre har startime ka sace min da radio har gida na Ni na taba cewa ka biya Ni?,Dariya akayi Mashkoor da Ahmad ne sai gidan su Aamna su Suka San zancen,Baba ya Basu labari aka dinga dariya, Mashkoor yace Nima gani nayi ya fito da su a hannunsa, Baba yace to har yau Bai dawo da su ba Kuma Bai biyani kudin ba, ka jawo na dinga zagin matata saura kadan na koreta, zunubi biyu ka dauka ga na sata ga Kuma na yunkurin raba aure. Sun fara Sha aka mikawa Ahmad lemo yace bazai Sha ba shi,ai Kuwa sai da suka Sha abinsu 10pm suka Mike zasu tafi,Humaira da Zuhra su Suka sake gyara palon da komai sannan Suka yiwa Aamna Sallama zasu tafi,Zuhra Tace Aamna ba ko dan kuka ma babu? Ahmad yace to jiya aka Daura Auren ko yau da zata Yi wani kuka,ko so kike Yi ki zuga min ita, Mashkoor Bayan su Mummy sun fita ya radawa Ahmad ko mu zauna muyi tamu Adduar? Zagi ya aika Masa Suka fita suna cewa sai mun dawo cin girki,Ahmad yace Nan da 3weeks ba,karku Zo da wuri Ni Zan na zuwa Muna haduwa Amma Kar na ga kafar wani shege a gidan Nan wallahi bazan Bude muku kofa ba,Suna ta dariya,Rakasu yayi suna ta Hira Brown yace yau ba sauki? Till down cewar Ahmad,Allah sarki Aunty Balaraba yau zata Yi larabci ta godewa Allah cewar Brown,Dariya sukayi harda tafawa yace ku tafi Dan Allah,Bash ya Mika Masa ledojin da suka zo da su yace gashi Kar mu manta,thanks ya Furta yace sai munyi waya oya maza aje...aje...ya juya yayi tafiyarsa,Tawaga yace Kai jaraba King Kamar ba shi ba,to Nima nayi sauri Yar China ta tazo,In Banda kuka wannan me zata maka cewar Jibson,Dan Kai taka bazawara ce shine kake min bakin ciki,Jibson Yana dariya yace Ni dama bana bukatar Virgin wlh ban damu ba,Kuma Nima na taba yin sex Allah na tuba an bani bazawara kaga 1-1, Brown yace Ni Kam na dauki jinin Larabawa nima kwana Nan sai yalla yalla tafiya sukayi abinsu. Ahmad Kuwa Yana shiga Aamna ta Shiga wanka a Bedroom dinta Wanda yake nata ne,Bedroom dinsa ya wuce tare da yin wanka shima,wasu sababbin kayan bacci ya saka milk color wasu silk dogon wando da Riga me dogon Hannu,Gaban rigar me botin ne sai Bai kulle ba ya barta a Bude Yana fesa turarukansa Aamna ta shigo tana zuba kamshi sanye cikin wani Dan short da kadan ya rufe Mazaunanta sai rigar karama me Hannun bra kirjin rigar me tafe da bra ,wasu pink da wani bakin lace black a kasan rigar da wandon,sun kamata daf daf, ta zuba kyau,Da sauri Ahmad ya juyo Yana Kare Mata kallo Yana murmushi,Hannayenta da kafafunta yake kallo lallen da aka Zana Mata ya Masa kyau,Bai taba ganinta da lalle ba sai yau,Lalle Yana birge shi a rayuwa,hannayensa ya Bude taje tare da shigewa kirjinsa yasa hannayensa tare da Rungume ta a kirjinsa Ido Suka lumshe a tare itama ta rungumeshi,Hannayensa ya maida saman Mazaunanta Yana shafawa Fuskarsa tana gugan gefen fuskarta,a hankali ya furta kin Kara Dadi skin dinki Kamar flour,Kamshinta ya Shiga shinshinawa,Aamna Tace kaima ka Kara kyau da kiba My King,janta yayi Suka zauna saman wata sofa ta hutawa,shape din love ne da ita a Samantha Suka ci abinci shi ya Bata a Baki har Suka Gama ta Kai kayan kitchen tare da brush,shima haka lokacin data shigo ya juya Yana jona system dinsa a charge da wayarsa ya kashe komai. Ta baya tayi tsalle tare da daneshi tana Dariya a Haka ya Gama jona charge din Yana dariya shima yace Zaki Balla Ni fa My World,jawota yayi gabansa tare da sa hannayensa ya tallafo kumatunta Yana karewa kyakyawar fuskarta kallo a hankali ya hade bakinsu wuri daya ya Shiga tsotsa cikin salo da Iyawa,Martani take maida Masa ta Rungume shi sosai tare da cewa a kunna Mana kida,an Gama ya Furta tare da kunna tv ya kamo American film me kyau,speakers kuma na kirki ya kunna Shegun Nigerian music,volume din film din ya rage sosai ya rageshi har karshe ga film nayi Amma ba magana sai kida ke tashi kasa kasa,a kunne ya rada Mata yau Naga Alama anyi Missing dina? Sosai ma ta Furta da wani salo,yatsunta yake ta kallo yace lallen yayi kyau ki dinga Yi min Ina so, Alright Inshaallah,Gashinsa ta kalla ta fara Dariya Tace ai sai yanzu na kula wlh Ashe an canja style,wow kayi kyau My Man,Gashin ta gani da yawa an kwashe kadan gefe gefe an Kama gashin an wani murmude shi kamar anyi twisting Amma Kuma ba twisting bane,abinka da gashin Larabawa gashi kyakyawa jajir da shi duk abinda yayi kyau yake masa,Aamna tana ta kallon gashin tana murmushi tana ta faman shafawa tace kayi kyau Allah,duk kyan da kitson ya maka wannan har yafi wancan kitson,ai dama nasan zai Miki shi yasa nayi,yanzu tunda nayi aure duk wata za a dinga sabon style din Aski sai kin gaji da gyaran gashi,Aamna Tace mashaallah,Dan gemunsa da Sajensa ta ja tana shafawa tace shima yayi kyau an sake kalkale min shi,Hannayensa suna saman hips dinta Yana shafawa tana jikinsa a rungunme ya zauna gefen bed tare da zaunar da ita a cinyarsa Yana Furta ai duk ke nayiwa. Tana saman cinyarsa ta juyo tare da Zama daram a cinyarsa suna facing juna ta tura shi saman bed ya kwanta ta kwanta a samansa tare da Buda Hannayenta ta sarkafasu cikin nasa kirjinsu ya hade Dana juna,Kallonsa takeyi shima Haka,kiss ta fara Masa a goshi tare da sa harshenta ta fara laso goshinsa zuwa Karan hancinsa,Cikin wani slow ta saka bakinta me kamshin mint cikin nasa me kamshin strawberry tana Masa wani zazzafan kiss,dama kadan yake jira hannayensa dake saman Mazaunanta Nan take ya janye Dan wandon Dake jikinta ya cillar da shi,Ya Shiga lailaya Mazaunanta yace Kai My world sun koshi me kike Basu ne haka Yana magana yan Dan marinsu kadan,can karshen Bed Aamna ta koma tare da Kama Ahmad ta cire Masa rigar Tace Wai kaima sai ka wani saka dogon wando kasan Kuma Ina nan ta furta da shagwaba kamar zatayi kuka,Kara susucewa yayi yace idan kina min shagwabar Nan My World mantawa nakeyi da komai,kayan jikinsu Suka cire kaf,Aamna an goge an fetsare me gyara ta koya Mata yanda zata cire kunya ta tallafi mijinta,Da jikin fuskar bed din ta jingina,Nonuwan Nan a tsaye sosai manya sai sheki sukeyi,Ahmad ne ya kwanta a samansu,Ido ta lumshe tare da riko hannunsa ta Kama Yatsansa na tsakiya ta sa a bakinta tana tsotsa,Kirjinta ta sake Mika Masa Tace My King.... kafin tayi magana ya Gane nufinta ya fara mursitsika boobs dinta Yana murzasu,Zan Sha abina My world ya Furta tare da daura bakinsa a kan Daya Yana Sha Yana shafa su, Aamna ta wani Yi kamar gawa sai Nishi takeyi tana shidewa,Itama tana sarrafa shi yanda yake so,ai Kuwa Suka sake rudewa tun sunayi a hankali Suka koma Yi da zafi zafi,sai da suka Gama gigita kansu da lobayya me tsayawa a Rai sannan Ahmad ya gyarata sosai yanda zaiji dadin buga shagalin. Aamna tace a hankali King please Kar naji zafi Dan Allah naji dadi Nima,Murmushi yayi yace Inshaallah yau sai kinji dadin manta Uwa kema,Dariya ya Bata tace au sunansa manta Uwa? Ahmad yace ae Mana ai na sa Masa suna manta Uwa sabo da lokacin baka tuna kowa My World,Har Ni? Yace har ke ai Nan wajen Kawai shi ake tunawa Ina Yi Ina sa Masa Albarka ya Furta tare da shafa wurin Aamna Tace Ahhhh.....tana lumshe Ido,gaba Daya ta Gama jikewa,ai Kuwa yau a hankali ya bi da ita Yana abinsa hankali kwance,Aamna taji Dadin yau Amma ta danji zafi sabo da Bata Saba ba Kuma ta sha gyara,Sai da suka samu gamsuwa sannan ya kwanta ta sake makalkale shi suna kissing juna,a hankali yace kin Karo wulakanci Baby,kin kara Honey,kin ninka da sau dubu,My world manta Uwar Nan Taki yayi,Ni Kam a duniya na dace ya Furta tare da sake makaleta a jikinsa,baccin ma yau kasa Yi Suka Yi sai dai Hira sukeyi iri iri. Yace yau sabo da murnar wannan ranar bazan iya bacci ba,Aamna tace Nima haka Mijina,Ina sonka da yawa,Yana shafa fuskarta yace ai Ni ban ma San irin son da nake Miki ba,bana so na nace Ina sonki yawa ne Beb na kwaikwayeki Ina mugu mugun kaunarki,Breast dinta ya shafa yace Dadi gare su wannan ba a ba yaro me kyuya,Dariya Aamna tayi,yace zanyi second round? sai da safe cewar Aamna tana rufe Fuska tare da shigewa bargo,kwaye bargon yayi yace Ina kallon abina kina wani boyewa pls ya furta da shagwabarsa. Aamna tana shafa kirjinsa tace King? Kamar me bacci Haka ta Kira sunansa,Ina jinki yace Yana kwantar da Kansa saman lallausan gashinta me kamshi,Tace zanyi aikin Gomnati? da sauri yace No Allah kiyaye,Ina da kudin rikeki Zaki wani wahala,Aiki ai wahala ne,duk Rana da gantali ya lalata min ke,Shi Aiki ai zuwa ne akwai Wanda idan Mijin baida Hali ya kamata tayi Aiki ta samu su rufawa juna asiri ta taimaki dangi da Yan Uwa,ko Mijin Yana da shi baya Bata to ya Dace tayi aikinta ta samu nata. Aamna Ni Kinga dai Allah ya hore mana,Ina da shi Ni ba stingy husband ba,duk abinda kike so Zan Miki ko Mene,duk wani taimako da zakiyi Zan Baki kiyi taimakon,Zaki ci Zaki Sha,sutura sai kin zaba ga Muhalli me kyau to me kike Nema,ai wallahi wani aikin da Mata keyi rashin godiyar Allah ne,wasu Kuma Dan kar suyiwa mijinsu biyayya suke Aiki Kinga suna da kudi sai abinda Suka ce da shi,ai mace Bata hadu ba wlh ta fado ace mijinta bazai iya Mata Abu ba sai tayi Aiki ko ta fita ta Nemo sannan zata siya kanta ko Sabulun wanka to ta Gama fadowa,ai idan mace ta cika mace Kuma ta hanyar bin aure da Umarnin Allah da Sunnar manzo,ladabi,biyayya,kwalliya tsafta,kula da Miji iya girki, kullum mace cikin kamshi da tsafta take,sannan ace duk kwalliyar da zatayi tayi ta zamani wacce zata birge wlh sai ya yaba Kuma idan ta daraja kanta Bai Isa ya hanata hakkinta ba. Amma Mata sun watse,kwalliyar ma a gida baza tayi ta kirki ba Sai Kuma Tace miji Wai yaki yabawa,duk ta lalata kanta,Miji yazo ya Iske gida gashi Nan ne dai,toilet ba tsafta jikinta gashi Nan dai,ko ta samu kudin sai dai ta Tara tayi dinkin zuwa gidan biki,idan zata biki kamar Yar Gomna Haka zata fito a gida Kuma a sa wasu banzan Kaya,magana Bata iya ba,babu Iya sarrafa fushi lokacin da me gida yake Nan,Iya kwanciyar aure sai mace ta zauna sharaf Kamar Randa,sai jarabar Shan maganin Mata an bar sauran abubuwa masu muhimmanci ba a yiwa Miji su,Tunaninsu maganin Mata zai sa Miji ya canja ne,an kasa bin dokokin Allah na aure da Sunnar ma'aiki tare da kuma salo da dabaru iri iri na zaman aure an kasa Yi sai uban Shan maganin Mata,a Gama Sha Kuma Miji yaci ubanta washe gari,an kasa ganewa gaba Daya sai lalacewa aure keyi,mace tana Budurwa tana kunya ga aji da respect a Gaban saurayi amma sabo da ta aure shi tunaninta ajinta ya Kare Wai an Zama Daya ai Bata kunyar furta kalmomin da suke rage darajar mutum,Kashi,tusa,da duk wani abin sirrintawa ita ta daina Wai ai kowa yanayi,wannan rage darajar mutum yakeyi a wajen mutane,ya daina ganinki a Yar gayu,kin Zama jakar Mata,a waje kullum Ana da Bra a matso kyau, idan anyi aure wata a gida ta daina sawa,duk ta kashe kanta idan ya shigo baiga komai cif ba,lokacin bacci sai a sakata a Wala ba a son a sa bra, Amma Ina da yawa ba'a ganewa, akwai abubuwa da yawa da suke rage Kimar mutum a Gaban miji,ko Miji a Gaban matarsa an kasa ganewa, Aamna Tace to ai Ni da na sani wajenka Nazo ka min lecture,duk a Ina ka sani? Yace kin dauka Bamu da hankali to muna hirarmu da su Jibson,idan Muka ga hauka Muna tattaunawa,Ki shirya yarinya duniya ta waye baza ayi min Haihuwar awakai ba,idan kika Haihu sai kinyi 4-5 yrs Baki Karo Daya ba,Aamna ta turo Baki Tace Haka Kawai ka cuceni ka min kishiya tazo itama ta wuceni,Murmushi yayi tare da rungumeta yace Idana kina min abinda nake so My world kin tsira Ni dayar ma da Yaya Mummy ta min bare wasu Kuma,Aamna Tace to Zan dage Allah Kuma ya amsa addu'ata Allah yasa Ni kadai aka rubuta maka zaka aura a duniya,yace Ameen My World,karfa kiji Dadi ki saki jiki Matukar ba'a bani Manta Uwa yanda ya kamata Ana min style iri iri to lahu na fara neman wata,Aamna tace Haba kaima kasan bazan hanaka ba,ai ko yaushe I'm available Kawai ka zo,Yaga Aamna ta tsorata da kishiya Yana ta dariya a Haka har suka tsarkake jikinsu ya kashe musu kallo da kidan tare da light Suka Yi baccinsu. Washe gari Tawaga wanka ya dauka da motar Ahmad ya tafi gidan su Yar China zance,Yar China taci kwalliya ta sa Atamfarta me kyau dinkin ya Mata kyau gata fara ta yafa dan mayafinta ta leko Tace shigo Mana Iyalle Tace ka dinga shigowa ciki,Tawaga ya fito yasha Shadda wata ruwan kwai,Yar China tana ta kallonsa,Tace Yaya kayi kyau,Tawaga yace kema haka,Yar China Tace Allah Yaya nayi kyau? Yace sosai ma,Tace wayyo dan Allah sake fada min muryarka Dadi ne da ita,Dariya Tawaga yayi a ransa yace Ina Shan shirmen Yara na shiga uku,a fili yace Allah kinyi kyau,Yar China ta fara murmushi tare da yin tsalle ta dafa kafadarsa da kyar tana cewa Yeeee na kamo ka na kamoka Ashe Nima me tsayi ce sai taci gaba da tsalle Wai sai ta tabo Kansa,sai da ya Mata tsawa,Tace gashinka me yawa yayi kyau a Ina aka maka askin Nan? Yace wani ne,ya sunansa Dan Allah? Yace Salman Tace ya birgeni Allah ya Masa Albarka inji Iyalle tace Haka za a dinga cewa,tunda Ya Shiga Iyalle ta shige dakinta ta barshi da Yar China a Palo tana ta kiriniya Taki Zama daga tsalle tsalle sai surutu . Hannunta ya kamo Yar China ta fisge Tace da shagwaba Allah Ni Allah idan ka tabani sai naji Wutar lantarki a jikina wani zuuuuuuu......Tawaga Yana ta dariya yace to zauna muyi hira Mana kince kin min kwalliya Kuma kinki nutsuwa na kalla,Yar China ta rufe idonta Wai kunya tace Kai Yaya Ni dai ba ruwana Kar Iyalle ta jini,Zama tayi a kusa dashi ta dafa kafadarsa Kamar sa'anta Tace Wai kaima baka da Baba kaima? Tawaga yace indai Kinga Ubana a duniya ki harbe shi na Baki dama,Yar China ta kyalkyale da dariya tana Wasa da kafafunta Tace kenan ya rasu mun Zama Daya,Tawaga yace ae tafi tayi Tace Good gwara muyi yawa a duniya Duk mu Zama marasa uba,Nima idan kaga Uwata da ubana ka harbe su bani da su idan ka gansu Kuma ka harbe su,Dariya yayi yace an kusa bikinmu fa na Gama shiryawa,Tace Dan Allah? Yace ae Tace to ayi Mana Nima na shirya,Dariya ta bashi sosai dololancinta yayi yawa,gaba Daya Iyalle ta lalatata zai Sha Aiki,sai dai yayi ta Binta a haka,Nawa ne Yan Secondary masu hankali da nutsuwa Amma Banda Yar China ita goyon Kaka ce,Gata da tsayi ta girma sosai Kirjinta a cike fam da kyan dirinta hips dinta mashaallah sai tarin kuruciya,Kallonsa tayi tana tsaye a gabansa Tace na shirya ayi bikin Mana Nima,yaushe za ayi daurin auren? Zan kaiwa kawayena Iv ne,Ni sauri nakeyi na gayyato su Allah ta karasa da shagwaba harda dire diren kafafu. Tawaga a ransa yace tun kafin auren Zan kaiwa Aunty Balaraba ita ta Dan Wayar Mata da Kai. Yace ki shirya Zan fadawa Iyalle jibi zamuje ki gaisar da Umma ta da Kuma Aunty Balaraba,Tace matar abokinka da kace?yace Ashe bakya mantuwa,Tace Allah ya kaimu. Zama tayi tare da nutsuwa yace lafiya? Tace tunawa nayi yau Ina wani Abu amma Iyalle Tace Kar na fadawa kowa,tun Rannan nace Zan fada maka har Chemist Iyalle ta kaini wancen watan yanzu wannan watan da maganina Bamu je chemist ba,amma Iyalle Tace ba a fada wai,Bai kawo komai ba yayi tunanin shirmenta ne yace fada min bazan fadawa kowa ba,Tace to ai sirri ne,yace ae Tace sai dai na rubuta maka kunya nake ji,Indai sai kin rubuta bana so,Kai Yaya to shike Nan tunda kayi Fushi Zan fada maka,Fuska ta rufe tare da cewa Period na fara wancan watan inji me Chemist,Dariya ta bashi ma yace duk girmanki sai yanzu kika fara? tace uhm to ya zanyi na Dade Ina ta jiransa yaki zuwa,kawayena suyi ta min tsiya suna ce min yarinya to yanzu Nima yarinya ta girma na Balaga na huta da gulma,Tawaga Kansa ya dafe Yana tausayawa Kansa shi Bai San Taya zai iya canja Yar China ba. Sharhi fans AsmaBaffa 10/26/21, 2:19 PM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 96-100 Official By AsmaBaffa Page naku ne Laweewarra Ummu Amaturrahman Sadiya B Ahmed Nana Khadija Muhammad Nafeesat Umar Muhammad Sa'adatu Tijjani. Kallon Yar China yayi Kawai Yace zauna sosai ki daina wannan tsalle tsallen,Zamanta ta gyara tace to,yace kika ce kin Balaga? Yar China Tace ae na Gama cika ka'idojin balagewa....Tawaga ya dinga dariya ya kasa dannewa Wai Balagewa,Yar China ta tsura Masa Ido tace kana ta min Dariya ai dai gaskiya na fada Kuma Dan baka sani bane sauran duk na gama yinsu dama wannan abin ne ya rage shima jiya Allah yayi Karasowarsa nace Alhmdllh na gode Masa,Tawaga yace Uhm kice ke tun jiya kazama ce,Yar China ta Mike zatayi bayani ta zaunar da ita yace Fadi a zaune,Tace to Iyalle ta koya min tsafta ai ka gani ma mu masu tsafta ne idan bani da tsafta kaji kamshi a jikina yau? Shinshina Ni kaji kamshi nakeyi,Yama sunanki na gaskiya?Halimatu Sa'adiya,Baba na Kuma Mustapha,Sadiya Mustapha China ake ce min,Dariya sukayi yace ke ba Yar garinsu ba harda sa wani China,Ai za a fi ganeni cewar Yar China,sai bayan yayi Sallar Isha ya bar gida tare da bawa Yar China 5k. Daddy washe gari duk wani shiri ya gama da Nemo Baban Aamna,an samu sa'a ya samu number dinsa fada yayi ta Masa yace zai sa a dakko shi yazo yaga yarsa itama ta ganshi kafin Nan gaba itama Aamna taje taga danginta,Baban Aamna ya Amince zaizo Inshaallah Nan da kwana Uku ko biyar. Tunda Ahmad Suka kwanta da Niyyar idan Asuba tayi za a Kara yin Manta Uwa ai bacci barawo ko farkawa basuyi ba sai ma makara da sukayi sai ganin hasken Rana suka Yi,a tare suka farka Suka kalli juna tare da sakarwa juna murmushi,a kwance suna facing juna cike da shaukin kauna suna wani murmushi a hankali cikin Muryarsa ta Wanda ya tashi daga bacci ya Furta I love you kasa kasa,jikinsa ta kalla me kyau sumul sumul Wanda rabinsa a waje yake Rabi Kuma Yana cikin bargo ita kuma iya kafadunta ne a waje Bargon ya rufe daga Breast dinta Rabin Boobs din ma a waje suke itama tana murmushi ta daura Hannunta a saman wuyansa ta baya tana shafawa a hankali Tace Love you More My King,gefen fuskarta ya shafa ta lumshe Ido tare da Bude su a kansa,Daren jiya ya Shiga tunanowa yanda yaji Dadi fiye da tunaninsa a duniya,wani sonta da kaunarta ne ya sake shigarsa,sake shigewa yayi jikinta tare da furta Ya jiya My world?,kin tuna? kunya Aamna taji ta rufe Ido tana tuna Sanda Yana yi tana Kiran My King zafi da Dadi-dadi,abinda taji jiya shi ta dinga fada Masa Tace zafi Tace Dadi Kuma,Shima Dariya yayi sannan yace tashi muyi wanka da Sallah mun makara,a cikin bargon ta maida rigar baccinta shi Kuma ya sa Boxers. Kasa ya dira sannan ya dauketa irin yanda ake yiwa jarirai,kwacewa tayi ta gudu bedroom dinta,Dariya Kawai yayi ya shige toilet dinsa,wanka kowannensu yayi tare da Gabatar da Sallah sannan ta zura wata Yar gown me Kama da t-shirt tana da Fadi amma iyakarta gwiwa, Lipgloss da powder ta shafa tare da gyara gashinta ta sake shi Kamar wata balarabiyar Masar Haka ta fito,wata Humra me kamshin gaske ta shafa tare da fesa wasu mayun perfume sannan ta kalli kanta a mudubi tare da juya baya ta kalli kanta Tace Allah na gode maka daka azurtani da duwaiwaka Haka ba tare da na Sha kwaya ko Allurar bature ba,bakinta ta kalla tace ga bakin kiss Dan cukut Dole ma King yaji dadin wannan lips din,Kirjinta ta kalla tace Uhmm....ba kwaya ba cream gashi Nan bul bul,King ya zuka Nan gaba jariri ya zuka ruwa tunjum,Dariya ta Bawa kanta tace Allah na gode maka ta fita kitchen,tana Shiga ta Iske Ahmad a ciki sanye cikin 3qrt da Yar t-shirt marasa nauyi Yana ta soya chips,tunda yaji kamshi yasan itace ba tare da ya juyo ba ya fara murmushi Yana jiran hug ta baya yaji Shuru,kusa da shi ta tsaya a gefensa tare da Kallonsa tana murmushinta tace Yau ka hutar dani kenan? Baki ya turo cike da shagwaba yace Hug dinfa? Warm hug mana pls my World,kin manta farkon da Mum ta kawo min ke gidana sai da kika ce ta dole nayi Hugging naki,Aamna tana Dariya ta Rungume shi ta baya a Haka ya hanata yin komai shi yake girkin. Haka da ya Gama hada musu komai ta tayashi dauka a Palo suka zauna Bai damu da wani Dining ba,saman sofa suke ya zaunar da ita saman cinyarsa suna kallon wakokin turawa a tv,a baki ya bata shima Yana ci,Wakar Rihanna aka saka shigarta tsira tsira,Aamna ta Suri remote tare da canja Chanel,why? Ahmad ya furta,tace haka kawai sai kallon jikin wata kakeyi idan ta birgeka ko aka hasko na wata Wanda ya fi nawa Kawai su jaja min masifa,dariya yayi kawai yaci gaba da kula da abarsa,Su Kuwa ma'aikatan gidan idan Suka gama aikinsu tafiya sukeyi Wanda suke main gate na Estate din suke kwana,Ahmad suka tamabaya ba Wani abu?yace ae zaku iya tafiya idan Ina son wani abu Zan kiraku a waya,Ya kasance gidan Ahmad ba kowa sabo da wai Amarci sukeyi Kar a sa musu Ido. Bayan sun gama Aamna ita ta gyara ko Ina Yana dan tayata suna soyewa,a haka ta gama komai sannan ta wanke musu kayan baccinsu na Jiya da abinda suka bata, Bedsheet din bedroom din Ahmad ta canja sabo sabo da Wanda aka sa jiya duk sun lalata shi,daukan Sheet din yayi yace muje mu wanke a garden akwai tap,dauka sukayi da Omo sai da ya rakata Suka zaga gidan ta Sha kallo sannan a garden wurin tap din har da tiles,a Kai ya shimfida bedsheet din yace a Nan zamu dinga wanke kazantar mu,Dariya Aamna tayi Suka saki ruwa tare da zuba Omo Suka hau Kai tare Wai da kafa zasu tattaka Kamar masu kwaba,a Haka zasu wanke kawai wasansu sukeyi.,da Suka gaji Hannu Suka sa Hannu. Bayan sun Shanya ciki Suka koma Yana rike da hips dinta. Da rana abinci ya musu order lafiyayye yace ba girki Mai wahala sai gobe,5pm ball ya dakko musu Suka koma ta kusa da garden yace suyi,ya iya shi amma haka suke yi Yana ta cinyeta,tana binsa da gudu idan ya kwace ball din har rigarsa take rikowa suna ta dariya suna buga abarsu cike da nishadi,Sai wurin Magriba suka hakura,goyata yayi a bayansa suka shiga ciki tare da Alwala ya wuce masallaci ita Kuma a gida tayi sallarta,da dare ma abinci order yayi abinda suke shi Suka ci,Aamna ta dirki maganin matanta ba tare da ya sani ba Wanda sai gab da za a kwanta ake Sha,tasan Ahmad ba kyaleta zaiyi ba taga ma kokarinsa da ya barta sai dare. Ai kuwa Yana dawowa daga Sallar Isha yace muje ki min wankan bacci,Fuska ta kwabe Yana binta da mayen kallo ya furta kinyi kyau My world,tashi ya furta tare da kashe Mata Ido daya Yana Mika mata hannunsa,hannunsa ta Kama tare da mikewa,ka Bari sai anjima idan munci abinci,no ni yanzu nake so dare mahutar bawa ai da anyi Sallar Isha Kawai Ango ya hau bed dinsa a bashi gadonsa,abinda na gada a jikinki Zaki bani,kin San fa nayi kokari tun jiya fa haba yau duk jina nakeyi ba Dadi sabo da banyi wani aikin Lada ba,na yini a banza ba tare da nayi aikin lada kwakwara ba,Ina so na tarar da Allah salin alin muje dan Allah ya ja Hannunta Suka shige tana Dariya yanzu duk abin Nan Ahmad ya maida shi kamar karatun Qur'ani komai yace zaiyi aikin lada,ko da Suka Shiga toilet cewa yayi cire min Kaya so nake na cika mizanin Lada na taf,Aamna ta bude baki tare da cewa ka dinga yi a hankali King,hararar wasa ya aika mata tare da cire kayansa da Kansa,Aamna ya cirewa Yana cewa idan kika sake sai dai a San miki ladana ki tsallake siradi,Kuma wlh ance wata kugiya ce take Fitowa daga wutar jahannama tana fisgar wasu dake tafiya kan siratsi,wani ya wuce kamar walkiya,wani Kuma ya wuce kamar an harbo kibiya,wani ya wuce da gudu,wani ya wuce da rarrafe sannan kasa Kuma wutar jahannama ce karafunan suna fitowa Suna yagar fatar masu wucewa ta siradi,wani duk jikinsa yaji rauni ko Ina Haka zai tsallake da kyar,dole Kuma ta kai kowa zai bi ya shiga Aljanna,sai na bi,sai kinbi,kin San dai a lahira ba wanda ke tuna wani,duk son Nan naki da nake bazan iya tunaki ba a lokacin ta kaina nakeyi to ki dage Kar ki jawo na Zama na Hurul ein kadai,Aamna tana Dariya tace amma Kun San da haka kuka dinga shaye shaye,ai ya wuce wannan tunda mun tuba,to dole Kuwa na dage Kar matan Aljanna su kwace min kai Nima Ina so nayi mulki a can cewar Aamna. Ahmad yace to ki dage kinga dai ga hanyar samun lada a saukake ga dadi,kayan jikinta ya rabata da su tana Jin kunya sai nokewa takeyi tana Kare jikinta da hannunta,ki daina kunyata Baby ni kunyar Nan cutata takeyi Kuma ma ni ba kaunarta nakeyi ba please ki daina,I'm serious bana so,Aamna tana rufe Kirjinta da hannunta tace to,to ai gashi nan baki daina ba My World, shower ya sakar musu Aamna sai Kau da kai gefe takeyi,taki yarda su hada ido,da Kansa ya Mata wankan shima yayi,duk ya hana Nonuwanta sakewa da shafawa,duk ya tayar Mata da hankali, cikin wata Yar kujera ta Yan gayu ta karfe Kalar tiles din fara itama idan kana bukatar Zama kayi wanka,ita ya ajiyewa Aamna yace zauna Dabas,Dariya ta dinga Yi yanda tsofaffi suke cewa idan za ayiwa mace wankan jego,bata San me zaiyi ba ta zauna,yace bude kafafunki yana wani lumshe Ido,mene ne? ki bude Mana magani Zan miki, idonta ta rufe sannan ta bude cinyoyin. Dan Tsaki yaja yasa hannu tare da wangale su,saukar ruwa taji me zafi a wajen,Wai ashe gashi zai mata Wanda idan yace Zama zatayi cikin ruwan zai Dade Aamna tace da zafi fa, shower ce ya sirka ruwan take zuwa da zafi zafi Yana fesa Mata sosai,Ya furta to Ni baza ki jawo min ba da tsoronki bakya wani gashi sosai,Aamna tace Ina yi Allah,Ina bazan Kyaleki ba ni,sai da taji ruwan zafi sannan yace to an Gama,dama ita Bata daurewa ruwan zafi,sai taji wani Dadi a wajen,yace Mummy tace kina Zama a ruwan Magariya ko? a Ina kaji? naji Sanda ta fada Miki mana,ta Mike da Niyyar daura towel ya kwace yace jikina bai fita ba sai mun sake wankan Nan,shagwaba Aamna ta dinga yi harda jawo Mata kujerar Kamar abin kirki ya sake cewa Dabas,kallon kujerar tayi yace Dabas nace,Zama tayi yace ba wanka za ayi ba yau a Nan za a bani Manta Uwa. Aamna zata Yi kuka tace dan Allah ka Bari na Saba sai kayi style din kake so,karfa ki gaji Umma kina ji dai Baba yace kullum wayyo wayyo ko kema wanzamin yayi Aika aika ne?Dariya sukayi gaba daya,dakkota yayi suka dawo saman bed,gaba daya yanda ya jagwalgwala Aamna a toilet ya tayar mata da hankali ya fuskanci Aamna akwai jaraba itama,a ransa yace ashe Zan rakashe Nan gaba gwara da na samu irin Aamna,dukkansu rigar wanka ce sanye a jikinsu farare saman bed Suka zauna a Haka,Aamna kanta daure da towel shima fari tas,jira take Kawai yaci gaba da murzata taga Kuma bai fara ba ya tsaya latsa waya Yana duba sako,leka Wayar tayi taga ai WhatsApp yake dubawa,a hankali ta sake muskutawa ta matsa jikinsa,Yana ta danna wayarsa Yana jinta ta zame Masa rigar baccin ta koma kasan kugunsa,itama igiyar tata ta kwance tare da cirewa ta ajiyeta gefe,ta baya tasa hannayenta tare da rungumeshi a jikinta,Kirjinta manya ta shiga murza masa a jikinsa tana manna Masa su,Ahmad ya sake kamawa da wuta ya dauki zafi,juyowa yayi suna kallon juna ta fara kissing dinsa tana Nishi,Wayar tana a hannunsa Kiran Brown ya shigo,dagawa yayi ta koma kirjinsa tana Masa wani salo a nipple dinsa tana shansu,Dick dinsa take shafawa a hankali ai Ahmad a Wayar Muryarsa na rawa yace Brown ya akayi ne?..ai wani abu da Aamna da ta Masa Bai San Sanda ya saki Wayar ba sulululu ta Fadi a kasa,Brown Yana ta hello hello sai kashewa yayi ya sake Kira yafi sau uku amma ba'a daga ba Kawai ya hakura. Shi Kuwa gogan tuni ya juya ya bada amanna suna shoshalewa kamar zasu kashe kansu,sucking ya fara yiwa Aamna bata San Sanda take cewa ka Iya ba,Baby ka Iya....Dariya ta bashi ya bita a Haka idan tace ka Iya yace ae na Iya sosai....wani salo ya Mata ta kankame Kansa da hannayenta jikinta Yana wani uban rawa,tace Baby ka gama Iyawa ka huta....Ahmad yace ai na kware My world,tace basira ne da Kai.....a ransa Yana ta dariya,kukan dadin ma ta rasa wanne zata yi lokacin Daya fara Mata Wasa da Yatsansa a down......tayi wani shidewa tare da furta na samu Kalar da nake so.....ganin ta birkice yasan ba matsala,cikin rada yace My world na yi? Yesss....yess....ta Furta cikin Kalar muryar da yake mugun so idan tayi magana,Kuma sai ta Gama kaiwa karshe take yin irinta,sabo da haka a nutse yake Manta Uwa dinsa,tana Jin dadi kuwa,shi Kuwa yanzu ya karbe aikin zubar da surutun kalamansa barkatai. Sun Dan dade kafin Suka samu gamsuwa kusan a tare. Sai da suka gama nutsuwa Aamna sai murmushi takeyi ita kadai ta manta ma King Yana kallonta tana ta murna ita kadai tana Jin wani nishadi tana tuna abinda sukayi yanzu dama su dawwama a Haka,Ahmad shima bangarensa haka ji yake kamar ya hadiye Aamna,dariyar ta mene My World? Kunya tasa ta dukunkune a cikin blanket tana Dariya,yace na Iya ko.....Yana kokarin janye blanket din tana dunkulewa tare da dukunkunewa a ciki,Haka su Aamna Suka kasance suna darje Amarci har na kwana Uku. lokacin Kuma Brown yaje wurin Humaira wacce suke tare da Mummy a gidan Amma sun Sha soyayyarsu, Mummy tace Brown ya Kai Humaira wurin Aamna zata Mata yini kafin jibi su tafi Lagos,a ranar Kuma Tawaga ya dakko Yar China taci gayu cikin sabon lace dinta Daya dinka Mata wani Brown and sea blue tayi kyau Riga da skert,takalminta me Dan tudu da mayafinta da jaka gaba Daya Brown Yar China tasan darajar wanka,a motar da Daddy ya Siya musu tasa baka ya zaba a ita ya dauki Yar China,gidansu da Suka tare Wanda yake a matsayin na Ahmad a da shi ya fara kaita ta gaisar da Mamasa da Yan Uwa,Dama komai tsakaninsa da abokansa ya bawa Yar China labari,Haka Nafeesat da Sameera duk sun San komai Suma irin alakarsu da abokai,Yar China anga gida me kyau tace Daddy ya kyauta Allah saka Masa da Alkhairi gashi gidan surukaina me kyau na masu kudi,da yanzu sai dai a kaini dan kangon gida,Dariya Tawaga yayi duk da Iyalle tayiwa Yar China magana akan ta nutsu Kar tayi hauka a gidan surukai amma Yar China Bata iya Shuru,har ciki Suka shiga tana so tayi kalle kalle a gidan sabo da ya hadu amma sai danne sabo da Iyalle ta tsawatar,da Sallama Suka Shiga,ai gaba daya taga Yan gida suna ta Fitowa da murna Yara suna ihu da tsalle ana Oyoyo Yaya Ana makalkale Tawaga,Yar China tana kallon ikon Allah,Hafsat Budurwar Bash wacce taci gayu cikin Arabian gown tazo ta tarbi Yar China tana murna sai kallon Yar China akeyi tayi Kama da Yan China sai dai ta fisu Hanci ita,Hafsat tace Yaya ka iya zabe kyakyawa fara,Yar China tace na gode ai haka ake ta cewa yayi dace naji dadina,Dariya Suka dinga Yi Yar China tana yabon kanta,Hafsat tace Kuma kinyi Kama da Yan China wlh,Yar China tace na fisu Hanci Kuma lips Dina da bakina ba irin nasu bane nifa cutata akayi da Yan Korea nayi Kama sunfi kyau Amma sabo da hassada ake cewa da Ni Yar China,Hafsa tace gaskiya kinfisu,ai Suma akwai masu kyau,ae ai irin masu kyan nayi cewar Yar China,Yaran kaf Suka dinga zuwa suna gaisar da Yar China tana amsawa,wani yaro Bai wuce 3yrs ba ya nacewa Yar China sai da ta gaji ta dauke shi tare da dora shi a cinyarta tana cewa to taho Sarkin nacin tsiya,Tawaga Ummansa ya Kira tazo Suka gaisa ta yaba da Yar China Bata da duhun Kai ga hira,Tawaga yace Hafsat shirya muje gidan Ahmad ku gaisar da matarsa,tana murna tace to. Tare da Yar China da Hafsat ya tafi da su,Bash suna waya da Tawaga yaji ance da Hafsat budurwarsa za a tafi ai sai shima ya tafi gidan Aamna,can ya Iske Humaira da Brown Palo,Yar China tun a mota take cewa Nima a layin zamu zauna ko? Idan munje kusa da gidan Nawa ka nuna min na fara ganinsa,Tawaga yace to,sai da taga an shigo unguwa ta kirki Yar China Tace kar dai ka fada min cewar Nan ne Unguwar da Za'a kawo Ni,Hafsat Dariya take Kamar cikin zai ciwo,Tawaga yace Nan ne Mana,Yar China tace na haye,Ni Kam na gama hayewa na baya sai labari,Hafsat tace nima Nan za'a kawo ni abokaine Bash abokinsa,Yar China ta juyo baya tana kallon Hafsat tace ban mu tafa,Suka tafa Tace ba dai wannan Dan santalin ba? Hafsat tace ae da sauri,me Suma fa tafi ta Tawagana tsayi,Hafsat tace shi fa,Hafsat Tace Dan Allah ya kika ganshi? Yar China tace fessss,to shine cewar Hafsat,Yar China tace mun Zama kawaye daga yau,ga gidana ga naki,Idan Muka haifi yara idan zanje Unguwa sai na turo su gidanki,kema Haka ko? Hafsat tace sosai ma,Tawaga ne yace gaskiya kun dameni Kuma,Shuru Suka yi har ya Shiga Estate din ya nuna musu ko Ina,Yar China tace an kure karyar kudi a Nan,ayi ta Neman kudi ba a samu ashe kudi Yana Nan, to a Nan duk tsiyar kudi an gama kure shi. Yar China harda saita sabuwar Wayarta tana ta daukan Hoto Wai zata nunawa Iyalle. Tunda Suka nufi part din Ahmad Suka lalace a kallo,Yar China tace ba sai an fada ba Nan na babban kwaron ne,Hafsat tace ai na masu abin ne,suna Shiga Ciki sukayi Sallama aka amsa Aamna tana zaune tare da Ahmad,Humaira da Brown ga Bash a gefe Daya, Hafsat ce ta radawa Yar China karki nuna bamu waye ba muyi yanga Kar aga Muna kalle kalle kamar Yan Kauye Yar China suna tsakiyar palon amma ita ba sirri da karfi yanda kowa zaiji tace ban gane Kar ace daga Kauye muke ba? Ni wallahi bazan wahalar da kaina ba kallo na zanyi Kawai sai a hanani Allah ya min Ido ace bazan gode Masa ba ta wajen kalle kalle ba,ka gani Yaya zata hanani kallo Wai bazan kalli gidan Nan ba Yar China ta Furta da shagwaba,Tawaga yace wane mutum ai bata Isa ba matar babban Yaya guda yi kallon ki kinji,Ahmad dukkansu kallo Suka tsaya yi suna dariya Yar China ba sirri ta tonawa Hafsat asiri,a fili Ahmad yace tsigarallahu kenan Tawaga za a Sha fama,Yar China ce ta karewa palon kallo sai lokacin ta kula da mutane a ciki Tace salamuaikum bayin Allah ,Aamna ta Aamsa suna dariya,Lokacin Yar China ta kalle su ta juya ta Kalli Tawaga tace Yaya Tawaga ai Nasara Ne tsoronsu nake ji,Turawa ne,Tawaga yace baki ji suna hausa ba hausawa ne, Yar China tace turawa sai kwai dan Allah ku yo min kwai ko guda goma ne na kaiwa Iyalleta gobe ta soya Mana muyi breakfast me Dadi,Ahmad duk danne Dariyarsa sai da ya dara. Humaira tace Ni Kam nayi kawa sa'ata,Yar China tace kaji Yarinyar Nan jibeki fa Nawa kike zakice wani shekarunmu Daya kalle ki fa ni da na Gama Zana waec Zaki ce Ni sa'ari ce,Aamna Suka dinga dariya Wai tayi Candy ita Humaira da take University ma,Brown ne yace Yaya Tawaga ku zauna,Dariya Suka saki Wai Yaya Tawaga. Yar China tace to ku duk abokan Yaya ne bazan durkusa na gaisar daku ba wlh nasan Kun girmeni kuyi Hakuri Ina yininku ta Furta tare da Zama a saman kujera,Suka amsa Kuwa da fara'a,Ahmad tsokanarta yayi yace matar mu. Yar China tace ba ruwana ban ce Ina sonka ba Kai dai da Allah ya maka kyau kaje da abinka Ni sai Aliyu Tawaga,Aamna tace Yar China kike ce mun balarabiya haskenki fa yafi nawa,yar China tace Alhmdllh saura kadan ai a Haifo Ni a zabiya Allah ya tsallakar dani, ku tace ku kunna Mana kallo mana,Ahmad ya kunna kuwa ya kamo India Yar China tace Kaini tashar hausa zalla inda aka san darajata da kimata kasar da Tawaga na yake Amma ka daukeni ka kaini India Ni ba Gunkiya nake bauta ba Sannan ba saniya ba, Ahmad da Tawaga ne suka Mike zasu fita,aka bar Humaira da Brown suna Hira harda komawa Daya palon,Bash da Hafsat aka barsu a Nan palon,Aamna ta ja Yar China wani bedroom. Shigarsu ke da wuya sai Daddy da Mummy sukayi Sallama,sai Kuma ga su Ahmad suna dawo Duk Suka hadu a palo,Jibson ya shigo tare da Mashkoor,Aamna tana Fitowa ita da Yar China sai ga wani Mutum baki siririn gaske sanye cikin suit bakake ya shigo da Sallama,Daddy yace kowa ya nutsu ya zauna,kowa ya zauna sai ga Baba da Mama sun shigo,Baba Yana shigowa ya rafka Salati da karfi tare da furta Rahilu Menk???????Allahu Akbar,Rahilu Kaine ka dada bushewa ka tsotse haka? Rahilu haka ka dawo Kamar Dan gudun Hijira,Rahilu kalli wandonka yanda ya maka yawa,Wannan Hannu naka Rahilu Kamar Sanda,Mama tace wuya sai kace na zalbe,Aamna Karki ga Baku Yi Kama ba shine mahaifinki maza ebo Masa abinci ya ci da Alama yunwa ta gama dashi a Sudan,ku bashi yaci ya koshi,yanzu dama zaman da kakeyi a can ba Dadi kake ji ba? Nayi zaton ma kudi kayi ka watsar da yarka ashe wahala kake Sha Baba ne yake ta magana,Aamna ta kalli Wanda akace Babanta wani mugun bushashe. Yar China bata San Kan zancen ba tace amma wannan daga Tanzania yazo ko? Baba yace Allah Miki Albarka yar nan kema Kya fada ko Kenya ko Tanzania ko Kuma Senegal,to a Haka Wai Balarabe ne larabci yake yi,Yar China kirji ta dafe tare da toshe kunnuwanta tana cewa bazan ji ba...bazan ji larabcinsa ba,ta bawa mutane Dariya amma akayi Shuru,Baban Aamna Yana Jin hausa Amma ba sosai ba kadan kadan, Yaji abinda suke cewa Dariya shima Yar China ta bashi ya murmusa,Wai baza taji larabcinsa ba. Masu Sharhi Ina godiya,duk inda yayi ma mutum Dadi ya fada haka ake so AsmaBaffa 10/26/21, 2:20 PM - A Maryam: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 101-105 Official By AsmaBaffa Page naki ne AUTA Ahmad yana kusa da Aamnansa a zaune tare da rike hannunta,kasa kasa yace a Gaida Abbu mana My World ba'a Fushi da iyaye,Kallon Ahmad tayi idonta taf da Hawaye Kai ya girgiza mata Kar tayi kuka ya rada Mata a ajiye min kukan Nan sai anzo manta uwa,Murmushi tayi ba shiri,Ahmad ne ya juya harshe ya shiga suburbuda larabci Wanda ba kowa yasan yana ji ba,Baban Aamna yayiwa tare da Daddy dinsa Yana ,Abbun Aamna shima Yana yarensa cikin kwarewa,Baba yace shu'umi Rahilu akwai murya dama Indai kaji murya me dadi idan ka duba yawanci mummuna,Yar China tace kaji Larabawa Amma Banda Abbun Aamna bazan yarda Balarabe bane daga Tanzania yazo,Abbu ne ya kalli Aamna cikin Muryarsa wacce Bata fita sosai ya Furta Aamna ki yafe min,bani da bakin magana kawai ki yafe min,Yo a yafe maka ba'a San tsiyar daka shuka ba ka gudu,ko Kuwa can mun San me kakeyi? Cewar Baba. Abbu ya kalli Baba yace Ni ban San dalilin da yasa na gudu na bar Aamna da Sumayya matata ba bani da dalili ban San me yazo kaina ba, ko me yasa hakan ta faru? Baba farat Daya yace Dan Iska ne Kawai Kai shine dalilin da yasa ka gudu algungumi Kai kamar na kwarangwal zaka ce baka San dalili ba sabo da Iskanci ya maka yawa,ai shi yasa aka ce a guji bawa bako 'ya aure,yanzu matanka Nawa da Yara? Baba ne yayi tambayar, Rahil yace Sanda na auri Sumayya matana uku itace ta hudun,bayan na samu labarin ta rasu Allah ya hadani da wata Yar libiya na aura,Baba yace Rahilu kaji tsoron Allah Wato Ashe ma munafuki kana Jin ta mutu ka Kara aure wato ka cike gurbi kenan zaka ce Allah ya hada ka da wata kaje dai ka kakai kanka Wai Kai wayo ko Dan muce kaddara ce to anki wayon,mu ka barmu a Nan kana can Kuna dancewa da Amaryarka,Dariya Baba ya bawa kowa Wai dancewa,Daddy yaji Dadi da Baba yake cin uban Rahil, Baba yace itama wacce ta aureka a Haka tayi asara mene abin so a jikinka Rahilu,Kuma har daga kasar libiya kaje ka auro ta karya kakeyi Yar wanke wanke da shara ce baza ta wuce Yar Niger ce taje Sudan aikatau ba ta rufe ka Tace Yar Libiya ce ita. Inama tana Nan wajen na kure Yar banza yanzu nace idan ta Isa ta bani dutse dan Libiya na jefa a randar Aishatu maganin ciwon ciki,aka sheke da dariya,Baba shi baya Dariya da gaske yakeyin fadansa,Sannan yace to da ka Gama dancewar da matan naka Yara nawa Suka Tara maka? Rahil ya daga Kai Yana tunanowo,Cab Baba ya Furta suna da yawa kenan ya kasa irgasu,Rahil yace na Uwar gida Guda tara,ta biyu bakwai,Baba yace na hada Sha shida cif, Rahil yaci gaba ta uku Kuma guda shida,ta hudu Aamna kenan,sai wacce na aura bayan Sumayya ta rasu yanzu tana da uku,na hada talatin cif cewar wace Kuma me ciki yanzu take Shirin juyewa? Baba ya tambaya,Rahil yace Amarya ce,Dole wando yayi maka yawa Rahilu Nan gaba ma Sai dai idan ka koma saka jallabiya zalla Amma Riga da wando Ina tabbatar maka ka kusa rasa size din da zai maka dai dai,gashi turawa basa tazuge irin namu bare ka zamge kugunka. Rahil ne yayiwa Daddy magana da larabci Wai ya gaji da masifar Baba zai yi tafiyarsa inda ya fito,Daddy ya tabbatar Rahil bashi da Imani yanzu wato Dole ma aka Masa yazo,Haushi yasa Daddy da hausa ya fadawa su Baba me yace ,Baba yace au haka kace ma? Yar China ce tace dan Allah Baba ku bashi abincin yaci ni Allah tausayinsa nake ji,Aamna ce tayi magana Tace na yafe maka koma mene kaje Kawai tunda dama Dole aka maka,kallon Aamna Rahil yayi rin mamanta sak,murmushi yayi tare da Furta na gode yarinya ta,Mama Tace rufe Mana baki wani yarka me ka kawo Mata tsaraba tun daga Sudan ko Dan lallensu baka kawo Mata ba domin ta dinga yiwa mijinta kwalliya ko Yar muhallabiya babu gata can tana tashi a can a banza,Baba yace sai ka dakko wani bushashen jikinka ka taho zikau zikau,Kiran Sallah aka kwala na Magrib,Daddy yace muje ayi Sallah mu dawo a karasa abinda ya kawo mu,Alwala sukayi gaba Daya su mazan suka fita masallaci Matan kuma Suka Yi a gida. A hanyar dawowarsu Baba ya kalli Rahil Dariya taso kwace Masa yanda ya ganshi Yana tafiya kamar Yana tausayin kasa,Baba yace Rahilu kayi tafiyarka sosai kasa fa ba kyaleka zata Yi ba Matukar ka mutu aka binne ka matsar Nan sai ka shata,Sai kallon Rahil yakeyi Dariya tana kamashi,Baba yace Rahilu da gani kana ji a jikinka,a cikin yaranka ka kawo min da daya na rike maka shi,Rahil yace to Zan baka wallah,Baba ya sheke da dariya tare da dafa kafadar Abbu yace Rahilu anji wuya Dan gandal uba to bazan rike ba tunda baka da mutunci kai ai wallahi sai dai wuya ta kashe ka Ni Nace ka auri matan kana can kana Dancewa da su kana danno Yara duniya sannan kace na rike maka,Aamna ma da muka rike Allah ya karba,Daddy yace ai bazan Bari ma ka karbi wani Dansa ba wa yace ya tara Yaran,shi ga ayu to Kai ka jawa kanka,Baba ya sake dafa kafadun Rahil yace kayi Hakuri Rahilu Ina ci maka Fuska Kaine ka jawo. Kafin su koma gida su Aamna sun shirya kayan ciye ciye a palon sai abinda ka zaba,abincin Suka zagaye Yar China Tace Ni Zan yi Serving kowa,haka kowa ta zuba Masa abinda yake son ci,Baba yace Ni bazan zaba ba komai Ina ci a zuba min komai zanci akwai waje me fili a cikina,Yar China tace ashe Muna iri daya da Kai Baba,kema haka kike? Baba ya tambaya tace ae komai Zan cinye,kin birgeni cewar Baba,Yar China tana zuwa kan Rahil ta cika Masa plate kamar zai zubo abincin har wani tsiri yake Yi a plate tace ci ka koshi Abbu in Allah ya yarda kafin ka koma Sudan gidan jiya ka danyi bulbul,idan ka koma sai kowa yace America kaje,mu Nan ba yunwa akwai abinci Kuma Abbu ba ruwanka da Yaranka bare su cinye maka rabonka,Baba yayi Dariya Yar China da tsiya take yace da zai yarda yayi wata Guda a Nan Ina tabbatar muku kafin ya koma can sai ya saka Leda a kafarsa kafin ya cire wandonsa sabo da kiba,Rahil ya kalli abincin da aka zuba Masa yace bazan iya cinye wannan ba ai ko quarter bazan ci ba,Ni ba Jaki bane ya sa spoon ya Dan kwashi ganyayyakin Vegetables yana ci sai fruits. Baba ya kalle shi yace Rahilu wa zaka ji kunya a nan kaci abinka karka zo kana dana sani,Wai mu zaka kife ai da ganinka an San baka Jin dadin rayuwa,Wai Kai nufinka Balarabe ne? Rahil yace sosai ma,Kana cutar kanka Kuwa mu idan sama da kasa zata hade baza mu yarda ba,asalinka Dan Kenya ne,Rahil ya Bata Rai har da buga plate da cokali cikin hausarsa wacce bata fita dai dai yace Allah kiyaye Ni...Ni... hadani da Kenya... baka ganewa Sudan can... ni Sudan Yana daga Hannu sama. Baba Yana cin nama Yana dariyar gwarancin Rahil,Rahil harda cewa Dan an rike Masa yarinya za a dameshi,shi idan hakane a bashi yarsa ya tafi da ita,Baki su Baba suka bude yace gata Nan dauke ta ku tafi idan ka isa,a ka'ida ma Rahil Kara ya kamata mu kaika kotu Amma Muka Yi maka alfarma,Rahil ya Bata rai,Baba jinjina Kai yayi yace wannan da a Isra'ila yake harbe mu zaiyi,Yar China ce tace Kuma jirgi ya hau yazo Nan? Baba yace ae Mana,tab ai da akwalar mota ya dace a ganshi ciki,Mummy ce tace gidanku kaji yarinya a gabansa ga yarsa babban mutum,yar China da sauri Tace Yi Hakuri ai nufina yafi dacewa yazo a Private jet Yar China ta wayance,kowa Dariyarsa ya kunshe. Sai Bayan Isha sannan duk Suka tafi gida,Yar China tace sai Nan gaba Zan dawo yau Baki sun Hana suyi hira,Aamna tace to Allah ya kaimu,Daddy da Rahil da Mummy,Humaira gaba Daya suka tafi masauki,su Jibson duk sun tafi saura Aamna da Ahmad a gidansu an barwa Aamna tarin wanke wanke da gyara Palo,na gaji Ahmad ya furta tare da mikewa saman sofa,Aamna ta kalle shi tare da cewa Ni kadai zanyi aikin My King ko dan tayani baza kayi ba,Fuska ya yatsina yace I'm sorry bazan iya ba idan kema kin gaji ki barshi da safe sai kiyi,Rabani da kwana da uban dirty haka,Aikinta tayi ta Gama ta Iske yayi bacci,Aamna girgiza shi tayi da karfi ya farka Idonsa cike da bacci,tace baza kayi min baccin wuri ba kazo cikin tsakiyar dare ka farka ka hanani bacci ba,Cikin shagwaba ya furta please Baby ki barni nayi bacci na,Aamna tace Ni Allah ka tashi kawai,ba Kya tausayina? to ai ba Aiki kake zuwa ba da Zan tausaya maka ba,tashi muje wanka,Ido ya rufe zai koma baccinsa Aamna sai hakura tayi tasan bazai tashi ba Kansa ta dage a hankali tare da zama a kujerar ta maida Kansa saman cinyarta,da muryar bacci yasa hannayensa tare da rungumo hips dinta yana Furta so sweet yaci gaba da baccinsa,Gashinsa take Wasa da shi tana kallon Nigerian Film dinta,tunda ya fara bacci Bai tashi ba sai 9pm tana ta kallonta,taji Dadi da Bai dade ba Yana baccin,Kallonta yayi Yana murmushi yace thank you My world for your cinya,murmushi tayi tace sai wanka ko? Kai ya gyada Mata Yana cire Mata wani dan abu a gefen idonta kayan kallon Suka kashe tare da haurawa sama. Ita kuwa Yar China tunda Tawaga ya dauketa direct shopping ya kaita ya siya Mata abinda take so sannan tace Yaya ka manta Icecream din,Komawa yayi ya dakko Mata guda Uku manya ta karba tana murna tace Thanks alot. Tun a mota ta bude abinta tana Sha Tace Kar ya narke,a spoon ta ebo tace Yayana,Tawaga Uban tafiya,Yar China sai Tawaga haka Tawaga sai Yar China,Dariya Tawaga yayi yace haka yake Yar Chinata,to Sha ta bashi a Baki Yana driving tana bashi a baki Yana Sha itama tana Sha. Yar China tace Yaya Wai kaji Yar Aamnan nan da iyayi Wai Ni zata koyawa wani darasi,Maganar Aamna ta gwada sabo da Aamna akwai Iyayin jaraba tunda me gyara ta koya Mata shike Nan,Yar China tace Wai a gaban saurayi nutsuwa akeyi ana Jan class,Allah na tuba Ni har a gayamin class Ni da kwana Nan na zana waec to ta Daya nake zuwa a aji,wanne ajin take so Naja idan ba na A.b.u Zaria take so na ja ba,Tawaga a ransa yace Zan Sha wahala kafin ta gane ya zanyi Ina son abata haka,a hankali zata canja,a gida ya sauke Yar china tare da rakata har Gaban Iyalle yace Iyalle ga Amanarki na dawo da ita,Iyalle tayi Dariya tace to an gode,sai da ya tafi Yar China ta fara bawa Iyalle labarin inda Suka je da Tawaga. Kwana Uku Daddy da wasu dangin su Jibson aka Kai kudin auren Jibson,Humaira da Yar China,a Nan aka tsaida ranar aure gaba Daya Rana Daya dana su Jibson da Mashkoor,Ahmad yace baza ayi party ba tunda shima nasa ba ayi ba walima zasuyi iya abokai,Ranar da aka tsaida ranar aure Yar China Bata sani ba sai da ta dawo daga Islamiyya Iyalle tace to Yar Jikalle an kusa girma bikinki watan gobe an Kai kudin aurenki dubu dari da arba'in Yar china Tace me ya cinye goman? Dan jaraba su cika Mana ya koma dari da Hamsim,Iyalle tace uwaki Yar China Dan Iskanci to wasu ma dubu sittin ake Kai musu,sai kace ragon layya wallahi idan nice na fasa aurensa haba Iyalle dubu sittin fa? Ai gwara Kawai a bashi Ni Sadaka,Harararta Iyalle tayi Yar China tace yanzu fa Iyalle kwana Nan za a dinga ce min Amarya? Kwarai Kuwa cewar Iyalle,to gyaran Amarya fa ya za ayi ne Iyalle? Iyalle ta rike Baki Tace oh yaran zamani mu a zamaninmu ai ko magana yarinya Bata Isa ba,idan aka Kai yarinya gidan miji sai miji ya kwana Uku Bai ga fuskar Amaryarsa ba tana lulle cikin gyalenta,Yana shigowa zata rufe kanta,Yar China ta kyalkyale Dariya tace hmm ai wallahi da nice sai na sa reza na Dan yanka gyalen idan na lulluba sai na dinga leko idona ta Yar kafar Ina kallon Tawaga na,yanzu Kuwa Iyalle ai zamani ya canja idan kika zo gidana shayi Zan hada Miki me kauri na barki a Palo Ina can wurin Tawaga na Muna ta Jan zuga abin mu,Baki ji sunansa ba Tawaga Uban tafiya ma'ana ya ja runduna,Yaja zugar mutane shine uban tafiya,Dariya Iyalle tayi tace to kije kuyi magana da kawayenki akan gyaran Amaryar,Wanne kawaye ai wlh ba ruwana sai dai na gayyace su biki amma ni Zan Kai kaina wajen gyara,ai nasan Mata da yawa,ga makwafciyar mu Nan Ummin Zainab can zanje ta gyarani fes,Zaki ce Wani kawaye so kike su aure min miji Dama anyi candy duk gamu Nan jiran kadan mukeyi. A ranar Yar China tayi status a duk wani social media nata ALHMDLLH GOT ENGAGE tawaga Yana online ya gani Dariya yayi shima yayi irin status nata,Sunanta ta canja nan ma ta saka Mrs Aliyu Tawaga,frnds nata suna ta budewa Ana Mata Addua,Tawaga Kuwa Ya canja zuwa Tawagan Baby,Jibson suna gani Suka dinga Masa dariya,Ahmad yace Allah ya shiryeka yarinya ta maida ka sususu,Tawaga yace ai Kai baka da bakin magana gwara Ni ban siyar da citta ba Kuma ban saci kayan kallon surukai ba akan love,Ni banyi kuka ba,Mukus Ahmad yayi kawai yayi Dariya, Aamna tana kwance a jikinsa a saman bed Yana chat tana ta Masa shagwaba Wai sai ya koya Mata mota Nan gaba,Yana jingine da fuskar bed tana jikinsa kafafunsu rufe da bargo brown, ta maida kanta saman kirjinsa tana please King, please....sake hayewa takeyi jikinsa a hankali Tare da daura Hannunta ta Bayan wuyansa tana shafawa tare da kukan shagwaba kaji...kaji Baby...Damunsa tayi yace Alright Nan gaba Zan koya Miki shine Nan? Murna ta dingayi tare da kankame shi tana dariya. Bayan sati Daya Rahil ya Gama shirinsa tsaf zai tafi da yamma,jirgin 5pm gidan Aamna yazo Suka gaisa har Ahmad sannan King ya Basu waje,Aamna da Rahil Abbunta Suka Yi har Hira sosai sannan ya musu Sallama da Niyyar tafiya,Aamna Tace zata Zo Nan gaba,Daddy kyautar ban girma yayiwa Rahil suka je gidan Baba Rahil ya sake Yiwa Baba godiya na rike Masa yarinya da yayi,Baba yace ba komai ai da na kowa ne duk da dai baka kawo Mana tsaraba ko Jallabiyya ba ai ba komai . Amma Rahilu Kamar a kanka a saukar da Babu yanzu ko Yar tuffa ai ka taho Mana da ita ta jirgi Amma sai ka taho zikau daga bushashen jikinka sai wannan Yan iskan kayan Wai sut (suit)Kai a Dole ka cinye zaka Mana burga to ai jikinka ya bada Kai,Daddy yace Baba a barshi Haka ya tuba,rakasu Baba yayi yace Allah ya tsare Rahilu in Allah ya yarda tare da Aamna zamu zo Sudan zanga yaranka,Rahilu yaji masifar Baba da mita da lalatacciyar hausarsa yace bana so zuwanka....kar ta zo Kai da ita....Ni...Kai...Bama tare .. Bama...shiri...karka zo Sudan....Baba yace dan ma ance Za'a zo sai kace garin arziki,Sudan din fin Nigeria tayi? duk gaku Nan ragowar yunwa ku kanku Yan kasar Baku koshi ba,Rahilu ka dube ka fa har mu zaka ce Kar muzo muku gari,Sudan din Wanda duk irinku ne a cikinta me zamu kalla? Kuma wallahi Inshaallah sai nazo naga matsuguninka sai na sa maka Ido Naga yawan yayanka,sai Naga waye a ciki Allah ya Dora musu Suka yo Kama da kai,Rahil da gaske ya dinga cewa Ni bance kazo gidana ba bana so....Baba yace Allah baka Isa ba sai na zo,Daddy Yana ta dariya Yana kallon rikicin Baba da Rahil,Rahil motar Baba ya shige Yana Jan Tsaki Driver ya ja mota Suka wuce airport,Baba Kuwa gida ya koma Yana dariya yace airport zasu Sha kallo. Bayan kwanani biki Yana ta matsowa ko wanne bangare shirye shirye sukeyi yayin da su Aamna suke Shan love abinsu yau saturday tunda Ahmad ya fita da safe sun fita da su Jibson Basu dawo ba har Bayan Isha Aamna duk ta shiga damuwa,gidan ya Mata Fadi,ta rigida ta Saba da mijinta kullum suna tare,ta Kira wayarsa Bata shiga,ga wankanta ta sha tana ta zuba kamshi a Palo ta zauna tana ta jiransa hankalinta duk ya tashi ko ba kalau ba,Number Tawaga ta Kira lokacin suna tare da Ahmad suna cike wasu takardu masu yawa duk akan aikin da zasu fara Nan gaba a companies na Daddy Wanda Lokacin suna tare da Daddy a Hotel din da yake shi da Mummy da Humaira,Wayar Tawaga ya daga yace Aunty Balaraba ce fa King,maybe Kai take Nema ka manta tunda kasa wayarka a charge ka kashe baka kunna ba. Ahmad Wanda hankalinsa gaba Daya Yana Kan Aamna yasan dama tana can tana jiransa ga Daddy a wajen ya hanasu sakewa da Aiki,Tawaga Sallama yayi Suka gaisa sannan tace Dan Allah Kuna tare ne? Yace ae Muna tare aikine ya Sha kanmu amma yanzu zamu taho gida,Ahmad ne yace bani Wayar,Yana karba Aamna da shagwaba tace Ina ta kiranka ka jawo na shiga damuwa ko ba lafiya ba,Idan na dawo Zan Miki bayani My world,Daddy ne ya samu Aiki Amma yanzu Zan taho,fatan kinci abinci? Ae tace yace good, me Zan siyo Miki? Tsire Aamna ta Furta alright. Suna gama Wayar Basu Dade ba 8:30 Ahmad ya dawo gida,tana jiransa Jin motarsa da Alama shine,Yana shigowa palon tayi tsalle tare da rungumeshi tana murna sosai shima ji yake kamar yayi kwana Uku Bai ganta ba,Kallo ya Kare Mata tare da furta kinyi kyau My World,Ledar hannunsa ta karba tare da rike hannunsa daya tace let's go Suka haura sama tana cewa na Sha wahala Ina zaman jiranka,Eyya I'm Sorry Beb,never mind ta furta,kayan jikinsa wani shegen yadi ta taimaka Masa ya cire Yana Shiga wanka taje ta Hado Masa abinci ta kawo sama,kafin ya fito ta fito Masa da kayan baccinsa masi kyau,itama bedroom dinta taje ta canja Kaya kasancewar Bata Dade da yin wanka ba. Bata dawo ba sai da ya Gama shirinsa sannan ya zauna inda ta Ajiye Masa abincin yunwa yake ji sosai sai Samunsa tayi Yana ta cin sakwara da miyar Egusi,ita Kuwa tsirenta ta bude taci yanda take so tace baka ci Kai? Yace ae Ni tsire Bai Dame Ni ba,sai da ya Gama sannan ta maida komai kitchen ta dawo Yana ta deshe jikinsa da turaruka da Alama brush yayi,na gaji ya furta kawai tare da kwanciya a saman bed,itama saman bed ta haura taho ya furta tare da Rungume ta Itama Haka da wuri bacci yayi gaba da su. Sai wurin 4pm ya farka Yana farkawa ya Mike ya Shiga toilet,Bayan ya fito taji ya fara zare Mata Kaya a hankali. Ayi Hakuri da wannan AsmaBaffa 10/26/21, 2:20 PM - A Maryam: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY 106-110 Official By AsmaBaffa Page naku ne UMMI DEEJAT MAMAN SAMHA MAMAN MUNIBA MUNEERA HAFSATOU Aamna farkawa tayi kadan,My world ki tashi,Cikin shagwaba ta juya tana cewa bacci King Dan Allah muyi bacci,Ni bazan iya bacci yanzu ban samu nutsuwa ba Ina wani bacci Ina tuna Mummy ta yanzu fa ki tashi ki bani Manta Uwa,Amma yanzu kin jawo Ina ta tuna Mummyta,Dariya ya bawa Aamna tana Jin bacci Haka ta Mike tana murmushi,jikinta yake karewa kallo rigar baccin tayi mugun Mata kyau gata sharara,to ka Jira nayi fitsari first,Alright ya furta ta Mike ta shige toilet,tsarki tayi da ruwa me zafi har da wanke Hq dinta da Genital wash me kamshi wanda ke maganin Infection Yana karawa mace Niima da dandano,Sai da tayi matsi da musk me Kama da Madara me dadin kamshin, sai da ta Gama kyalekyalenta ta fito ko Ina Yana kamshi Wai fitsari tayi,tun kafin ta karaso ya Mike tare da rungumeta babu Bata lokaci ya cire Mata Yar rigar,abinda yafi daukar hankalinsa ya shiga murzawa suna kissing juna a hankali Aamna ta fara ji a jikinta tana bankarewa,Saman bed ya jata Suka fada, tausayi ta bashi tunawa da yayi tana baccinta ya tashe ta,Kallonta yayi tare da Furta ban takuraki ba My world? Murmushi tayi Kawai tunaninsa Kara take Masa Kawai Bata so ta nuna ya takurata ne,Wani kallon kauna ya Mata tare da dakko rigar baccinta da Niyyar maida Mata ita jikinta,Hannunsa ta rike a hankali tana Masa wani kallo Wanda ke nuna tana bukatarsa itama,ya rigada ya gane abarsa,a hankali da rada tace I need you My King,baka ji ba nace you know how to do it,ka Iya ka huta,Dariya ya saki,Ido Daya ta kashe Masa tace oya let's do it,Yatsunta ya rike Yana murzasu ya furta I love you My Wife,I'm gonna fuck you well Darling cewar Aamna yau itace zatayi yakin,Ahmad yana murna yace yau zamu Danse kenan,Dariya tayi tace Baba ya iya abin Dariya Wai Dansewa amma fa King seriously naji haushin Yar China yau,wlh badan Tawaga ba yau sai na ci uban Yarinyar nan Dan Kawai bata Sanni bane,yanzu ta Sanni Kawai nayi laushi ba Aamnan ce ta baya ba,Fuska Ahmad ya bata Nan take kallon Aamna yayi yace bana son wannan shirmen, Baki gani yarinya ce ba,Budurwar Abokin nawa ke kina Babba mene haka,? so kike a kawo su ku fara fada ku bata Mana abota,dama ko a dangi wallahi wani hargitsin da fadan Mata ke haddasa shi da gutsiri tsoma da gulma,abinda Bai Kai ya kawo ba ku Dora shi a ranku, goyon kakar Zaki biyewa kina ga yanda Tawaga ya dauke ki har fada Miki yayi zata dinga zuwa kina Dan ganar da ita wani Abu,tsakanin Hakuri da rashinsa kadan ne fa,to Zan fada Miki Estate din Nan kowa gidansa daban Kawai Estate ne Daya gida kin gani kowa da nasa daban,idan wata Bata je gidan wata ba babu wacce zata ga wata,wlh karki sake naji ance kin samu sabani da wata,Mijin kowa daban,Yar China duk cikinku itace karama,Muna zaune lfy zaku fara haddasa fada,shi Baba Baki ji haushinsa ba sai ita, Ahmad a ransa yasan Yar China bata kyauta ba amma yasan halin Mata gwara yayiwa tufkar hanci shi yasa ya dinga yiwa Aamna masifa tasan halinsa bai iya Fushi ba. Amma ita baka ga abinda ta min ba? Shut up ya Furta da fada yace ance Miki Tawaga baida hankali shi Bai gani ba a gabansa akayi kina nufin bazai Mata fada ba? Tawaga ya fimu saurin fushi zai iya marinta ma akan wannan wlh karki sake na Kara Jin zancen nan,Aamna Idonta ya kawo ruwa yanda ya lullube ta da Fada kamar Bai Santa ba,Aamna tace ai dama nasan abokanka sun fini matsayi a wajenka,Sanda Suka Yi hatsari da nice nasan baza ka haukace Haka ba Ana gama zaman makoki zaka fara Neman auren wata sabuwar budurwar,Ahmad a ransa Dariya yayi a fili Kuwa Tsaki Yaja tare da maida kayansa yace kin Bata min Mood sai ki Danse ke kadai,Aamna da zuciya tazo Mata wuya Tace ai Zan Iya Ni kadai,da me? Ya tambaya ta bashi amsa da hannuna,Yau Kuwa wallahi da an Bude Miki kofofin Jahanma da yawa. Aamna ta saki kuka tare da cewa Yar Iska Yar China 'Yar Yarinya Kawai ,da gani kanwarta ce ta Raine ta,ba Kaka bace haukarta ta wuce ta goyon kaka goyon kanwarta ce,kanwarta ce ta yayeta Kuma bazan koya Mata komai ba,Dariya ta ba Ahmad Wai kanwarta ce ta raineta Wato karewar yarinta, Kwanciya yayi tare da juya Mata baya,Zama tayi abinta tare da kin kwanciya sai da Ahmad ya gaji ya jawota ta kwanta a jikinsa tare da makalkaleta a jikinsa Yana cewa bana son taurin Kan Nan naki My world,taurin Kaine da ke shi yasa Baba yake miki fada kullum kina Jin haushi,Aamna tace ai dai ba taurin Kai na maka ba gaskiya ka take min ga gaskiya Kiri Kiri amma zaka dinga min fada ko Hakuri baza ka bani ba sai fada ai dai mu Mata kashinmu a tankware yake Bama mikewa idan aka takura Mana Kara lankwashewa zamu yi ,to naji ya Isa daina zubar da Hawayen Haka ban sanki da kuka ba,Aamna tace wallahi bazan daina kukan Nan ba sai na zubar da gurbataccen Hawayena,Dariya yayi tare da rungumeta sosai yace to ya isa,Aamna ana kuka harda tari kuful-kuful kuka yayi kuka wai,sai da ta gama kukan shagwabarta sannan bacci yayi gaba dasu,washe gari Kuwa da Asuba suna idar da Sallah ranar baije masallaci ba a gida Suka Yi tare,Ko Adduar kirki Bai Bari sunyi ba ya shige cikin Hijab dinta Aamna tana ta Azhkar shi Kuma Yana Wasa da Boobs dinta Yana cewa kici gaba da adduarki Lada Kan Lada wannan ma Azkhar ne Babba, Dole ta hakura tare da Furta wannan ai tsokana ne King,Nan suka fara murza junansu suna wani nishi,Ahmad ya shiga buga harka cikin nutsuwa,a kasa sukeyi yau ko bed Bai Bari sun hau ba,Aamna tana Enjoying sosai cewa take Yeah....Baby Fuck me.....fuck...fuck....Ahmad Kuwa cewa yake do you like it? Aamna tana yeah fuck.... Washe gari da Yamma Tawaga gidan su Yar China yaje ya sameta,ta gyara gidansu fes Yana ta kamshi,tana zaune a kitchen tana girki a Murhun gawayi,sanye take cikin skert din atamfa da vest sai wata hula Kalar vest din da ta saka pink, Kamshi taji ta juyo da sauri sai taga Tawaganta,kunya ce ta kamata jikinta ba ko mayafi,Tawaga yaga jiki me kyau fari tas a ransa yace na gode Allah,kujera ya jawo tare da Zama Yana cewa Baki fa amsa min Sallamarta ba kina ta faman kallona,Firgit Yar China ta dawo daga hayyacinta yanda take Kallon Tawaga ya Mata kyau matuka,Yaya kayi kyau,ai kin fini kyau gimbiyata,Murmushi tayi Tace Bari na dakko maka Tabarma ko carpet,no..no ba Zama zanyi ba shigowa nayi na ganki ko naji sanyi a Raina tunaninki ya hanani sakewa Baby,Yar China ta rufe Ido tare da furta Kai Yaya Ni kunya nake ji Allah,Ina Iyelle ne? Ta tafi Unguwa gidan Kawu kaninta sai dare zata dawo,Zama ya gyara Yar China tana girkinta suna Hira,me kike dafa Mana? Yar China tace kasan Iyalle da son tuwo,Tuwon shinkafa nayi na gama miyar nake karasawa ta nuna Masa Danyar kubewar da ta goga,yace Ashe yau zanci abincin naji matar ta iya girki ko Bata iya ba,Dariya Yar China tayi tace na Iya girki fa Yaya,Haka nake so ai,Kin San me ya kawo Ni wajenki? Yar China tace a'a,yace Akan Aamna ne,kamar Ahmad ya sani yace yasan Tawaga sai yayiwa Yar China fada sai Kuwa gashi. Tawaga yace kin bani haushi fa abinda kika Yi duk fadan da Iyalle ta Miki Baki ji ba,Baby Baki iya magana ba taya kina yarinya a Gaban manya suna magana kina magana har Zaki dinga ciwa Baban Aamna fuska a Gaban yarsa,duk wajen ga mutane kina tunanin zasu ganki a me hankali,sannan Ni zasu ce banyi dacen Mata ba tunda na auro marar kunya,ko ba komai Mahaifi ne fa,kin San Kuwa me ake cewa Mahaifi? Kuma gashi Babban mutum dattijo,a Gaban manyan mutane Ina ta kyafta Miki Ido kiyi Shuru Amma ke Baki San ma Harara ba,sonki da nakeyi Allah ne ya sa min sonki Amma wlh da bazan so ki ba,ko Ni farko fa a makarantarku Haka kika zageni wannan zagin da kika min shine silar Haduwar mu,Kuma na gani naji Ina sonki a Haka,Amma shine matar abokina ta girmeki Zaki je har gidanta a gabanta kici fuskarta Kuma ke ba ruwanki ko a jikinki,haka Zaki yiwa dangina? Yar China ta kebe Baki zata Yi kuka Tawaga yace wlh kika min kuka sai na mareki a Nan wajen kin San Halina ya dan Iskanci Ana gyara Miki Abu ke kuka ma zakiyi,me na Miki? Yar China tace ai dai Sanda na zage ka dama sonka nakeyi,kullum Ina kallo kana kawo kannenka makarantar mu, Ni Kuwa in buya a bakin gate inyi ta kallonka Ina Jin dadi. Ka tambayi Iyalle wallahi kullum na dawo daga makaranta sai na Bata labarinka,Ni Kuma Dana gaji zuciyata tana ta bugawa idan na ganka shine naji haushi na zageka ashe Allah yaga zuciyata shine ta Haka ya Zama silar komai,Kuma Ni Aamna ai ban San zata ji haushi ba Amma ka kirata a waya na Bata Hakuri,Indai zaka daina Jin haushi na Zan Bata Hakuri. Tawaga saukin Kan Yar China yana birge shi Bata da taurin Kai Sam,tana Jin Tsoronsa ko ya idan ya nuna Mata fushinsa sai ta sakko,Wai dama ta Dade tana sonsa Bai Sani ba Amma Taki nuna Masa ko Alama sai da ya gaji ya fada da Kansa Lallai Yar China Ashe da hankalinta sai yaji ta dada samun guri a zuciyarsa. Kallonta yayi yace Bari na Kira Aamna ki bata Hakuri,to Kawai tace,Ahmad ya Kira a waya bugu Daya ya daga lokacin suna garden suna hutawa shi Aamna,Ya akayi Tawaga? Tawaga yace King Ina Aamna? gata kusa dani,Okay please Bata Wayar zamuyi magana,Ahmad bai tambaya ba ya mikawa Aamna waya,Bayan sun gaisa yace Aunty Balaraba Hakuri zamu Baki akan abinda Yar China ta miki kiyi Hakuri dan Allah kuruciya ce gata zata baki hakuri,Yar China waya ta karba tace dan Allah Auntynmu kiyi hakuri nasan nayi kuskure bazan sake ba,Aamna sai kuma taji kunyar masifar da tayi jiya har suna fada da Ahmad akai,gashi baiyi karya ba Tawaga Yana sane zai dau mataki,Aamna tace ba komai kanwata karki damu ya wuce,Yar China Tace na gode Iyallace ta lalatani bata iya tarbiyantar Dani ba,komai nace sai ta kyaleni,ko me nayi sai tace nayi dai dai Bata min fada,Bata Nuna min hanya duk laifin Iyalle ne bata iya tarbiya ba,Iyallace da laifi Dariya Aamna tayi tace to ya wuce sis,Iyallace ta karasa shigowa gidan tana cewa da nayi Miki Ubanki? Dan Ubanki to naji abinda kika ce Wato Ni na lalata ki ban iya tarbiyya ba,duk abinda kikeyi bana Miki fada ko? Tun yaushe kullum sai nace ki bari ki Bari kaza ba kyau Amma bakya Jin magana,na nuna Miki fari da Baki amma ba Kya ganewa kullum sai kinyi laifi an kureki kice nice na lalataki,Haka rannan a makaranta kinyi laifi aka tara Yan makaranta za a zaneki kika ce nice na lalataki a Gaban Yan makaranta da malamai ai naji labari wajen kawarki Habiba,Rannan Haka kika je har gidan sabuwar Amarya kika ce kayan dakinta da katakon dalbejiya aka Yi shi,Kuma kika ce mijinta Maye ne,Babarsa Mayyace Kuma kika ce a wajena kika ji,Tawaga ya dinga dariya,Iyalle tace harda cewa wai ai Ni na tsufa na Dade a duniya Duk mutanen garin Nan a idona aka haife su sabo da haka nasan waye Maye nasan waye Wanda ba mayu ba,Yar China tana ta rokon Iyalle tayi Shuru amma Iyalle tace sai na fada Yar banzar yarinya. Saura kadan ki kashe aure da kyar na samu case din ya mutu,yanzu kin tabka rashin kunyarki kince nice,tunda tonon asirin kike so ai Nima nasan sirrinki Bari na fada Masa,Iyalle tana kallon Tawaga tace bawan Allah kaje kayi zamanka ta dade tana sonka fa Kaine baka sani ba,tun tana Jss3 yau shekaru Uku kenan Kai baka sani ba,kullum ta dawo daga makaranta sai ta bani labarinka,lokacin ma Bata fara nono ba,Iyalle Tace ai kwanaki ma...Yar China ce ta fara ihu yeeeeeeyeyehhhhhh ta cika gidan Wai Dan kar Tawaga yaji Maganar Iyalle shine take ta Ihu. Tawaga ne ya ja Hannunta suka koma Palo shi yau fess ashe Yar China ta Dade tana kaunarsa,sai yaji wani sanyi da nutsuwa a ransa yasan ba Wanda zai iya kwace Masa ita,fada ya dinga Mata da Nasiha tace Zan daina Yaya,Tawaga yace indai baki daina ba zamu bata,Kinga Amarya guda ango ya daina kulata sai ya? Yar China tace babu lafiya Amarya da ango suna fada ai sai lahaula,Yaya baza muyi party ba? Tawaga yace ae sai dai mu Danse idan an kawo min ke,Yar China ta tuno Baba ta dinga dariya,yace kuyi Dj a Kofar gidanku da kawayenki,Iyalle tace fa ranar da aka Daura aure ranar za a Kai amarya idon Yar China ya ciko da hawaye tana tausayawa kanta zata rabu da Iyallenta. Tawaga yace kukan Kuma fa ya Furta Yana goge Mata hawayen da Handkerchief dinsa,tana shesheka tace Iyalleta....shike Nan Zan tafi na barta Ina tsoro Kar Yan iskan Unguwa su hauro suyiwa Iyalleta Fyade,Tawaga ya kwashe da dariya yace Iyallen da ta Shekara kusan Tamanin da wani Abu ita za'a hauro ayiwa fyade?. Aamna tace to ake yiwa mahaukata Mata fyade Wanda suke ciwon hauka suna bin bola bare me hankali Kuma Iyalle ma ai da sauranta,jikinta Bai Gama saki ba,shi dai Tawaga dariya kawai yakeyi ita Bama kukan rabuwa takeyi ba,Tawaga yace ai gidan Kawu kaninta zata koma Kuma zamu ci gaba da kula da ita,tace to shike nan,na fadawa kawayena bikin saura Iv idan ka buga shi a kawo min da wuri sabo da Ni gyaran Amarya za'a fara Yi min bana son fita Rana na lalace,Tawaga yace karki damu,duk kyan jikin Nan naki sai an Kara gyara shi? tace so nake fa na dinga kashe maka Ido da haske na Walwal. Kudi ya Bata masu yawa yace gashi idan Basu Isa ba ki kirani a waya,Yar China taga kudi Tace Kai Yaya sunyi yawa ai gwara ka siya Mana abinci a gidan tunda kaga dai Ni ba wata garar arziki za a min ba tunda bani da gata,Murmushi yayi yace ai wannan an wuce Wajensa,Yar China tace Allah Yaya munfi marfin cikin mu? Sosai ma ya Bata amsa tace to Allah ya Kara budi,Tun a gabansa Yar China ta fara kasafin kudin, tana dubu biyar kudin maganin Infection duk na San bani da shi amma sabo da tsaro ko ya makale a lungun cikina ban sani ba,Iyalle tace za a siyo Dan mannau dubu hudu,duba daya da dari biyar kudin bagaruwa...Tawaga Jin irin bala'in da za a hada masa duk a Kansa yace Haba Baby duk Ni kadai so kike na kasa tashi,Yar China Bata Gane ba tace Haba Yaya sai kace wacce zan daureka da Igiya? Tawaga yayi kicin kicin yace bada Ni ba gaskiya Ni Kawai ki gigitani da kyawunki,kyan halinki,kwalliya,tsafta da Iya girki,iya soyayya shine Zaki birgeni,Yar China murmushi tayi Kawai Tace ai girkin Ina sake koyen Kalar na zamani na gargajiya na iya,Tawaga yace yawwa ki dage a Nan,Iyalle tace cab Kaine fa zaka fi kowa cin moriyar,Yace no Ni dai karki fi karfi na,Yar China ta kyalkyale da dariya ta manta da wani Sex ma. Tunda Tawaga ya bar wajen Yar China yake tunano irin yanda yaji Ana tsuma Amaryarsa,wajensu su Jibson ya wuce yace Wai ku bakwa gyaran Angon ne kamar yanda amare keyi? Jibson yace akan me Kuma? Amare suna ta tsumi mu mun zauna haka karfa Sufi karfinmu, Mashkoor yace Nima Haka nace muma mu nemi namu,Brown yace zamu danyi kadan gaf da biki Haka suka Gama tsarinsu Suma zasu tsumu. Lokaci na tafiya ana zaune cikin farin ciki ana ta Shirin biki,biki ya rage Saura sati Daya su Yar China an zuba kyau da kanta take zuwa gyaran jiki,Kawayenta duk ta gayyace su,Haka su Sameera ma,Sameera ta kashewa jikinta kudi sosai sabo da tasan ta taba aure ai Kuwa kyan da ta zuba kowa ya kalle ta yasan ba karya duk Wanda ya ganta sai ta birge shi,Haka Nafeesat ma da Hafsat bare Yar masu da shi Humaira an kashe Naira. Ba Wani shagali za ayi ba Ana daura aure da Yamma za a Kai Amare,,Iyalle duk kayanta an kwashe an maida gidan kaninta dakin daya bata,ana kai Yar China gidan miji zata koma. Jibson suna tare da Mashkoor yace Yar bazawara ta akwai hankali Haka nake son mace ta Gama hada hankalinta,bani da hawan jini yanda take ji dani,Dariya Mashkoor yayi yace to dama Bazawara ai dole ka huta,Jibson Yana murmushi yace Ina fada maka Danfa ta hadu da gogagge ne,zata nuna min duniya na nuna Mata ai nima babban Kai ne,badan ni bane yanda suke sakin layi kasan Bazawara sun San komai ba ruwansu idan baka goge ba sai su kalle ka wani can,ai Kuwa Zan Sha dadi ba Wani kuka da jiran sai ta Saba,Tawaga dai zaici ubansa da wannan yarinyar, Mashkoor Yana dariya yace Yarinyar Tawaga girma ne Kawai da ita amma ni tana birge ni ko ba komai zaka Yi dariya, zai Sha fama amma ai jikinta Kuma ba karama bace gata doguwa Kuma akwai diri komai ya ciko cewar Jibson,Mashkoor yace ai Yarinyar akwai abin Moro a jikinta,Tawaga zai more akwai kayan aiki,Dariya Suka yi,Jibson yace ni da kuke cewa yarinya ce nayi zaton kwaila ce ashe ta nuna luguf,Dariya sukayi, Mashkoor Yana cewa Kaine aka cuta Jibson,Jibson yace karya kake Yi wallahi sameerata tafi Nafeesat dinka komai kana kallonta cif cif,ai duk ta fi Su Hafsat cika,to ba ta fisu girma ba maybe ma Boobs din nata sunyi doguwar sujjada wacce kafin su dago sai dai Hakuri,Jibson yace karya kake Yi wallahi Ni fa nasan abina tunda na taba tabawa, Mashkoor yace dan Iska Allah ya Kamaka dama wlh tunda Naga idan munje zance kana korata wai na Baku waje minti biyar zaka fito nasan baka kulla gaskiya ba,Baki Jibson ya tabe yace sharri zaka min ai dai Allah ya sani watarana ne tayi kwalliya me kyau na kasa Jurewa shima kissing Mukayi sannan hannuna ya Dan samu tabaraki yasa Mata Albarka amma daga shi ban sake ko wani kiss ba,ai na tuba ni bazan iya aikata wani Abu da Yar wani ba nayi hankali,Dariya suka Yi Mashkoor yace yayi daidai mutumina. Yar China ankon su iri Daya dana Hafsat Kanwar Tawaga wacce Bash zai aura,Humaira Kuwa Bata ma Yi ankon ba sabo da babu wani time,Haka Nafeesat Yar Malam babu anko dama,su Ahmad ba Zama ita kanta Aamna sai hakuri tayi da mijinta Bai fiye Zama ba ana ta shirye shiryen biki,Yar China tayi gyaran jikinta tayi kyau Dangin mamanta Dana Babanta dake an dauke musu komai na kayan daki Daddy yayi komai sai Suka tsaya a sauran abubuwan biki da abinda ya shafi Amarya,Yar China Tasha gyara na musamman,Haka sauran matan ma musamman Humaira da Sameera ba a magana,Humaira su suna da masu gidan Rana,Sameera kuma ta taba aure shi yasa tayi kamar me,bangaren Hafsat ma ta gama ba karya haka Nafeesat da take Nurse gata Yar me kudi in kazo Nan an wuce wajen. Angwaye sunyi dinkuna na musamman Suma Kamar masu hadawa kansu lefe,gidan kowanne ya dau kamshi Daddy ya zuba komai har abinci store Guda,Lefen Amare Kuwa Tawaga Akwati takwas aka yiwa Yar China Haka su Mashkoor ma takwas takwas ko wanne Kalar design din akwatuna daban Haka kayan ciki ma ko wacce da nata Kalar daban,Mummy da Amarya tare da Dangi sabon gidansu na Kaduna suka dawo Wanda Daddy ne ya Gina shi daban idan sunzo Nan zasu dinga sauka a tunda ya Bawa Tawaga gidansa da Ahmad ya Bari sunzo sabo da saukakawa Dangin Ango ba sai anje har Lagos ba. An Gama komai ana gobe daurin aure Yar China ta tura Yara makwaftan da suke mutunci su sanar musu,sai dai suji yaro ya shigo yace Wai Yar China tace ranar asabar ne daurin aurenta Kar kuyi girki ranar ku zo kuci abinci da ku da yaranku,ai ta dariya ace kace Allah ya kaimu,Bayan Kuma ta raba musu Iv sai da ta Kara sanarwa da baki. Amare sun Sha lalle da gyaran gashi ko wacce mashaallah,Gaba Daya a babban masallacin Malam baban Nafeesat a Nan aka taru da dunbin tawagar angwaye da Amarya aka Daura Auren ko wacce,Jibril Jibson aka fara daurawa aure da Sameera Ana Gama nasa yace Alhmdllh na Haye ni Saura na Baya,yasha Uwar Shadda me shegen tsada fara tas harda babban Riga da hula me kyau,ga takalmi da agogo masu tsada,idan ka kalli Jibson sai ka sake Kallonsa ba karya da gani kasan wanka ya samu gindin Zama a jikinsa. Bash da Hafsat sune na biyu Wanda aka Daura aurensu,Bash yace Nima nabi layinka Jibson na tsallake Alhmdllh,Bash kuwa Shaddarsa Arsh color ce,yanda ya tsira hular nan ga saje da Dan gemu ya zauna das kwance a fatarsa me haske haske abin kallo ne Bash,Na gaba Kuwa Mubaraq Brown aka daurawa nasa da Kanwar Ahmad Humaira,Daddy Yana ta farin ciki shi Kuma Brown kayansa wasu light brown ne,Yana da tsayi sosai da Dan jikinsa cif chocolate skin dinsa wata sumul sumul gashi dama shi akwai Isa da tamaka haka yake ya gama tsula kyau. Mashkoor da Nafeesat aka daurawa aure Wanda yake sanye cikin wata Shadda ta Alfarma Grey color ba karya sai Wanda ya gani,Na karshe Aliyu Haidar Tawaga ne aka Daura da Sadiya Yar China, shi Kuwa Tawaga Sea blue ya saka tana sheki,ya kafa hula hancin Nan nasa dogo ya fito sosai,gashi jikin Tawaga na daukan wanka ne,ko me yasa kyau yake masa Allah ya bashi ba wata mace da bazai birge ba,Dukkansu ba Wanda zaka ce ya taba gwada ko shaye shaye,dama Sai Hali yazo Daya ake abota,Dukkansu akan Sadaki dubu Dari dari Wanda Malam liman Baban Nafeesat dukka shi ya biyawa kowa Sadaki a aljihunsa. Masu kade kade suna Yi Ana ta kashe pics,taro yayi taro Uban gayyar King Ahmad duk Yana cikin wakilan ango Wanda Suka karbi aure dan shishigi Wai har da shi a ciki,Wani yard ya saka me Arnen tsada kana kallo kasan an gama kure karshen Naira a jikin Ahmad komai Silver color ne,shima yau ya sa Yar hula duk sun tsirata irin na matasa,Ahmad uban gayya reception suka wuce da tawagar abokai da sauran manya duk aka tafi katon hotel a Nan aka Kama hole kowa yaci abinda yake so ga kida na tashi,Aamna Kuwa itama tana sabon gidan Daddy bangaren Amarya Humaira wacce taci Uban lace na gagara wani dark blue and Brown yanda zasu danyi matching da kayan Brown,Tace ai Nickname din Mijina Brown Dole mu sa Brown yau,Ana ta dariya ta Sha make up tare da Yan Kawayenta kadan. Hafsat ma kayanta akwai Kalar kayan mijinta Bash a jiki,Haka Nafeesat din Mashkoor komai a tsari sukayi,Sameera wacce itama hakance ta diga kyau tana ji an daura Aure tace Zawarci ya Kare Allah bamu zaman lafiya Kawayenta suna Mata tsiya da dariya Suka ce Kai marya. Bangaren Yar China cikin Yan uwansu ne da Suka cika gidan suka fara kawo labari,Kanwar Babar Yar China Salamatu tace ga Ogana ya bugo waya Yar China an daura aurenku an gama kece ta karshe an daura,Yar China Wanda yanzu ma ta shigo gidan ta dawo daga makeup,ta Sha wani dakakken material Sea blue yafi Shaddar Tawaga dark sosai da adon Golden a jiki,Yana wani walwali Yana kashewa mutane Ido,daurin dankwalin da aka nada mata da Golden headtie tayi kyau kwarai,dama gata fara sosai,dukka Dangin su Yar China farare ne yawanci gado Suka yo Yan Fulani ne usul Yar China ce tayi Kama da yan China Kalar Idonta da Dan shape din fuskar sai ta Zama Kamar ruwa biyu irin Babanta Dan China Babarta Yar Fulanin Nigeria Haka ta zama,kawayenta masu yawan jaraba gari Guda,wani gida me kyan gaske da girma ya sha tiles ko Ina a Nan ta sauki bakinta abinci iri iri na Yan gayu ta bayar aka yo Mata na saukar Baki,su Friedrice with chickens ta Sha hadin salat,ga Waina da Miya,sinasir,wani faten dankalin turawa da nama,Jullof rice,Dan Iyayin Yar China harda fura da Nono me yawan gaske an zuba a robobi kamar rufaida dink,gurasa ta Sha cabbage da Albasa da tumatur,harda Dambun shinkafa,alala,Tuwon shinkafa,ga lemukan roba da ruwan Roba da sauransu Yar China har makwaftan da suke mutunci sai da ta sanar musu Kar suyi girki ranar bikinta kowa yazo a Nan zaici ya sha. Yar China sabo da surutu da tsokana kowa ya santa ta kwashi jama'a da yawan gaske,tana shiga wajen Iyalle taje tace Iyalle Kinga kwalliyata yanzu na dawo nayi sauri sabo da kar Ina can a daura auren ban sani ba,Iyalle tace an daura fa ga Salamatu Nan ta fada Miki,Yar China tace ai nayi tunanin Wasa take min au an daura Iyalle? Iyalle Tace kwarai,Yar China Fuska ta rufe tana kyalkyala dariya dangi suna ta dariya Ana kallon ikon Allah,Iyalle tace Umma salamatu na Miki Alkawarin dubu daya kafin ki tafi gida,Salamatu tace Yar banza fitsararriya abinci fa an Kai duk abinda kika ce wajen kawayenki,Habiba ta Ajiye na angwaye daban suna can gidan suna ta tsare tsarensu na Yan karya irinku can,Iyalle Tace gayu gayu ai mu akwai Harkar girma, Ana zafi Yar China ta dauki mufici tare da mikawa wata Yar Budurwa yar gidan Salamatu Yarinyar zata Yi 14yrs tace ungo Marsiyya duk inda nayi kina bi na a baya kina min fifita bana son kwalliyata ta baci tun kafin angwaye su zo. Haka Yar China take yawo da yarinya tana Binta da fifita Wai ita Amarya,tuni Yar China ta Shiga gidan da Kawayenta suke Suka lullubeta da tsiya duk gasu Nan Yan matasa masu tarin kuruciya sai haukarsu sukeyi,Yar China ta dauki plate da cokali tayi kida rakacal...rakacal sai ta tsaya cik tace duk ku saurara kuji an daura Aure tuni babu wacce naji ta min Addua,ihu Suka saki yeeeeee....sai Yar China wlh yeeew.....Duk sun Sha gayunsu sai kuruciya amma ba karya sunyi kyau,Habiba tace me Dj yazo dama munce ana daurawa zamu fara cashewa har lokacin Kai Amarya,Yar China tace iceko me Speakers Bakwai din Nan ne yazo? Suka ae mana,yawwa so nake a gigita kowa na unguwar nan so nake yau a San Yar China amaryace,Habiba kuje a fara sakin kida me fasa kunne,da fatan kunci Kun koshi? Suka ce ae har mun shirya na angwaye a palon da Muka ware za a sauke su,Yar China ta leka katon palon me kujeru na Alfarma ga girke girke daban daban an shirya na gayu gidan wata ce suna mutunci da Yar China shi yasa ta Basu gidan. Su dai kawayen Amarya suna ta rawa da danginta suna murgude murgude,Ana ta liki Amarya tana Jan aji bata fita ba tukun,Bangaren angwaye Kuwa duk sunje gidajen amare an gaisar da surukai lokacin Aamna gidan su Yar China tazo Driver ya kawota a Arniyar mota ta zuba kyau na gaske cikin wata Shadda ta kece raini maroon,kowa Binta yayi da kallo Kamar me,gidan ta shiga ta Gaida su Iyalle ta musu Allah Sanya Alkhairi,fita tayi aka rakata wajen Yar China ta isketa a wani Palo tana Shan ac Wai Dan kar kwalliyarta ta baci,ga me fifita da mufici tana gefe idan ta fita waje tana fifita Mata. Aamna sai kallon Yar China takeyi tayi kyau fiye da tunanin me tunani Kuma a tunaninta ma Yar China ba Wani gyara kanta zatayi ba tunda taga kamar Bata da nutsuwa sai taga sabanin Haka Yar China ma kamar tafi duk Amaren yin kyau,shigarta da dinkinta ya birge,Aamna ko Yar gidan Gomna abinda zata Yi kenan,Bayan sun gaisa ta Mata Allah Sanya alkhairi,Yar China tace Aunty Balaraba dama Zaki zo? Gani kin ganni cewar Aamna tana dariya,Yar China wajen abincin ta nunawa Aamna tace ki zuba abinda kike so Aunty,Aamna tace na koshi,ai Yar China ba Wani tunani tace ai Kuwa karya ne wlh sai kinci duk Wanda yazo bikin Yar China sai ya koshi,Aamna a ranta tace Direct karya ma nake Yarinyar ta fini wauta Sanda Ina budurwa,Hannun Aamna Yar China ta rike tace nasan mu talakawa ne shi yasa baza kici abincin mu ba wallahi sai na fadawa Yaya Tawaga sabo da yasan irin zaman da zaiyi dake,Aamna ba shiri ta shiga bude abinci tayi mamaki komai na Yan gayu harkar girma,harda wata Green spaghetti ai Yar China tafi ma sauran Amaren yin abincin girma,dama bikin da kake sa rai bazaiyi armashi ba shike yin kyau,Wanda kake tunanin zaiyi Dadi Kuma sai kaga ba shine ba,Aamna dai taga zahiri Kuma taji tsoro tasan tsaf Yar China zata fadawa Tawaga idan Ahmad yaji Kuma tasan sauran bai iya Fushi ba,sai ta ebi gurasa,ta zuba dankali daban yasha nama, ta zauna taci da yawa tare da Shan lemo da ruwan,Yar china tace to kin taimaki kanki wallahi da Baki ci ba sai na Kai kararki wajen Oganki direct,Aamna tayi Dariya Tace na fita sul to,Yar China cewa tayi ai har cewa zanyi kin harareni Ni da Iyalle ta,Aamna tana dariya tace Allah ya rufa min asiri King wlh Bai Iya Fushi ba sai ki jaja min,Dariya Yar China tayi tace to ki kiyayi tabani wallahi sai na kulla Miki sharri Dan Baki Sanni bane bani da kirki ban San na gida ba,komai sanina da mutum ya min laifi baruwana cinnaka ce ni,Aamna tace Allah baki hakuri suna dariya Yar China tace muje yau sai kinyi rawa,ta ja Hannun Aamna Suka fita wurin Dj. Suna zuwa wajen angwaye suna zuwa a motoci a Nan suka Sha kallon shagali sauran gidajen Amaren duk ba mutane ba kida kamar ba biki ba sabo da sunce auren yazo ba shiri,ai Nan Suka ga bataliyar Yan Mata an dau wankan sugar ba karya,sai ka kula matar aure baka sani ba kayi zaton Yan mata ne,su kansu bikin sai ya birge su,suka bige da kallo Ana ta rashin kunyar rawa,ga fararen mata na tashi sabo da Yar China danginsu ga Kawayenta na musamman sun Shiryawa bikin,Tawaga motarsu Daya da Jibson da Ahmad sauran Kuma su Brown ga wasu frnds na daban ma,Tawaga Yar Chinansa ya fara hangowa yaga Ana ta Mata fifita Ana take Mata baya ta rike Hannun Aamna gam,Dariya yayi yace Uhm kaga Ruhina can,abokai duk Wanda yaga Yar China akace amaryarce sai yayi Dariya tana ta hada hada,Fitowa sukayi Ana ga angwaye sunzo Ana ta kallonsu amma Ina Yar China biki yayi biki tuni ta kutsa Kai cikin filin rawar,aka tsaya da kida,Mc tayiwa magana abinda zaice da Yan bikin. Ai Kuwa Mc yace Amarya tace tana yiwa kowa Barka da zuwa wannan bikin nata me Albarka,tace a fada muku a madadinta ita Amarya Sadiya Yar China da Angonta Aliyu Tawaga Uban tafiya duk Wanda yazo bikinta Bai ci abinci ya koshi ba baza su yafewa kowa ba,sannan Basu daukewa kowa rawa ba a wannan fili ko tsoho ko tsohuwa. Dariya aka dingayi Wanda Suka San Yar China sun san zata aikata,angwaye suna ji Suka dinga dariya, Amarya aka Kira tsakiyar fili da angwaye,tunda Suka fito ake kallon matasan musamman Ahmad kamar Mata zasu cinye shi da kallo Nan take Aamna gaba daya farin cikinta ya dauke kishi ya kamata,Kamar zata Yi kuka,Ahmad Yana kallonta yayi Murmushi ta sake hade rai yasan dalilin,Yar China ma ta kula rada tayiwa Aamna tace ki saki ranki Dan Allah duk Nan wace ta fiki kyau? Babu me aure Miki Miji haba yau Naga mayyar miji,ba shiri Aamna ta saki ranta tasan halin Yar China yanzu sai ta tona Mata asiri. Angwaye ne Suka shiga suna zuba Yan dubu dubu kowa da bajintarsa,ana kwashe kudi Ana ta yiwa Amarya liki,Amarya batayi rawaba ko kadan Wai aji take ja,duk Amarya me rawa bata da aji cewar Yar China shi yasa Kawai Hannunta Tawaga ya rike Suka tsaya a tsakiya Ana musu liki, ta yafito babbar kawarta Habiba da Hannu. Habiba ta karaso filin tasan Shirin Kawai ta fara liki itama,Haka kawaye Suka shigo Suma,Tawaga Hannun Yar China ya riko ya Bata Yan dubu dubu itama tana lika masa,sai da suka gama Suka fito daga filin tare da tsayawa a jikin mota gaba Daya har Yar China. Wata Yar Budurwa ce tazo wajen Yar China da Alama Yar uwarsu ce tace ke Yar China an damkawa Iyalle kudin sadakinki dubu dari cash,Yar China ta washe Baki taji kudin Sadakinta da yawa,Tawaga tayiwa rada tace dole na maka biyayya,sai ka juyani yanda kake so,sai abinda kace, su Ahmad suna ji radau sabo da kida sai anyi magana da karfi dole, suna ta dariya su yanzu Suka San Ana biki sabanin sauran Amaren. Yar China tana ganin wata kawarta Yar Gayu tazo itama ta kashe kala an sauke ta a mota Yar China ta Bata hannu Suka tafa a Gaban angwaye tace shegiya ashe Zaki zo ai wallahi da na tanaji Rashin mutuncin da Zan Miki kwando kwando,Kawar tayi Dariya tace Yar China bikinki Guda yaushe Zan fasa zuwa ai ba Amana idan banzo ba,Wai an daura ne? Waye Angon a ciki Yar China ta tunana Tawaga tana kunya Tace gashi nasan dai ba snatching Zaki min ba,Gaisar da angwayen tayi itama kawar ba kunya Ana canja kida a Gaban mazan ta fara chashewa ta tafi har filin da rawa,Yar China Dadi ya kumeta tace shegiya Shamsiyya Mansur kina wuta...kina wuta,angwaye suka sheke da dariya,Aamna a ranta tace wannan Yar China duk Yan bariki ta Tara a bikinta sai kallon Mijina sukeyi ta koma wajen Ahmad makale ta hanashi sakat,Yar China ce ta taho da wasu kawayen Wanda yanzu ma suka zo su biyar tun a Hanya tace a fara zubar da girma a Nan dan Allah ya zaku bani kunya, ai Suma anga kawaye Yan school aka fara murna Ana Rungume juna Ana fitsara a titi. Wata ce tazo itama aka sauke ta a dalleliyar mota anci Uwar gayu,Yar China tana magana a waya tana kina Ina ne Haka? Kawar Tace gani a bayanki Yar China ta juya ta ganta taje da tafiyarta dagwas dagwas suka runme kawar ta kalleta Tace Yar China Wai kece haka? Wannan uban kyan fa? Yar China tayi murmushi tace Amarya ce fa ai Dole nayi kyau da kyallin goshi,Suka tafa irin Shegun kawayen Nan ,angwaye suna ta Jin dadin bikin sai Suka ki tafiya,Jibson yace a Nan ake bikin,Brown yace wannan ta shirya ba Sanya,su Mashkoor da Bash ma Suka ce Wai sunce mu tsaya fa Za'a kaimu wajen cin abinci Bari mu gani, ita dai Yar China tana kusa da Angonta suna hira,tana cewa yau sai da nayi kukan murna harda Hawaye,Haka nake da jama'a ban sani ba? ai ko mutuwa nayi na samu wannan mutanen Kawai kuce Yar China tana Aljanna karka sake kayi min kuka,Kalli Yaya duk sabo Dani aka zo Kai amma nayi kokari,Tawaga yace gaskiya kinyi kokari ko mu mun yaba,ba Dole ba wane mutum ba Dole ku Yaba ba,ai biki ma Sai anjima da yamma ansha anko. Angwaye suna ta Jin Yar China tana yabon kanta,wata kawar ce tazo da sauri tana zuba kamshi tace sauri nakeyi sai da Yamma Zan dawo,Yar China tace to matsiyaciya Zan Rama ne Jeki wallahi ai bikinki ya kusa duk abinda mutum ya min sai na Rama a Kan nasa,Dariya kawar tayi suka tafa cikin rada tace Yar China Haka naji sadakinki har dubu dari? Yar China ba sirri Tace wallahi nayi tsada Dan Ubanki dubu dari cas suna wajen Iyalle Yan dubu dubu je kice ta nuna Miki, kawar taja Yar China gefe tace suna jinki fa angwayen,to suji Mana da banyi tsadar bane Yar China ta furta ba ruwanta da wani rada. Tawaga yace Aunty Balaraba ga matata Amana idan tazo a Dan dinga ganar min da ita,Aamna tace cab ai wallahi wannan tafi karfi na Kai baka santa bane wannan Kar take ganin kowa,Ahmad ya dinga dariya yaga Aamna ta tsorata da lamarin Yar China,Tawaga Yana ta dariya yace ai nuna Mata Zaki dinga Yi,Aamna tace yanda take ji da kanta tafi kowa ai Ni ta nuna ma Ni sa'arta ce dazu fa haka tace min sai ta zuga Ahmad Tace na harareta,daga magana direct Tace min karya nakeyi wannan ce zata tsaya na wani Bata shawara,Kai baka gani ba wannan Yar Chinan taka Kawai Dan yarinya ce amma Ni na gano Watarana ma Sai dai mu ta koya mana,Dariya sukayi Yar China tazo wajen tace Aunty zo mu tafi kin makale a Nan sai kace ke kadai ce me Miji muma fa matan auren ne,ko Kuma tsaya ga su Habiba Nan zasu zo. Yan Mata ne na jikin Yar China suka Kai angwaye inda aka tanada Ana Bude palon kamshi da sanyi ya Dake su,cikin palon Suka gani an masa wata uban kwalliya na musamman da abubuwan kyale kyale Yana bada wasu colors, kidan soyayya na turanci na tashi kasa kasa, wasu hasken Fulawowi manya Yana kawo wuta kala kala tana rubuta Sadiya Wed Aliyu Abin sai ya birge kowa Aamna ta tsaya tana kallo cike da Sha'awa Nan tace Yar China tayi nisa ba Wani shawara da Zan bata,Yan matan Yan matasa ba ruwansu komai rawa komai rawa Basu da kunya irin Yar China ne ga Iyayin jaraba su a dole Yan Mata,sune sukayi Serving kowa abinda yake so,girkin ma ya birge su,Yar China Kuwa Tace Kar wacce ta zubawa wannan abinci tana nuna Tawaga,Itace ta zuba Masa da kanta harda wani durkusawa ta Mika Masa tare da cewa yau na fara Duty na,aka dinga dariya kuwa,ita Aamna Yar China kunya ma take bata gani takeyi idan itace baza ta iya katabus ba a Gaban mutane Haka maza da Mata masu yawa,Tawaga ya karba Yana murmushi,Bash yace Muna Shan kallo yau. Tawaga sabo da kadawa Kashi miya harda bawa Amarya a Baki ta karba a kunyace Nan ne Kawai aka San Amarya taji kunya,tana cinyewa tace a Kara min,aka kece da dariya Ana yabonta taji kunya Ashe Bata ji ba,Tawaga yace okay ya Kara Mata ta lashe tace tun jiya banci komai ba fa,Tawaga yace ba Mayafi kike ta yawo? Yar China tace Ina amaryar ai Kuwa sai dai kayi Hakuri ka yafe amma bazan saka Mayafi ba na Bata kwalliyar Kuma,angwaye suna ta zabga Loma Ana Santi,Labarin bikin Yar China tuni yaje kunnen sauran Amaren ance Ana can ana rakashewa a can,Hafsat duk da Amarya ce sai ganinta akayi tazo da wasu kawayen nata. Inda angwaye suke aka nuna Mata Bash yace wa ya Baki izini kizo nan,Dariya Hafsat tayi tace bikin Yayana nazo ni,Yar China tace na Miki kyautar dubu mutuniyar bayan biki kina bi na bashi,aka dinga dariya Yar China kowa ya birgeta sai ta Masa kyauta Tace ta bashi dubu bayan biki zata bayar,Tawaga yace zuwana nan naji da kunne na kinyiwa mutum biyar kyautar dubu kince bashi bayan biki Zaki biya yanzu har Hafsat ta shida? Yar China tace ai wajen mutum ishirin nayiwa kyautar dubu bashi ne Zan biya bayan biki Kaine sheda ko na mutu sai ka biya bashin Nan,Kuma Inshaallah Zan basu tunda na fada,Tawaga a ransa yace wannan kafin biki ya Kare zata ci min bashin dubu Hamsim ma naga alama,yace waye zai biya bashin? tace Kaine ai ko yanzu Ina da Rai Kai zaka biya,Tawaga yace to Indai kina so na biya Miki ki tsaya da kyautar dubunki Haka,Yar China da shagwaba Tace duk Wanda ya min abin bajinta Allah sai na bashi,su Jibson suna ta dariya Tawaga ya shiga Uku da biyan bashi,Aamna Dariya harda rike ciki tace wallahi Nima Ina zuwa Tace ta bani dubu Ina Binta bashi Kuma bazan yafe ba sai an bani,Ahmad Yana ta dariya ai sai sukaji wasu Yan matan sunce an Basu dubu wasu dari biyar,Tawaga yace Dan Allah ku yafe Mana,Yar China Kiri Kiri Ana kallonta ta shiga kyaftawa Kawayenta Ido Wai Kar su yafe tana makale musu kafada,Jibson Dariya harda kwalla,Ahmad yace duk wacce kika bawa kyautar Zaki iya ganeta? Yar China tace sosai ma,Habiba babbar kawa tace kawaye ma suna binku bashi ance baza mu zauna ayi siyen Baki da mu ba sai ku Bamu kudin siyen bakinmu kafin ku tafi,Kawaye Suka saki Guda wallahi hakane sister,Bash Yana ta dariya ganin Tawaga ya zaro Ido waje,Mashkoor Yana dariya yace ai an daina siyen Baki yanzu,kawaye Suka ce anayi mu Bamu daina ba suna gwalangwaso abinsu,Ahmad yace yanzu Ni a fara bani list din Yan bashi,Yar China ta dinga lissafi sai da aka lissafa mutum talatin cif harda Aamna da Hafsat Haka Ahmad ya bawa Yar China cas,Nan take ta mikawa Aamna ta karba tana Dariya,Ahmad yace My world ba Imani Haka?Hafsat ma ta karbe,Yar China ta kalli Kawayenta Tace ku kuci gaba da bina bashin sai na nutsu Zan Baku,ai kawaye suka ce Basu yarda ba,Yar China tace jaraba ku karba ta biyasu Saura dubu goma ta mikawa Habiba tace ki ajiye Zan karba Hafsat tunda taga shagali itama sai ta samu wajen Zama,Haka sauran Amaren duk sun zo Humaira ce ta karshen zuwa aka dinga hotuna har angwaye sai wurin 2pm Suka tafi,Dj ma Yar China ta sallame shi Tace da angwaye su dawo Karfe hudu Masu Algaita ne zasu zo suyi kidansu na sarauta,Ahmad yace Kun gaji sarauta ne Bamu Sani ba? Yar China tace ai Cousin din Iyalleta wani Dattijo ai Sarkin noma ne,shi aka bawa Sarkin noma last year, ai su Ahmad Suka dinga dariya akan Sarkin noma Kuma dangartakar ma tayi nesa Dan son bata kudi na Yar China,Haka Suka tafi suna ta dariya Aamna Tace da Yamma zata dawo su Sha kallo,tana ta dariyar abin tabi Ahmad Suka tafi gida idan ta huta zata koma,Wajen su Humaira ya sauketa ba tare da ta Kira drivern Mummy da ya kawo ta ba. AsmaBaffa 10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 111-115 Official By AsmaBaffa Page naku ne UMMU SHU'AB SHAHRY AUTATUL KHAIR Bayan Yar China sun huta Sallah sukayi Suka sake sabon wanka,cikin Kawayenta akwai me makeup musamman Yar China tace tazo ta Yi Mata da rana,karfe hudu ba African time suna yin Sallah aka fara kwalliya dukkan Wanda sukayi anko shi Suka saka,ankon atamfa wata blue and red tayi kyau,Yan Mata Dukkansu anyi ankon kamar masifa,Yar China Kuma lace ta saka me kyau wani black and Orange,an Mata dauri me kyau da Orange Headtie kana gani kasan itace Amarya ba sai ka tambaya ba,takalmi da Jakarta black,abinka da fara,tun kafin ta Gama shirin Yan Algaita sun fara,Yar China wata Gadara take ji,kanta ya sake girma ita Yar Uwar Sarkin noma,Fili aka bawa masu Algaita,Yan matan da basu Zo da safe ba sune suka fara zuwa da Yamma sai yanzu ma Yan gayun ke zuwa,Angwaye ma sun dau sabon wanka sun zo,Ahmad Kuwa bayan Aamna ta cakare ita ma ankon ta saka,wacce take wa Humaira Kwalliya itace ta tsarawa Aamna kamar wata Amarya,ga dinkin fitted gown aka Mata dai dai ita surar Nan tata ta sake fitowa habawa ai Aamna one in million ce,babu Wanda zai so ya daina kallonta musamman yanda ta Kara wani kyau da kiba ta Kara wani haske,Ahmad ne ya canja Shadda fara Kal yazo a rantsatsiyar motarsa baka yazo har ciki ya Shiga wajen Mummy. Humaira ta fesa gayu tazo ta rike shi ta saki kuka,Ahmad ya kalleta yace Mene haka Kuma sis? Kukanta ne ya karu tana kuka muryarta da kyar take fita tace Yaya Wai anjima za a kaini Inji Mummy Dan Allah Yaya Ahmad kace sai gobe,Dariya ma ta bawa Ahmad ya shiga lallashinta gani gaki sis ke da muke ma kusan gida Daya Mene abin damuwa? Ko kin daina so na ne? Kai ta girgiza tace Ina sonka Mana yace to ki kwantar da hankalinki Muna tare Baki da matsala,Humaira ta kwabe Fuska tana ta faman kallon Ahmad hankalinta a tashe da gani a firgice take,gashi ance ita za a fara kaiwa,Meke faruwa ne Humaira? Humaira tana so ta fadawa Ahmad me Mubarak dinta yace tana tsoro Kar ya Mata fada,Hannu ta Shiga yarfewa tace Yaya dan Allah ka yima Brown magana,akan me? Uhmm...uhm....cewa yayi ....Ahmad ya gane zancen Maganar first Night yayi ya firgita Masa kanwa,Murmushi yayi yace Jeki na gane Zan masa magana karki damu Wasa yake, Humaira tana Hawaye tace Allah Yaya ba Wasa yake ba,nifa na fada Miki sis Haba ko Baki yarda ba? Murmushi tayi tace na yarda,to shiga ciki kinji, okay ta Furta ta tafi wurin Kawayenta da suke ta chashewa da kida a mugun wasu speakers duk Yan Lagos ne Basu digon kunya ko ta minti Daya. Ahmad a bedroom din Mummy ya Iske Aamna tana saka takalminta me tsini ta yafa mayafi,Yana Shiga ganin ba kowa ya rungumeta Yana Jin dadi a ransa shi Kam ya Gama dacewa,Mazaunanta ya shafa Yana sinsinar kamshinsa itama haka,kinyi kyau My world,ai ka fini yin kyau My King,you are the love of my life,I give you all of me my king,Kissing dinta zaiyi ta matsa da sauri sabo da kar shanye Mata jambaki,hand bag dinta ta dauka me tsada tace let's go,a Haka Zaki tafi kalli fa Dan mayafin Ni gaskiya maza zasu kallar min Mata,Dan Allah King kazo mu tafi wanne maza kalli fa Yan biki duk ba gyale, amma Ni na yafa ma gashi da girmansa ya rufe fa har bayana,juya to na gani,mayafin ya gani ya Dan sauka yace to muje,tare Suka fita Ana ta kallonsu duk inda Suka gifta,Su Tawaga tuni sunje can suna jiransa,gashi kowannensu ya canja wanka,Angon wani milk yard ya saka Dan gaske ga skin din Tawaga Kamar wani Dan Latin America Haka yake. Ahmad Yana zuwa da Kansa ya fito ya zaga ya budewa gimbiyar tasa mota ta fito,Jakarta tana hannunsa ya rike mata ko kunya Bai ji ya rike Mata Hannu ga Jakarta ya rike,Yar China ce ta fito Daga cikin gidan da suke ta Sha gayu Aamna tace Yarinyar Nan tasan gayu fa Ina ganinta wata shashasha,Ahmad murmushi yayi yace Ni dama nasan tasan me takeyi tunda Tawaga ya sota zai aure ta,Yar China ta fito da Kawayenta can gefe Kuma masu Algaita ne da ganguna suke faman kida me shegen Dadi,masu busa Kamar zasu cire kumatunsu,Yar China ta biyasu kudi sosai ga ruwan liki suna Sha,ai Yar China tana hango Aamna da Ahmad tazo wajen tana murmushi Tace Aunty kina ji Dani kinzo da safe kin dawo da Yamma wannan ko kanwarki ce ni iyaka abinda Zaki Mata kenan Ina godiya da yawa da nayi Niyyar Yi Miki kyautar dubu yanzu amma Ango yace na daina,idan an kawo Ni nayi farfesun Amarci Zan kawo miki,Aamna tayi Dariya ita da Ahmad,Aamna a ranta tace Zaki bayani yarinya sai dai Ni na Miki farfesun nazo jinya,Masu Algaita Suka taho Gaban Yar China angwaye abokai sunfi su Goma suka fito da kudi za ayi liki,a tsakiya aka sa Ango Tawaga da Amarya Yar China,Mutane suna ta kallo Ana nishadi,masu Algaita Tsayawa sukayi da kida Suka fara yiwa Yar China Kirari Ana ta dariya suna cewa. Lafiya Yar sarki jikar Sarki,kaga Yar na gada ba Yar na koya ba,gaishe ki Jikar sarki,Yar China tana wani girman Kai an nutsu Ana Izza,cikin Kirari suka ce kayi dace saurayi samun Jikar sarki ba Wasa ba,gabanki lafiya bayanki lafiya Jikar sarki,Hajiya Sadiya Yar Fulanin asali ta Ango Aliyu Haidar sa gabanka inda kake so kayi dace...ka tsallake rijiya da baya...sai Suka ci gaba da kida tare da busa algaita angwaye suka dinga fyalli da Naira,Aamna tazo tayi liki itama,ta likawa ango da Amarya Yan dari biyar biyar sababbi sannan ta koma likawa mijinta,Iyalle ce ta fito da sauran dangi suma Suka zuba nasu,Yar China tana murna ta rike Hannun Iyalle tace Iyalle ta Dan Allah kiyi rawa,bikin Yar Chinanki guda,Iyalle tace Allah ya sauwake min da rawa,Iyalle da sauranki fa birgewa zakiyi a Nan wajen,Iyalle tace ja'ira,Wai Ni Yar China Ina kika samo mutane Haka ne? Yan Mata sunki karewa,Yar China tace duk kwayena ne kowa da yazo wajen Nan Indai Ni na gayyace shi to ya sanni na shi babu wani gayyar sodi anan da kike gani,Iyalle tana Dariya tace amma sun Miki Halacci,Kar ma suyi Mana nima idan na hadu da yarinya naci ubanta,Iyalle ta furta Yar Nema to ayi sauri sunce 6pm Za'a Zo daukan Amarya sai an gama Kai sauran amaren kece ta karshe,Yar China tace Dan Allah Iyalle a Bari Mana sai gobe a kaini a nutse,kinyi kadan yarinya biki Daya zamuyi yau za a kaiki nasan halinki bakin Nan ba karewa zai Yi ba ana Kara Miki kwana daya Zaki ce gobe yini su dawo,Dariya Yar China tayi harda wani tafawa da Iyalle tace Iyalle kin San jikarki ai da Kun sake Kun Kara min lokacin alakoro to gobe Dan asharalle ne zaizo,to Baki Isa ba yanzu ma ya kamata ku sallami masu Algaita,Na fa biya kudi da su za a kaini suna bina da Algaita,Iyalle ta Bude baki tace dama Haka kika ce? Kwarai Kuwa na biya kudi Ni ku kyaleni Dan Allah yau Daya bafa ba Kara Yi zanyi ba har abada,Iyalle tace ai shike Nan ku karata ta tafi gida. Yar China wajen Aamna taje ta ganta ta rike Hannun Ahmad Gam,Tace Kai Yar Mannau Dan girman Allah ki kyale bawan Allah ya sake wannan azo dake Unguwa ai masifa ce wlh Zaki jawo ya daina fita dake,Aamna tayi Dariya tace Wai ke Ina ruwanki ne kije ga sababbin kawayenki can sun zo,Yar China ta duba ta hango su an sauke su a Napep,Hannu ta Shiga daga musu su taho gata,Ahmad ta kalla Yana can suna magana da su Jibson Yar China Tace wannan ba gata bane ka saketa wayo take maka zata kashe maka kasuwa,Dariya Ahmad yayi ba tare da ya juyo ba. Bash ne yace mu tsaya Kawai mu tafi da wannan Amaryar,Yar China Idonta ya kawo kwalla ta koma wajen Tawaganta tace baza a Kara min alakoron lokaci ba? Kina gani dai Yan Uwanki sunce sun fara shiri kina kallo duk kayanki har Wanda kika cire yau an Kai can gidan kice wani Karin lokaci,Yar China Baki ta rike tace Yau naji mayu yaushe suka kwashe kayan? Tawaga yace Brown ne fa ya Kai tare da Salamatu ai sunce tsinke naki babu a gidan Nan,sai kayan jikinki sai Wanda Zaki canja yanzu,Yar China tace shike Nan karyata ta Kare yau kuma,Tawaga yace na Gama gajiya ni maybe ma yau bazan iya ko motsa yatsa na ba idan na kwanta,Yar China taji sanyi a ranta tace na godewa Allah ya gaji yau ba abinda zai min,Yan bakin ciki su Habiba harda cewa wani Zan Sha zafi to suzo su gani ya gaji ma,tana Maganar zuci Batasan ma a fili ta fada ba Tawaga yaji,Dariyarsa ya kunshe dama wayo ya hada mata sabo da ta kwantar da hankalinta,su Habiba ne suka janye Yar China tazo ta shirya za a tafi kaita,Wanda baza su je Kai Amarya ba sun Gama biki duk sun tafi kasancewar magrib ta gabato,Dangin su Yar China kaf sunje sun ga gidan Yar China sun dawo da Santi suna mamaki. Haka wasu kawayen duk sunje sun Sha kallo sun dawo dake wasu Yan Mata Yan Uwan Yar China suna can sune suka Kara gyara gidan,kayan kitchen da kayan kyale kyale da Suka Kara siyo Mata na dangi masu kyau Suka Kara a gidan, gidan Suka shirya Mata komai yanda zai bada kala,komai a tsari suka Yi,Brown Kuwa shi ya maida Aamna gida ta wuce part din Humaira sabo da Humaira aka fara kaiwa Basu da yawa daga ita sai Kawayenta su hudu,Suma duk sune suka gyara gidan da komai,Humaira an sake saka Mata wasu kyalekyalen masu tsada sabo da su akwai abin. Itama Sameera lokacin da aka kawota sun sake zuba abinda babu da Kuma wasu abin na bukata na Yan gayu tunda an Gama musu me wahalar, Bangaren Nafeesat Kuwa wow itama ba karya sabo da Naira itama an Kara zuba wasu abin masu tsada musamman a kitchen,Ita Babanta da babarta su Suka kawota dakin Miji su biyu rak sabo da Yar Malam ce,sai da yayi Mata Nasiha,dama angwaye tun kafin bikin ya tarasu ya musu Nasiha sosai da sosai,Humaira da Sameera ma daidai gwargwado sun Sha Nasiha wajen Iyayensu sannan aka kawo su. Hafsat ce ta hudu da aka kawo da dunbun Yan Mata da Yan uwa,Basu Dade ba Suka tafi aka bar Hafsat tana ta kuka Ita Daya tal,duk cikinsu Sameera ce Bata Yi kuka ba,Itama Hafsat ita Daya tal aka bari ba ko mutum Daya dama su tuni duk gyaran gidan da zasuyi sunyi dama komai a Leda yake ba abinda yayi Kura da kansu Suka bare komai Suka shirya Mata,Suma abinda ya Dace zasu karawa Hafsat duk anyi komai ko wacce gidanta sai kamshi yake zubawa Yana walwali,ko wanne gida a kasa 2 bedroom and Palo ne sai kitchen store da dining area,sama Kuma 2bedroom and Palo shima ko wanne daki da toilet dinsa masu Fadi da kyau gidan ya kayatu,kowa ya gani sai abin ya birge shi, compound din ko wacce yasha Interlock da fulawoyi ga parking space,harda Dan wurin hutawa anyi wata rumfa ta haduwa da shuke shuke ga wasu kujeru da table masu kyan gaske a wajen. Yar China kawaye sun sata a gaba sai tsokanarta sukeyi yau zata gane kurenta,Dariya Yar China tayi tace to algungumai ya gaji da yawa Angon yau bacci zaiyi yace ko motsi bazai iya ba ta Allah ba Taku ba,Dariya Suka dinga kyalkyalawa Yar China Suna cewa wlh wayo ya Miki,Yar China Tace bama wasan karya da Tawaga na,wanka tayi ta fito Suka kwashe kayan data cire da komai nata Suka zuba a leda,wata kaza Salamatu ta kawowa Yar China kafin ta shirya aka takura Mata sai da ta cinye,aka Bata wasu tsumin ta Sha,Salamatu Tace kayan maganin tsuminki ki ya bedroom dinki an ajiye Miki su Safiyya zasu nuna Miki ki boye Banda hauka karki Bari ya gani Kuma,Tace to tana shafa lotion bayan ta gama wata atamfa super aka Bata ta saka dinkin Riga da skert sun kamata cif,Yar China ta tsula kyau,Atamfar Wata brown and red ta tsaru ka rantse ma ba atamfa bace wani material ne daban,gashin da yasha gyara Yan matan suka gyara Mata shi aka Mata wani acuci da shi Suka ce baza ta daura dankwali ba ai Amarya za a Kai Mayafi zata yafa,Mayafi Kato Amma me sharara da kyalli mayafin ya hadu shi aka bawa Yar China ta yafa sai ta fito kamar wata Yar India,takalminta me tudu Kalar mayafin red Haka jakar ma,Habiba ce ta rike kayan da Yar China ta cire a Leda har Inner wears baza su Bari ba sai an Kai gidanta,Kuma Iyalle ce ta sasu,Sallar Nafeela aka sa Yar China tayi tare da adduoi,tana Idarwa taji ance motoci sun Zama Ready Amarya ake jira,Yar China tana Jin Haka ta fara kuka Tace karyata ta Kare Ashe da gaske akeyi bikin Nan,Ashe ba karya bane kaini za ayi wayyo Iyalleta,Yan Mata suka dinga ihu da shewa Ana dariya,Habiba tace masu Algaita ma sun Zama ready suna mota sun shiga,Yar China Tace sunci Uwarsu Shegu dasu aka hada baki za a kaini yau,mutane Suka dinga dariya itace fa tace sune zasu rakata da Algaita. Wajen Iyalle aka shigar da Yar China Iyalle taga Yar China tana kuka sai itama ta fashe da kuka tace bazan iya nasihar Nan ba naje daga baya nayi Mata a dakin mijinta,Yar China tana kuka tace Iyalle ki min Nasiha Allah idan Baki min ba sai tafka tsiya gobe bazan Yi girki ba a gidan,Iyalle kukanta ya tsaya cak ta bude Baki Tace Dan Ubanki karki girkin Mana yunwa ta Miki Illa,Yar China tace dama Baki Iya Nasiha ba tsoro kike ji Kar a kureki Baki iya ba komai ba,irin na mutanen da kike Yi,Iyalle maimakon Nasiha sai Suka bige da fada tace bazan Yi nasihar ba Dan ubanki idan nazo nayi Miki ai zanzo ganin gida salamatu ku tafi da ita ana jiranki,na fasa yin kukan rabuwar dake Yar banza fitsararriya cewar Iyalle, aka dinga dariya,Yar China taji ance a tafi sai kuka ta dinga Shure Shure da burburwa ana riketa taki fita daga dakin an rasa yanda za ayi da Yar China,tana kuka tana cewa Allah...Allah sai na fasa kofin da kika siya min Iyalle,Iyalle tace kinwa kanki marar kunyar karya,ke Baki ji kunya ba duk bikin da kika Yi kin koma kuka,ba fitsarar da bakiyi ba Ashe karamar marar kunya ce,Yar China kuka ta dage Jin koshi ko kunya babu,babu Wanda Bai lallabata ba taki hakura ta tashi a tafi,Iyalle tace ku jata ta karfi ku tafi,Yar China ta Dan Bude mayafinta ta leko tare da gallawa Iyalle harara ta rufe fuskarta again,Iyalle Tace Zaki ci Ubanki Kuwa wlh ku Kira min Tawaga Angonta Yana Nan a waje suna Jiran Amarya,ai Kuwa su Habiba suka tafi da sauri Suka Kira shi tare da fada Masa Taki yarda ta fito tana ta kuka an rasa yanda za ayi da ita,Tawaga Wanda da shi za a dauki Amarya yace gani Nan,su Jibson suna ta Masa dariya ya tafi gidan Haka ya kutsa har dakin Iyalle,yaga Yar China a lullube ta dunkule tana kuka,tana Jin Muryarsa tayi Mukus tsoron Tawaga take ji,duk haukarta tana nutsuwa idan ta ganshi,Iyalle tace gata Nan anyi anyi ta fita Taki,Yar China tana shesheka tace Haka nace Miki bazan fita ba? ai dai bance ba ko daga nace a Bari na huta,Iyalle tace to tashi ki bisu ko wallahi na Hana kowa zuwa rakaki ya dauke ki shi da Kansa,tun kafin Tawaga yayi magana ma ta Mike ta cikin Mayafi ta gallawa Salamatu Harara tace ai sai kuje ko. Tafiya akayi aka sa Amarya a tsakiya,Sadiya tana kusa da Yar China ta Mata rada tace wai Yar China Ina kika samo wannan guy ne? Kinga yanda har abokansa duk hadaddu,Yar China ta daina kukan tace daga zagi wallahi,suna magana ai tana tunawa kaita za ayi gidanta sai ta sake fashewa da kuka tace shike Nan Yar unguwarmu,ga makwaftanmu duk su Maman Yusrah shiken nan ta sake sakin kuka angwaye suna ji,motar Ahmad da tafi ta kowa kyau Nan aka shigar da Amarya da Kawayenta su biyu sun sata a tsakiya,Yar China tana Zama tace kudi na Dana Tara a gidan Maman Yusra a karbo min abina na tafi da shi nasan kafin nazo Unguwar Nan sai da tsohon ciki na Dan Allah Habiba karbo min Tawaga ba mutunci ya sani ba wallahi ciki zai min da wuri,su Habiba suka dinga dariya Allah yasa Ahmad Bai shigo motar ba. Haka suka je Suka karbi Mata dubu ukun ta duk akan dubu Uku take wannan abin,lokacin Ahmad ya Shiga motar Ana karbowa yaji Amarya duk uban kukan ta daina Tace ku rike kudin dubu ukun ku raba idan kun koma gida ku Siyo maltina da Madara ku Sha jininku ya tsatsafo sabo da a bikin Nan Kun Sha wahala,Suka ce mun gode Amarya. wurin motoci goma Suka Yi harda ta masu Algaita sun sauke gilasai suna ta uban hurawa suna kida a motarsu an sasu a tsakiya,wannan algaitar ta jawo duk inda motocin suka wuce sai an kalla babu tambaya mutane ke cewa wata Yar Sarkin ce ake bikinta,wasu suce kaga masu abin Yar sarki ce wlh,Har aka Shiga Unguwar Wanda Basu je ba Suka dinga Santi,dayar kawar Yar China Bilkisu tace Yar Chi na Kan uba wlh kin bar mu a baya Kinga Unguwar da zaku zauna,lokacin kuka Yar China takeyi amma sai ta daina kukan tace ai Baki gama kallo ba sai anje latinmu da gidana Dan Uwarki harda lilo,Ahmad Yana jinsu Yana ta dariya a hankali,Habiba tace bayan biki da sati Daya zamu Zo cin abincin Amarya,Yar China harda dukan Cinyar Habiba Tace rankem Zan Muku ranar shinkafa dafaduka zazzafa,suna ta dariya ta manta ma da wani kukanta sai ta Bude mayafin sai ta Gama kalle kallenta sai tace uhm bari na rufe Ni Amaryace,da taji su Habiba suna yabon wani wajen sai ta sake dage mayafin, sai da aka zo gidan tace Kun gani ko sai kuka Kuma wayyo Iyalleta wayyooo.....duk sun cikawa Ahmad kunne sun isheshi da surutu shi Aamnansa ma yake tunawa yanda kwalliyar yau ta Gama tafiya da Imaninsa gashi ba sukuni bare yaje ya bada tukwici,a ransa yace Nima yau wani First Night din zanyi. Bayan an fito Amarya tana ta kuka, masu Algaita suna ta Yi duka sauran kawayen da Suka rage Wanda suka kawo sauran Amaren sai da suka fito kallo Jin Algaita su kansu sunyi zaton wata hamshakiyar Yar sarki Tawaga ya auro,aka sa tayi Addua kafin ta Shiga gidan da kafar dama,can Bedroom din Ango aka kaita kowa Yana ta Santi Ana kallo,Aamna ta shigo gidan itama,Mamakin Kukan Yar China ya kamata dama duk bikin Nan Yar China zata Yi kuka,Masu Algaita sun Gama aikinsu motarsu Suka hau aka maida su gida cike da murnar irin kudin da suka samu. Mintuna kadan aka kwashe kowa aka maida su gida Bilkisu da Habiba Kawai aka barwa Yar China,su ma Basu Dade ba su Mashkoor Suka tattaro kansu na kowacce Amarya aka maida su gidajensu,Yar China taci kuka Lamar me,ita da Humaira sunfi kowa kuka,Aamna dai Ahmad gida ya ja abarsa a matse yake, yace ba Wani Ango da zai raka,Jibson da ledojinsa na kayan makulashe ya kalli sauran su Brown yace kuzo muje ku taka min,ai kowa yace Ina wlh bazan iya ba wajen tawa Zan tafi,Jibson ya shige gidansa ya barsu nan Yana cewa na San dadin abin nayi Nan. Mashkoor yace Ni tawa tun dazu ita Daya ce Kar damuwa ta Mata yawa hawan jini ya kamata yayi nasa wajen,Juyawa Brown yayi sai yaga babu Bash ma a wajen ya neme shi ya rasa suna tsaye tare Kuma Kamar Aljani ya bace,Brown ya kalli Tawaga yace Ni muje ka raka ni kaga Nima tawa yarinya ce,Tawaga yace Ashe zaka mutu baka je ba,Ni Nan ma gangar jikina ce a Nan tuni ruhi na ya tafi wajen Amaryata shima Tawaga ya tafi da ledojinsa,Brown Baki ya tabe yace Yan iskan tuzurai shima yayi nasa part din. Baba shima sai dare ya koma gida Yana can wajen Daddy suna karbar Baki,sai da ya dawo yace Aishatu su Kam Yaran Nan abokan Ahmad sunyi dace Suma matansu kyakyawa gasu Suma mashaallah,Mama Baki ta tabe tace to me Budurwar zuciyar masifa Ina ruwanka,Baba yace daga na yabe su na sa Albarka shike Nan bazan ce Yara sun fimu yin sa'a ba? Yanzu ki kalleni Sanda muke matasa Ina na Kama kafarsu a kyau da haduwa? Ke Kuma ko rabin rabin mace daya cikinsu Baki Kama ba shine Dan na Fadi gaskiya Zaki hau Ni da masifar kishinki,daga fadar gaskiya lokacin kina Budurwa kyau ne da ke? Mama Tace to Kai kyan ne dake lokacin ma duk noma da wahala ya kashe ka sai kace kolon Almajiri,Baba yaji Haushi yace naji amma ke a lokacin Naga ko wuya Baki da shi sai kace kunkuru Haka kike,Mama ta tashi fuuuu ta bar Masa dakin. Baban Brown Kuwa Wanda Jibson ya Masa kwacen Budurwa yau yini yayi jikinsa ba kwari yasan yanzu Kam ya rasa Sameera har abada, Juyi yayi a saman Bed dinsa tare da Jan Tsaki yace ai tun a duniya ga sakayya Nan Jibson ka gani kana saurayi Allah ya jarabceka ka auri bazawara sai kaje ka karata,Kana matashi irin wannan ai da Budurwa ma ka dace da kafi Jin dadi ai gashi kaga sakayya ya ja tsaki ya sake yin Juyi yace shike Nan Sameera yau wani zai ji dadinsa,Maman Brown ce tana gefensa a kwance Tace kaji kunya wallahi, da masifa yace ki barni naji da abinda yake damuna ko yau da akayi bikin danki na lakada Miki mugun duka Yan bikin da Basu karasa tafiya ba duk suji mu,ai ke kika zugasu munafukar banza,Shuru ta Masa tayi kwanciyarta. Bangaren Siyama Kuwa Bata San komai na bikin ba,duk ta shiga damuwa ga bikin Faisal da sabuwar budurwarsa Saura sati Daya,ga babu Wanda yazo yace Yana Sonta Sai Hashim,abin duniya ya Mata zafi Nan tace tunda suna mutunci da Jibson a baya Bari ta lallaba ta dinga shige Masa ko zai so ta,Nan take cikin Daren Jibson sunci kaji da Amaryarsa Sameera sunyi Nafeela tare da yin wanka Suka shirya cikin kayan bacci na kirki suna zuba kamshi ya dauki abarsa Yana karewa Surarta kallo yace Kamar Baki taba aure ba a duniya gaskiya na dace,murmushi Sameera tayi tana shagwaba ya Shiga Sarrafata duk ya rude Sameera akwai Kaya na birgewa ba karya,Jibson ya zare Yar rigar wacce babu marabarta da tsirara wow ya Furta ganin albarkatun kirjin Sameera,Nan take ya Bata suna Soulmate, Sameera Ana Jin kunya cike da kissa irin ta tsohon Hannu,ai Jibson yace akwai garabasa nan sai nayi sati ban Bude gida ba,hope an kawo duka kayanki Dan gobe duk Wanda yazo ganin Amarya ko kawo Kaya sai dai ya koma da abinsa, Sameera har da wani girza kirji ai Jibson yace Ina bazan Iya Jurewa ba ya fara Sarrafata itama Sameera tana tayashi Kamar zasu kashe kansu dama an taba Yi me za a jira,Yana cikin rakashewa zai nemi Hanya kenan Kiran Siyama ya shigo wayarsa ,banza yayi da waya aka dame shi da Kira kamar hauka,Takaici yasa Jibson ya jawo Wayar ko duba me Kiran baiyi ba yace wanne dabba ne wannan Dan Allah yau aka kawo min Amaryata a dameni da Kira wannan wanne naci ne tunda ka Kira sau daya sau biyu ba'a daga ba ka hakura Mana,aikin banza Yaja Tsaki tare da kashe wayar gaba Daya. Sameera tace baka duba waye ba idan Babban mutum ne fa? Jibson yace babu wani mutumin kirki me hankali da zai dinga rada min Kira Haka cikin dare missed calls yafi goma,Share Kawai koma Mene maji da safe idan gari ya waye ba Wanda zai kashe min Night Dina King yace Kar mu daga kafa,Dariya sukayi Suka ci gaba da gashi. Ita Kuwa Siyama mutuwar tsaye tayi ita ba zagin ba ma aure taji Yana cewa,Nan take ta Kira Kawarta Hauwa ta tambayeta Wai Jibson yayi Aure? Hauwa tace cab ke Baki sani ba bikin Nan da kowa yasan labarinsa an Sha shagali to gaba dayansu group dinsu yau aka Gama biki an Kai amare ma,Siyama Hawaye ne ya silalo Mata,nadama ta zo Mata, Tace na cuci kaina nayi hauka,Haka Kawai Ahmad Bai nuna ko alamar Ina birge shi ba amma Ido na ya rufe har nayi saki na Dafe na Kori Faisal Dina,wannan wacce hauka nayi Haka,tun ban samu Daya ba na saki Daya na cuci kaina kuka ta saki me karfi tana ta zabgawa kanta Mari tas... tasss....Ummanta ce ta shigo tace lafiya? ai Siyama ko kulata Bata Yi ba taci gaba da Marin kanta sai da Umman tata ta rike Mata Hannu,tana kuka tace Umma dama karya na Miki na cuci kaina cin amanar Aamna nayi Nan ta kwashe komai ta fadawa Umman tata,Umma tace ai na sani dama zuba Miki Ido nayi ai munyi waya da Aamna ta fada min komai,jira nayi Naga iya gudun ruwanki banza dabba wacce Bata San Halacci ba,itama Umman ta zuba Mata Rankwashi tace sai ki shirya auren Hashim wallahi an Gama komai idan Baki sani ba,Babanki ya Gama komai baza ki Kara sati biyu ba sai da Auren Hashim umma tayi waje,Siyama taci gaba da kukanta. Mubaraq Brown shikam bayan sunci abinci,sunyi wanka da Nafeela ta sunna,Humaira wasu kayan bacci ta saka Yan ubansu farare masu tsada Riga da Dan karamin wando,Brown ya rude jikinsa har rawa yakeyi,Humaira ganin ba kyaleta zaiyi ba ta fara Kiran Yaya King Brown yace Yaya shima Yana can Yana yayewarsa da tasa,gwara ma ki daina kiranki Umarni ya Bamu yau ba daga kafa Ni ba hakura Zan iya Yi da ke,yanda kike dinnan Yar Balarabiya Ta'ali Ta'al Habibty Brown harda larabci Wai Ta'al,Humaira sai da tayi Dariya ba shiri,kasancewar yarinya ce a hankali ya bi da ita Yana sarrafa abarsa sai kace tsohon maye haka yake bi da ita,Humaira taji zafi sai kuka take rusawa tana Neman agaji ko kulata ma baiyi ba Kawai kalamansa yake masu Dadi amma Humaira ba dadinsu take ji ba. Mashkoor shi Bai Sha wahala da Nafeesat dinsa ba sabo da tana da Dan shekarunta sannan Kuma Yar Malam ce akwai nutsuwa Tasha wahala Amma Bata Yi wani kuka ba. Bash sai da suka Gama cin abincin Amarci da kaza sannan kowa yayi wanka da Brush Suka tada Sallar Nafeela raka'a Daya yayi ya sallame ya manta,Hafsat tace Baby raka'a Daya fa kayi yace Allah? tana Dariya tace wlh,yace tashi mu sake ya Kuma Jan sabuwa wannan karon yayi Raka'a biyu Amma sai yayi sujjada har uku,Sai da sukayi Sallama tace sujjada Uku fa kayi,Bash yace Ni bazan sake ba ta cika Inshaallah Allah zai karba Kawai yayi Addua duk ya rude,Tun ba a fara taba Hafsat ba ta fara Kiran Yaya Tawaganta,Bash ya rike Baki yace Haka zamuyi dake? Yanzu Hafsat Haka Zaki min ko Hannu ban rike ba? Hafsat tace ni wlh bana so na gaji bacci zanyi,Bash yace to Baki Isa ba yarinya kinyi kadan,uban kuturu yayi kadan,Bash ba boye boye yace Yayanki Yana can Yar wani shima yau ta shiga Uku Dole na ramawa Yar China a kanki,Hafsat ta fashe da kuka ta Mike tsaye a saman gadon Suka dinga zagaya daki Taki yarda,Bash yace gwara ma ki tsaya idan Zaki yini kwana zanyi ni,kullum ki dinga I love you Amma Baki San ma'anarta ba,ai yau ma'anar I love you Zan fassara Miki wallahi Dole sai na fassara Miki ita,Hafsat tace Amma kuka yaudare mu Baku fada Mana fassararta ba tun a waje ba kuka rufe mu,Kai Bash ya girgiza Yana dariya,sai da ya faki Idonta ya Mata caraf damka daya,Babu irin kukan da Hafsat bata Yi ba sai da muryarta ta dashe a yau kyar muryarta ke fita. Ahmad Kuwa tsohon Hannu shi second Round ma yakeyi tuni anyi first yai gwangwajewa sukeyi da Aamnansa. Yar China ta Tawaga tunda ya shigo Yar China ta ganshi da ledoji ta tuno ai kaji ne a ciki sai ta daina kukan tayi Shuru a cikin mayafinta take ta kallon Ledojin hannunsa,Zama yayi a gefenta cike da nutsuwa yace Amarya bakya laifi,Yar Dariya ta kamata ta kunshe abarta a Mayafi,Tawaga a hankali ya sa hannunsa tare da cire mayafin Yana murmushi itama murmushi tayi tare da rufe fuskarta da tafukan hannayenta,Dariya ma ta bashi yace me za mu fara a ciki muci abinci sai muyi wanka da Sallah ko me kike so a fara,Yar China ta tuno yanda aka biya Sadakinta tayi tsada da yawa tace yanda kace,Kallonta yayi tare da lumshe kyawawan idanuwansa,Tsaya tsaya a Haka Yaya kayi kyau tsaya na kalleka,Dariya yayi ba shiri,Yar China ta Bata Rai Tace ka kwafsa wlh,Hannunta ya rike Yana Wasa da yatsunta Yar China taji tsoro a ranta da wayo tace ai yau bacci kake ji ko? Ka gaji ma na sani,Tawaga yace sosai ma,Yar China ta Gama yarda da Tawaga,tace Malamin Islamiyyar mu da yaji za a min aure ya kirani ya dinga min Nasiha har da cewa wai duk wacce mijinta ya sata abu taki to ranar malaiku ne zasuyi ta tsine mata Wai hakane? Kasan Nifa kafi Malam a waje na,Tawaga Yana dariya yace Allah? Tace Allah ko wanne Malam ne ko Kabiru Gombe ne ba ruwana Indai Kai ka fada naka Zan dauka,Tawaga Rungume ta yayi yace I'm so Happy,Yar China Tace ai baka birge ba Yi min da yare na hausa irin wannan kalaman da yaren mutum sunfi shigarsa Tawaga Yana mamakin Yar Chinan tasa shi bai ma san ta Kai Haka ba. Kajin ya bude musu da su lemuka Madara da sauran Fruits,Yar China ta leka Ledar tace lallai kana ji dani Allah yasa Kar na Haihu da wuri Yara suzo su dinga cinye Mana dadinmu,Tawaga yace ai da yawa za Ana siyowa nasu daban,Yar China tace to shike nan,Tawaga ya Shiga Bata a Baki Yar China tace laaa Haka na gani a wani film Nima to gashi nina ana bani a baki,Yana bata yana ci tambayarta yayi da Dadi? Yar China tace sosai ma ai dai dama Dan kar na Fadi wata magana ne kace Santi nakeyi shi yasa nayi shuru,Tawaga ya fuske yace Fadi bazan Miki Dariya ba,amma Iyallace tace irin kajin Nan daga Saudiya ake kawosu a jirgi,Tawaga yayi Dariya yasan Iyalle Kawai ta kalawa sharri Dan kar ace itace,Sai yace Zan tambayi Iyalle a waya,Nan take Yar China tace Kai dai ba Iyalleta ce ba nice na fada,Dariya sukayi ta taba gashinsa tace ku Yan gayu ne Yaya Ina sonka,Yace Nima haka amma Ni Yaya za'ayi ta ce min Kamar bani da gata ya furta da Kalar tausayi,Yar China Tace ka cika gaggawa Yaya Zan canja ne, Alright,sai da suka Gama ci ya maida komai kitchen,Ya kalli Yar China yace muje in Miki wanka,Yar China tace a garin gaba gaba nake da Zan tsaya zagadar a gabanka bada Ni ba Allah Ni zanyiwa kaina,ta Mike ta gudu Daya dakin Wanda yake a nata. Sai da tayi wanka ta zabo wata purple night gown ta Kai cinya wata silk su Habiba ne suka ce ita zata saka,gashinta me Dan tsayi ta gyara Yana sheki,duk turarukan da akace ta shafa sai da tayi,Yar China a jikin mudubi ta kalli hakoranta tace fes,harda daukan wata sweet me kamshim mint tana tsotsa,Powder ta shafa sama sama harda lipgloss ta fito ras. Katon Hijab ta maka har kasa ta koma dakinsa Wanda shi har ya saka Jallabiyya Yana jiranta a saman Sallaya,Sallah ya jasu tare da adduoi,ya Mata tambayoyi akan Addini ta bashi amsa dai dai yace to jeki kwanta,Yar China tace Kai fa? Yace zanzo ne akwai abinda Zan danyi,Fuska Yar China ta kwabe ta cire Hijab din ta Ajiye ai Tawaga Ido ya zaro yanda ta tsula kyau kasa dauke Idonsa yayi,jallabiyarsa ya cire daga shi sai boxers,Yar China tace Kai a Haka kake bacci tana cikin Bargo kanta ne a waje tana kallonsa,ae Kawai ya furta ya kashe wayoyinsa da light. Yana Hawa bed din Yar China ta rumtse Ido tana Hasbiyallahu wa niimal wakil,Tawaga Yana jinta ta bashi dariya,a hankali ya matsa jikinta tuni jikin Yar China ya dauki rawa Karrrrr......a hankali yace Hira fa zamuyi,Dadi taji tace to muyi Hirar tafi ma Alheri. To ki juyo Mana Muna facing juna Haka ake kwanciya Mata da Miji,Yar China ba musu ta juyo Yar Alawar da take Sha ma tuni tsoro yasa ta ajiyeta a bakinta bata tsotsa,Tawaga ya kalleta tare da Furta kinyi kyau Yar China tace kaima Haka,dama Yaya Ina so na tambayeka Yace Ina jinki,tace lokacin da kake kawo kannenka makarantar mu amma a lokacin kana Shan cocaine ko? Kai Dan Cocaine ne? Dariya Tawaga ya dinga yi yace wannan sharri Haka to Ni wlh Bamu taba ganin cocaine ba ma bare mu Sha,Kai ta jinjina tace Amma wata munafuka Yar Uwarmu lokacin an sa bikinmu Tace sunyi Bincike Kuna shaye shaye nace to ko madarar sukudayin kake Sha Ina son abina,kasan aure Dole sai an kawo Suka,Tawaga yace ki kyale zancen Nan gaba Zan Baki labarin dalilin da yasa ake Mana sharri,Yar China tace to,San min Alawar yace,Yar China ta gane me zaiyi tace to ta cuno Dan bakinta gaba tare da furta gashi Nan na rage maka Hanya,Dariya Tawaga yayi,Yar China Tace yanda ka biya sadakin Nan na Isa nace wani Abu,Tawaga jikinsa ya hade dana Yar China jikin Yar China ya fara rawa tace Kai kaga bana Jin tsoronka amma jikina rawa yake Yaya ko Nima harija ce ban sani ba? AsmaBaffa 10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYA TA AAMNA is dedicated to Garba Butalawa family. 116-120 Official By AsmaBaffa Page naki ne UMMI DEEJAT Sai nan gaba za a gane ai cewar Tawaga Yana murmushinsa,Yana kokarin Shafa gashinta tana ja da baya,Tawaga bai zafafa ba yace na gode tunda dama ba kaunata kikeyi ba,daga na dan tabaki sai fara guduwa Kamar wani dodo,baki yar China ta bude tare da furta Kai Yaya ni nace bana kaunarka? to hakan me yake nufi kefa kika ce duk abinda nake so zaki bani shine zaki karya alkawarin tun ba'a je ko Ina ba,munyi fada mun bata gaba daya, Yar China taji tsoro a ranta tace yanda ya biya sadaki me yawa ga gidana me kyau komai shi yayi amma bawan Allah na masa haka ai banyi halacci ba,yanda yake kula dani yana ji dani komai Yar Chinata komai yace Yar Chinata amma yau na Masa haka ai ba Yar halak bace ni, komai wahala dai nayi hakuri tunda dai a haka aka haifi kowa,Kawayenta ta tuna tace ga firdausi last year aka Mata aure amma har ta haihu Kuma itama haka aka mata, ae Mana Haka aka mata Kuma ta hakura gata da danta,Nan ga kawarmu Na'ima yar karama da ita aka Mata aure yau Na'ima itace da katon danta gashi ma yaron sabo da girmansa yafi karfinta idan ta daukeshi har rinjayarta yake duk kankanta irin ta Na'ima ta jure,ai tunda Na'ima ta tsallake Nima dole na iya jurewa yanda ma nake da girma Kawai na hakura,Tawaga yaga tana ta tunani yace me ya faru kike tunani haka? Yar China tace ba komai Yaya,Tawaga yace okay daga lokacin ya fara raba Yar China da kayan jikinta. Shafa Yar China ya shigayi a hankali tana Jin wani iri a jikinta tayi Shuru a hankali yace My Angel Skin dinki tayi soft da yawa Dadi jikinki,Yar China muryarta na Dan rawa tace ai Iyalle tace tunda aka haifeni sai da nayi shekara Uku Ina tafiya dagwai dagwai ana min wanka da Sabulun salo dan Ghana,Tawaga Yana dariya yace kai amma Iyallen mu ta kyauta min,ai Ungozoman ce ta basu shawara shi yasa ka ganni haka fara haske na yaki dishewa duk Kuwa da irin gwagwarmayar dana Sha ta duniya, Tawaga ya jinjina Kai tare da furta Allah yayiwa wannan Ungozoma Albarka da ace na San Inda take kema idan kin Haihu sai na dakko ta ko Zan samu ta wanke min jaririna fes,Yar china da tausayi tace Allah sarki ta mutu tun last year,kaga goshi na Iyalle tace shi ake fara shafawa Sabulun shi yasa yake sheki,Tawaga ya fara daina ganewa ya fara nisa a sarrafa Yar China. Za tayi magana kenan sai ji tayi bakinsa cikin nata Yana Mata wani irin kiss,Yar China da taji Kamar ita bata iya ba amma Yana dora hannayensa a saman Breast dinta masu laushi taji tana iya maida Masa martani,Yar China mamakin kanta takeyi a zuciyarta tana Kai kaji kamar zan iya Nima,jikinta ne ya karbi sakonnin Tawaga taji canji da wani yanayi a jikinta me Dadi,Nan ma a ranta tace me nake ji Haka ne? dadi ne ko me? Yar China taji wani ta fara Zama wet, a ranta tana Kai shike Nan nayi releasing,zare bakinta tayi a hankali a fili tace Yaya na kawo Ni Alhmdllh an gama ko? shike Nan nasan ma yanzu zai wahala ban samu ciki ba,Allah yasa Kar na haifo me katon Kai,Tawaga ya dinga dariya Kamar me yace ai ko farawa ba ayi ba gimbiyata,Ido Yar China ta zaro tace duk wannan kokarin da nayi? Kai Yaya wlh karka rame fa,Ni bana so ka rame,ance yawan yin abin Nan ramewa akeyi ka dinga Hakuri Yaya,Tawaga ya dinga dariya kamar me yace Ni dai sai na Kara,Yar China tace a daren farko Yaya har sau biyu? Yace ae, to shike Nan tunda ba zafi Kara yin na biyu. Tawaga yaci gaba da sarrafa Yar China Yana ligwigwita yanda yake so,Yar China taji na yanzu ma yafi dadi,ta bada Kai kawai,Yana cewa duk abinda na Miki kiyi min kinji,Yar China tace hakkun...hakkun Yaya ai Ina Jin Dadi Zan dinga maka kaima,yace kina fada min sweet words,Yar tace ka hadu da su ai tuni ban San kana son jinsu ba da tuni Ina fada maka su,Shuru nayi dama karka ce min Yar Iska ce ni dama,yace Haba Ni da nasan a bata ai, Ni kadai Zaki na fadawa,yaci gaba da sarrafa Yar China son ransa,yace duk inda na taba kika ji da Dadi ki fada min kinji? Tace to,Yana ta aikinsa ya tsotsi can ya murza Nan,yana fara tsotsar Boobs dinta Yar China tace wannan yayi,ai Yar China har kanta take sosawa sosai take bawa Tawaga hadin Kai suna ta romancing,Yana zuwa Down dinta yaji wani kamshi,fara sucking Mata yayi Yar China ta Gama tafiya sabo da Dadi tace kara wuta na Yar China akwai Zuma,Tawaga yaji wani dadi yace you are so sweet my Angel,Yar China tace dan ma ba Kai akewa wannan Kalar ba ai Kai baka San dadin ba nice nake ji,Sai da Tawaga ya Gama susuta Yar China sannan ya Shiga koya Mata salon da zata Masa,Yar China tace shike Nan yau mun Zama Yan Iska sunanmu ya Shiga list,Tawaga yace Yan Sunna dai,Yar China dai Haka Yana koya Mata tana Masa ba musu kowa yaya idan taga ya fiye Nishi da kukan Dadi sai tace Yaya kaima ka kawo? Yace a'a Tace Kai baka da lafiya wlh Ni sau biyu na kawo,Tawaga bai Isa yayi kukan Dadinsa ba sai Yar China ta tsaya da Yi Masa tace ni gaskiya Naga baka Jin Dadi kuka kakeyi taya Zan dinga saka kuka kana Babba,Tawaga baida lokacin Shirmenta ya sata taci gaba,Kuma inda yayi sa'a duk abinda ya gwadawa Yar China tana Yi Masa iya yinta,wayo ya Mata Bayan ya kwantar da ita yace Sucking zai mata,Yar China taji dadinsa ba musu ta saki jiki,da wayo taji Yana Neman hanya tace me zaka yi ne? Yace ai wani salon ne,duk ya haukace har tsoro ya bata,da wayo ya samu ya sakalkaleta yanda baza ta iya ko motsi ba,sannan ya samu da wahala ya shigeta sabo da ta matse da yawa ya Sha wahala,dagewa tayi zata kurma uban ihu yayi sauri ya toshe Mata Baki da hannunsa,Kuma Bai fasa abinda yakeyi ba,Yar China Kamar wacce ake wa gunduwa gunduwa da sassan jikinta haka sai Idonta Daya zazzago Kamar ana Mata dure ga ba damar ko magana,sai da yayiwa Yar China dalla dalla yaji matsanancin Dadi mara misaltuwa,ya samu gamsuwa sosai,duk wani maganganu masu Dadi da yake furtawa Yar China ba ji take yi ba sabo da wahalar da ta Sha. Sai da ya zare jikinsa a nata bai cire hannunsa daya toshewa Yar China Baki ba,a gefenta ya kwanta yasan Yana saki sai tayi karar Nan,a haka hannunsa ya toshe Mata Baki sai da yaga hawayen ya ragu Dan mugunta sannan ya cire hannunsa dake bakinta. Yana cirewa Yar China ta kurma Ihu tace wallahi sai nayi kara'i baka Isa ba,Azzalumi kayi min fyade ka barbada min gishiri a Hq na,Tawaga yace Kai Angel gishiri kuma? Yar China tana kuka har da tari tace da me ka zuba min? kayi min fyade ka zuba min Kuma gishiri abinda ka sa min ai yafi karfin ace a jikin dan Adam yake sai dai idan mugunta kayi min ka hada da gishiri,yace to wannan shine asalin abinda akeyi ba Wanda kika ce dazu har kin kawo ba,Tsit Yar China tayi ta tsaya da kukanta tace yanzu a haka Na'ima kawarmu ta haihu?Tawaga Yana dariya cike da nishadi yace ae Mana, Tace Kuma yanzu a Haka Aamna take wani makalewa Ahmad? Tawaga Yana dariya yace yes,ai pillow ta dauka ta dinga kwadawa Tawaga tace bani ba Kai na daina yarda da maganarka daga yau,ai gwara naji Maganar gizo da koki akan maganarka,Ina kallonka me gaskiya komai kace na yarda Ashe gwara gizo da kai ban sani ba,Tawaga dariya harda rike ciki shi Kam ya Gama Shan dadinsa yau. Da kyar Tawaga ya samu Yar China ta yarda ya kaita toilet fafur tace bazai Mata wanka ba ita zata yiwa kanta ruwan zafi,yasan ba Yi zatayi ba yasan halinta Amma ba yanda ya iya,ai Kuwa Yana fita tace Haka Kawai zafi Kan zafi ga azabar da ya min ga ruwan zafi ai wallahi da ruwan sanyi zanyi wanka,Yar China ta sakarwa kanta ruwa me uban sayi tayi wanka tare da tsarkake jikinta ta daura towel tace haba har naji sanyi,Yar China ba mutunci Yayan ma ta daina fada sai Kira ta kwala Masa Tawaga....Tawaga...bai ji ba,tace Kai Tawaga uban mugunta kazo ka fito dani,shigowa yayi tare da zare towel a Gaban Yar China zaiyi wanka Dan ya tsoratata Yar china ta rufe idonta tayi waje da kyar tana dingishi saura kadan ta Fadi,wanka Tawaga yayi yana Fitowa yaga kokarin Yar China data iya canja Bedsheet ta gyara komai kamar ba abinda ya faru Kuma har ta maida rigar baccinta ta kwanta, Bedsheet ya dauka ya wanke ya Shanya shima ya kwanta a gefenta,tana jinsa tayi kamar tayi bacci,zafin da take ji yasa ta kuka kasa kasa,a jikinsa ya rungumeta Yana aikin lallashi,Yar tana kuka tace ai ka gama dani dama Indai kaji ana baka Hakuri to an cuceka,a haka har bacci yayi awon gaba da su. Washe gari da Sassafe Siyama ta shirya jiki a sanyaye ta tafi gidan Baba marikin Aamna,ita ce ta buga musu gida,Baba Yana tsaki an tashe shi a bacci ya bude gidan yaga Siyama,yace Lafiya haka?Siyama tace Bari na shigo ciki,Baba ya wani babbake Kofar yace ban gane ba ki shigo? Gidanki ne? Ko ajiya kika min? Siyama tace a'a wata magana ce ta kawo ni,Baba yace Allah yasa ta kudi ce,shigo Matukar ba Maganar yanda kwandala zata shigo bace sai naci mutuncinki shegiyar kafa kamar kwarkwaro,me Zaki fada mana Yar banza wacce ta gaji cin Amana,Nan Ana zaune dake lfy ashe da abinda kike kullawa,Siyama dai tana bin Baba a baya Suka shiga har Palo Suka zauna,Mama ta fito suka gaisa tana mamakin ganin Siyama,Mama tace meke tafe dake Haka da safe? Siyama Kai a kasa tace dama zuwa nayi dan Allah ku tayani rokon Aamna ta yafe min,nayi kuskure nayi son zuciya Sam ban kyauta ba,nasan Aamna tana da taurin Kai Matukar baku sa baki ba baza ta yafe min ba,Ina so naje gidanta Ina tsoro Kar ta wulakantani,Tausayi Siyama ta bawa Baba,yace karki damu Aamna bata da wannan rikon zata yafe miki ki samu lokaci ko da Yamma ne kije,Baba da son gulma harda cewa ke gashi har yanzu Allah bai kawo Miki Mijin ba ko? Siyama saura kadan Hawaye ya zubo mata tace ai an kusa biki na,Ummata da Abba sunce ko sati biyu bazan Kara ba za a daura min auren dole da wani Dan Uwana Hashim,Ido Baba ya zaro tare da dafe kirji yace ba dai wannan Yaron ba Hashimu Mai gini dan Uwanku? Siyama ta gyara sunan tace ae Baba Hasheem ba,Baba ya daura hannu a kirji kamar mace yace Hashimu dai dana sani? da shi akayi ginin makwafci na gashi Nan wancen sabon gidan na gabas dani, Allahu Akbar yaro dan baki kakkaura haka,kin mori yaro me karfi,Indai karfi ne sai Hashimu haka Zaki ga ya daga bulo uku shi daya, plaster Kuwa sai ya gama gidan Nan Bai huta ba,Siyama Hawaye ya zubo Mata Jin ita bata Yi dace ba,sai ta tuno Faisal da yanzu yake da hadadden Office,Baba yace anyi Maganar auren ne? Siyama tace har sun kawo kudi ma dubu sittin,Baba yace haka farashinki ya karye Siyama? Kin fadi rasha rasha Haka kinyi resheshe? Siyama sai da tayi dariya ba shiri,Mama tace ai irin wannan auren yafi danko ma Allah ya tabbatar da Alkhairi,gaskiya Hashimu ya dace shi Allah yasa ayi damu,Baba Yana Nasiha karki damu shi Allah Haka yake hukuncinsa,karki ga Wai baki auri Faisal ba kiyi tunanin ko Allah baya sonki ko Dan kinyi laifi kinci Amanar Aamna shine ya jarabce ki shi Allah ba ruwansa,sai ki ga kafiri Yana hawa Arniyar mota musulmi me tsoron Allah Yana yawo ko keke Bai da shi,sai ya bawa karuwa miji na kirki me kudi sai ya bawa ta gari Kuma Dan Iska talaka,duk kaddara ce ta Allah,shi Allah ba yanda bai Iya ba,wlh karki dauka ko dan kin so Mijin Aamna ne wannan kaddarar ta same ki Sam,shi ai so ba karya bane,Kuma Allah ne ya sa Miki Kawai laifinki da bakiyi yaki da Zuciyarki ba wajen hakuri,duk Dan Adam Yana kuskure Siyama,akwai Wanda suke abinda yafi naki girma Kuma Allah ya Basu abinda suke so. Ki dauka wannan kaddararki ce Kuma ba rabon Faisal bace Kuma ba rabon Ahmad ba, ke Rabon Hashimu ce,ya Dade Yana sonki dama Allah ne ya amsa Masa adduarsa,karki Yi zaton Hashimu dan Yana sana'ar gini Wai kinfi karfinsa ko Bai dace da ke ba,Allah zai iya azurta shi Rana daya, gashi Yana da NCE dinsa baki san me zai Zama ba,wallahi Hashimun da kike rainawa sai yazo yafi su Ahmad kudi Baki sani ba,sannan shi din duk Wanda ya kalleshi ya kalli Faisal yasan Hashimu yafi Faisal kyau da kyan diri Kawai haske Faisal zai nuna Masa amma Hashimu yaro ne me tsafta Dan gayu ga iya Muamula ga hakuri,kiyi Hakuri da zabin Allah,karki kalli Wai kin yaudari Faisal shi yasa yayi kudi Kuma ya samu wata ko wani Abu ba Haka bane Kawai ke ba rabonsa bace Allah yayi hakan Kuma Inshaallah Watarana sai kinzo kina murna,komai na Allah dai dai ne Kuma shine zabin Alkhairi,ki daina damuwa ki saki jikinki ki so mijinki shawara ce na baki a matsayinki na yata kawar Aamna. Mama tace wlh Haka ne ban taba sanin Baban Zuhra kana da Ilimi Haka ba sai yau,Baba yace to algunguma kwance min zani a kasuwa,Siyama ta Kama Dariya dama ta Saba da fadan su Baba tasan komai, Siyama taji Dadi da sanyin nasihar Baba yanzu sai taji bata da damuwa ko kadan ita kanta tasan Hashim yafi Faisal kyau da gayu ma Kawai dan baida farcen susa ne,a kasar nan Kuma yanzu an tsani talaka musamman me sana'ar karfi,Indai akace yau sana'ar karfi kakeyi kana cin halak da guminka Mata Basu damu da mutum ba shi ba kowa bane sai dai ya nemi me saukin gata irinsu ne kalarsu Wanda sau tari irinsu sune na garin ma Amma Ina masu Aiki a office ake nema masu ci da biro ko da kuwa Haram ne babu matsala indai da kudi da mota to fa ka Gama da mata,ko auren mace kayi sai tayi ta maka ladabi sai abinda kace sabo da kana da Naira,idan Kuwa baka da shi to Kare ma ya fika daraja. Siyama cike da kwarin gwiwa ta koma gida tana shiri da Yamma taje gidan Aamna. Bangaren angwaye Kuwa Jibson bai bude bangarensa ba ko daya,Dangin Amarya sunzo kawo wasu kayanta bugun duniya yanaji yaki budewa Yana makale da Sameera tunda sukayi wanka breakfast ma tare Suka Yi abinsu,dole sai wajen Aamna Suka je Suka bata idan sun bude ta basu, Mashkoor ma shine da Kansa yayiwa Nafeesat dinsa girki tana ta shagwaba,Hafsat Kam ita Kuwa daga gidan su bash aka kawo,Kanwar bash ta danna door bell Yana budewa ya karba yace ki gaida Ummi ya rufe garam sabo da Bai so suga Hafsat tana can Idonta ya kumbura luhu luhu lallabata yake Yi, Humaira Yar Madara ita da kuka tayi bacci da Kuma kuka ta farka har ya Mata wanka Suka Yi Sallah tana Hawaye,ko baccin data koma Ajiyar zuciya takeyi har 11pm Suka tashi ya sake gasa ta ya Mata wanka Brown ya shiryata da Kansa har kwalliya ya Mata amma kuka yasa ta bata kwalliyar ita sai dai a Kira Mata Ahmad,a haukarta ma da Mummy zata Kira ya kwace wayoyin tare da boye su,Oga Tawaga Kuwa har after 11am basu tashi ba Yar China tunda ta farka ta canja kwanciya tayi goho a Kan gadon a haka take ta bacci Wai tafi Jin sauki sauki. Aamna da gogan tsofaffin hanu da asubar ma Basu hakura ba sai da suka sake gwangwajewa,da wuri 11:30am Aamna ta Kira wayar Sameera tace abinci me za a dafa? Tace ai ita ta fara girki ma karta kawo musu komai,Ahmad yace to fa Kira min Brown please naji lafiyar kanwata,Wayarsa ta dauka ta Kira Brown Yana dagawa suka gaisa ta mikawa Ahmad kukan Humaira ya fara jiyowa,Ahmad yace ango me za a kawo muku? Shima Brown yace ai Ni nayi da kaina,Humaira ce tun jiya nake fama da ita abincin ma taki ci,bani ita Ahmad yace,da sauri ta karbi Wayar tayi tunanin ma lallashinta zaiyi ai sai masifa da bala'i Dan Ubanki ke kadai ce mace wallahi idan nazo baki daina ba saina tattakaki ya dinga cin uban Humaira,Brown ya fisge Wayar yace wanne irin wulakanci ne wannan zaka dinga yiwa matata masifa Kai waye yayiwa taka aikin banza ya kashe wayar,Humaira taji fada kuwa sai ta daina dama can shagwaba ce Wai ita Yar madara,ta daina kukan amma bata kula Brown sai da taji yace zai je ya taho da King sannan ta dawo dai dai. Ahmad Kuwa Aamnansa ya Rungume Yana dariya yace su Yar China Kawai Zaki kaiwa abinci itace yarinya,Aamna tayi Dariya tana sake kankame shi tace ai nasan Tawaga Yana can Yana Shan bala'in Yarinyar nan ya Shiga Uku zai Sha kuka,Aamna bata San Yar China tafi kowa juriya ba,lokacin Yar China tayi karyar gasa jikinta Tawaga kin yarda yayi ya dauke ta da Kansa yaje ta Sha ruwan zafi kuwa ba ji ba gani,Kuma taji Dadin jikinta sosai sai dai taji zafi harda kuka,wanka ya Mata sosai, itama tace kawo na maka Yaya?Sabulu ya bata Yar China tace ka min tsayi fa tsuguna Yana ta dariya Yar China harda sa soso Kamar wani danta ta Masa wanka,yace an Gama? Tace sabi Daya fa tal sai nayi maka sabi Uku,Haka tayi ta yi,tace daga hannu,ya daga ba musu ta dinga wanke Hammata tace yaro baya fita sai kyuya Dariya ta bawa Tawaga matuka ya dauke cak suka dinga nishadi,tace zaka fama min ciwo,a hankali ya ajiyeta a Haka suka karasa suka fito ya dato a Towel,Wayarsa ya dauka yaga Kiran Ahmad,bin Kiran yayi Yana yiwa Yar China chakulkuli da Daya Hannun tana ta dariya tana guduwa a saman bed,dariyar Yar China suka fara ji,ba shiri Aamna da Ahmad Suka kalli juna da mamaki,Abinci fa? Ahmad ya tambaya,Tawaga yace a kawo Mana Ni kasan bana girki ita kuma ba yanzu zata fara ba,Ahmad yace Dan Iska,Dariya sukayi ya kashe wayar,ya kalli Aamna yace kinji da kunnenki wannan Yarinyar zakakura ce,yunwa nake ji muje na tayaki please a Kai musu Nima na ci.. Lafiyayyen Kari Aamna ta hada ta bar musu nasu Ahmad Kuma ya bawa me kula da garden ya Kai part din Tawaga a wani basket. Aamna Kuwa tana saman cinyar king dinta a Haka suke cin abincin cike da so da kauna suna nishadi,Aamna tace Amma yau ba inda zaku fita tunda an gama biki ko? Dole Zan fita su Mummy suna shirye shiryen komawa ga Saddeeq da matarsa Su yau zasu wuce ya kamata muyi Sallama,Zan rakaka My King,no yawon yayi yawa haka My world ki zauna ki dan leka wajen Amaren da Yamma sai dare Zan dawo,Fuska ta Bata cike da shagwaba tace yanzu har sai dare Kuma kace bazan bika ba? Kin fiye rigima Daddy ne ma fa zai bani wani Aiki kin San su Jibson suna Gama Amarci zamu fara Aiki Kuma Daddy yace dole na fara zuwa Office kafin su,Aamna cike da tausayi tace Ina tausayawa kaina yanzu shike Nan sai wurin dare Zan dinga ganinka? Kuma ka fita tun 8am ko 9am? Ahmad yace sosai ma Watarana ma Haka zamu dinga tafiye tafiye kasashe,Aamna Hawaye ya zubo Mata tace wlh ni bazan iya Zama Ni kadai ba ba sai ka dinga tafiya Dani ,Ahmad yace dama duk inda tafiya ta kamani ta kwana ai da ke Zan tafi,Suma da matansu zasu na tafiya su Bash,Sai lokacin Aamna ta saki ranta,Hawayen nata ya shiga lashe mata daga Nan suka fara kissing juna Kamar mayu yace muje muyi wanka Zan fita ne ya furta tare da Daukanta cak Suka haura sama abinsu cike da kaunar juna. Yar China ta gama shafa lotion tana zaune a Gaban mirror daure da guntun towel Wanda Ya Dan zame daga Kirjinta ana ganin rabin Boobs dinta masu kyau,Tawaga ya dawo gabanta Yana ta janta da Hira amma Idonsa Yana Kan Kirjinta Yana ta kallonsu kamar maye,ita Kuma Sarkin surutun bata kula ba sai da taji Yana bata amsa da Uhm...uhm-uhm..ta kalle shi sai taga Kirjinta yake kallo hankalinsa ma gaba Daya Yana wajen,Yar China tace Yaya Kai daka biya Sadaki irin Muguntar da ka min jiya ai da iya kallo ne da yafi Indai baza ka Kuma Yi min Muguntar Nan ba to Zan na Bude maka kana kallo,Tawaga yaji ya samu sabon dabara da sauri yace ae bazan sake ba na daina ma gaba Daya gwara kallon nafi Jin dadinsa a Haka ma Sai na kawo ya isheni,Yar China taji Dadi tace to Shikenan Indai kallo ne kayi ta kalla ko yaushe tunda ka daina min me zafi,Da sauri Tagawa yace ae Kamar tsohon maye yasa hannu ya sauke Towel din kasa Yar China taci gaba da kwalliyarta tace kayi ta kalla fa abinka karka dawo kace me zafin zaka min tunda na hanaka kallo,kayi ta kalla ai kabiya sadakinka,Tawaga sai saurin daga Kai Yana ae-ae,Yace to Tabawa fa? ah Indai baza ka barbada min wannan gishirin ba kayi ta tabawa ma,ya sake tambaya kissing fa? Romancing dai? Yar China tace Feel free da wannan Indai ba barbada gishiri to komai ma kayi Zan yarda. Tawaga ya dinga Murna ji yake kamar ya tashi ya taka rawa baiyi zaton zata Bari ko yatsa ya rike Mata ba,akwatuna ta nuna Masa tace me Zafin? zabo kayan da kake so na saka maka,Tawaga Yana dariya yace Jiya kika ce min nine me Sanyin yanzu Kuma kin canja,Tace yo wani sanyi naji da Kai jiya ba zafi ka bani ba Haka Kawai sai nace maka me sanyin ka godewa Allah bance maka me tafasa ba ma,wata atamfa data birge shi a lefen Daya hada ita ya zabo Mata dinkin Riga da skert me kyau na zamanin gaske yace su zata saka. Pant ta zabo zata saka ta zauna da kyar a saman bed tare da dago kafarta kadan tace rike min ita Haka,Tawaga ya rike kafa Daya ta zura pant din,ta sake dago dayar tana cije baki tace rike,rikewa yayi Nan ma ta saka sannan ta Mike tare da Furta ja min shi sama,yace ai gwara ki bani na sa Miki gaba Daya,Yar China tace au magana zaka fada min ma? Da sauri yace Ni na Isa,Harara ta balla Masa Yana kallonta Yana murmushi ya sa mata tare da ja Mata sama ya saki robar wandon wani tas ya bada Kara a jikinta,Ihu ta saki zata Yi kuka ya bata Hakuri I'm sorry sweet Angel,Jallabiya fara ya saka Yana zuba kamshi,Itama Yar China kayan sun Mata kyau sosai ta danyi daurinta ture kaga tsiya tace ba lafiya Ina Naga ta wani wahalar daurin dankwali , Rungume ta yayi suna tsaye a jikin Mirror Yana murna a kunne ya rada Mata kin Yi kyau,I love you,Yar China itama murmushin tayi tare da cewa me too, abincin da Aamna ta Aiko musu ya dakko yayi serving nasu tare da hada musu tea lafiyayye,Nan ma a baki ya bata shima Yana ci,Sai da suka gama ya gyara inda duk bai Masa ba a gidan ya taimaka Mata,ya fesa roomfreshner me kamshi,Yar China tana kallonsa sabo da gidan ko alamar dirty Bai nuna ba jiya duk an kalkale ko Ina sai taji sauki zuwa gobe zata fara. Tana kwance a lumtsumemiyar kujerarta Yana Zaune a gefenta kafafunta suna saman cinyarsa Yana Mata tausa ta jawo Wayarta tare da Kiran Iyalle,Iyalle ba gane suna takeyi ba ta Gama sallamar Baki kenan ta daga taji muryar Yar Chinanta,Iyalle tayi Dariya tace Yar gari dama yanzu nake Neman Habiba tazo ta latso min ke naji ya kika kwana,Dariya Yar China tayi tace Iyalleta lafiya lau banyi kuka ba,dama kince In zauna lafiya to gamu Ina ta Zamana lafiya banyi Masa abin Allah wadai ba yau ma da safe ya dinga sa min Albarka,Iyalle tace Iyyeee ja'ira kinyi hankali Ashe,Yar China tana ta kyalkyala dariya tace Iyalle yaushe Zaki zo gidan Nawa ne? Zanzo cikin satin Nan Inshaallah,to Allah ya kaimu Iyalle Ina binki bashi fa,Iyalle Tace na me Kuma? Nasihar da kika ce Zaki min Allah sai kin biya bashinta ko Mai dadewa gwara ma kizo da wuri,Dan Ubanki ba gashi kina zamanki lafiya ba? To kwana daya tal shine nayi hankali? Allah Kawai kizo ki min Nasiha idan Baki iya ba Kuma kuzo tare da wakilinki yayi min a madadinki,Iyallle tace ke dai anyi sakarai Kamar me hankali Watarana,Yar China tace Iyalle jiyama Sai da ya sa min Albarka yafi sau talatin da biyar Ina ta irgawa Bai Sani ba,Iyalle Tace yayi kyau jikata,Yar China tace Iyalle yanzu ki chanka me nakeyi? Guess Indai Zaki iya ki canka naji,Iyalle tana Dariya tace yo zai wuce kina kwance a Dan gadonki,Dariya Yar China tayi Tace to Baki ci ba Taus......Wayar Tawaga ya fisge ya Kara a kunne tare da gaisar da Iyalle Suka Yi Hira tana ta sa musu Albarka Suka rabu. Yana kashewa ya bata Rai yace sirrin namu Zaki fada? Yar China taji Tsoronsa sai ta wayance tare da furta ba fada Mata komai zanyi ba,Tausa fa zakice,Yar China rantsen rantsen wayo ta Shiga Yi Tace da ubana ce Mata zanyi tausayina kake ji Ni ba cewa zanyi tausa kake min ba,kasan dai bazan fada ba sai kace baka Sanni ba Ina fa da hankali Ina zuwa Islamiyya, Dariya yayi Wai rantsuwar ma da Ubana shine rantsuwa,Alright ya furta yace to karki sake ko da wasa,Harara Yar China ta galla masa tace sake min kafata in tafi Amarya guda wanda ko Dan masu gida na kashe na kashe banza sai dace Allah yaji Kansa shine ni tun daga yau ma Za'a fara min fada,Jawo Yar China yayi jikinsa Yana dariya Yana aikin lallashinta ba wahala tace na hakura tare da gyara kwanciyarta a jikinsa. Aamna wanka suke a toilet tare da Angon nata,ya fara wanke Mata kirji ya canja salo ya koma shafawa Yana sarrafa su yanda yaga dama,Aamna rudewa tayi ta haukace masa ta kankameshi tana kissing dinsa tare da saita Hq dinta a Hajiyarsa ta Shiga murzawa a haka,gigicewa suka sake Yi suna Nishi da kukan Dadi Aamna ta dafa jikin bango tare da juya baya tace fuck me Baby,Ai Kuwa Ahmad dama kadan yake jira ya fara harka suna Nishi tare da Furta dirty words sai da ya dauki lokaci sannan yasa ta canja salon Blowjob, sai da suka Gama kashe junansu da love sannan Suka sake wanka Suka fito suna nishadi, bayan sun shirya har mota ta rako Ahmad dinta sai da ya shiga mota ta shiga ciki Suka dinga kissing din juna kafin su hakura ya tafi,sai Yamma take tunanin Shiga sashen Amaren Wanda Lokacin Siyama ta shirya zuwa gidan Aamna Neman afwa. AsmaBaffa 10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYA TA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY 121-125 Official By AsmaBaffa Page naku ne Aisha Ummin Sadeeq Mamu Galadima Ummu Amaturrahman Mummy sani Ummi Manga Aamna bayan ta gama aikinta na gyara gidan wanka tayi tare da Shiryawa cikin wata Arabian Gown black tayi kyau sosai ta Dan yafa mayafin,Fitowa tayi da Niyyar fita tana bude Kofar palonta sai ga Siyama tana Shirin dannan door bell,Aamna tayi mamakin ganinta,daure Fuska Aamna tayi,Siyama tasan Haka zata faru,jiki a sanyaye tace Aamna nasan dole kiji haushi na,ba sai na shigar Miki gida ba,Hakuri nazo Baki akan abinda ya faru,nasan ban kyauta ba amma yanzu na gane kuskurena ki yafe min,Aamna jikinta ne yayi sanyi tace amma kin San kinci Amana ta,na daukeki Kamar Yar uwata,komai Nawa kin sani Ashe ke ba Haka bane sai ma gurguwar shawara da kika dinga bani sabo da na rabu da Ahmad ke ki Maye gurbin,ban sani ba kina ta bibiyarsa,Ashe gidan Nan da kike zuwa badan Allah bane Mijina kike so,Bayan kin zugani na bar gidansa ke Kuma kika koma ya aureki,ai ana barin halak ko Dan kunya Siyama. A tunani na ko Ahmad cewa yayi Yana sonki baza ki amince ba sabo da ni,sai gashi kece ma da kanki kike so ya aureki,da ace Ahmad me son Mata ne da tuni sai dai ya auro min ke ki Zama kishiyata Siyama,wannan wanne son zuciya ne irin naki? Nima maganina kenan da tun wuri ban gane halinki ba naci gaba da Bude Miki sirrina na maida kaina wawiya,Siyama tace nasan ban kyauta ba,Dan Adam ne kowa Yana laifi kema ai kina laifi dan Uwarki to Dole ki yafe min ki hakura,Dan Iskanci ma Ina baki hakuri kina min wani wa'azi da me zanji,Har kasa Siyama ta durkusa Bayan ta gama zazzage Aamna abinka da kawaye Kuma schools mate,Murmushi Aamna tayi tace na Dade da yafe Miki Ni dama ni ban rike ki ba,Siyama ta gallawa Aamna hararar Wasa tace in ma kin rikeni Kya gaji ki sakeni ya zakiyi dani,Cikin palon suka shiga Aamna tana cewa meke going bayan rabuwa? Gist me,Siyama ta Bata labarin Aurenta da Hashim,Aamna tace Allah yasa Haka ne mafi Alkhairi,Siyama tace Ameen tana kallon Aamna tana cewa Kamar ciki ne dake Aamna,Dariya Aamna tayi tace ba Wani ciki dalla Kawai Hutu ne tana fari da Ido ta furta as you can see mijina Yana min abinda nake so ba Dole na canja ba,muje gidan Amaren can mu dawo. Fitowa sukayi suna tafiya suna hira gidan Jibson Suka fara Danna door bell lokacin Jibson suna wanka ma tare da Sameera, suna ta wasanninsu suna dariya, cike da shagwaba harda girgiza kafada yana cewa Ni a wanke ni....Sameera ta dinga dariya Kamar me,tace kaji munyi baki fa,baza su shigo Mana ba ko su waye su juya,Sameera tace idan kannenka ne fa,su koma gidan ubansu Nan gidan 'Ya'ya nane gidan uban wasu ne,kafadarsa Sameera ta daka suna ta dariya har su Aamna Suka gaji tace wannan dama baida ta Ido muje wajen Bashi,Door bell Suka danna sau Uku Bash ya Bude,Aamna tana murmushi Suka gaisa yace ku shigo Alhmdllh gwara da kuka zo na samu salama masifa tun jiya nake fama kuje ku taimaka min Aunty Balaraba,Aamna ta sheke Dariya tace har Ina tunanin buga maka kofa Ina tsoro,Bash yace ai Neman agaji nakeyi karku ga nayi kus a gida wahala Kawai nake Sha,Ni dai ango Yana sheki amma Banda ni,Dan Allah ku Shiga tana bedroom Ni Bari na fita Nasha iska,Dadi ya Zama wahala Kai wannan Tawaga Basu iya raino ba,Su Aamna suna ta dariya suka haura sama Bash yayi waje. Yana fita Wayar Tawaga ya Kira Yana dagawa ya fara zagin Tawaga Dan uwarka kasan Haka kanwarka take kuka rufe Ni,yarinya sai bala'in kuka tun jiya ta hanani bacci wlh baka Iya tarbiyya ba,kayi asara ana ta ce maka baya Goya marayu ashe kyale Yara kayi suke abinda suka dama,akanta aka fara? Daga yin Abu sau naya Yarinyar Nan ko kwakwarar Nishi Daya banyi ba ta dinga ihu tana fisge fisge kamar me ciwon jijjiga, Dariya Tawaga ya dinga Yi yace ihu Kuma? Bash yace au Baku ji ba? ai Yaya Tawaga Kawai take Kira,na fada Mata Yayan Nan shima Yana can Yana Yaye wata,Tawaga Yana ta dariya yace karfi ka gwada Mata zaka kashe min kanwa,Bash harda rantsuwa wlh ko wani gama Jin dadin banyi ba bala'in Yar Nan yasa na hakura,Tawaga yace kanka ka cuta Kai da zaka Mata wayo ta ko Ina ta kasa motsi to yanzu ya akayi? Kai Malam Nifa ba abinda nayi wlh,Tawaga Yana dariya yace to yau Kuwa ka cika aiki,Bash yace Fadi da ihu ta jawowa kanta na daina tausayinta tunda Bata da mutunci,Tawaga Yana ta dariya. Aamna Kuwa suna shiga kukan Hafsat Suka ji duk ta firgice,ko ya aka Yi motsi sai ta tsorata,Aamna Tace lfy Hafsat? Hafsat ta Dan goge hawayenta tace lafiya a'a ba lafiya ba,Siyama tace to fa me ya faru ne,Hafsat ta galla Mata Harara tace ki fita ke Budurwa ce Baki San komai ba Aamna Zan fadawa,Siyama ta rike Baki tace to Yar Iska Nima na kusa sanin koman ku karata tayi kasa ta bar Aamna. Aamna tace mene Haka Hafsat wannan wanne shirme ne? Da girmanki,ki kalli yanda kika jefa mijinki a wani Hali akan wannan,Yar China ma da take yarinya ta nutsu bata wannan haukar sai ke,Tashi kiyi ruwan zafi,Hafsat tace tunjiya yace zai min naki yarda,Aamna Kamar Babba ta dinga fada tare da hada Mata ruwan zafi da gishiri ta shiga Kuwa ta gasa sosai har sau Uku sai Kuwa taji dadi,sai ga Hafsat an daina kuka,har Kaya Aamna ta zabo Mata tayi kwalliya sosai cikin wani lace dark green,ta zuba kyau,fada Aamna ta dinga Mata ko da Bash ya shigo ba karamin Dadi yaji ba Ganin gimbiyarsa a Haka,Kuma ta saki ranta tana ta walwala,Bayan su Aamna sun tafi a gefenta ya zauna tare da Kiranta da Hafsat Nigeria limited,Dariya tayi tare da rufe fuskarta da tafukan hannayenta. Mashkoor Zaune suke tare da kannensa,Nafeesat ta Sha kwalliya suna ta Hira abinsu,Bayan su Aamna sun Shiga suka gaisa Siyama tana ta kallon tsarin gida me kyau,Basu wani Dade ba suna Yar Hira da Nafeesat Suka tashi bayan sun musu Sallama suka wuce. Kannen ma Mashkoor ce musu yayi Yamma tayi ku tafi gida,Yara basuyi Niyyar tafiya ba ya kore su, Tafiyarsu ke da wuya ya koma jikin Nafeesat Yana mata Kirari Nurse dita ke kike da Quinone da Gentamicin, Sirinji ma idan ya ganki tsoronki yake ji,Nafeesat akwai sanyin hali sai dai tayi ta dariya Kawai. Sashen Humaira Kuwa Kawayenta ne Suka zo Mata Brown din ma Yana Bedroom har su Aamna suka Gama zamansu Suka fita abinsu. Hajiya Yar China Suka Iske a Palo ta sake sabon wanka cikin wata English gown me gajeren hannu,rigar purple ce me adon fari,tana kwance a kujera tayi matashi da Cinyar Angonta,suna kallon Film a katuwar plasma,sai da su Aamna Suka shigo ta Mike tare da gyara zamanta tana murmushi tace Aunty Aamna Sannu da zuwa,Aamna tana karewa Yar China kallo duk ta fisu walwala da sukuni ka rantse ba ayi komai ba,Siyama tace Amarya bakya laifi,Yar China ta kalleta Kawai sannan tace Ina yini? Lfy Alhamdulillah cewar Siyama,Tawaga Kuwa Yana sanye cikin wasu kana Nan Kaya marasa nauyi arsh color,gaisawa sukayi da fara'a,a American Film din da suke kallo aka fara kiss Budurwa da saurayi,Aamna kunya ta kamasu,Yar China wani Dan pillow ta dauka tare da Kare gefen fuskarta ta bangaren su Aamna yanda baza su ganta ba,tana Dariya tana kallon Tawaga shima ita yake kallo da rada take Masa nuni da irin najiya...irin na Jiya Suma sukeyi,Murmushi yayi tare da daga Mata gira Yana Mata nuni Kar su Aamna su gane, Dariya take ta Yi a hankali yanda baza suji ba,Siyama da Aamna suna kallon abinda sukeyi,rada Siyama ta yiwa Aamna tace Kinga Yar Iska yarinya karama. Cire pillow din Yar China tayi tare da mazewa ta Mike tare da kawowa su Aamna abin motsa Baki harda wani Naman kaza soyayye da Iyalle ta Aiko da shi su dai suna ci suna kallon Yar China tana ta yiwa Tawaga magana da gira da Baki da Ido suna ta Yarensu Wanda su kadai Suka San me suke cewa,Mikewa Tawaga yayi yace Bari naje gida na gaida Mama tunda ga Baki kinyi,Yar China da shagwaba tace Kuma yaushe zaka dawo? Ni...ni....Allah ban so ka zauna su tafi su barni ni Daya,Ido Siyama ta zaro a ranta tace Yau Naga tsohuwar balagaggiyar yarinya,Sama ya haura da Niyyar dakko key din mota ta Mike tana kallon su Aamna tace Ina zuwa tabi Bayan angonta a hankali,Basu dade ba sai gasu sun fito Yar China ta saka hularsa a kanta,Aamna tana kallo yasha wani yadi me laushi brown. Sai da ta rakashi bakin Kofar palon sannan ta cire hular daga kanta ta sa Masa a Kansa,gyara zamanta yayi yace sai na dawo,karka Dade please, Inshaallah ya Furta tare mata kiss a kumatu,ko kunya Yar China tace I love you my Man,Tawaga yaji dadin sunan da ta rada Masa yace sai na dawo zamuyi celebration na wannan sabon sunan,Dariya tayi tare da rike hannunsa tana Wasa da Yatsunsa kanta a kasa tana uban murmushi tace will you miss me? Alot ma cewar Tawaga,Ni na fara missing ma tun yanzu,I'm so Glad ya furta sannan yace ki kular min da kanki,I will,kayi Driving a hankali karka jawo min masifa, Inshaallah yace Yana dariya,har ya tafi ta riko hannunsa ya juyo da sauri tace banda kallon mata,karka yiwa kowa murmushinka me tsada,Tawaga Yana wani Jin nishadi kamar ya hadiye Yar Chinansa yace me Zan siyo Miki? Icecream da tsire me dadi,an gama my Queen harda cewa Aamna pls Aunty Balaraba karku tafi ku barta ita Daya har sai na dawo,Aamna Tace kasan idan King ya rigaka dawowa bazai Bari na zauna ba,Na sani bazai rigani dawowa ba ma,Aamna tace to,ya tafi ma amma Yar China sai data leka ta window tana cewa ka kula da titi da Trailer,Banda Overtaking,Allah ya tsare min gabanka da bayanka,Tawaga juyowa yayi Yana daga Mata Hannu tare da cewa Ameen,Kiss ta aika Masa daga nesa shima ya amsa tare da huro Mata nasa. Yar China wajen Aamna ta dawo ta zauna tana murmushi ta kalli Aamna tace Aunty Allah ciki ne dake,Kamar sa'arta ta cafki damtsen Aamna ta latsa Kamar Likita tace Ahayye Muna da suna very soon kinji yanda kika Yi wani luguf wannan soft skin din bana body lotion ne ba,Dariya Aamna tayi tace to period ma nakeyi bare kuce Ina da ciki dazu na fara,Yar China tace Kai Banda Karya dai Aunty nasan Ya Ahmad yayi ajiya tuni ko ya kika ce? Yar China tana kallon Siyama harda Mika Mata Hannu Suka tafa. Dariya sukayi gaba daya Yar China tana kallon Siyama tace Yan Mata ke yaushe Zaki shigo sahun mu ne? Aamna tace Wato Dan kina da Aure shine harda wani ce mata Yan Mata to an kusa bikinta itama Saura sati biyu zamu gayyace ku. Yar China ta Furta mashaallah amma Kin San lokacin ban fara fita ba Ogana bazai Bari na fita ba,ko yace ma na fita bazan fita ba Nafi so sai nayi kibar amare na canja sai na fita a ganni,Aamna tace tab ai Ni ranar da aka kaini washe gari na fita,Yar China tace tab ai ke ta daban ce lokacin baku fara son juna ba,da yanzu ne yanda yake sonki Haka ke kin Isa ma ki fita,Siyama da Aamna suna Jin Yar China ko tunanin sun girmeta bata Yi Kawai kawaye ta dauke su ba ruwanta aunty a Baki Kawai take fada. Suna ta hira Yar China ta kalli Aamna tace Aunty akwai fa magana amma sai Nan gaba Dole mu saka labile,Aamna tace Allah ya kaimu Amarya suna Hira Ana yin Sallar Magriba Siyama ta tafi gida,sai da aka Yi Sallar Isha sannan Tawaga ya dawo tun kafin ya shigo palon Aamna ta yiwa Yar China Sallama tare da tafiya gida. Tana karasawa part dinta ta iske motar da Ahmad ya fita da ita ya dawo kakenan ,shiga tayi da sauri bata ga kowa ba sama ta nufa ta baya taji an dauketa sama,tana Jin kamshin tasan waye,Oyoyo ta Furta Yana murmushi a haka tana dauke a hannunsa ya haura da iya sama suna karewa juna kallo cike da kauna,Saman bed dinsa ya ajiyeta tare da sunkuyawa Yana binta da kiss ko Ina na jikinta,Hannayenta ta sakalo ta wuyansa a hankali cikin salo ta shigar da bakinta cikin nasa tana tsotsa sosai,a hankali ya bita saman bed din tare da kwanciya a kanta ba tare da ya sake Mata nauyinsa ba,wani sake kankame juna suke suna kissing Kamar ba gobe,jikinsu na rawa tasa Hannu tare da cire Masa riga shima rigarta ya zare Mata a hankali. Bra din ya Balle ya cire mata tare da jefota kasa,wow ya furta kamar yau ne ya fara ganin Albarkatun kirjinta,Fuskarsa ya daura a kansu ya shiga mata Wani salo,Aamna ta susuce Masa gaba Daya da sambatu tana shidewa,Wandonsa ta karasa cire Masa tana Masa wasu zafafan salo,Basu kyale junansu ba sai da suka Kai Bus stop,Wanka sukayi suna Fitowa tace me Zan dafa mana? Kin tuna min ma na taho da Abu suna mota ba sai kinyi girki ba My World,daga shi sai dogon wando na jean black pencil a Haka ya fita ya dakko ledoji a mota ya dawo nama ne yasha gashi yaji cabbage da tumatur ga wasu hot abubuwa na makulashe da su fruits salat,Aamna sai da taci ta koshi tayi dam sannan tayi brush ta dawo ta zauna tana dafe Kai tare da yatsina Fuska,Ahmad ya kalleta sosai yace lfy? Kwanciya tayi a jikinsa tana lumshe Ido tace Ina turaren Nan Guchi? Wanda ya kusa karewa fa? Ahmad yace me zakiyi da shi? Ina ka saka shi? Yana saman dayan mirror fa na Bedroom dinki jiya na kaishi can sun cike min mirror,Tashi tayi da Yar guntuwar rigarta me siririn Hannu taje ta dakko ta dawo ta kwanta a jikinsa Yana danna laptop dinsa,yace ki kawo min coffee,Aamna tace bazan iya ba fa Allah I'm sorry bana son tashi, Alright Bari naje na hada da kaina,Aamna nan ma tace Ni gaskiya a'a naji dadin kwanciyar Nan Dan Allah karka tashi,ban Gane ba my world? Yaushe zanje gida ne ganin Baba? Ahmad yace Jiya fa aka Gama biki kinyi zurga zurga da yawa Kuma Mama da Baba ai sun zo Kun hadu a bikiin,gidan Zuhra fa? Itama tazo biki jiya Kun Dade fa a dakin Mummy,Shuru Aamna tayi ta bude kwalabar turara tare da tura Kan turaren a Hancinta tana ta Shaka,Ahmad yace ke lafiya kike Kuwa? Aamna tace idan Ina Shaka wani Dadi nake ji Kamar na mutu wani nutsuwa nake samu. Baki Ahmad ya bude yace sai kace Ina manta uwa,cikinta ya shafa yace yaushe Zaki samu cikin Nan ne? Na matsu naji kin samu ciki,wlh tunda na fara sonki naji Ina mugun son Yara,Ina so Naga ance yau My world ta Haifo min Yara jininta da jinina sun hadu,duk aikin Nan da nakeyi My world Mahaifarki taki karba,wannan wanne irin receptors ne Dake marasa Imani baza su ja sperm Dina su shigar dashi saman kwanki suna min yawa wlh,Dariya Aamna takeyi tace Kuma kullum sai ka dura sperm sunfi kwalaba uku a ciki amma sai yanga sukeyi baza su Fisgi ko Daya ba su kai,Ahmad yace kema dai Kya fada Allah ya kawo Mana to Ni na fara karaya Anya Kuwa Zan haihu? Idan bana Haihuwa fa? Aamna tace nice a cikin tashin hankali sabo da Kai zaka iya Karo kishiya,ai wallahi duk ranar da akace zaka Yi aure Kawai fita zanyi da gudu tun daga gidan Nan ban San iya inda Zan tsaya ba. In Allah ya yarda ma zamu haihu amma fa Ni bana son Haihuwar awakai ratatata, Inshaallah a nutse zamuyi Yan yaranmu kadan,Aamna tace Allah yasa yace Ameen,Aamna ce tace yanzu dai kyanta in samu atile da gishiri in kwana Ina ci,Ido Ahmad ya zaro shi baita ji tace wani Atile ba sai yau,kafin ya Gama maganar tace ko na samu fura da Nono me sanyi,ke da fura Bata dameki ba? Me yasa Dana fita baki fada min a waya ba? Aamna Tace yanzu naji Ina son Sha,ko in samu Gauta,ko Data,ko Kuma tsamiya danya in ta Sha,ko miyar shuwaka shuwaka haka,ko Kukar kwalaba,idan ma Zan samu Taura duk ita zanfi ci,tana ta wutsil wutsil da kafafu tana faman lissafi,Ahmad yace tab ai duk cikin wannan fura Zan Iya sawa a kawo Miki ko Data amma Ni wannan abin da kike fada ban San Inda Zan samo ba,Kuka Aamna ta saki ai dama baka kaunata na Dade da gano hakan da Yar China ce da yanzu Tawaganta ya samo Mata ni kuwa daga fada wata fura to Ni bana Shan furar na daina sonta har datan Kuma Ni Atile nake so da gishiri idan baza ka Nemo min ba fine ta Mike fuuuuu ta bar Masa dakin tare da banko kofa tana cewa Kuma Ni kifi nake so karfashe tayi waje, bedroom dinta taje ta zauna ita Daya sai da ta Dade tana kumbura ta gaji ta fito tare da sa Hijab dinta ta fita ta koma garden tayi zamanta a kujera tare da zuba Uban tagumi tana Hawaye zirrrr...zirrrr. Bedroom dinta Ahmad ya tashi ya duba Bata ciki ,tsorata yayi ya shiga dubata lungu da sako,a garden ya hangonta tana ta kuka mamaki ya kashe Ahmad ba abinda yayi Mata yace daga wannan Maganar shine kike kuka? Aamna tace to ai ba so na kakeyi ba nasan dama lika maka Ni akayi tunda ai ba zabinka bace zabin Mummy ne ba Dole ka min abinda kaga dama ba,toooo....Ahmad ya Furta da mamaki,Yana lallashinta masifarta tana karuwa har ya gaji yaji Haushi ya Bata Rai yace tashi mu tafi ko na Miki ae yane yanzu kin Sanni Sarai kin San Halina bana daukan Iskanci fa,ko tashar kike so na nuna Miki yanzu na dawo King na asali,Tsawa ya buga Mata tuni ta Mike tsaye Hanya ya nuna Mata zungui zungui tayi gaba tana shesheka. Dakinta ta wuce tare da banko kofa ta barshi a tsaye shi Kam mamakinta ne ya kamashi Kamar me Aljanu Bata taba Yi Masa Haka ba sai yau,Tsaki Yaja ya dauki jallabiya Milk ya zura tare da zarar key din mota zai fita,Jibson ya Masa waya yace kallo Ni ta sama King,Ahmad ya kalli saitin gidan Jibson ya hango shi Rungume da Sameera sun wani shige blancket tare suna ta wani Corridor ta sama ta baya sun kudundune tare suna shakawata,Dariya Suka ba Ahmad ma,yace to kwarto na ganka sai me? Yawwa idan ka fita ka siyo min Chicken da Fresh milk sai hot Shawarma idan ka kawo ka ajiye min a bakin kofa Zan Bude na dauka ba sai ka ganni ba Kawai ka ajiye ka min waya yawwa Zan fito na dauka,Ahmad yayi Dariya yace karfa ka cinye musu yarinya,Ina ruwanka munafuki ka siyo min ka ajiye ka tafi,in ba irinka ba King waye yake fita daga gidansa bayan sallar Isha ai sai lalura,Ahmad yace ya zanyi ta koro Ni da masifa daga wasa ya Zama tashin hankali,Tsaki Yaja ya kashe wayarsa ya shiga mota zai fita Mashkoor ya wani fito da gajeren wando shi a Dole Ango wait wait,Ahmad ya sauke glass Yana dariya yace Mashkoor sanyi fa ake? Inji ubanwa ake sanyin? Dumin Amarya ya ratsani bana jinsa kune kuke jin wani sanyi Ni yanzu sai nayi yawo a machine a Haka Kuma fes Zan jini,yanzu na ganka da key a Haka da gajeren wandon zaka fita? Yo Mene a ciki Ina mota ba Fitowa zanyi ba Zan siya Abu a miko min ta glass,Ahmad yace a dawo lfy,tunda zaka fita na fasa ga Sako na a siyo min wannan hantar da muke siya ka tuna? Ahmad yace baza ku maida Ni Dan Iska ba wlh Dan aikenku ne ni,Jibson ya bani Sako Kai ma Haka,Au Jibson ya hakura ya fito? Ahmad yace wannan mayen ta waya ya min magana, Mashkoor Yana dariya yace Kai Jibson bala'i ne yace sai yayi 3days zai fito Yana shekin Amarci,Ahmad tunawa yayi da Aamna yaja motarsa yayi gaba,Da tambaya Haka ya dinga tambaya sai da aka nuna Masa gidan wani me siyar da atile,yaci sa'a Yana zuwa akwai Kuwa mutumin ya Bude gida ya bawa Ahmad na 2k da yawa a Leda,yayi godiya ya tafi harda karawa mutumin dubu kyauta,Sakon Jibson da Mashkoor ya Siya har zai tafi kawai ya tuni da kanwarsa ya hada har su bash ya Siya musu,Yana dawowa kowa ya kirashi a waya ya fito ya karba Amma Jibson sai a bakin kofa aka ajiye Masa ya kirashi a waya yaje ya dauka ya wuce. Jibson ya rantse bazai fito ba sai yayi kwana Uku kofa kawai ya Bude ya Miko hannunsa Yaja Ledar ciki ya rufe kofarsa ko Fuskarsa Bata leko waje ba,Ahmad Yana zuwa ya ajiye a fridge tare da ebo wani a plate ya wanke shi tas ya zuba Mata gishiri a gefe ya nufi Bedroom dinta,Yana tura Kofar ya hangota a gefen bed tayi tagumi kamar wacce aka ce Babarta ta mutu,a gefenta ya zauna tare da daura Mata plate din a cinyarta,Mamaki da farin ciki Suka mamaye Mata zuciya Yana binta da kallo yaga yanda take murna ya bashi mamaki ya kalleta sosai yace ko dai kina da Aljanu ne My world? Ko kulashi Bata Yi ba ta fara cin Atilen karshe ma plate din ta dauka Tace muje mu kwanta,Ahmad yace Kai Kina da matsala,akwai matsala dole a wani wajen,Dariya Aamna takeyi sabo da Murna tace Allah bani da wata matsala,Ahmad yaci gaba da kallonta suna tafiya yace Kai no...har suka kwanta tana ci Taki yin bacci sai gajiya yayi ya kashe light tare da yin addua ya fara bacci. Yar China Kuwa ganin Tawaga ya kawo wata hanta me ruwa tace Kai Kuna kaunar junanku Haka Ahmad ya sake siyo mana abin dasi, to bani da cin kayanku ba masifa kazo kace zaka Kara bada min gishiri irin na jiya,Dariya Tawaga yayi yace nifa yau bance Zan Miki komai ba wlh kici idan kina so ba abinda Zan Miki bacci zamuyi,Yar China Tace Hmm ai yanzu maganarka Tawagana gwara ta gizo da koki,na tsorata da Kai,Tawaga Yana dariya sanye da kayan baccinsu farare color daya yace kici mu kwanta na gaji,Yar China kadan taci Tace da safe nayi warming dinsa muci,Brush tayi ta haura saman bed kusa da Tawaga tana cewa Allah ka tsareni da Tawaga cikin dare Ya Allah karka Bari Tawaga ya kawo min hari,Allah kasa idan bacci ya kwashe shi sai Rana ta fito zai farka, Tawaga Yana jinta Yana dariya ta Gama karanta su Ayayul kursiyyunta ta kwanta,taji Kuma Yana lalubeta,tace Dan darajar Allah kayi hakuri har naji sauki wajen Nan yanda ka Masa Allah Kamar bera yabi ta Kan gari duk ka gwigwiye,nace ba abinda Zan Miki Kawai dai kin San bazan iya barinki ban taba komai bai,irin wannan baiwa Haka ya Furta tare da daura hannayensa Biyu a Boobs dinta Yana shafawa bayan ya rabata da Yar rigar tata,Yar China tace wayyo a hankali,yace Lafiya? Yar China ta Dan matsa gaba daga jikinsa tace abar Nan Taku Bata da Amana ko kadan naji ta canja yanayi tayi fushi,Dariya yayi yasan dama abinda take Jin tsoro kenan. Birkitota yayi Kansa ta kwanta a jikinsa gaba daya ya lalubi bakinta Yana tsotsa,Yar China tace Kai jama'a wannan Amarci da wahala yake,da Rana da dare ba lokacin banza,gaba Daya skin Dina ta koma ja tsabar murjeta da akeyi,Tawaga Ina rabaka da Zama Hariji tam,Yana dariya yace ai kema itace Kinga mun Zama Daya,a Iya jiya da yau kadai ka lashe sadakinka ,Zaki zo kina Nema na Miki da kanki Hajiyata,Yar China tace ban maka musu ba na fara gano kamshin gaskiya, na gano gaba akwai show Babba on the Bed,Yana lailaya Yar China Yana janta da surutu tana ta bashi dariya ba'a kada ita a magana. AsmaBaffa 10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 126-230 Official By AsmaBaffa Page naki ne NICE GIRL Har ta fara bacci Yar China ta farka tace Kun kusa girma zaku Zama Baba Aamna ciki ne da ita,Tawaga yace ke bana son karya a Ina kika sani? Ko Ahmad to Bai Sani ba sabo da Indai ya sani sai mun sani,Yar China tace da kaina na gano,Iyalle ta koya min yanda ake Gane me ciki ko na Yan satikai ne,shirme Tawaga ya dauki abin yace to muyi bacci Allah Raba lafiya,Yar China tace baka yarda ba?na yarda mana,a Haka bacci ya kwashe su yayinda Aamna shi Sam ta hanashi bacci da taunar Atile,suna Dan kwance tace ka tashi kenan? Uhm Kawai ya furta,Aamna tace na dameka ko? Ahmad yace na rasa abinda ya Shiga kanki My world ni baki taba min Haka ba,hirarsu suke yi tace My King yace naam? Yatsanta take Masa Zane a kirjinsa a hankali cike da kissa tace... Alfarma nake Nema a wajenka idan zaka min,nasan Inshaallah ma baza ka kasa Yi min ba,Ahmad yace Ina jinki,Kasan Siyama yau tazo fa,yace Alfarma so kike na auro Miki ita ku Zama kishiyoyi ko me? Aamna ta Duke shi a kirji tana Dariya tace Allah ya kiyaye ta Kai Hannunta Kan sandar girma tana cewa bana kaunar Sharing dinta da kowa sai kaddara My King ka daina kawo min wannan zancen, Alright ya furta Yana dariya to me kike so nayi Mata? Aamna ta bashi labarin Auren Siyama da Hashim sannan tace Dan Allah tunda Nan gaba zaku ebi ma'aikata a company Dinku NCE ce da shi Dan Allah Babyna ka dauke shi Aiki sabo da Allah,mutum ne me Amana da hakuri,Ahmad Shuru yayi,Tace Please Dan Ni zaka Yi,Ni nace ka min Alfarma tace na Nema,idan kayi min ni kayiwa kaji please ta karasa da shagwaba,numfashi ya sauke yace My world Yarinyar Nan ba Yar mutunci bace ki duba fa Ni fa Ahmad dinki guda your king tace tana so common My life sai kace bakya so na,Ni nayi Fushi ma Kawai bakya so na bakya kishi na,wannan neman Alfarmar ya jawo Miki na gano ba kishi na kikeyi ba,wannan Yar banzar Yarinyar kin San Kuwa irin farin da ta dinga min,idan kika Shiga kitchen ta dinga bankaro min kirji tana zazzago min wuyan rigarta,Aamna tace Yar Iska matsiyaciya Ina can ban sani ba,Ahmad yace hmm Ina fada Miki har tallafo Kirjinta takeyi min,da badan Ni Allah yasa nace sai ke ba,zuciyata Bata taba son kowa ba sai ke,bana sha'awar kowa sai ke da tuni kinji kida magwan,ai ko Malam ne ta dinga Masa abinda ta min sai ya manta da karatunsa,Aamna tace yanzu da baka so na da yawa da shike Nan sai ka so ta? Ahmad yace ai tuni ma Zan karba,Dan Adam ne fa zuciya ce Bata da kashi,yanda a lokacin ma ba Wani tsoron Allah ne Dani ba lokacin Ina shaye shaye ai sai dai Kuma kiyi kuka ki hakura to Allah ya taimakeki bana layin Mata ni,ki kiyayi kawaye wlh maza su ba kowanne aboki ne ke canja su ba amma Mata ba Uwar da kuka Iya sai gulma da cin Amana. Ni dai kayi min Alfarma kaji...ta karasa zata Yi kuka,it's okay zanyi Inshaallah Zan dauke shi Aiki sannan za sa shi a inda zai samu Albashi me tsoka Inshaallah ki dauka anyi an gama but sabo da ke ba Dan ita ba,Rungume shi tayi tana murna tace thank you King,I love you tare da hade fuskarta da tasa,Tace gobe su Mummy zasu koma yaushe zamuje Lagos ne? Nima Ina so Naga gidan surukaina,Zamuje ne verysoon,Suna Hira har bacci ya kwashe su. Washe gari da Yamma su Mummy duk sun Gama Shirin tafiya sabo da tasan Idan Suka yiwa Humaira Sallama tasan kuka zata musu sai basu sanar Mata ba gaba Daya da kawayen Suka tattara zuwa airport,Ahmad yaje rakasu Suma,sai da suka je airport Daddy ya riko Hannun Ahmad yace ya naji Shuru ne? da me fa Daddy ya furta da shagwaba,Daddy yace ba score har yanzu? Ahmad Yar kunya yaji yace Daddy verysoon,Nasiha ya sake masa sosai sannan suka Yi Sallama ya Rungume Mummy yace zamu Zo verysoon da My World,Marar kunya a Gaban Nawa cewar Mummy suna dariya gaba Daya ya musu Addua ya tafi Suma Suka Shiga jirgi abinsu. Aamna yau ma Yar China Kawai ce Bata girki ita ta kaiwa lafiyayyen lunch da kanta taje ta Iske Tawaga ya duka a kasa Yana rarrafe Yar China tana bayansa Wai jaki jaki yake mata,Gashi ta daure Masa Ido da bakin kyalle,Yar China Bata sakko ba tace Aunty Balaraba kin ganni ajiye abincin an gode,Tawaga ya cire kyallen Yana Shirin cewa Yar China ta sauka tace ja muje sai ka kaini can bangon,Aamna tana ganin Haka ma Yar China ba kunya gareta ba ta juya ta tafi gida ma kawai,Karatun Qur'ani tayi sosai tayi Adduointa kasancewar me gidan baya gida Yana can shirye shiryen fara zuwa Office. A saman Sallayar Bacci ya kwasheta har after 5pm ya dawo tana bacci Bai tashe ba ya wuce yayi wanka,Abinci yayi serving Kansa Yana ci Yana Santi har ya gama,sai da zai wuce masallaci ya tashe ta,tana tashi Tace Sannu da zuwa yanzu ka dawo? Murmushi yayi yace tun 5:20pm ,lallai nayi bacci Sannu da zuwa abinci fa? Naci tun dazu nayi wanka kije kiyi Sallah zanje masallaci,Okay ta furta sannan ta Mike ta wuce toilet. Sai Bayan Kwana Uku Jibson ya fito Shar da shi har ya wani canja,su Bash suna ta Masa dariya ana tsokanarsa,Ranar ne Kuma Ahmad ya fara zuwa Aiki Office,ranar Daddy ya Sha Kira a waya komai kafin yayi sai ya Kira a waya,sai 5pm ya nufo gida gaba Daya ya gaji Kamar an Masa duka abinka da ba'a Saba ba,Yana yin wanka Abinci yaci ko masallaci Sallar Isha bai iya zuwa ba a gida yayi Yana idarwa ya kwanta sai bacci,Ganin Haka Aamna ta gyara Masa blanket ta koma main Palo tana kallo sai ga Sameera taci gayu tare da Jibson Kamar Wanda zasu je wani party,Aamna tace Ango da Amarya Allah yayi fitowarku sai kace wasu kaji masu kwanci,Jibson suna wani zuba kamshi ya Sha shadda ita Kuma wani material ta zuba Malam peach,Jibson yace Ina mutumina? Aamna tace bacci yakeyi yanzu Bai Dade da dawowa daga Office ba Bai Saba ba sai bacci,Jibson yace ai Dole muma kafin mu Saba sai munji jiki,Hannun Sameera cikin nasa sai kunya take ji tana murmushi Kawai,Aamna tace ke Sameera Ni bana son kunyar Nan shi yasa Yar China ke birgeni da itace da yanzu Muna zuba Hira,Jibson yayi Dariya tare da furta ai wannan da kika ganta authentic ce, genuine and Lovable,Dariya Aamna ta dinga Yi tare da furta yayi kyau,suna ta Hira Yana ta wani koda Sameeransa. Bayan sati biyu da bikin su Yar China duk sun Hada kansu suna zaman su lafiya sun Zama kawaye lokacin Kuma Saura kwana daya daurin auren Siyama,Hashim ya Kama gidan Hayarsa me kyau harda gate yasha tiles dai dai na rufin asiri,Iyayen Siyama ba laifi Kaya me kyau Suka Mata da Aamna akayi ake komai,ta bada gudunmuwa na kudi sosai da shi ma suka Yi kayan kitchen,Washe gari Saturday Amarya tayi kyau sai sheki takeyi ta Sha lalle da gyaran gashi 11am aka Daura Auren Siyama da Hashim,duk su Ahmad sunje group dinsu,Ango burinsa ya cika sai murna yakeyi ga albishir da Aamna ta Masa na karbar takardunsa an bashi Aiki zai daina aikin wahala,Da kwarinsa yake komai,Siyama Amarya dai ba yabo ba fallasa ta hakura Haka,Zuwa Yamma aka Kai Amarya abinta tana can yau ta hadu da Sarkin karfi cewar Baba Wanda shima ya Halacci daurin auren,Haka Mama taje bikin. Aamna Kuwa da dare Ahmad ya tura driver ya dakko Masa matarsa,Suna Hanya Aamna tace Musa tsaya Amai nake ji, Musa da sauri yayi parking tare da mikawa Aamna bakar Leda har biyu yace Hajiya Yi anan sai ki jefa a kwalabati ai Aamna ko kula Ledar Bata Yi ba ta fita waje tare da tsugunawa ta Shiga sheka Amai Kamar zata fito da hanjinta,Musa ya Kira Ahmad yace Oga Muna dai dai sabon masallaci ka ganmu Hajiya ba lafiya gata tana ta Amai na tsorata fa Oga tun dazu take Amai yaki karewa,Ahmad gabansa ya Fadi yace me taci a gidan bikin? Karfa su kashe min Mata sauri ka kaita Hospital kafin na karaso,Sai da Musa ya jira Aamna ta gama tas ya Bata ruwan Roba ta wanke bakinta sannan ta shiga mota tana Nishi tace muje Musa naji sauki,Musa yace Oga Yana hospital yace na kaiki can,Aamna itama abinda takeji a jikinta kullum ya isheta Tace muje to. Suna shiga Likita ta gani ta fada musu abinda take ji,Dake private ne Nan aka Mata wasu gwaje gwaje,tana jiran Result Ahmad ya shigo da sauri daga shi sai 3qtr da t-shirt fara,Zama yayi a inda take zaune ta jingina da bango tare da lumshe Ido,Ahmad yace Sannu My World,me kika ci a can? Aamna tace daga ganin Alala sai nayi sha'awa na ci Shikenan na fara Jin Amai,Ahmad yace Oh....me ya kaiki cin wani alalar biki kema,Ana zaune lafiya idan so kike Yi ai sai ki dafa da kanki. Doctor ne ya karbi result din gwaji ya duba nan yace ranka ya dade na tayaka murna matarka ciki ne da ita na wata biyu, Ahmad murna tasa yayi mutuwar zaune ya wani Bude baki Yana murmushi,Takardar ya karba a wani slow ya duba,Aamna ya kalla da fara'a ya rike kafadunta tare da girgiza ta sosai yace I make it my world,Haba Ni San Ina buga game din Nan dai dai ah ki tayani murna na samu first score,kallon Doctor yayi yace Likita mace ko namiji? tsaya karma kace min Namiji Baby girl ce ko? Zanyi Yar Budurwa kwana Nan,Ya kalli Aamna yace ki dinga Mata irin Calabar Nan tawa ta da kin tuna? Ai kullum da ita Zan dinga fita sai duniya tasan King yayi 'ya,Likita ya Bude Baki Yana kallon Murna Ahmad ya mike ya Hana Kansa sukuni gaba Daya, Doctor yace Dan Bamu waje Zan Mata wani gwaji,Ahmad yace ban Gane na baku waje ba? Ina mijinta wallahi baka Isa ba nasan latse latsen Nan da kukeyi zaka Mata ka Kira mace ta mata,sabo da ka Mai Dani gara ka kalli matata one in million na barta ka saki wannan shegen labilen naku ka latsa mata kafafu da ciki baka Isa ba bada Ni ba. Likita yace Allah ya bada Hakuri ya Kira mace tazo ita tayi abinda ya dace ta basu shawarwari da Maganar zuwa awo etc.Aamna karar murna ta saki da sauri Kuma ta rufe bakinta tare da furta au na manta,Ahmad yace Adana ta sai munje gida,Hannunta ya rike Suka taho a hankali,Musa yace ya maida motar gida,tsohon me gadin Ahmad an Kara Masa matsayi ya tashi daga me Gadi ya koma Driver sabo da Amana irin ta Musa,tun kafin su koma gida Ahmad yace a shirya yau akwai party a gidan,Su Jibson duk Suka Zama ready Suka tafi da matayensu sashen Ahmad suna Jiran dawowarsu,Kafin ma Ahmad ya dawo Su Jibson an tanaji lemuka wannan karon babu Shan barasa,Tare da Aamna Suka shigo,tana rike a hannunsa,Ahmad ba jira yace a goal,Suma Kamar Yan siyasa Suka amsa da a goallllll......a goal....suka ce a goallllll......Yar China tace na Gane zancen,Ahmad yace na Zama Daddy matata tana da ciki na 2mnths tafi suka fara raf raf raf.....Jibson yace music .. Bash ne DJ ya danna,Su dai matan Dariya suke ta Yi,Yar China harda cewa a kashe kida sai na fara rera Mata wakar Dana tanaja,aka tsaya Nafeesat tace Muna jinki,Yar China ta fara Waka wai me ciki turtsi bulli.....me ciki turtsi bulli,Tawaga yace a amshe mata Yana Tafi suka ce Suma Me ciki turtsi bulliiii me ciki turtsi bulliiii....Tace ta kasa Zama,Tawaga yace turtsi bulli harda tafi sauran har Ahmad Dariya Kawai suke yi,Yar China taci gaba da cewa tsaiwa ta gagara....Turtsi bulli....Tawaga ya sake Amsawa,Aamna tace wannan ai wulakanci ne wallahi Zan rama, Ahmad ta kalla wannan tijarar daka min fa,Cikin murna Bash ya Danna kida Aamna sabo da kunya guduwa tayi ta kasa Zama sun Dade suna shagali suna ta tsare tsare. Ahmad harda cewa a Ina za a Kama ayi suna? Humaira tace Kai Yaya ko kunya,Hararta yayi tayi Shuru tana dariya,Hafsat Tace ba Wani suna an daina yanzu,Inji uban wa? Cewar Tawaga zamu samu karuwa baza muyi murna ba sai mun kashe kudi,Nafeesat tace Ni dai nice me kula da me jego,Yar China Tace Muna wajen Bikin suna mu Allah ya sauketa lafiya,Ahmad yace Halina Dake hankali Yar China,ba Wanda yayi Addua sai ke,party fa kace za ayi cewar Mashkoor,to naji an Gama kuje Kun korar min ita sabo da kunyarku,Jibson ne ya fara mikewa ya rike Sameeransa zai tafi Ahmad yace gobe karku manta akwai zuwa Office,Allah ya kaimu suka tafi Yar China kin tashi tayi tace Allah bazan koma da kafata ba sai dai ka goyani,Abu me sauki cewar Tawaga ya goyata Kuwa Suka tafi Yar China akwai son wasa Kamar me. Washe gari Ahmad waya ya Kira Mummy ya sanar Mata ta dinga Murna tana bawa Daddy labari,su Saddeeq da Mufeedansa sai murna sukeyi,Basu Dade ba Kuma ya dauki Aamna Suka tafi Lagos,can ta Sha kallon kudi satinsu Daya Suka dawo,lokacin Kuma Ahmad yana Shirin tafiya da Aamna da Baba Sudan suje gano Rahilu,Baba ya rike wuta sai anje da shi,Kuma ya kamata aje da Baba sabo da shi ya rike Aamna,Baba ranar da Ahmad yaje ya sanar Masa ya Zama cikin shiri bayan an Masa passport,Baba yace Nima ka siyo min Sut (suit) irin ta Rahilu da ita zanje Masa Nima,Ahmad ba musu ya nemowa Baba size dinsa kala Uku,yace da jallabiya shima sai ya saje da Rahilu a Sudan. Ranar da zasu tafi Aamna harda Shan abaya baka,Ahmad shi dai kana Nan Kaya yasa Yan ubansu,Baba kuwa harda sa jallabiya fara yayi Nadi da rawanin larabawa,Baba yace nasan mutanen Sudan ma tun a jirgi zasu fara Yi min larabci su Aamna suna ta dariya Mashkoor ya ajiyesu a airport Basu Dade ba jirginsu ya daga,Baba yace wayyo kunne na ya toshe wani dummm nake ji ice ko kamfanin mu na Najeria be? Basu iya jirgi me kyau ba,Ana ta yiwa Baba Dariya,duk ma'aikaciyar data wuce sai Baba yace baiwar Allah abincin jirgi ko baza a Bamu bane sai dai suyi ta kwantarwa da Baba hankali suce za a bayar idan lokaci ya cika,Wata Yar Budurwa ta fito cakwas cakwas itama ma'aikaciyar jirgi ce ta dafa kujerar Baba tare da cewa Baba a sa Belt,Baba yace yau Naga fitsara da gani ba'a kulla abin arziki ba ace ma'aikatan jirgi gaba Daya Yan Mata fella fella suke yawo suna kashe ma Ido sabo da a koya min fasikanci idan gaskiya ne a zuba maza Mana su dinga dakawa pasinja tsawa wallahi Baku da halin arziki kunyi asara an maida ku hotiho Ana talla daku a sararin samaniya,sai kunyi sama sosai sannan kuke tafka tsiya wallahi da Allah kuke bada mu ba,sai Dariya akeyi a jirgi Baba Yana ta masifa har aka kawo abincin jirgi. Baba yace aikin banza shinkafa ce da nama Baba ya cinye nasa ya dauke na Aamna ya cinye,Ahmad ma ya bashi nasa ya cinye Baba yace abinci Kamar na Yaron Yaye Haka dama jiragan suke wannan rowar mutum ya biya kudi a bashi abinci naira Hamsim a dubu goma. Baba Yana ta murna ya fita kasar waje zaiga Sudan yankin Larabawa,sai da suka sauka a jirgi Suka Shiga lafiyayyar Taxi Suka shigo har wata state,Baba yace me Zan gani? Sahara nake gani fa Ahmad,me Zan gani Haka? Yo wannan ai gwara naje Kano Kuma Sudan din ne? Aamna tana ta da dariya,Baba yace cab Dole Rahilu ya Shiga Uku a Haka amma Yaran wasu masu kudin suke Mana Iyayi Ana wallahi Yana can Sudan Yana karatu,tana Sudan tana karatu,ai wlh gwara Kayi Ado bayero iniversity (University) Ahmad Yana so ya dan rike ko Aamna amma yasan Baba. Suna tafiya a mota Baba yaga wani Dan fari Yana tafiya a titi Baba yace wannan da gani bako ne shima baiyi Kama da su Rahilu ba duk yanda akayi daga Seria yazo gashi Nan a koshe bulbul,Driver dai suna ta larabci da Ahmad Yana Kiran Rahilu Yana Basu Address,Baba ya kalli wani Symbol kato Ana tallan omo Klin,yace Ashe Daya muke da su kaga jaraba Klin a Nan inama Aishatu tana Nan Sarkin ta'adi tazo ga mutuminta a Nan ma,Baba shi kadai yake surutunsa har Suka sauka a wani gida Kato me bene Hawa biyar, Aamna tace Baba anzo gidan Abbi na kaga gidan me kyau,Na Haya ne uban wa yace Miki gidansa ne,?Ahmad Yana jinsu dai suna Fitowa a taxi sai ga Rahilu ya fito sanye da jallabiya wata baka,Baba yace kaga bakin mutum ga bakin Kaya Rahilu manyan gari wuya kamar na zalbe,Rahil da fara'a ya tarbesu ya dauki akwatin Ahmad Suka nufi ciki,wani Palo yasha adon Larabawa shi aka kaisu,Babba yana kallon gidan Yana Kallon Rahilu yace Yan karya an iya tsara gida,Matar Rahilu ce ta fito wata balarabiya fara tas,ta zauna sai da Ahmad Suka yi maga suka gaisa su Baba basa Jin yaren,Wata ce ta fito itama fara ce Amma ba Kal ba irin dai Bata fi farin mu na Yan Nigeria ba,bayan sun gaisa itama ta Mike tayi ciki,gabansu aka cika musu da Abinci iri iri na Larabawa,Baba yana kallo,wani kwano me kyau ya bude yaga kubewa Danya Guda Guda a cikin kwano da wani ruwa tsululu Yana yauki ya Sha tafsrnuwa da kayan Hadi,Wani kwanon ya bude yaga wani Abu shi kamar Tuwon Zuma da Dabino,Rufewa yayi ya Bude wani kwanon yaga miyar ganyen kabewa,Can Kuma wani tuwo ne Kamar na madara har da Cheese,Ga Fruits iri iri,Baba yace Rahilu Ina shinkafa inda Muka Fi wayo,Dan Iskanci kasan wannan ba abincin mu bane na awaki ne zaka sa a kawo mana,kalli kubewa Guda Guda, Rahilu Yana murmushi yace yanzu shinkafa zata Zo harda lemon Tsaki,Karka sake ku matsa min lemon tsami salon na barke da zawo. Suna zaune sai ga wata shinkafa taji Hadi da hadin salat,Sai ga kaji an kawo,Baba yace yanzu naji zance Baba ya sauka kasa ya shiga cin Abincinsa Suma su Aamna suka gyara Zama tayi Serving Ahmad,Bayan sunci sun Sha suka Yi Sallah sannan aka kirawo Yaran Rahilu Suka dinga gaisar da su,Dake suna makaranta suna Jin turanci sai suka dinga magana da Aamna,Baba yace mu Kuwa sai kallo Allah wadaran rashin Boko,Sai dai Kawai Baba ya dinga cewa Hey...Hey....Ahmad Yana ta dariya a zuciyarsa yanda Baba yake ta aikin Furta Hey ga Yaran da yawa,Yaran Rahilu basa Bari suyi baccin kirki sabo da Hayaniya, Baba cikin dare kullum sai ya tsine musu Wai sun hanashi bacci,yace Rahilu Dan Iskan banza ya dinga dirkawa Mata ciki suna ta zazzago yara Haka kamar zomaye. Masauki me kyau aka Basu Aamna cikin Yan uwanta Mata ta shiga,washe gari Kuwa Daya gidan Rahil Suka je Suma Mata biyu da Yara da yawa Ahmad yayi Larabci ko turanci Aamna ma Haka Baba Kuwa sai Hey kawai,Nan ma kwanansu Daya aka raka su wajen Dangin Aamna na uba sannan wani babban matashi Mahmood shi ya dinga fita da su Aamna yawo suna ganin gari suna pics,Baba duk inda akaje sai yace ayi Masa pics shima,Ana dauka zai ce da Aamna maza dorani a yanar gizo duniya ta ganni a Sudan,Rahilu ya Gama tsorata da cin mutuncin da Baba ke Masa amma wannan lokacin sai yaga Dan kadan ya masa,kwana hudu tsakani Ahmad ya kafe shi gida Za'a taho Rabonsa daya kwanta a jikin matarsa kwana hudu kullum tana wajen Yan uwanta shi bazai iya ba,Baba yace Kai Nima na gaji da garin Nan mutane kamar konannu kowa baki sai Larabcin tsiya akan me,Aamna ita tana Jin dadin haduwa da Yan uwanta sai Ahmad ya yini Bai ganta ba,ai Kuwa Yace gida,kwanansu biyar Suka dawo gida Nigeria Aamna tana ta faman Fushi da shi har Bash ya dakko su a Airport aka sauke Baba a gidansa da tarin tsarabarsa. Baba Yana shiga ya Rungume Mama,Tace yau me Zan gani Baban Zuhra sai kace yaro? Baba yace na dakko darasi baza a barni a Baya ba,a gabana Rahilu yake Rungume matansa Yana musu kiss da shegen bakinsa kamar Kofar gari,Ni nafi Rahilu fasali shine bazan Yi ba sai ace na tsufa,shi yasa aka Yi Mana nisa a duniya,da Allah tsaya Rahilu ya mannawa Mama kiss a kumatunta biyu yace Haka akeyi yanzu duniya ta waye anci gaba kina Nan a dinkime Baki zaga duniya kin Sha kallo ba,kije Sudan kiga yanda tsoho tukuf Wanda ya haifeni yake tarairayar matarsa itama tana Masa,ke Baki waye ba,Mama tace Indai wannan ne bada Ni ba,ai Kuwa wallahi Baki Isa ba kullum sai na dinga Miki da safe da Rana da dare ko ta karfi,Baba ya zuge akwatunsa ya dinga fito da tsaraba daga Kan sutura har su turare da lallen Sudan kala kala,Ya mikawa Mama yace Henna sunan wannan lallen Haka ake cewa gobe ki Kira me lalle ta lallaba Miki shi,karki sake da Yamma na dawo daga kasuwa Banga Henna na tashi a Hannunki ba,Mama tace Kai Baban Zuhra ka canja gaba Daya ka koma Wani Dan bariki,Baba yace shine ai wlh idan Baki Yi Henna din nan ba sai nayi sati banci abincinka ba Karki ce ban fada Miki ba yawwa ya Mike ya shige daki Yana cewa na koyo soyayya wajen Larabawa Zo kui cude Ni ki wanke min gadon bayana,Mama tace Ni wannan Sudan din Bata Yi ba wallahi Ka dawo Dan Iska gaba Daya,Baba daga daki yace Dan Guguwa na dawo karewarta. Tun kafin Bash ya Kai su Aamna gida Ahmad ya like ya nane mata ya hanata sakat,kwana har hudu ko Rungume matarsa baiyi ba tana can wajen danginta ko ya kirata a gurguje take zuwa ta tafi Sam shi baiji dadin Sudan ba ga Baba ya hanashi ya Kama hotel bare ya dan samu ya shakata da Aamna a sudan shi yasa yaji Kamar akan Kaya yake,Aamna Kuma haushinsa take ji yace sati biyu zasu Yi Amma kwana hudu Kawai Ana biyar ya kafe su dawo gida ko Yan uwanta Bai Bari sun Dan Shaku ba,Bash Yana kallonsu ta Mirror Aamna tana Fushi Ahmad ya manne a jikinta Kamar zai shige cikinta gaba Daya ya haukace baya ganin kowa baya tunanin wani Bash ma Yana kallo,Aamna ta hade rai tace Kawai ko Gama ganin dangina banyi ba ka damu sai fada kake min Kai ka gaji gida zaka taho,yanzu ka min Adalci? Baki Ahmad ya bude yace kutmar...yace yanzu duk abinda nayi Miki banyi komai ba? My world???? Na kashe kudina na dauke ki har Baba Muka je har can sabo da na faranta Miki kiga danginki Ashe ban birge ki ba? Yanzu da Allah bai hore min ba da wanne kudin Zan kaiku? Kin min Adalci kenan? Fine and Good zamansa ya gyara ko yatsa Bai sake rike Mata ba. Sai a ranta ta tuna Bata kyauta ba,tunda take arayuwarta Bata San ma inda Dangin Ubanta suke ba sai ta Silar Ahmad,Daddy dinsa kudi ya saka ya dakko Mata Babanta har Nigeria ita Kuwa me zatace da su,Jikinta ne yayi sanyi ta riko Hannun Ahmad ya fisge Hannunsa,Bash ta Glass yake kallo Yana ta dariya a ransa,Yana yin parking Ahmad shi ya fara fita yayiwa Musa Magana ya dakko Masa jakarsa,Aamna ta dauki tata da kyar ta bishi da sauri tana kwala Masa Kira My King kayan Nan sun min nauyi cikina zai zube,ko kulata baiyi ba,a compound ta bar kayan tayi ciki,Bash a waya ya Kira Ahmad yace please karka kulata kuyi fada,kayi Hakuri akan Dan abinda Bai Kai ya kawo ba haba King, Ahmad yace Yarinyar ta rainani da yawa in kashe kudi in kaita har can kaji Maganar data fada min,Matane sai hakuri King Haka suke sai anyi Hakuri shine zaman Auren karka biye mata Shedan ya dinga hadaku fada please, alright Ahmad ya furta tare da kashe wayar,Wanka zai shiga Aamna ta shigo da sauri tana cewa I'm sorry My King, me kika Yi? Aamna tace laifin da nayi maka,Baki ya tabe yace ba Wani abu ai ya shiga wanka,ya fara wanka kenan Aamna ta shiga tare da tube kayanta taje,ko kulata baiyi ba,Tace har yanzu Fushi kakeyi dani? Fushin me Kuma? Gashi Nan kana share ni kayi Hakuri nace kaji ta furta da shagwaba tana riko hannayensa,a kirjinsa ta kwanta ruwan Yana zubo musu ta Rungume shi tare da fashewa da kuka,Yaron cikinta ya tuna ya shafa bayanta yace it's Okay ya wuce,Ki kiyayeni Aamna wallahi Dan kece kin Sanni a baya bana son taurin Kai da raini,Dan Ina sonki bazai hana na dauki mataki a kanki ba,Ni bazan dinga daukan wannan abin naku na Mata ba na shirme,ke ba yarinya bace,Ya isa Allah bazan sake ba cewar Aamna,cikinta ya shafa yace Babyna ya fara girma,Aamna tace muyi sauri naje na Mana abinci,nayi Order fa za a kawo kiyi zamanki sai gobe Inshaallah. Wanka sukayi tace yunwa nake ji ka danyi Hakuri muci abinci sai na baka manta uwa,Ahmad Yana Jin Dadi harda cewa yau kwana zamuyi ko? Aamna tace as you wish,I'm all yours,I miss you ya furta,miss you much more My King,Abinci Musa ya shigo da shi wata sakwara da miyar kwai taji nama,yasan tana sonta shi yasa sai wani gasashen Naman rago Suka baje ya Bata a Baki da Kansa Suka koshi sannan ta daga Kai tana Shan Watermalon Juice ya fara zare Mata rigar wankan da take jikinta Dake ma Basu cire ba Suka zauna cin abinci. Kirjinta Wanda Suka sake girma sunyi sake sake sai kyalli sukeyi ya shiga Matsawa Yana sarrafa su,Yace dama dai su dinga zubo da ruwan milk,Aamna tace sai an Haihu to,Allah ya kaimu a dinga Dan rage min Nima Ina zuka,sunyi missing juna kamar zasu cinye kansu Haka suke sarrafa juna suna wasanni iri iri daga Nan suka fada Manta Uwa. Washe gari da Rana 2pm su Habiba su Hudu kawayen Yar China suka zo mata,ai Lokacin Tawaga Yana bacci ihunsu Sai da yasa ya farka a tsorace Yana daga Bedroom,Yar China yake jiyo muryarta tana Yan Iska sai yau?Fatima Bala Baki da mutunci Wallahi ai nasan inda na ajiyeki,Fatiman da aka Kira Tace Sorry kawata nayi laifi banzo biki ba wlh zazzabi ne ya rufe Ni,Habiba ta kalli Yar China Kinga yanda kika koma Kuwa Yar China? Kinyi kiba kinyi wani fresh Haka,Yar China tace sirrin Yana jikin Angon,Shewa sukayi da tafi su a Dole Shegu,Ya zafi Yar China? Yar China Tace wanne zafi? Duk karya Mata keyi dadi ne Kawai,Habiba tana Dariya tace kice mu daina jiin Tsoro? Ku daina Jin tsoro duk karya ne cewar Yar China Kawai ta barsu a haka,Ina Angon? Bacci yakeyi ku rage Voice dan Allah karku tasar min shi ya dawo dazu Allah sarki yaje Nemo Mana halaliya a gajiye ya dawo daga Office a Haka ma Basu fara dadewa a aiki ba,Tafawa sukayi wata Maryam Tace kice kina bashi kulawa kawata Yar China tace ke dai bari jira nake ya tashi naje na wanke shi tas na shafe abina da mai,Sai dariya da shewa,Yar China ta kawo musu kayan ci da Sha harda Dambun nama, Tawaga ne ya sakko sanye cikin Shadda da Alama fita ma zaiyi,Yar China Tace Kun Gama Dani Kun cuceni Kun tashi My Man,Dariya sukayi suna Gaida shi ya amsa da sakin fuska,Rada yayiwa Yar China a kunne Wai ya tafi wajen Ahmad sai dare zai dawo,Su Habiba Yana fita Tace kina wuta Yar China Allah ya bamu I Taku,Yar China harda gyara zaman rigarta tana basarwa tare da cewa Ameen. AsmaBaffa 10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDU NE DUNIYATA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 131-135 Official By AsmaBaffa Page naku ne Ummu Amaturrahman Mrs mukhtar Aisha Maman Muniba Sai Yamma likis bayan kawayen sun tafi Tawaga ya dawo ya Iske Yar China tana wanka,Direct Toilet din ya shiga sai da ta tsorata,Fuska ta kwabe tana cewa ka bani tsoro,Yunwa nake ji ki fito ki bani abinci, Yar China tana wanka tace Babu lafiya Tawaga na Jin yunwa gani Nan,Dariya yayi ya fita Yana Fitowa da guntun towel dinta tayi kasa da sauri sai gata da tiren Abinci tana Subhannallahi gari yaci wuta Mijina na Jin yunwa yaga Friedrice ta Sha Hadi ga couslow da soyayyar kaza,Yace yaushe kika Yi wannan girkin? Ba naji kince Jullof din taliya zakiyi ba? Naga taliya Bata dameka bane shi yasa na canja shawara,tana serving dinsa ta tsuguna can Kuma towel yayi guntu da yawa Ana ganin Yar China tasan Yana gani amma Taki gyarawa tana satar kallon Tawaga yanda ya daina komai ya koma leken Yar China,ba tare da ta kalle shi ba Tace Allah ya yaye maka Wlh,muyi wanka tare kullum sai ka gani Amma baka koshi,Dariya yayi yace waye yake koshi da abin Dadi ya furta tare da jawota saman cinyarsa ta zauna Yana cin Abincinsa a haka. Yar China tace Anya Kuwa ban samu ciki ba,sai da tasa Tawaga ya kasa hadiye Abincinsa yace me? Sati Nawa kwata kwata da Auren wata Daya kice kin samu ciki yaushe ma naci amarcin?Yar China tace kaga Allah maybe Ina da ciki sabo da lokacin period Dina yayi amma banyi ba,Tawaga yace au lokacin period yayi? Yar China tace tun last week Amma banyi ba,Tawaga yace Amma Baki fada min ba so kike Kawai ki fara period ban shirya ba,Shirin me zakayi Kamar Kaine me Yi tana Dariya ta tambaya,yace banci Amarci sosai ba ya kamata ace kafin ki fara nayi final,Yar China tana ta dariya ai Kuwa da sai dai kaji na fara yanzu ma maybe time ya canja min,Tawaga ya fara cin Abincinsa da sauri sauri ya gama,Wankan ma da sauri yayi ya fito ya Iske Yar China jikin Mirror ya jawota jikinsa tare da cewa bana bukatar kwalliyar ta fili,kwalliyar ciki nake muradi,Yar China Sarkin Dariya tace to saka min tozalin,Tawaga ya dauketa tare da furta farin gani kenan tozali,Saman bed ya direta tace Yaya Gazal me Dadi zaka saka min,Dariya Tawaga ya shiga Yi daga cewa Tozali shine harda Kara gishiri Wai Gazal,da waka ta Rungume shi tace a sa min Gazal me dadi...sa mini kaya...a sa mini Kaya,sa Mata....sa Mata....a sa mini Kaya.....Tawaga ya dinga dariya sabo da Yar China ta Gama lalacewa yanzu fitsararta take Masa ba ruwanta,komai girman magana fada takeyi. Dama shi Haka yake so idan zaiyi Harkar nan Yana Jin dadin Yar China tana Kara Masa kaimi da Jin dadin Harkar. Washe gari Sunday 5pm su Ahmad suna gidan Mashkoor a katafaren palonsa,Nafeesat ta kawo musu kayan motsa Baki ta Basu waje suna Hira, Mashkoor ya kalli gefensa dama da hagu harda leka jikin kofa ya tabbatar Nafeesat Bata kusa ya kalli Jibson yace na yarda da maganarka Virgin wahalar sha'ani gareta,har yanzu Taki sabawa da abin,Ina tunanin tana da Yan shekarunta Banda matsala amma har yanzu ta kasa sabawa gata Nurse Guda amma Ina Wai Dan wulakanci ma Dana tambayeta nace Wai har yanzu ke baki Dan Saba bane Wai sai cewa tayi Mashkoor ya gwada muryar Nafeesat Wai sai ce min tayi to ai Kaine Baby Dick din naka tarago Guda ne,Su Jibson Suka dinga dariya harda rike ciki, Mashkoor yace Wai Mene ma tarago? Ahmad Yana ta dariya yace ai kasan jirgin kasa ko? Mashkoor yace sosai,to wannan datsi datsi na jirgin kasa zaka gani gida Gida ai shine taragon jirgi, Mashkoor ya dafe Kai Haka taci mutunci na ashe? Da nasan Haka ne wlh sai taga bacin raina taragon jirgi fa? Jibson harda rike ciki Yace da Kuna ganina a banza Kuna cewa ai Ni ba mace ma Zan aura ba ai duk sai Kun Gane kurenku, Mashkoor ya shiga nanata kalmar taragon jirgi fa,suka dinga dariya,Brown yace ai Ni tawa ta washe ta Saba Kaya nake ja,Harara Ahmad ya balla Masa sabo da kanwarsa ce,Brown yace bani da jaraba a baka auren kanwa ba babu dama kayi magana,Dariya sukayi Bash yace ai Ni Nawa surukin ba ruwansa tunda ya bani Hafsat ya kyaleni to shima yasan Yar wani yake cinyewa,Tawaga Yana jinsu Yana dariya,Yar China ce ta shigo Basu ganta ba Amma sunji muryarta tana yiwa Nafeesat tsiya Nafeesat kiji tsoron Allah Mene duniyar kin wani makalewa Miji ba fita ba Shiga da Allah kizo muje mu hau lilo muyi wasanmu,Su Tawaga suka dinga kyalkyala dariya ita Yar China Wasa ne a ranta ma,Nafeesat tana Dariya tace rufa min asiri lilo Kuma sai kace Yar Secondary,Yar China Tace har abada a Haka zaku Kare ku zauna ku tsufa da wuri mazajenku suyi muku kishiya,ku Sam Kamar Baku waye ba Allah yasa ma Mijin naki kina bashi hadin kai,Da sauri Mashkoor yace Allah ya Miki Albarka duk da bakya jina Yar China Bata wani bani komai da kyar nake lallabawa kin gani na Zama Maraya. su Jibson Suka dinga dariya,sai Kuwa suka sake ji Yar China tace karfa ki maida mijinki Kamar marayan karfi,Nafeesat tace kiyi a hankali suna palon can zasu iya jinki,Yar China ba sirri sai ta Kara daga Murya to Mene Dan sunji Ni Allah yasa nasiha nake Miki ba zugaki nakeyi ba,Ke kina Likita ma ku da aka koya muku a aji ko Baki karanta Biology bane? Anatomy to gashi Nan an Zana kayan aikin a jiki har can ciki bala'i bature sai da ya dauko hotonsa,mu da muke mata Muna da shi a jikinmu ba mu San cikin ba Amma bature sai da ya bude sirrin,Ai wlh da nice nayi Likitanci ai da ba Haka ba,ke kullum wani salab salab dake ba Energy ko ba Vitamins ne da yawa jikinki? Nafeesat kiji tsoron Allah ba abinda ba a Baki na kayan Dadi Amma kullum wani salab da ke,Nafeesat tana ta dariya yanda Yar yarinya ta tsaya Kamar uwarta,Yar China tace shine Your eyes,da nice nayi degree da anga bugaggiyar Yar duniya wlh amma ke kenan a kunshe a gida,Rannan Ina kallo mijinki Yana Miki magana kin wani hade rai kina latsa waya kin wani shareshi wayarki ta fishi muhimmanci. Nafeesat tace na shiga Uku da sa ido ke Yar China ki raba kanki da sa Ido,Mashkoor Yana can Palo Yana amsa Hirar yace Haka kikeyi Yar China gaskiya ta fada,Baki Yar China ta tabe tace shike nan kici gaba da feeling Big girl ke me degree ko nurse kina daukan salary to ai shike Nan,Nafeesat a hankali tace ke Nifa har yanzu zafi nake ji idan Yana Yi ko wani abin kuke Sha ki sanmin? Yar China ta dinga dariya, Mashkoor yace banji me Nafeesat Tace ba kunji suna dariya,Allah dai yasa Yar China ta gyara min ita,Yar China tace muma ba sabawa Mukayi ba Hakuri mukeyi amma Ni dai yanzu bana Jin wani zafi Zan dai San Miki wata zumar tsumi da Yaya Salamatu ta kawo min,Tawaga yaji a kunnensa shima yace a can palon Wanda Kawai su Ahmad me zasu ji wai ban yarda ba a bayar Mana da tsumi ba bazai yuwu ba ya Kare na Shiga wani Hali,su Basu ji ma me Yar China Tace ba Amma shi Tawaga ya ji fes. Gida Yar China ta koma ta Shiryawa Nafeesat mugunta ta kawo Mata na karfin sha'awa da Niima,Dan kadan ake Sha Amma Tace shanye du daga yau kin daina Jin zafi,Nafeesat ta karba tana murna tace Ina da magunguna Nima Amma bani da irin wannan,Yar China tana boye dariyarta tace wannan na daban ne shi na Hana Jin zafi ne,kafin dare yayi yayi aikinsa,Nafeesat ta daga Robar karama ta shanye Nan take,Yar China tace Bari in tafi gida Nima na Sha Nawa idan kinji zam zam gobe kizo na Kara Miki Ina da shi da yawa,Nafeesat harda rako Yar China tana godiya tace kina birgeni gaki yarinya amma kinfi manyan ma,Yar China tace Haka nake ai sai gobe ko a waya Kya bani labari Suka Yi Sallama Nafeesat tana ta godiya ta koma gidan. Minti biyar Nafeesat ta fara Jin canji a jikinta,Ji tayi Niima duk ta sakko Mata Kamar me,Sha'awa ce me zafi ta riske ta,ji tayi ba Wanda take bukata sai Mashkoor,Abu kamar Wasa tun tana basarwa har ta kasa,girki ta daura Amma ta kasa ta kashe gas din tare da dawowa Palo ta zauna tare da zuba tagumi,Kwanciya tayi Nan ma ta kasa ta Mike agogo take kallo tana cewa sai yaushe zasu Gama Hirar Nan ne su dawo gida,6pm ta gani tace Kash yanzu ma nasan sai sunyi Sallah maybe ma har Isha sai sunyi,Kasa daurewa tayi ta Kira wayar Mashkoor Yana dagawa tace sai yaushe zaka shigo?sai Munyi Sallar Isha,lafiya? Tace lafiya shike nan ta kashe wayar. Kasa hakura tayi ta tura Masa Text me Zan dafa maka? Ya Mata Reply da kin manta nace tea Kawai Zan Sha da dare,Okay tace,Zirga Zirga ta Shiga Yi tana safa da Marya ta ciji yatsa,ta koma saman bed ta kwanta,mikewa tayi zaune tare da Jan Tsaki,wanka ta Shiga ko zata sama salama Amma Ina Sam,Daure take da towel ta sake tura Masa da text yau da wuri zanyi bacci ka dawo da wuri, Inshaallah yace kawai,Nafeesat bata hakura ba tace Ina yin Sallar Isha zan da key a kofata ka dawo da wuri please,Shi Mashkoor Bai kawo komai ba yayi tunanin ma tsokanarsa takeyi dan yaje ta ja Masa Rai,sai da sukayi Sallar Isha sannan Yar China ta dinga Kiran Tawaga a waya Kamar mayya,Yana dagawa My Man Dan Allah ka dawo na gaji da Zama Ni daya,Ya lallaba abarsa ko mintu biyu ba ayi ba ta sake Kira Tace kasan fa nayi missing dinka ka taho gida Ni gaskiya,Kafin yayi motsi ta sake sambado kira tace kazo kaga kwalliyar Nan idan Bata Yi ba na canja maka wata,Mashkoor yayi tagumi yace kaga masu sharafi,Kuna Sharafi a kasar nan,Basu San Jibson ya tafi gida ba tuni sai gani sukayi baya Nan suna kallon gidansa Suka hango karshen rigarsa ya shige ciki,Brown yace kaga mayen Sameera ko Sallama,Brown yace karku manta gobe zamu je gaisar da Abbana Yana ta min masifa akan Jibson ya aure Masa Budurwa,Dariya sukayi Ahmad ya mike yace nasan tawa ba irin ta kowa bace tana can tana jira, Haka kowa ya nufi gidansa. Mashkoor Yana shiga mamaki ya kamashi yanda Nafeesat tasa rigar bacci sharara komai nata a waje matar da a baya idan taga dare yayi sai ta saka wando jean pencil Wai dan Kar yayi Mata wani Abu ita zafi take ji, Mashkoor yace a ransa ko Yar China ce tayi gyara? ai Kuwa Zaki ga taragon jirgi iya ganinki. Murmushi ta sake Masa me tsada a ransa yace uhm anga Taragon jirgina za a min wayo,basarwa yayi yace kinyi kyau,taga ya Saba like Mata sai taga yau Sam yaki ma ko taba Yatsanta,tana karairaya Tace Bari na kawo maka tea din sai mu kwanta ko? Mashkoor yace kawo Amma sai dai ki kwanta ke daya Ina da aikin office Zan karasa a gida kafin Monday,Wani dukul Nafeesat taji Kamar zata Yi kuka tace ko laifi na maka ne? Laifin me Kuma? Okay ta furta tare da kawo Masa tea,yau itace harda Zama a cinyarsa abinda take Jin Tsoronsa,Yana ta murna a ransa,Tea din ma yau a Baki ake bashi Yana sha,Har ya gama ya jawo system dinsa Yana dannawa ba Uwar da zaiyi amma yace Aiki zaiyi,Zama tayi tare da kafeshi da Ido kamar zata lashe shi. Rungumeshi tayi ta baya tare da kwantar da kanta a bayansa,a hankali yace wayyo Zafi yanda take ce Masa idan ya fara harka,Baby zafi ne dake,tunawa tayi Sanda Tace Zafi ne da shi,Wato ramawa yakeyi,Wata wutar Sha'awa ce ta sake ruruwa a jikinta,ta janye System din tare da kashe wa ta koma gabansa ta Rungume shi suna facing juna, Mashkoor da kyar yake fuskewa ya Furta da Allura kike Yi zafin Hannu Zaki Yi,yanda ta fada Masa Wai da Allura yakeyi zafin Hannu zaiyi sabo da Yana saduwa da ita tana Jin zafi take fada Masa Haka,Kuka ta fashe Masa da shi tace Kai baka manta abu to kayi Hakuri ai kasan zafi Dole naji tunda Virgin ce,yace to yanzu me ya faru kike bukata? Hawaye ya sake zubo Mata tace Yar China ce tsinanniya ta bani wani tsumi tace maganin Jin zafin da nakeyi ne, Mashkoor ya dinga sawa Yar China Albarka a zuciyarsa a fili yace to yanzu me kike so?......kafin ya rufe Baki tace ci na,Ido Mashkoor ya zaro yanda take kunyarsa yace me? ta sake furtawa tana kallonsa da idanunta farare tas Amma sun canja sun koma ja,Idan kika ji zafi fa?bazan ji ba wallahi ta kamo hannayensa tare da dora su a Kirjinta ta Shiga kissing Dinsa a Baki kamar mayya,Yace muje bedroom,no muyi a Nan Dan Allah,Yau Mashkoor yaga love, gashi bata gajiya ko kadan duk bala'in gwarzontakarsa sai da ta so kure shi,Ya Dade Yana Mata tace Baby ko ka kawo anjima zaka Kara min, Mashkoor yace Alhmdllh Ni ai Haka nake so Muna hutawa muci abinci a sake ta Yi ba ruwana,Nafeesat Tace ae,yace to yanzu bakya Jin zafin? tace Babu zafi wallahi ko Daya sai dadi,ka daina fita yawo kaji kullum Zan na yarda, Mashkoor ya dinga dariyar Jin dadi,yace kutmar duma du yau na samu yanci.sai da ta gamsu sannan suka Yi wanka tare da sake cin abinci sai bacci me Dadi ya kwashe su, Mashkoor harda cewa idan kika ji kyaram cikin bacci ki tasheni na shige ciki tace to. Sai da Asuba bayan sunyi Sallah Suka koma sabon harka,sai da safe Nafeesat ta samu maganin ya sake ta,Amma Bata ji zafi ba Kuma tayi Enjoying matuka,ranar yini tayi tana tunawa sai tayi ta dariya tana murmushi, Mashkoor Yana kallonta shi Dariya ma take bashi,Yau ga kalaman soyayya Mashkoor yini yayi Yana Jin sababbin kalmomi wajen Nafeesat har da yanke Masa farce,yau komai da kanta take masa ai Kuwa Yana ji Ahmad ya kirashi Wai yaje Office ya kwaso wasu takardu yace wallahi bazai je ba idan an isa a sallame shi daga aiki,Dariya Ahmad yayi shine fa ya kamata yaje Office din Amma sabo da Aamna tana jikinsa suna soyewa yace bazai je ba Bari ya tura Mashkoor,to Mashkoor ma yaki zuwa,Aamna Tace kace Jibson yaje Wannan Dan Iskan ne zai je gwara ma Tawaga ko Brown,Bash ma ba zuwa zaiyi ba,Tawaga ya Kira yaji muryar Yar China tana Yayana kazo ka taje min gashin ya bushe,Ahmad Yana ji ya fuske yace Tawaga Office fa zaka je ka ebo min takardun Nan Dana ajiye a saman Table,Tawaga yace kash...okay Bari na lallabata sai na je,Ahmad yace zanci Uwarku wallahi ya Kuna Aiki a karkashi na ban Isa na da kowa Aiki ba Haka ake ma'aikatan? Shi yasa gwara ka dauki bare Aiki Dan Kun San bazan iya korarku ba ko,Tawaga yace to bazanje ba sai kazo ka Jani Dan Iska Kawai ya kashe wayarsa,Aamna tana ta dariya tace ka hakura Kawai kaje da kanka,Yan iskan Yara ne sun rainani cewar Ahmad. Sai wurin Magriba suka je gaida Baban Brown sabo da Yana Fushi da Brown,Abba da kyar ya amsa gaisuwarsu yace bana bukatar girmamawarku tunda Baku ji kunyar hada neman aure Dani ba,da girmana kuke gani da Bai kamata idan kuka ji naje gun wata ba kuje,sai da kuka Gama ci min mutunci lokacin da kuka kwance min zani a kasuwa yanzu kuce zaku dawo ku daura min,me zaku Gaya min,Abba ya kalli Jibbonsa yaga yanda jibbon yayi kyau ya Kara kiba yayi wani Fresh haushi ya Kama Abba yace a ransa da yanzu nine na canja haka Amma jiba fatata ko yaushe cikin shan ruwan gishiri Da suga nake sabo Yar fatata ta rage yaushi,a fili yace ku tashi ku barmin gida bana Fushi da ku tunda Kun rigada kun Gama Dani kuje Allah bada zaman lafiya wani girmamani Kuma bana bukata ku rike abinku,Tawaga yace Abba sai da sa albarkarku zamu ci gaba a rayuwa,da Masifa yace da kun San da Haka kuka je inda nake zuwa bakin kinibabbe kaima ai naje wajen taka Neman aure tun a mota na hangoku a can Kun tare ko Ina Kun kankane na juya salin alin ba tare da Kun ganni ba kuje ku karata Yan iskan yara. Suna ta boye dariyarsu Suka ajiye Masa kudi yace an gode kuje Allah bada zaman lafiya tattabaru sarakan Aure ko Shedan ya ganku Haka sai Kun firgita shi,Dariya sukayi Suka Shiga motocinsu har biyu Suka tafi. Nafeesat Kuwa da Yamma taje har wajen Yar China a can ya Iske su Aamna da Hafsat suna hira,tana shiga ta antayawa Yar China ashar,Dariya Yar China tayi,Aamna tace lafiya? Nafeesat tace wallahi in fada muku Yarinyar Nan ta bani maganin Wai na daina Jin zafin XXX na Sha Ashe maganin sha'awa ta bani,Hafsat Tace Yaya kika Kare? Hmm ke dai bari,Yar China tana Dariya tace tsakani da Allah kinji dadinsa ko Baki ji ba?Nafeesat tace zuwa nayi ki Kara min ma Zan na Sha kadan kadan ba yanda kika bani Overdose ba. Aamna tana ji tace ai Ni irinsa nake nema Yana Ina ku San min,Yar China ta dakko wani galon Guda na hadin zumar ta musamman,Aamna anji harka ta rude a Ina ake hadawa na bada kudi na? Yar China tace Yaya Salamatu ce ku kawo kudi a hado muku dubu goma goma,Aamna da sauri tace ki karbo Mana accnt number dinta har wasu Kalar ma Ayo Mana,My King ko Nawa ne nasan zai bani,Hafsat ta Mike tsam ta dakko cup a kitchen ku bani dama Bash ba Hakuri ne da shi ba Nima baya daga min kafa ku bani Nima,Suna Haka sai ga Sameera da Humaira sunzo,Ai Sameera mayya tace Kan bala'i ai na shanye tawa irin wannan dama Ina ta Nema ki bani na kurba,Humaira tace Mene ne bayin Allah? Aamna tace kayan harka ne Wanda ke sa me gida Hawaye,Yar China harda shewa tace har kuka ma Wiwi zai Miki,Humaira Tace ba ruwana Haka Kawai ma ya Muka Kare da shi bare na Kara da wannan Ina da wasu abubuwan ma so nake sai na Saba sai na fara,Yar China tace ke dalla kauyis Kamar bada Lagos kika fito ba yanda kike Yar balarabiyar Nan ai ya kamata Brown yasan can ciki dinma Balarabe ne idan Zaki daina zancen zafi da wani takura ki daina mu mun watsar Gazal ake sa Mana kullum,Suka dinga kyalkyala dariya,Yar China ta Zama fetsararriya bayan itace karama kuma. Humaira tana Dariya Tace Gazal? Tozali ba yarinya zauna mu ba ruwanmu shi ake gwaguda Mana kullum kin zauna can wata katuwar tana wajen tana siyen gishirin Mata tana yafawa ciki ke a barki a Nan,to mazan yanzu Zina ba komai bace a wajensu Allah kiyaye idan Zaki Sha ki sha,Aamna tace wallahi ai mu Bama daga kafa Bama Free,Nafeesat Tace ku bani Dan Allah tsarin Nan yayi Yar China Uwar Mata,Hafsat ta bulbulawa cikinta,Aamna Robar ruwa ta dakko aka zuba Mata sannan ta Sha wani,Haka su Nafeesat ma aka barwa Yar China ragowar nata itama ta Sha kadan tace kadan Zan Sha sabo da tun safe na Sha wani,ta mayar da abinta,suna hirarsu Aamna dake dama Yaya bare anyi Kari tace Kai na tafi Good Night yanzu zai dawo,Yar China Tace za dai kije kwada Masa Kira a waya ya dawo,Nafeesat tace Nima nayi Nan,Daya Bayan daya suka tafi kowacce. Baba kuwa ya Canjawa Mama sabon suna daga Aishatu ta koma Ya Hajja,Mama tayi ta Jin kunya Amma Baba yace Ina ya dakko darasi wajen Rahilu,Mama Tace kaji kunya wallahi,Yana daga kwance yace kalle Ni Nan nafi Rahilu komai Amma Rahilu yanda naji Yana Kiran Hubby abin ya firgitani Dole Nima na dauki mataki Ina laifi ma dana Yi Kara nace Ya Hajja karki jawo wallahi ma koma sweetner ma,Mama tayi Mukus. Siyama tunda aka kaita Hashim Bai wani Bari sai ta so shi ba ko wani abu ba jira yake karbar Hakkinsa kullum,Siyama ba yanda ta iya gashi Yana kyautata Mata sai abinda take so Bata da bakin Yi Masa musu akan komai,Jin Dadi ba Wanda baya Bata sabo da duk Samunsa gida yake kawowa mutum ne me zuciya, da ka samu me kudi da mota marar zuciyar kyautatawa Iyali gwara Dan dako me zuciya. Ga Aiki tuni Ahmad ya dauke shi bashi da matsala shi kam,Ita kanta Siyama sai ya fara birgeta,Waya ta Kira Aamna suna waya,Aamna Tace ya me gidan fatan ba a bashi wahala? Dan Allah karki amfani da kiyayya ki cutar da shi,Dariya Siyama tayi tace wa? Ai in fada Miki Ni wallahi ya fara birgeni,Ni yanzu masifar birgeni yakeyi in fada Miki ga tsafta ga iya daukan wanka,ke in fada Miki ga iya love har mamaki nake yanda ya iya Romancing ko bature Albarka mutuniya ta,Aamna tana dariya tace kice yafi Faisal? Siyama tace Faisal din banza Ni sai yanzu Naga ma Ashe yafi Faisal kyau da komai wlh kawai kudi Faisal ya fishi Kuma Inshaallah shima kwanan Nan zamu Faso gari tunda ya fara Aiki da Ahmad,Baki gani ba sai abinda nake so abinci yanda me kudi yake cin me kyau Haka Nima komai available,sunansa ma me Dadi Hashim Dan Allah yaushe Zaki hada shi da sunan Faisal,Wai Faisal Abu ba Dadi Haka Kalar karya feso karya shine Faisal,Aamna tace iyye Dan Adam kenan kayan Allah,Kawai Hashim ya tafi Dake? Siyama tace Ni yanzu ma na gano ba birgeni yake Yi ba sonsa nakeyi,Lokacin da suke Wayar Hashim ya shigo da danyun kajinsa a Leda za a zuba farfesu,farin ciki ya kamashi yaji da kunnensa tana sonsa shi Kam ya Gama dacewa,tun Siyama tana jaririya yake kaunarta,ba irin wulakancin da Bai Sha ba a wajenta sabo da baida kudi Amma gashi yanzu cikin sauki,Godiya yayiwa Allah Dan murna ji yake kamar ya tashi sama,Sabo da murna fita ya sakeyi ya sake siyo kifi da wasu tarin abin makulashe. Siyama yau taga tattali da soyayya wajen Hashim,sai ta Kuma Jin sabon sonsa. Lokaci na ja cike da kwanciyar hankali da kaunar juna cikin Aamna ya shiga wata Biyar har ya fito Ana gani,Bata wani laulayi me wahala,a satin Kuma Humaira ta fara zazzabi da Amai yaki karewa,Ana zuwa Asibiti akace ciki ne da ita har na wata biyu,Brown harda rawa a Palo a Gaban su Tawaga ya fara Break dance suna ta dariya,lokacin Kuma Nafeesat canjin da taji a jikinta tana zuwa hospital wurin aikinta Tace a Mata test sai gashi tana da ciki na wata daya sai Result ta kawowa Mashkoor,Yar China tana ji tace Allah ya tsare watakil muma Muna hanya badan Allah yasa last month nayi period ba da Nima asibiti Zan tafi a gwada Ni Naga abin Kamar gasa ne ai muma ana Mana aikin ba finmu rakashewa aka Yi ba sai dai a nuna Mana shekaru,Hafsat tafi kowa son ta samu ciki tana son Yara a rayuwarta Amma itama Shuru Tace to Muna jiran tsammani,Sameera Kuwa da Jibson dama su ko a jikinsu idan sun samu suna maraba. Kwanci tashi sai da cikin Aamna ya shiga wata Shida sannan Sameera ta samu cikinta,Jibson harda yanga zaiyi da shima,Hafsat ma ta samu ciki,Yar China ta damu kanta Bata San tana da cikin ba ma garin jarabar wasanninta ta tafi part din Aamna ta hau lilo tana ta shillo a kai daga lokacin Mararta ta daure ta Shiga kwala Ihu ba ji ba gani,Aamna ta fito,Allah yasa sun Iya mota mazajensu sun koya musu Yar China ce Kawai Tawaga yaki koya Mata sabo wasan tsiyarta Kar ta kashe kanta da mota shi yasa duk inda zata shi ke kaita ko Driver, Aamna ce ta fito ta hango Yar China a kasa ta zube Jini malalala Fitowa ta kasanta,a gigice ta Kira Nafeesat Suka saka ta a mota sai asibiti suna kaita aka Kira Tawaga Suka sanar musu suna Office ma,Tawaga ya gigice yace me ya sameta? Aamna Tace ka kwantar da hankalinka Bari tayi,yace Ni ba barin ba ya lafiyarta? Tana Nan ma an canja Mana dakin Hutu har mun gyarata bacci ma takeyi, Kasa tuka motar yayi sai Jibson ne ya dakko shi Suka wuce Asibitin Basu Dade da shiga ba Yar China ta farka da kuka,sai ihun kuka takeyi an zaci ma wani ciwo takeji aka yo kanta,Ana tambaya lafiya? Yar China ta sake rushewa da kuka tana shafa cikinta ta kalli Tawaga Wanda ya rike Daya Hannunta Tace ance Wai Bari nayi? to menene tunda lafiya kike ai Yaron yaje zamu samu wani,yar China ta sake rushewa da kuka wallahi bazan yarda ba sai an bi min hakki na sakakin likitocin Asibitin Nan ne,sune Suka jawo cikina ya zube,Wa yace ki hau lilo da shegen wasanki cewar Iyalle da ta shigo yanzu hankali a tashe,Yar China tace sai an biyani cikina bazan yafe ba,duk wahalar da Muka Sha ai ban San Ina da ciki ba da ace na sani yaushe Zan hau lilo,Wata Likita Tace dalla malama rufe Mana Baki kin cika Mana asibiti da kuka mijinki gashi Nan Zaki sake samun wani. Bed din Yar China ta doka da karfi tana burbuwa ta nuna Likita da yatsa Uwarki ce zata min Cikin shegiya tsinanniya duk ba kune kuka jawo ba da kunyi aikinku da kyau cikin zai zube ne Shegu Yan Practical duk irinku ake zubawa kuna kashe Yaran mutane,Tawaga ta kalla tace sai an biyani Diyyar dana da aka kashe min a Asibitin nan, Iyalle da karfi Tace Diyyaaa? Yar China Tace ae,Likita tayi Dariya tace to madam ki Gama zamuzo muyi Miki wankin ciki,Yar China ta saki sabon kuka tana za a zura karafa a cikina so suke su karasa min mahaifata,yahudawa ne America ce ta dauki nauyinsu sabo da a rage yawanmu a duniya,yahudawa ne suke biyansu ta karkashin kasa,Duk Wanda yaji haukar Yar China sai yayi Dariya,Yar China tace ko America ce ta Basu kwangila ko kasar Denmark matsiyata sune basa kaunar musulunci kasar Denmark sune ma. Barin tayin Dan aka bawa Tawaga a kwali Yar China tace ku Bude min Naga gudan jiinina tana kuka sosai Iyalle ta karba ta Bude Mata Yar China ta bangale Baki tana murmushi Yaron da ko halitta ba a fara Masa ba Amma take zuba Uban murmushi tace Allah sarki zamu hadu da Kai a makarantar Annabi Ibrahim,aka kyalkyale da dariya,Yar China ko kulasu batayi ba tayin dan da kusan ma jini ne shi take kallo Tace ga jini na can na Gane shi ga bangaren Tawagana can Suka hadu a broader, da tuni sunanka Ahmad sunan Babana za a mayar idan mace ce Kuma Salma sunan Babata Amma Ina,Iyalle ce zata rufe kwalin Yar China ta dage sai ta sake ganin Danta aka Bude Mata Karo na biyu tace Babanka ya Sha wahala kaji Amma mun yafe maka sai munzo ka jiramu a madakata kaji Allah yayi maka Albarka sai Watarana Amma kayi Hakuri zaka Dade baka ga munzo darul salamu ba sabo da Inshaallah baza mutu da wuri ba sai mun Haifo kannenka Suma sun Haihu yayan kannenka sun Haihu sannan ka ganmu,kayi gaggawa Dana, da ace ka zauna ai da kaga kaun....Yar China ta karasa da kuka Tace First Night dinmu nake tunawa Iyalle ke Baki San turanci ba First Night Iyalle shike nan,Allah sai na Suma Yar China tayi luuuu akan bed Wai ta Suma,Dariya aka dinga Yi har Tawagan nata Haka ya tafi da tayin,Yar China tana cewa karku cike Masa Ido da kasar kabari Kai Jibson wallahi karka sake ka taba min da baka Yi Addua ba nasan halinka. Baki Iyalle ta make Mata,ai Kuwa Yar China ta Sha wahala da aka Mata wankin ciki duk bakinta sai data daina magana,Tawaga hankalinsa ya tashi yasan duk abinda ya Hana Yar Chinansa magana ba karami bane,Sai kuka Kawai takeyi da kyar tace Dan Allah ka barni Iyalle ta tafi dani wajenta nayi ko sati biyu ne Dan Allah? Tawaga harda wani kwalla yace na yarda My love zanci gaba da Zama a Gwauro kafin ki dawo,Yar China da slow tace ai a dakin Iyallen ma Sai ka kwana Watarana,Iyalle Tace inji Ubanwa wallahi Baku Isa ba sai na fasa tafiya dake,Tawaga yace Wasa fa take Miki,Aamna tace da an barta ma Sai mu kula da ita,Yar China tana Jin jiki tace me kuka sani na Haihuwa Kuna Yara me zaku iya gwara tsohon Hannu,Iyalle Tace Ni Zan gyara abata,washe gari Yar China taji sauki aka sallamesu,Tawaga ya Hado mata Kaya ya sauke su a gidan Iyalle gidan kanin Iyalle kenan a dakin Iyalle. AsmaBaffa. 10/29/21, 7:46 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 NA KUDI NE Duniya ta Aamna is dedicated to Garba Butalawa family. Official By AsmaBaffa Page naku ne DUNIYATA FANS Tayi tunanin zata iya Zama ba tare da ta damu ba amma ganin Tawaga ya tafi duk sai taji ba Dadi Dan ma Allah yasa gidan Kanin Iyalle da Dan kyau ko Ina yasha Siminti bandakin Iya harda tiles a toilet din Kalar na zamani,shima Toilet din matarsa Haka yake,Ruwan Zafi Iyalle ta tafasa Cikin Yar China ya duri ruwa ganin ruwa me yawan masifa gashi na zafi ya tafasa,Iyalle ta tasa Yar China a gaba sai da ta Mata wanka da towel ta gasata sosai ta Sha azaba sosai harda kuka,Allah yasa Tawaga ya kawo Nama iri iri da kayan Karin jini ga magunguna,Fruits ba Nema ba,maltina da su Madara available, Sha Kawai takeyi tana ci ba ruwanta,Ko kwana Uku Bata Yi ba ta wani murmure har kiba tayi da kyau,Iyalle tuwon shinkafa Miyar Alayyahu ta Sha man shanu da kifi ta girkawa Yar China da kanta,Lokacin Yar China tana wanka Tawaga ya shigo da ledoji,Iyalle tana Masa tsiya baya gajiya,Ya zauna a Kan gadon Iyalle,Iyalle tace ga abincinta Nan a flask Bari ni na leka gidan gaisuwa,a dawo lafiya yace ta tafi,Mintuna kadan Yar China ta fito daure da guntun towel ga karami Kuma tana goge jikinta,Tawaga ya bita da kallo,ta Masa kyau sosai tayi wani kiba da haske,a gefensa ta zauna tare da kwantar da kanta a kafadarsa tace Sannu da Zuwa My Heart,Murmushi ya saki yace Dole kice Haka ai tunda kin gudo kin barni,Dariya tayi Tace ai Zan dawo Kamar yau ne,Abincinta ya nuna Mata Iyalle Tace ki cinye,Murmushi tayi tare da mikewa ta shafa lotion dinta me shegen kamshi ta dakko wata Yar bakar Vest me kyau ta sa Skert din atamfa ta sa bra tare da vest din tayi kyau,gashinta ta gyara fes sannan ta bi jikinta da turaruka masu kamshi ta shafa powder da lipgloss tayi kyau matuka. Tawaga sai kallon Kirjinta yakeyi yanda Suka cicciko,spoon ta dakko Guda biyu ta bude Tuwon na Danyar shinkafa Tace Busmillah,tare sukaci suka koshi,ya Bata ledojin Nan ma kayan ciye ciyene ga Naman kaza gasashiyar,Yar China tace Ina Jin dadina wlh,kwanciya tayi a jikinsa sai Kuma ta fara kuka,Mene ne haka? Zaki fara ko? Bata Rai yayi yace daga min jiki na tafi gida abina naga Alama daina zuwar Miki zanyi,tunda kika Yi Bari Dan ma ba'a sanshi ba babu Wanda ya Shaku da shi kullum nazo sai kin min kuka ki tashi to mu koma gida sai nayi miki wani cikin,Yar China tana goge hawayenta tace Allah jaririn ne akwai shiga Rai,wannan tayin jinin shine abin Shiga Rai? Yar China tace ae Ni Ina son abina jinin kalarsa me kyau Kamar ruwan zuma,Dariya ta kwacewa Tawaga,Tace Kuma ma ai Nonuwa ne suke ciwo duk sun cicciko wallahi sun min nauyi,wannan ai me sauki ne Indai ruwan zai fita sai na shanye,Yar China ta makale kafada,yace mu gani to tayi masa Shuru,Hannu yasa tare da janye rigar sama. Wayo ya Mata tare da Furta Wai Wai wannan ai Massage suke bukata,Yana tattabawa yace Massage suke bukata,da sauri tace Allah? Yace ae mana, ai ban sani ba da tuni idan munje wanka zance Iyalle ta dinga danne su da Towel cewar Yar China,da sauri Tawaga yace no Miji ne ya kamata yayi ai Hannu na tafi na Iyalle girma da laushi idan na Miki yau ma gobe Zaki ga sunyi sauki,sai na dawo gobe na sake Miki Haka dai kamar sati Daya yanda kafin ki dawo gidana kin warke,jinin ya dauke ne? Ya tambayi Yar China Yana son Yi Mata wayo,Tace a'a Saura kadan Nan da kwana Uku ma Iyalle tace zai dauke,hakan yayi kyau cewar Tawaga Dadi ya Gama kamashi,cike da nishadi ya shiga massaging Dukiyar fulaninta tana Jin Dadi tana lumshe ido,Yace da Dadi ne? Kulle Kofa kasa key Kar wani ya shigo abin Nan na Yi ne cewar Yar China,Ba musu ya dannawa Kofar Iyalle key ya dawo,Yar China da Yatsanta ta daura a saman lips dinta tace nan,ya Gane ya shiga tsotsar lips dinta,Yar China ta sarkalo da hannayenta wuyansa suka kwanta a saman gadon Iyalle Yana luguiguita ta yanda yaga dama,Yar China ta shiga sarrafa shi itama da kanta yanda zai samu ya rage zafi ba tare da sai anyi babbar harka ba,Zaucewa sukayi ya furta matse min cinya Honey,Duk ba Kaya a jikinsu Yar China ce Kawai me pant,ai Kuwa dai da Cinyoyi a samu gamsuwa a nutse ba tare da sun batawa Iyalle komai ba,Yar China harda dabara ta sa tissue a jiki ya fitar ta wani saka a bakar Leda ta daure,sai da suka daidata kansu tsaf kamar ba abinda ya faru ta Bude kofar ta tarkata na zubawa a shara ta Kai Dust bin ta dawo. Suna Shan Fruits Iyalle ta dawo Bata Gane komai ba sai da Tawaga ya Mike zai tafi taga jikin farar shaddarsa duk jambaki da powder,ga lips dinsa yayi red shima sabo da jambakin Yar China Daya Sha,Fuskewa Iyalle tayi sai da Yar China ta raka shi har mota ta dawo,Iyalle tace Nan da sati Daya Zaki tafi baza kiyi min sati har biyu ko Uku ba,Sabo da me ? Sabo da na gaji da sintirin mijinki,Yar China Tace to shike Nan Ni gwara ma na tafi dama na gaji gida duk zafi ba AC ba komai,can abinda Naga dama nake Yi Amma Nan duk kinbi kin takurani,Mijina Yana can Yana ta kamshi ke Kuwa jikinki duk kauri,dama Ni manage nakeyi da ke Ina kwanciya a bayanki wani fayauuuu....ba hug ba komai da Mijina ne fa sai nayi shagwaba ta,Mufici Iyalle ta kwadawa Yar China a baya tana Yar banza fitsararriya. Kamar yanda Iyalle ta furta Yar China tana yin sati Tawaga yazo Suka tattara tare da komawa gidansu tana ta murna. Rayuwa na tafiya Sannu Sannu sai lokacin cikin Aamna ya cika cif dai dai edd dinta Amma Bata Haihu ba,tayi nauyi da yawa Dole sai masu Aiki Dattijai masu kwari Guda biyu aka kawowa Aamna suna tayata aikin gida,Yayin da Suma cikin su Sameera duk ya tsufa Banda Yar China babu ciki. Bayan Sati daya da cikar edd din Aamna cikin dare suna kwance ta kasa kwanciya,nakuda ta fara,kasan bed ta koma ta zauna tana daurewa,tun tana dannewa har ta kasa ta bigi kafar Ahmad dake banci Bai San me ake ciki ba,a hankali ya Bude Idonsa tace ka tashi Dan Allah mu tafi asibiti wallahi Ina Jin Haihuwa zanyi washhhh Allah marata wayyo gadon bayana,Ahmad Yana ta nuku nukun tashi ta fashe da kuka tana buga jikin bed,ba shiri ya dire a kasa da kayan baccinsa ya dakko Mata wani zani ta daura a saman kayan baccin ya kifa Mata Hijab tare da dakko kayan data nuna Masa ta shirya a cikin wata jaka duk na Haihuwa ne ta tanaji komai abinta,Dauka yayi tace dakko har Bowl din jaririn,Ahmad ya dakko ya sauka da gudu gudu sauri sauri ya saka kayan a mota ya dawo ya dauke ta ya kwantar da ita a bayan Mota,Nafeesat ya Kira da Mashkoor,Yar China ta saman window dinsu ta leko Jin maganganu ta tashi Tawaganta Tace ga Aamna can tana fama Allah ya tsare mugun ji yau zata San uwarta ta kawo ta duniya tashi mu tafi na koyi darasi kafin nawa,Tawaga yace ke da kika Yi Bari,ance wani barin ma ai yafi Haihuwa azaba Kuma idan kunje Kun tarar Mata a Kai me zakuyi mata muyi Mata Addua Kawai,Sameera ce ta fito Dake itama ta taba Yi aka tafi da ita,kafin ma su karasa Hospital an sanarwa Mama tuni Mashkoor a daren 1am yaje ya dakko Mama Suka taho Asibitin. Aamna Kuwa tana ta daurewa bata kuka Shuru kawai Bata magana da Alama tana Shan wahala,private ne Single room ita Daya aka basu,Bayan an duba Suka ce Haihuwa ce tazo gaf,Ahmad suna waje hankalinsa a tashe Kawai tagumi ya buga,Mama da Su Sameera suna ciki tare da Likitoci,taimakawa Aamna sukeyi har aka samu Aamna ta santalo katon danta namiji Kamar yanda suka gani a scanning,tana Haihuwa ta suma sai da kyar Aamna ta farfado ta Sha wahala Amma tayi Hakuri tayi juriya matuka,Jaririn Nafeesat ta goge da man Zaitoon dana Habb fes a towel aka nadeshi,Yaron girmansa ya Isa Kamar ba daga jikinta ya fito ba,Sameera ce ta kaiwa Ahmad jaririn,Bai ma San ta Haihu ba suna Zaune da Mashkoor hankali a tashe sai jariri Suka gani, Ahmad ko jaririn Bai karba ba yace ya My world take? Ras take Ahmdllh Bata da wata matsala yanzu ma gyarata akeyi,Sai lokacin Ahmad ya saki ransa tare da godiya ga Allah Yana me karbar Jaririn,shagala yayi da Kallonsa Baki Nan a Bude, Mashkoor yace to Malam Addua fa zaka Masa,Sai lokacin ya shiga Masa Addua a kunne sannan Mashkoor ma ya karba tare da Yi Masa,sai ga su Tawaga Suma a daren sunzo sun Iske an Haihu ma,Jibson ya karbe Jariri Yana cewa mun zama Iyaye yau,Bash da Brown ma Suka karba suna ta Masa Addua,sai Tawaga shima har da cewa bari na Masa shillo ya daga karmar zai shillashi sama,Ahmad da bala'i ya dakawa Tawaga Tsawa zai kwace dansa Yana masifa aikin banza so kake ka hallaka min yaro,Dariya Suka dinga Masa gaba daya,sanadin Haka ya karbe dansa ya Hana Tawaga fafur. Humaira sai Waya take bugawa taji ko ta Haihu aka ce Haihu lafiya,Haka Hafsat da Yar China Suka ji a waya,sai bayan Aamna ma tayi wanka ta canja Kaya aka canja Mata dakin hutu,komai an gyara Neat ba matsala sannan aka bada dama su Ahmad Suka shiga,Tana kwance ta lumshe Ido tana hutawa,Ahmad kamar zai shige cikinta duk yabi ya kankane ta,Sannu su Tawaga suka Mata da Barka sannan kowa yayi waje ya barta da Ahmad dinta da jaririnsu. Aamna ta kalle shi Suka hada Ido tare da sakarwa juna murmushin kauna,Yace me Kama Dani aka Haifo,Aamna tace Haka naji su Sameera suna fada,Ahmad ya nuna Mata Yaron ta karba ta Masa Addua itama sannan tace ka duba jakar can akwai Ribbom Dina ka Kama min gashin Nan ya dameni,Ahmad ya ajiye jaririn a gefenta tare da dakko Ribbon din ya daure Mata gashin sosai yanda bazai dameta ba,yunwa nake ji ta furta,Yanzu Jibson zai kawo abinda Zaki ci ki Dan Kara Hakuri ya Furta Yana shafa fuskar jaririn,Aamna tana satar Kallonsa tace ai fuskata zaka shafa ba ta Jariri ba idan da a baya ne kafin na Haihu ai fuskata kake shafawa,Dariya ta bawa Ahmad ma shi,ba a Dade ba Jibson ya dawo da ledoji Naman kaza da fruits sai gida da yaje ya taho Mata da tea a flask da komai na amfani,yace Mama tace na taho Miki da me Dan nauyi gashi Nan Humaira ce Kawai Allah yasa tayi faten doya ya rage kiyi manage kafin safiya,Aamna tace hakan ma yayi,Nafeesat ce ta hada Mata tea me kauri da kaza taci ta koshi har faten doyar. Bacci ne ya kwashe Aamna,su Ahmad sai murna da bige bigen waya duk sun cika Asibitin da surutunsu,Su Yar China Kuwa suna tare da Humaira a gidan Hafsa Suma sun hadu suna zuba Hira,Yar China tace Yau Aamna karshen Sirri ya Kare yau likitoci sunga Hq,Basu da mutunci matan Nan Haka suke zura Masa Ido,Dole su makance da wuri cewar Hafsat,Humaira Tace to yanzu ma ba mu zo Haihuwa ba Ana ta duba mu Ina ga Haihuwa,Yar China tace ai ku shirya ba Wani sirri idan da duhu ma wata shegiyar touch suke sawa me haske,Dan ma matane Amma ai da kunya,lokacin Dana Yi Bari Ina dawowa nace to Tawaga sai dai kayi hakuri dakinka dai yanzu ba sirri ,Humaira suka Kama dariyar Yar China,Yar China Tace shegiya ai Kuwa likitar ta kiyaya wlh taga tsafta iya tsafta da kamshi sai da ta min jinjina Tace da wasu matan ne Haka dagajaja ake gani,Humaira tana Dariya Tace a gidan Ubanwa ta ganshi fes lokacin kina Bleeding,Ke banza ce yanzu fa Dana warke ai mun koma Hospital ta dubani taga ko Mai normal,Humaira tace sai kace wacce ta haihu,Yar China tace su Ina ruwansu Abu ba abu ba sai suce sai sun duba ya na iya,Hafsat tace ni wlh Nima abin ya isheni ayi ta sa ma yatsu. A daren Mazan Suka dawo gida har Ahmad,Yar China Suka koma part dinsu,Ahmad sabo da Murna da kyar yayi bacci,Nafeesat aka Bari sabo da ita Nurse ce sai Mama,Itama Sameera mayenta ya taho da abarsa gida,a daren Ahmad ya sanarwa su Mummy suna ta murna,Washe gari jikin Aamna yayi kwari ka rantse ba ita ta Haihu ba,da wuri Yar China,Hafsat da Humaira Suka zo da kayan Kari,Yar China ta kinkimi Jariri tana wayyo Allah ji Dan Allah yaro zukeke me Kama da ubansa,Ina ma Nawa ne mashaallah,Kai Aamna kinyi Aiki yanzu daga jikinki ya fito? Gaskiya kin Sha wahala,Aamna tana dariya tace wlh abin ba a cewa komai,ai naso jiya nazo ko darasi na dauka Amma Yaya Tawaga ya hanani,Aamna tace akwai azaba wallahi da ikon Allah bazan sake ba Allah ya tsayar min iya Nan,Karya ma kike fada wlh sai kin Karo Ina laifin ma biyar ko hudu,Humaira Tace ai fa Amma Daya jal idan aka Miki kishiya ta wuce ki fa? Aamna Tace ga fili Nan Indai wannan abar ce taje ayi ta sa Mata Ana Mata ciki Ni na hakura,Na rantse da Allah nayi zaton a kabari Zan farka na ganni,tunda nake ban taba Jin azaba ko rabi rabin wannan ba,kukan ma kasa Yi nayi na koma kurma Kawai. Yar China harda cewa Ahayye taji uwar Bari,Ni kaina Kinga dai Bari ne Dan Blood ne Amma naji a jikina,Kai Ina tausaya Mana Mata,Mama da shigowar ta kenan tana ta kallon Yar China Kamar Tv Tace wannan yarinya da jarabar iya zance take sai kace Babbar mace ko dai tsohuwa ce ta rike ki? Yar China tace a Hannun Kakata na girma,Yanzu naji zance cewar Mama. Siyama ma da duk wasu abokan arzuka Haka Suka dinga sintiri,Baba yazo shima ya dauki Jariri Yana Masa Addua karshe yace Allah yasa karka gado taurin Kan Mamanka,sannan karka dakko rashin kunyar Babanka kaji,yaro Babanka har satar min kayan kallo yayi Akan son Mamanka,maza ka girma idan Ina da Rai ka biyani startime Dita da radio,kakanka Rahilu Haka Muka je Sudan Muka dawo ko kyallen Handkerchief Bai Bamu ba sai da kudinmu Muka Yi tsaraba,Yana can Yara da jikoki zasu hallaka shi Yana ta karmashewa,kaf kamfanonuwan duniya babu wando Size dinsa,idan ka girma ka kalli Rahilu sai kayi Takaicin Fitowa a tsatsonsa,ga tsayi Kamar bishiyar turare wani zamarke da shi,Mama ce ta kwace jaririn tana cewa Kai dama ai baka son mutum idan ba kudi zai baka ba,yanzu da Rahilu zai maka kyauta me tsoka cewa zaka Yi yafi kowa kyau,Baba yace to ayi min kyautar a gani Mana dama yace zaizo idan Aamna ta Haihu yau Zan fada Masa a waya sabo da dama ya min Alkawarin wani takalmin fata da yace zai kawo min Yana da kwari sai nayi shekara goma Ina sawa ba tare da ya tsinke ba Rahilu duk Harkar tsumulmula ya kware a cikinta. Aamna Tace gaskiya Baba ka daina,In daina Ubanki? Sanda na Sha wahalar rike ki ya taimaka min da kwandala ai wlh Rahilu Matukar Bai min kyauta ba ya shiga uku,har yanzu Bai iya Yi min godiya ba a matsayina Wanda na rike Masa yarsa ta girma na Bata Ilimi na Aurar da ita,shi ba ruwansa ko a jikinsa ai kin gani da idonki ko yayi min godiya? Aamna tace a'a amma ai Dan Allah kayi,to bazan daina ba idan kinyi zuciya kisa ya gode min Sannan ya girmamani ta hanyar Yi min kyauta,ai Ni babbar girmamawa ayi min kyauta,Mama Tace a Haka zaka Kare,Suna Haka Ahmad suka shigo ya Sha wani shegen wanka cikin kana Nan Kaya Yana kamshi,Baba yace Iyye kaga Wanda basa tsufa Kamar ba shi ya Haihu ba,kaga Danka fa Kato Amma bakwa saduda da daukan wanka wannan kamshi Haka kamar turaren dakin Ka'aba,su Ahmad suka dinga dariya,Baba yace ga Aski na banza Kun iya to dai Kun fara Haihuwa,Ahmad Yana dariya yace Baba ai wanka yanzu ne ma zamu fara,Kin shiga Uku Aamna Mata yanzu zasu fara sintiri a gidanki kuwa cewar Baba,Aka dinga dariya Aamna tace wlh Bai Isa ba gida Zan dawo,Baba Baki Bude yace gidan wa? Gidanka Mana,karya kikeyi Kai yaro idan tace zata hanaka aure kayi Mata shegen suka ka kirani a waya ka Kara min kukanta kana jibgarta Ina jiyo kukanta ta waya,Ahmad suna ta dariya da su Jibson,Yar China tace Baba kana ba damu wlh wa yake Yayin Kara aure yanzu ai tsohon yayi ne,Tawaga harda cewa wlh Ina zamu Kai Yara wannan ta Haihu wannan ma Haka,Baba Baki Bude yace sun shanye ku,ku daina Kiran kanku mazaje sam,Mata sun Gama da ku,a Haka kamar wasu mazajen kirki,Hafsat tace Baba kaima fa Daya ce jal,Gata can itace ta kankaneni ya nuna Mama da baki,Baba da abin Dariya Yana ta Basu Dariya ana Wasa da dariya ba ruwansa,Sai Yamma aka sallami Aamna,Mama Tace zasu tafi da ita Ahmad yace bazai yuwa ba,da kyar ya Amince zata Yi sati daya tal. Kullum suna gidan Baba mazansu da matansu suna sintiri,Baba yace Jaraba akan Jariri daya tal samarin Nan da matansu sun hanani sakewa a gida,wannan suzo da Yamma wannan da Rana wannan da safe,kullum ba ranar banza,Tawaga harda zuwa Wai sai an bashi Jariri ya tafi da shi yawo a mota,Aamna ta hana,Kuma da sanin Ahmad Wai su a Dole sunyi da,akan sunan Jariri har wuri me tsada aka Kama,anan Suka shirya party Wanda yafi na aure tsaruwa da komai,Katon sa da raguna biyu aka yanka yaro yaci sunan Baba Hussain sabo da rike Aamna da yayi Ahmad yace Baba zai mayar,Baba ya dinga murna,jaririn Nan Yana ganin gata wajen Baba komai ya siyo yace na takwaransa ne, Aamna suna kiransa da Fu'ad,Zuhra an sa Babanta sai murna,Su Yar China ranar suna sun chashe da Kawayenta Wanda itama ta gayyata. Bayan suna da kwana Uku Aamna dai tana gidan Baba Allah ya kawo Rahilu tare da matarsa Uwar gida da yaransa biyu mace Daya Namiji Daya,Tsaraba Rahilu yayiwa Jariri kaya masu tsada,Baba Kuwa Jallabiyya aka kawo Masa har kala biyar da takalma harda turaruka,matarsa Kuma ta Bawa Mama da Aamna dogayen riguna masu Kyawun gaske,Baba ai sai ya canja ka rantse Rahilu wani Dan Uwansa ne,Satin su Rahilu Daya Suma koma kasar su,Baba suna zaune da Aamna da Mama sai Siyama da Zuhra da Suka zo,Baba yace Rahilu kenan Ana can Allah sarki ai idan Rahilu yaso mutumin kirki ne Watarana,wannan karon ma Sai Naga yayi fes da shi ya canja yayi kiba,ko dai Rahilu wasu kulli ya taka ne? Aamna da Mama suna ji su dai sun San babu abinda Rahilu ya canja Yana Nan yanda yake Amma sabo da yayiwa Baba kyauta harda yabonsa. Baba harda cewa Indai mutum ba a Nigeria yake ba to Dole sai kaga canji Dole sai kaga mutum nutsatse da hankali,idan Dan Nigeria ne Marar hankali ya kalli gidana ai bazai bani kyauta har ta kudi ba,amma Rahilu Dake a kasar masu hankali yake bayan tsarabar Kaya ma da zai tafi har dollar Amurca ya bani,su dama wajejen yankin su Rahilu hankali ne da su,a nutse suke komai,ko wata kasar suka je zaka gansu daban,shi yasa Watarana nakan so mu hadu da shi Ina samun Karin Ilmi na zaman rayuwa da kula da Iyali,Mama ya kalla yace Ya Hajja ko ke Baki ga canji ba? Mama Baki ta tabe tace daga baka kyauta duk ka haukace,sai nasa Aamna taje dake kasar su Rahilu sannan Zaki waye,Naga Alama kina cikin duhu har yanzu,Baba Yana ta yabon Rahilu suna jinsa. Satin Aamna Biyu Oga yazo ya tattara Suka koma gida,yabi ya hanata sakewa da bin kwakwafi Wai Kar ta fara Sallah Bai Sani ba,Aamna Tace yanzu Arba'in dinma baza ka Bari nayi ba? Kina fara Sallah Kuma ai kinyi Arba'in me Zan jira,Aamna tace to yaushe zamuje Hospital game da planning din? Ido Ahmad ya zaro yace Fu'ad Daya tal ai yayi kadan Ni yanzu nasan dadin Yara ki Karo min daya sai ki huta,Aamna ta fashe da kuka ta tuna wahalar data sha,Ahmad ya dage shi Kuma kome zata Yi sai ta Karo Masa wani Yaron suka dinga fada ba Wanda yake yiwa wani magana a junansu,Aamna da ta gaji wajen su Jibson ta Kai kararsa to bakin su daya abinka da abota ta Amana,Su Tawaga suka ce ya Bari Yaron yayi kwari idan ta yaye sai ta samu cikin wani,Ahmad yace ni Sam wlh ban yarda ba,a shekaruna ace yaro Daya Ni bana son Kara aure Allah ya gani Amma Ni yanzu Ina son Yara idan ta Haifa min ko biyu ko Uku sai tayi ta planning dinta Nima Ina son haka,Tawaga yace Nima Haka na tsara na gani Yara suna da Dadi Niima ne Amma ba irin yanda muke Haihuwa a kasar hausa ba barkatai ba a iya daukan nauyin Yara,ba Ilimi,ba ci ba Sha Ana ta zubar da Yara suna dawowa su addabi duniya,gwara dai kadan sabo da halin rayuwa ma,Aamna dai gani tayi yaki yarda tayi duk abinda zata iya Amma Bata samu Nasara ba. Shi kanshi fushin da takeyi da shi ya dame shi duk ya rasa Jin dadin gidan,Wajen Bash yaje yace yanzu ya zanyi da ita? Bash yace kaje Kawai ku shirya ka fahimtar da ita nufinka ba Wai fada da Fushi ba,kasan Mata fa in taga dama zata ma Yi a boye baka sani ba sai dai kaga Taki samun wani cikin,Ahmad yace wlh da Kuwa ta Gane kurenta Aamna ta fiye rigima da taurin kai amma ba komai kyaleta,Bash yace masalaha itace kasan ta Sha wahala ita tasan me ta ji. Yau da dare Ahmad dakinta ya shiga ya Iske tayi kwanciyarta ita da Fu'ad dama tunda suka fara fadan wurin 4days kenan ta daina zuwa bedroom dinsa. Tunda ya shugo tana kallonsa tayi kamar bacci takeyi amma Kuma zuciyarta tayi fari kwal da shigowarsa sabo da ta Gama gajiya da fadan Nan nasu ta hakura ma zata Haihu hakan tunda Yana so. Jaririn ya dauka tare da maida shi bed dinsa da ke jikin nasu,Addua ya Masa tare da kashe light ya koma Bayanta ya kwanta Yana me Zura hannayensa ta kasan Hannayenta ya rungumota jikinsa. Masu Sharhi Ina godiya wlh Kuna birgeni. AsmaBaffa 10/29/21, 7:46 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵 KARSHE NA KUDI NE DUNIYA TA AAMNA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY. 141-150 Official By AsmaBaffa Page naki Ummi Deejat Aamna an samu dama harda yanga,nasan ba bacci kike Yi ba kina ji na,duk akan Haihuwa ne kike ta wannan fushin? Aamna a hankali tace ai Ni ba Fushi nakeyi ba,tunda kana so ai shike Nan ko mutuwa zanyi na hakura ai Sanda kake so sai ayi planning din tunda dama mu Mata Bamu da yanci,Dariya yayi kadan yace za muyi Mana Amma ki daure ki Karo min biyu Kinga Uku kenan sai muyi Kinga bamuyi aure da wuri ba ya kamata ace tun tuni Ina da Yara sun Kai hudu ko ma biyar,Aamna Tace ba matsala Allah ya bamu na gari,Ameen ya furta sannan ya fara rabata da kayan jikinta,Aamna ta Sha gyara itama a matse take sabo da haka Suka fara kashe juna da kauna,an Dade ba a hadu ba ai Kamar zakuna Haka suka koma yau. Sai gaf da Su Humaira zasu Haihu Yar China da Siyama suka samu ciki,Yar China harda rawa,wannan lokaci lallabawa takeyi bata Wasa sabo da kar cikin ya sake zubewa,sai da ta sa Tawaga ya kawo Mata Yar aiki duk sabo da kar ciki ya zube,komai a hankali take lallabawa har Humaira ta Haifi Yarta mace santaleliya,taci Suna Farhat an Sha shagali,bayan tayi kwana talatin Hafsat ta haihu itama mace,ranar suna taci Amrah,Sati biyu tsakani Nafeesat ta Haihu itama ta Haifo Namiji Kato Mashkoor ya maida sunan King Ahmad,Sai da Nafeesat tayi Arba'in sannan Sameera ta Haifi mace itama taci sunan Ummatinsa data rasu Safiyya suna Kiranta da Little Aamna. Abubuwa suna tafiya normal sai sake bunkasa sukeyi arziki Yana yalwata yanzu ma Basu fiye Zama a kasar ba sai tafiye tafiye suke Yi zuwa kasashe Daddy ya sakar musu komai,Siyama tuni mijinta Hashim ya Siya musu katon Gita me gate ga motar Hawa lafiyayya sai abinda tace. Su Ahmad duk inda zasu da matansu suke Tafiya Matukar zasu Yi Kamar sati Daya basa tafiya mutum Daya,Baba tuni Ahmad ya Siya Masa mota sannan Suka je aikin hajji shi da Mama,Haka su Tawaga ma Iyayensu duk sunje da Wanda ya kamata duk Ana ta biya musu. Aamna sai da suka shirya tare da Ahmad,Mummy,Daddy,Humaira, Sadeeq da Mufeeda tare da yaransu Suka je can kasar su Daddy taga Dangin mahaifiyarta da kowa satinsu biyu suka dawo,Gaba Daya su Aamna sun sake gogewa da wayewa,sun Zama matan manya kana kallonsu kasan suna hutawa,yaransu bulbul kyawawa gwanin sha'awa. Siyama ce ta Haifi Yarta itama kyakyawa taci suna Fadeela,Bata Dade ba Yar China yau Sunday da Asuba ta fara nakuda,Bata wani daure ba tana Jin ehem ta saki kuka,Weekend ne Tawaga ya koma baccin hutunsa yaji Yar China tana kwada Masa Kira da karaji tunda yaji yau ko Dan My Man din Bata ce yasan ba lafiya yanda yaji tana Tawagaaaaaa...kazo kafata ta rike....Yana Fitowa room dinta ya ganta ta fito daure da towel da Alama wanka tayi,tace wani ruwa ne yake zubo min da yawa kafata ta rike,wayyoo....mutuwa zanyi.....ruwan jikina zai kare,Tawaga ya rude tare da zura jallabiyya ya sa Mata kaya,itama ta hada kayan haihuwarta tsaf a jaka yanda sauran sukayi ai kinkimarta yayi,Yana Fitowa da ita Nafeesat ta fito zata tafi wajen Aiki ai sai ta fasa Driving motarta Suka tafi tare da Yar China,Humaira ma ta bisu a tata motar dake Dukkansu suna da mota ta kansu mazan sun siya musu,Aamna motocinta har biyu masu tsadar gaske ko tayi Driving ko driver ya tukata,Yar China ce Kawai Tawaga yace sai tayi hankali Bata Jin magana. Yar China duk ta cikawa mutane kunne da kuka duk ta tashi hankalin Tawaga ya rasa yanda zaiyi,Iyalle tuni tazo Asibitin ita da matar kaninta,Yar China tana Iyalleta rike ni Iyalle mutuwa zanyi wayyo marata Iyalleta....ai Sanda Kan jaririn ya fara Fitowa Yar China Tace gashi Nan Iyalle.....gashiiiii.....wani nishin tayi gumi Yana keto Mata ta ko Ina ta wani shide gaba Daya sannan da taimakon likitoci Yar China ta Haifi katon danta Namiji, tunda ta Haihu akaji Shuru Yar China wahala ta kare,komai da ya kamata anyi sai Yamma aka sallame su,Wannan lokacin Iyalle gidan Yar china ta koma gaba Daya da Zama sai Yar China tayi Arba'in zata tafi. Yar China Kamar zata cinye danta,ranar suna ba ayi wani biki ba kasancewar Yar China jininta ya Dan hau dalilin Haihuwa sai akace Kar ayi suna sabo da Hayaniya,ranar suna yaro yaci sunan Baban Tawaga da ya rasu Wato Abdallah Yar China tace wow suna me Dadi badan suruki bane Bai kamata a boye sunan ba Amma Dole nayiwa Tawagana kara,Su Aamna suna ta shawara wanne sunan za ana kiransa da shi,Aamna tana sani Tace a sa masa sunan Babana Raheel,Yar China tace wlh Sam Haka Kawai ai Baba za muna tunawa yanda yake ce Masa Rahilu hhhh Suka dinga dariya,kowa ya fara kawo suna a junansu matan,Sameera tace ga Aalim ga Affan,Humaira Tace Farhan,Siyama tana gidan itama Tace ga Faisal,Yar China ta doki Siyama a cinya tana Allah ya kiyaye Ubangiji ya yaye min ai akan na sa Faisal gwara Zubairu Kawai,Suna Dariya Yar China Tace na Dauki Aalim din kawai,Allah yasa Aamna ta Haifo mace next Aalim Dina ya samu budurwa nasan zata Yi kyau tun tana Budurwa Kinga idan ta yoki zata Yi katon Nonuwa ko ba komai Dan Aalim Dina ya samu na tabawa,Suka kece da dariya,Humaira tace wallahi Allah ya shiryeki,Yar China tana Dariya tace Ni dai kuyi sauri ku haifo wasu matan sabo da Aalim Dina ya zaba ya darje ciki,ko wasan bayan murfin kofa sukeyi ai kunga ya dinga rage zafi,Suna ta dariya Yar China tace Aamna sai ki dinga yiwa Yar budurwar Taki fada idan kin haifowa Aalim Dina da Allah idan shine a dinga San Masa Yana dumbula,Suna ta dariya Aamna tace Allah ya shiryeki bazan yarda da Kwarton danki ba,Nafeesat tace Ni dai ga Nawa shima Yana jira,Sameera me mace tace tace ku karata tawa ta samo bare,Hafsat ma tace wlh bare Aamna kije da yaranki,Humaira tace Ni dai bance komai ba,Yar China tace dan Allah Humaira ko ke ko Aamna Ina yiwa Aalim riko sabo da jinin larabawa zai dace da fara shima kunga gashi fari ko Yaya? Aamna tace ke da Zaki koya Masa kwartanci uban wa zai Baki yarsa,Yar China ta gyara rigarta zata bashi nono tace yaro fara Dana Mamanka Ana maka gorin Nono,Yar China harda Dora Hannun Dan Jariri a dayan Nonon Dayan Kuma Yana Sha tace ja Kaya kafin Ubanka yazo shima duk zanji daku,Su Aamna suna ta uban dariya,Humaira tace Yau fa akayi suna Yar China Amma kike Neman Miji? Yar China harda turo Dan karamin bakinta tace to Mene Ni ba kazama ba wallahi Indai da sama sama ne yazo,karku ce wani waye wannan madarar jaririn akwai ta ubansa a ciki Yara ku zauna can,ai mu ba a barin mu a baya,tsafta iya tsafta yarinya Bai San Sanda zai Sha ba ma ta furta tana dukan Cinyar Aamna,gaba Daya Yar China ta Raina su babu wani Babba a ciki. Sai da ya Gama Sha ta mikawa Siyama Dan Tace rike shi na dawo Anya Yaron Nan ba idona kanana ya gado ba kuwa? Aamna tace a'a wallahi idon Tawaga ne haskenki yayi Kawai duk shima Tawaga ba Baki bane Amma kinfi shi haske kalleki Kal fa Yar China Nima kin fini haske sosai sai dai kiyi haske Daya da Ahmad dina,Yar China taji Dadi an yabeta tace to Idonsa ne yaki budewa sosai har yanzu sai dai ya kyallo shi ya rufe haba yaro Kamar munafuki,Humaira harda rike ciki sabo da dariya,Yar China tayi kitchen Ana wani rausaya harda Murguda Kunkumi ita ta ciko tayi dam,Aamna Tace Tawaga Yana hutawa mutuniyata,Yar China Tace wlh sai a aza room( Other Room) ma inji Shugaban kasa,Hafsat Tace ai yayi gaskiya Women belong to the kitchen and ze Aza (other room). Sai dare su Aamna Suka kyale Yar China da Iyalle,Iyalle ta tasa Yar China gaba tana Mata fada Kar ta sake ko ta daina jini ta Bawa Tawaga kanta zai Mata wani cikin da wuri,Yar China tana shirya Aalim dinta tace to Iyalle bazan yarda ba,karki damu shi bashi da wannan zalamar ma,Iyalle ta harari Yar China Tace makaryaciyar banza Naga kwananki biyu da Haihuwa da idona na ganku a kitchen Kuna wannan jarabar tsotsar bakin naku Dan Ubanki Wai Uwar me kuke ji ne wannan wacce masifa ce bakin ma baza a barshi ba,Ni na taba ganin wannan jaraba Yar China ki raba kanki da wannan halin maitar,Yar China tace to Wai ke Iyalle Ina ruwanki? Ai sa Ido ne ya kaiki kallar mu a kitchen,aikin Reno fa da kula Dani kika Zo Taya Zaki hanani kula da Mijina,Ni wallahi baza ki Rabani da Mijina ba Yar China ta fashe da kuka,Iyalle ta saki Baki tana kallon ikon Allah,Yar China tace ai dama tunda akazo bikina Naga kinki Yi min Nasiha nasan da wata a kasa a ranki,gashi Nan Zaki ce Kar na kulashi,mu ai ba tsofaffi bane irinku yanzu Kai ya waye,da Ilimi ake Aiki,bazai samu abinda yake so ba Ina jinin biki shine Zaki ce Dan kiss dinma na Hana bawan Allah, bariki kike so yaje ya dinga cakumar Yaran mutane ya dakko min cuta Ina zaune gandandan akan na Haihu Allah bazai yuwu ba. Iyalle ce ta dauki Robar ruwa tare da bin Yar China da gudu zata kwada mata tana Dan Ubanki daga Miki fada Zaki ce Zan rabaki da mijinki ki bashi abinda yafi jikinki ma Dan Ubanki ki bashi har duwawunki ma,bayan gaba ki bashi har baya ma Dan ubanki,marar kunya fitsararriya,Yar China tana Dariya tace Iyalleta Sorry Kinga dai jego nakeyi karki jawo wajen da aka min Dinki ya sake kecewa Mana Haba,Iyalle jaririn ta dauka ta karasa shirya shi tana cewa Zaki ci Ubanki da son Miji wallahi idan kika Yi wani cikin kafin Arba'in kiyi kuka da kanki,Yar China ta dafa kafadun Iyalle tana Dariya tace Iyalleta Tawaga hankali ne da shi fa,Wani Namiji ne yake da hankali akan wannan abin? Ina yaga hankali Zaki ga hankali marar kunya Jeki,Allah yaji Kan mahaifinki ai laifinsa ne tunda aka haife ki nace a samu wanzami ya cire Miki Beli Amma yace Sam yanzu an daina Yayin hakan cutarwa ne ai gashi Nan Baki da kunya kin koma Harija. Yar China ta dinga dariya,Iyalle Tace ai Dole kiyi Dariya tunda kika Haihu kika sake sabon salon daukan wanka na Jan Hankalin me gida,kullum ki dinga Shiga ta rashin mutunci kina kwarkwasa da karairaya a gabansa Ina kallon abinda kike Masa,kici kwalliya ki Sha turare wallahi Zaki Yi Dana sani,Dan masifa kina jegon ma baza ki huta ba,kin makalewa Miji Haka kika ga anayi,Idan ya shigo kika bishi sama sai ki shafe kusan awa biyar Baki sakko ba uban me kukeyi a saman da jego? Yaron Nan kullum Ina jiyo kukansa idan kika tafi dashi tsakar dare zai ta kuka ba'a lallashinsa,Yar China tace to mutum bazaiyi bacci ba sai mu zauna lallashinsa idan ya gaji ya daina Ni bazan dauki wannan iskancin na jariri ba ace sai dare zai tsiri kuka uban me aka Masa ai wlh sai dai in ki dinga kwana da shi amma mu dai cikin dare Indai na bashi nono baiyi Shuru ba baccinmu zamuyi. Iyalle ta saki Baki tare da furta Haka kika ga anayi Dan Ubanki? Ke Haka aka Miki? Baki da Hankali Sadiya amma a Haka kike cewa kina son danki Wai?Yar China dai shuru tayi ta shiga kitchen ta hadowa Tawaga Abincinsa ta haura sama ta Ajiye sannan ta koma bedroom dinta ta gasa jikinta sosai yanda Iyalle ta koya Mata sannan tayi wanka da Sabulun me kamshi ta fito ta ci gayu cikin wata sabuwar atamfa super wacce Tawaga ya dinka Mata cikin kayan suna Blue and White,sun Mata mugun kyau Riga da skert,gashi ta Sha uban lalle me kyau,gashin Nan yaji Gyara a dakin Iyalle ta sameta tana shafa turaruka Baki Iyalle ta tabe tana cewa aikin banza Yaran zamani Baku San ciwon kanku ba ga danki Nan yayi bacci, Karbar Yaron Yar China tayi yasha kayan baccinsa masi kyau farare dama wanka aka Masa Yana ta zuba kamshi,Iyalle Tace sai da safe,Yar China Tace Allah tashe mu lafiya Naman suna fa da aka fara soyawa Yana kitchen idan Zaki ci,Iyalle tace na eba ma a plate kizo ki hada min shayi me kauri da breadi na naci na koshi,Yar China tasan Iyalle da son shayi, Yaron ta Saba a kafada ba tare data wani tallafe shi ba Jin ya zauna daram a Haka ta bi steps sai ga Tawaga ya dawo suna magana da Iyalle tana tsokanarsa dake itama ta Zama kakarsa. Da sauri ya karasa ya cafke jaririnsa Yana cewa Baby Ganganci ne fa wannan Yana binta da mayen Kallonsa yace kinyi kyau Yar China ta Mika Masa Hannu Suka rike Hannun juna tace gani Nan zuwa yanzu Bari na sallami Iyalle,okay ya furta ya haura sama da jaririn nasu,Sai da Yar China ta Gama sallamar Iyalle sannan ta kashe kayan wuta tare da haurawa sama,tana shiga lokacin ya fito a wanka Yana goge jikinsa da towel,Yar China ta karba tare da karasa goge Masa jikin,Lotion ta shafa Masa sama sama sannan Tace kayi Sallar Isha ai? Yace ae da su Ahmad Mukayi ma,Yanzu sai abinci? Yana murmushi yace kadan Zan iya ci Aamna ta Riga da ta shirya Mana abinci,Yar China hade Rai tayi tace Amma ai sai ka fada min tun wuri Kar na sa Hafsat tayi girki,itafa tayi ta kawo sabo da Kai,to tunda Hafsat ce ta Yi ai ba laifi idan banci ba,Amma idan naki ne kin San ban Isa naki ci ba,Murmushi tayi Tace kazo da magana,yanzu kayi magana ta kirki My Man Bari na kaiwa masu Aiki yanzu zasu cinye,Abincin ta sauka da shi ta Basu tana dawowa ya jawota jikinsa Yana sinsinar Kamshinta yace Anya Zan iya Kiran Arba'in Kuwa? Yau sati Daya banyi komai ba gaskiya Ina Shan wahala,Amma ai Ina gamsar da Kai ko ba ta wannan hanyar ba,Yeah ya furta Yana zuge Mata zip din riga. Jibson Kuwa Sameera tana bawa Jaririya Nono kasa hakura yayi jaririya tayi wayo sosai tana Shan Daya ta rike Daya Jibson ya cire Hannun jaririyar ya sa nasa a Kai Yana cewa duk ke kadai sabo da sangarta da Rashin tausayin Mahaifi kina Sha ma baza ki hakura da Daya ba sabo da son kai Anya wannan ba hadamar Baban Brown ta kwaso ba kuwa,Dariya Suka dinga Yi har Sameera tace Dan anace kenan,Yarinyar ya kwace yace Kar cikinta yayi Kato ya isheta haka,da Kansa ya shiryata sabo da an Mata wanka,har Pampers shi ya sa Mata tare da kwantar da ita a bed dinta sannan Sameera tayi Shirin bacci itama Suka kwanta,Jibson Yana Wasa da gashinta yace Ina tausayawa Tawaga kafin matarsa tayi Arba'in ba karamin wuya ake Sha ba,Sameera Tace to Kai ai baka jira Arba'in ba 2weeks fa Kawai ka dawo Aiki,To ai 2weeks a wajena yafi shekara ma,rashinki ai masifa ne a gareni cewar Jibson Yana lalubeta. Bash da Hafsat dinsa Kuwa kallon wani film sukeyi a Palo daga Nan suka fada lobayya,a Nan palon Suka rakashe abinsu,yayinda Mashkoor me kwasar bacci a jikin Nafeesat dinsa yau wacce Rana Ana bacci da wuri sai Asuba zai gwangwaje,Brown Kuwa yau fada sukayi da gimbiyar tasa shi yasa Suka kwanta kwanciyar Kai da kafa,shi ya juya Kansa can ita ta sa kanta saitin kafarsa ba mutunci,Cikin dare Bai ma San sun koma sun manne da juna ba,Yana farkawa Yaja Tsaki tare gyara kwanciyarta ya koma yanda suke a farko Kai da kafa,Itama Humaira Haka ta sake Matsawa can gefe Amma kafin Asuba sun dawo sun makale juna,Brown Yana farkawa Karo na biyu yace mayya kin dawo kin manne min ai shike Nan sai kiyi ta kwanciya,Humaira tace gaka Nan bakin Maye Ni da Kai waye yazo wajen wani kowa ya matsa Wajensa mana,to daga min kirji na tashi,sai lokacin taga Ashe ma a saman kirjinsa ta kwanta,da sauri ta matsa ya tashi ya wuce Toilet da Niyyar Alwala ya wuce masallaci. Oga kwata kwata King ba Bata lokacin yau da wuri aka Yi harkar sun gwangwaje abinsu,sai Asuba Suka Yi wanka sosai tare da Sallah,Fu'ad Yana ta baccinsa Aamna ta haura saman bed ta kwanta a jikin mijinta tana shafa Sajensa da gemunsa tana son yin bacci tace yaushe zamu tafi Lagos din ne kaga fa Mufeeda ta Haihu jibi suna ya kamata mu je,Ahmad yace hmm ni wanne suna Kuma? Ki Bari zamuje wani meeting sai na tafi dake,Ni da Tawaga zamuje sai mu tafi daku ku biyu ma Amma sai Nan da 2weeks,Aamna zata Yi magana yace bana son jayayya fa,ai Allah ya kaimu zance Kawai, Alright ya furta Yana shafa gadon Bayanta suka koma baccinsu. Bayan Yar China tayi wata biyu da Haihuwa Tawaga ya sama musu Admission shi da ita Amma shi dama NCE ne da shi Degree ya tafi Yi,ita Kuwa Yar China fresh level one ta samu Health education, Part-time sukeyi a private University,Shima Jibson da Bash sun koma schl,sai Hafsat da Humaira,Nafeesat,Aamna,da Sameera duk suna da Degree Basu da matsala Kuma ba Aiki zasu Yi ba,Yar China Suna karatunsu sosai ba ruwanta. Aamna Bata samu ciki ba sai da ta yaye danta da watanni sannan ta samu wani,Ahmad sai murna yake yi,Sai da cikinta ya tsufa sannan sauran ma Suka samu ciki Banda Yar China again,Wannan lokacin Aamna mace ta Haifo zukekiya,Yar China Tace Alhmdllh Aalim Dina ya samu tasa, Siyama Kuwa kafin ma ta yaye ta samu ciki sai gashi ta Haifi Namiji itama,Sai daga baya duk tazarar ba Nisa su Nafeesat Suka Haihu suma,Sameera Namiji itama,Humaira ma Haka,Nafeesat mace ce tayiwa Danta kanwa,Hafsat Mace itama ta sake Haifa. Sai bayan ma yaransu sun shekara sannan Yar China ta samu ciki ita Sai da Danta yayi Shekara Uku sannan ta samu wani cikin sabo da Allura tayi ta planning,Suma sauran matan wannan karon duk family planning sukayi,Ahmad da kyar ya Amince sai da Aamna ta dinga kuka kullum sannan ya hakura. Gaf da zasu Gama school Yar China ta sake Haifo Namiji kyakyawa,Wannan lokacin Yar China an sake Zama Babba an Kara nutsuwa sai dai surutu da abin Dariya sai Wanda ya karu ma,ga shegen Iyayi da wani tashe da take ji,Sunan Yar Aamna Suhailat sai Yar China ta sawa nata Suhail Wai ko za a samu akasi Suhailat taki son Aalim sai ta so Suhail shi ya kwashi dadin cewar Yar China,Ahmad da Aamna ta bashi labarin target din Yar China ya dinga dariya yace wlh bashi Kuwa zanyi Ina bayan Yar China nima. Sai da Yar China tayi Arba'in sannan Tawaga ya Mata kyautar motarta sabuwa kantamemiya kasancewar karambanin Yar China yasa ta koyi mota wajen su Aamna,Sai Bayan sun nutsu suka sauke farali daga Nan Kuma sai yawan zuwa Umrah,suna zamansu lafiya da yaransu abin sai Wanda ya gani,Iyalle ma an kaita Aikin hajji da kaninta,Yayin da Aamna take waya da Yan uwanta na wajen Uwa da uba sannan sukan ziyarci juna jefi jefi,Abin gwanin birgewa sai Wanda ya gani,Daddy sai Hutu Kawai yakeyi bashi da matsala,Mummy ma haka. Yau Ranar auren Aamna da Ahmad ne ya sake zagayowa,Kamar yanda suka Saba shirya Dan kwarya kwaryan party a hadadden gidansu Wanda gidan duk kusan shekara sai an canja Masa fasali da furniture. Iya su ya su ba Wanda aka gayyata daga mazan sai matansu da Yan Yara su dagwai dagwai Yara Yan gayu da su,Dukkansu kowa ka gani ya dauki uban wanka na kece raini,shigar Ahmad da Aamna ta musamman ce wata maroon and white suit ya Sha gwanin sha'awa,Aamna ma kayanta wata gown white an nada Mata gogoro da maroon takalmi da pose dinta maroon gaba Daya,Tasha makeup ta kece raini,Ka rantse yau aka Daura Auren,anyi wani decoration a garden kusa da pool dinsu,gwanin birgewa,Ga kida Yana tashi sosai,Su cake dankareren gaske,Su Tawaga da matayensu an kashe wanka cikin shaddoji na kece raini,matan wasu da lace wasu da material,Siyama da mijinta itama sun zo,Yar China tana ta pics Haka ga me daukan pics daban na musamman,girki ba irin Wanda ba a shirya ba,kowa ka gani cikin nishadi yake. Bash ne ya fara magana tare da Bude taro da Addua,Ahmad King ya karba speaker din ya fara magana kamar Haka Yau ce ranar data fi kowacce Rana muhimmanci a wajena,ranar da Mummy ta gano min matar aurena,ranar da aka min auren dole,lokacin da muke tsaka da cin duniya,Muna tunanin cutata akayi wanda Ashe gata aka min ban sani ba,Munyi fada,munyi dambe da matata Ina ganin tana takura min,har ta gaji ta sare ta bar min gidana,Ina murna ta tafi amma Kuma na sake haduwa da ita a hanya naji Ina sonta duk zaman da mukayi ban so ta ba sai Dana ganta a kwararo Allah me iko Kuma lokacin na fada kogin sonta,Ina tsoronta ga sonta zai kashe Ni,Lokacin Ina King Dina,Sabo da ita na canja shiga,na koma shiga ta Kamala,na haura katanga sabo da ita,na siyar da citta sabo da ita,nayi wanki sabo da ita,Ni king nayi kuka dalilinta sannan Kuma karshe ta Zama silar shiryuwata na koma mutumin kwarai Wanda sanadin hakan ya jawo duk abokaina Suma Allah yasa Suka shiryu duk da cewa Su Hatsari silarsa tafi karfi,Dariya sukayi gaba daya. Yace Yan Uwana, abokaina, abokai na Amana,Ina ji da ku Ina kaunarku, sannan Ina addua Allah ya sake hada kanmu ya Bamu lafiya da tsawon rai,Ina tabbatarwa wata abotar tafi Yan uwantaka,Suna tafi Suka ce Ana tare Our King,Aamna ta kwace speaker Tace My King dai,Suka ce no our king Aamna ta dage ita Tace My King dai,Nan Suka zauna aka dinga ciye ciye da shaye shayen lemuka Wanda suna ta tuna rayuwarsu ta baya suna labarin wani ayi Dariya wani a tausaya,sosai abin nasu ya kayatar,su Mummy ma ta waya Suka musu murna. Lemo Suka tsiyaya a glass cup kowa ya daga tare da furta cheers. ALHMDLLH NAN NA KAWO KARSHEN DUNIYATA AAMNA. INA MATUKAR GODIYA GAREKU FANS MUSAMMAN MASU SHARHI BASA GAJIYA MUSAMMAN UMMI DEEJAT NA GODE DA ADDUARKU FANS ALLAH YA BAR ZUMUNCI . Saura idan Allah ya kaimu Kuma novel kyauta Next. AsmaBaffa