🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥 🐦‍🔥🪐 *MASARAUTA*🪐🐦‍🔥 🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Dr Yasmeen Ahmad😚 Autar alheri ✍️ Al'ajabi, hummm Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI. ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃 Book 1 Page 11 & 12 "Shidai yana isa parlor yafara cire kayan jikinshi domin hakan al'adarshi take kafin yaƙaraso bedroom kaya kaɗan ne zasu rage ajikinshi sedai duk wannan halayyar tashi baya cire boxes ɗinshi acikin bedroom harseya shiga wanka domin yarima sameer mutunne me matuƙar kunya dajin nauyi yanzu haka ko bindiga zaki ɗora akanshi bazecemiki ga yadda asalin halittarshi takeba domin bedamu dayasan yatakeba shidai muradi yayi wanka yawanke wurin kawai sabida atunaninshi kallon tsoraicinshi rashin kunyane...hakan yaƙarasa bedroom ɗin yana shiga kuwa yafaɗa wanka sabida duk agajiye yakejin kanshi....sukuwa su ameer a parlor suka zaune suna tattauna yadda tafiyarsu zata kasance agobe. MAYE BALWA danejo tunranarda innawuro tasha duka bata karabi takanta ba, sedai takan sakata aikin wahala wanda yafi ƙarfinta hakama bata bata'abincin daze wadaceta, kuma bata bari takwanta dawuri se salamainin dare, amma dai bata ƙara gigin dukantaba,,,sekuma abinda kebata mamaki akan danejon, bewuce yadda take ganin duk aikin data sakata bazata wuce minti ashirin ba ko talatin takama, wanda ko babbar mace ce zatayishi seta ɓata fiyeda awa biyar bata gamashiba sedai kuma dudda wannan mamakin datakeyi besa innawuro ta saurarawa danejo ba. Tafe take ita kaɗai acikin fadamar malam baffa tadawo daga kaiwa hamma Ishaq madarar data tatso mishi, tahango wasu samari tafe maƙotan rugarsu kuma sune suke shiga lambun baffa suna mishi sata, aiko tatunkaresu wanda su ɗinma ita suka tunkaro kasan cewar ta taɓa kamasu suna satar amma bata gayawa kowaba shiyasa yanzu sukeso suyi mata gargaɗi, shikuwa jauro sonta ne yakeyi amma dalalaci bawai danya auretaba, shiyasa yakeso yahaɗu da Ita a irin wannan wuraren dabakowa. Suna zuwa suka riski juna ahanya. "Hai danejo dama nemanki mukeyi aradun Allah kika sake kika gayawa wani kinganmu a lambunku semun karyaki a rugarnan, cewar sani cikin gargaɗi..sukuwa saura duka ido suka zuba mata suna kallon zallar baiwar kyau da tsarin halittar da Allah yayi mata. Wani banzan kallo danejo tayi musu kana tace "ai wlh baku isa kuyi mana satabq kuci bilis dama aranar nabarkune har muhadu domin bawai barinku zanyi kuci gaba da mana sataba, kuma dena tunanin wani zan gayawa dakaina zanyi muku hukunci Dede da laifinku yawwa. Taƙarasa zancen tana murguɗa baki cikin tsiwa darashin tsoro....aiko kamar jira sukeyi tayi magana ɗaya daga cikin samarin ya ɗauke ta tareda toshe mata baki suka yanki wani lungu da ita, tanata dukan bayanshi da wutsil niya da kafafunta amma yaƙi sauketa seda sukayi nisa sosai inda babu ko alamun mutun kana suka ajiyeta ita bayan sun kewayeta dukansu suna murmushi. Ɗagowa tayi takallesu babu alamun tsoro ko ɗar aranta wani irin kallo take jifansu dashi irin na ina tausaya muku ɗinnan...suko se zabga murmushi sukeyi kafin ɗaya daga cikinsu yace "badai muzakiyiwa rashin kunyaba humm aiko sekin gane bakida wayo aradu, nidamacan haushiki nakeji agarinnan kawai ina ɗaga miki ƙafa ne amma yau tunda kika shigo gonarmu sekin yabawa aya zaƙinta, dan Allah ku tuɓe mana ita wai mikuke jiranee? Yaƙarasa zancen cikin bada umurni...cikin sauri jauro yace "amma giɗaɗo kabari nafarayi domin nine nakesonta tunda jimawa aradu kaga idan nayi sekuyi kuma. "Shikenan naji kayi da sauri kafin wani yazo wurinnan. Aiko sunajin hakan biyu sukayi kanta domin su aiwatarda umurnin giɗaɗo na cire mata kaya kamar yadda yace, sedai basukaiga jikintaba wata irin iskar guguwa ta turnuƙe awurin wadda basusan mafarintaba kawai dai sunji tabazar dasu domin seda tayi sama dasu kana tawatsar can nesa, hakan yasa suka saki ihu atare jin sun garu dawani dutse...sekuma ta ɗauke kamar bata wanzu awurinba, hakan yabawa su giɗaɗo hango sani da gainako waƴanda guguwar tawatsar,,,,juyawa sukayi suna kallon danejo inda suka barta zaune sedai me, azaune suka ganta ko yanzu amma akan wata arniyar kujera me masifar ɗaukar hankali da sheƙi anyi mata wani matsiyacin ado na alfarma duk jikinta gwal ne da zinari ke tastas,niya sukeyi, itako se wani malalacin murmushi take jifansu dashi, taɗora ƙafa ɗaya akan ɗaya.....ido kusa waro cikin mugun tashin hankali suna nunata da yatsa, kafin susamu zarafin yin magana idonsu yasauka akan kujerar datake zaune da kyau, ashe ba asalin kujera bace wani ƙaton shirgegen macijine yanaɗe tamkar kujera me hawa,hawa, danejo tazauna daga kanshi kuma yafasashi asama dashirin zara, yadda yafito tamkar kan kujerar sarki amma yana buɗar baki irinna baƙin kumurci, sekuma wasu biyu wanda basukai girmanshiba sun zagaye wurin kan nashi sunyiwa kan kujerar wani irin ado me ɗaukar hankali dajikinsu ta hanyar nannaɗewa adede kan babbansu hakan yaƙarawa kan kujerar girma da ɗaukar hankalin me kallonta tareda fiegitarwa. Daga ƙasanta kuwa wasu irin halittu ne wanda bazaka kirasu namun dawa ba kuma kai baka isa kace musu mutaneba dubada yanayin halittarsu, gasu tiƙa tiƙa tamkar samudawa sunzagaye kujerar DANEJO tamkar yadda fadawa keyiwa sarki a faɗa, se mazurai sukeyi suna kallonsu giɗaɗo da jauro wanda sukayi mutuwar tsaye tamkar mutun mutumi. Murmushi danejo taƙarasa saki akaro na ba adadi wanda ke masifar ƙara fitoda kyawunta me firgita ɗan Adam domin ba yadda za'ayi kayi ido huɗu da ita baka alaƙantata da aljanaba sabida tsananin kyawunta koda kuwa haɗe da fuska kaganta balle kuma tana jifanka da wannan shi'umin murmushin nata me tafiya da duk wata halitta me rayuwa. "Jauro, tafaɗa cikin sweet voice ɗinta me masifar daɗi tana kallon jauron... firgigit sukayi dukkansu kamar wanda suka suma, aka watsa musu ruwa suka dawo, se suka ƙara sauke idonsu akanta, amma abin mamaki kamar yadda suka ajiye ta zaune hakan take babu waƴannan halittun dasukagani yanzu atareda ita, tana zamanta tana murmushi...ai wani irin zabura sukayi kowanne yacika bujenshi da iska na shirin gudu sedai kuma sunkasa motsa koda ɗan yatsan sune ankafesu wuri ɗaya da shirin gudunsu sakamakon sakawa datayi aranta bataso sugudu shiyasa aka kafe matasu tun kafin tafurta abinda ke zuciyarta, anka cika umurnin zuciyar....murmushin jin daɗi tayi ganin an aiwatarda abinda takeso ta faɗa tun kafin ta faɗa ɗin kana tamiƙe tsaye tareda ɗaure fuskarta tamkar batasan minene dariyaba, kai baka isa kace itace ke doka murmushi ba ayanzu..takowa tayi har inda suke jikin kowannensu se rawa yakeyi gaya sun kasa gaba balle baya kuma ga danejo na tunkarosu aiko suka ɓare baki suka fashe da wani irin kukan ceton rai me wuyar saurara. Cikin daka tsaya tace "kumin shiru mutanen banza mutanan wofi kawai ɓata gari. Aiko sukayi ɗib kamar anyi ruwa an ɗauke. Ganin hakan yasa danejo ƙara haɗe fuska tace "kunsan Allah zan barku ne ayau domin kuhana sauran ɓata gari irinku aiwatarda wannan munanan ɗabi'un acikin rugarnan wato kune sata kuma abin betsaya isa hakanba hadda wiya ƴara fyaɗe ko? Humm to naƙara ganin wata ɓarna makamancin hakan agarinnan kugani aradu koba kubane to kune aruwa domin ku zan hukunta wannan nauyin daga yau yarataya awuyanku kubari ayi ɓarna agarinnan koku hana dabara yarage naku, tana gama faɗar hakan tajuya taɗauki ƴar tsumagiyarta data faɗi tun lokacinda suka kamota...tana juyawa sukaji kamar an sakesu, ai suka zura aguje tamkar zasu tashi sama sabida tsananin gudun dasukeyi na tashin hankali....murmushi kawai danejo tayi kana tanufi gidansu. MASARAUTAR MAHAR Tafe take tana sauri kamar zata kifa tana tafe tana wai wayen bayanta kallo ɗaya zaka mata kaga alamun rashin gaskiya atare da ita, ahakan harta ƙarasa pert ɗin matan sarki kaitsaye tawuce wanda ke yamma da sauran. Hakince tasamu wata kasaitacciyar dattijuwa akan kilisa tareda ciroma mubarak wato abba ciroma, wasu hadimai biyu na ɓare musu ayiba sunaci suna fira dagani kasan ɗa ne da uwarshi dudda kuwa taɗan manyanta amma mulki da sarauta sun hana manyancinta bayyana. Sallama tayi tashigo parlor tareda zubewa aƙasa tana faɗar "Allah yaƙarawa Fulani daraja da nisan kwana gaisheki nakeyi Fulanin memartaba tantabarar masauratar MAHAR. Murmushin fuskar Fulani abu ne ya faɗaɗa, kafin tagirgiza kanta alamar ta amsa kenan. Ganin hakan yasa wannan hadimar juyawa ga babba ciroma tana faɗar "Allah yaƙarawa ciroma girma da daraja ɗan sarki jikan sarki kuma sarki uba ga sarkin wata rana barka da wannan lokacin. Ahankali abba ciroma yace "yawwa barka laraba. Daga hakan yamiƙe yana yiwa mahaifiyar tashi sallama yafice...ita kuwa mayarda hankalinta tayi kan baiwa laraba tana faɗar "laraba Mike tafe dake hakan domin naga alamun akwai magana abakinki. "Hakane ranki yadaɗe a yau ne wannan yaron yashigo masarautar nan wato yarima sameer kuma sun shiga wajen memartaba shida yan uwansa shine nace barana garzayo na sanar muki domin ƙila bakisan da shigiwarshiba Allah yaƙara miki daraja...ɗan shiru Fulani Abu tayi tana nazartar kalaman baiwa laraba kafin tanisa tace "aiko dai nasani domin sun shigo nan shida ƴan uwanshi,, kuma ina ta jan kunnenki laraba akan banason gulma da dakawomin zancen da ban tambekiba amma ƙinƙi kidenako? Tafaɗa cikin tuhuma..dasauri baiwa laraba taduƙarda kanta tana faɗar"tuba nakeyi uwar gijiyata amin aikin gafara. "Humm kawai Fulani abu tace kana tajanyo wata salka dake rataye agefenta ta fidda wata ƴar batta aciki tamiƙawa baiwa laraba, tana faɗar ga wannan kozakiyiwa yara anfani dashi. "Jikina rawa baiwa laraba takarɓa tana zuba godiya kamar zatayiwa Fulani abu sujjada takwashi tarkacenta tabar parlor aranta tanajin daɗin kyautar Fulani abu domin hannunta asake yake itada mebabban ɗaki domin duk sunfi Fulani huraira alkhairi.....itako Fulani abu da kallo tabi baiwa balaraba harta ɓacewa ganinta kafin ta girgiza kanta afili tace"gidan sarauta gidan gulma da munafunci kome hakan ze anfaneta dashi datazo zuwa gayamin oho? gaskiya bayi nada matsala sabida wannan gulmar tasu tayi yawa, tana gama faɗar hakan tamiƙe zuwa turakarta. Washe gari Dashirinsu suka fito dukkansu ukku sunyi kyau matuƙa kamar kasacesu kagudu musamman princes sameer da kyawunshi yakasance nadaban acikin duka family nasu domin kallo ɗaya zaka mishi ka alaƙantashi da Balarabe, kowannesu manyan kaya ne ajikinshi wato dinkin shadda nazamani daga Ameer har Anwar sedai shi gogan ƙananun kaya yasaka kuma duka farere ƙal ga dukkan alamu fari shine kalar dayafiso, daga wandonshi har rigar fararene sedai ahannun rigar kawai yakeda ratsin blue, takalmin shima fari ne hakan yaɗora cap fara wanda ta kwantarda lallausar sumar kanshi kuma tafitarda dan zagayayyen gemunshi nagayu wanda yaƙarawa fuskar tashi haiba tamkar wanda yayi makeup, duƙawa yayi yaɗauki wayoyinshi dake ajiye akan teble kana suka fito daga pert ɗin nashi, aƙasa suka samu mammi tana juye furarda tadamawa abbey, domin mammi komai itakeyin abinta Indai abinda yashafi girkine sam batason aikin hadimai. Suna gama saukowa yazo wurinta tareda rungumeta ya manna mata kiss agoshi. Murmushi kawai tayi tana kallon su Anwar domin su sungaisar da ita tun lokacinda suka shigo pert ɗin kiran princes yafito sutafi. "Ameer harkun fito? "Eh mammi munfito amana addu'a, yafaɗa yana murmushi, "to Allah yakaiku lafiya kuma yadawo daku lafiya amma kafin kutafi karku manta kushiga gadinfa domin kusan dai al'adar masarautar ku inbaso kukeyi asamu matsala ba wadda bana fata ayarana. "In sha Allah zamu shiga yanzu mammi kafin mutafi, cwar Anwar. "Yawwa Allah yayi muku albarka, kai kuwa Muhammad da ƙananun kaya zakaje? Dubi ƴan uwanka mana kowanne da manyan kaya gwanin sha'awa amma kai kasaka wannan na jajayen mutane. "Mammi zansha fura, yafaɗa kamar bayaso sabida yakauda zancenda take mishi batareda yace tama komaiba akan zancen domin yasan yanzu setace seya sauyasu kumashi bayason manyan kaya se dole. Ita kuwa sarai taganoshi hakan yasa tayi murmushi kawai tana zuba mishi furar a cup. "Kuma zakusha? "Dasauri suka girgiza kai suna murmushi domin dukkansu bacimarsu bace. Murmushi kawai tayi dama tasan bazasu shaba kawai faɗa ne tunda tasan abinda sukeso da wanda basaso...shikuwa Anan tsaye yaɗan sha kana ya ajiye cup ɗin, addu'a sosai mammi tamusu kafin suka fice daga pert ɗin, suka nufi gadin kamar yadda mammi ta umur cesu, princes na tsaki yana ƙarawa dominshi Allah yagani yatsani wannan al'adun na masarautar nan abu tamƙar tsafi..suna shiga babban get ɗin shiga gadin ɗin, wani ƙaton Shuri dage wurin yasaki algaita wadda ke sheda shigowar ahalin sarki habibullah cikin garin ɗin.cikin hanzari yarima sameer yayi saurin toshe kunnenshi jin kamar dodon kunnen nashi zefi sabida ƙara. atake tsuntsayen dake kan Shurin suka tashi sama suna shawagi.....! Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp. Autar alheri ✍️ 🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥 🐦‍🔥🪐 *MASARAUTA*🪐🐦‍🔥 🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Dr Yasmeen Ahmad😚 Autar alheri ✍️ Al'ajabi, hummm Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI. ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃 Book 1 Page 13 & 14 "Suna shawagi..sukuwa takawa suka shigayi sunabin dabbobin dake cigin wurin da kallo ga tsuntsaye masu kyau da ɗaukar hankalin me kallonsu, sunyi tafiya meɗan nisa kafin suƙa isa tsakiyar gadin ɗin wurin wani ƙaton bishiyar gamji suna tunkaroshi yafarayi sama yana buɗewa kamar yadda bishiyar lema keyi wato fruat, domin dai duk wanda yasan bishiyar gamji yasan cewar katuwar bishiya takeyi kuma ganyenta ma manyane, konace kunnenta suna zubowane sumata runfa harse sunrufe kasan bishiyar wanda hakanne kebawa duk wanda besaba ganintaba tsoro ko wanda baya tu mamali da ita. Tofa ita wannan dake cikin gaɗin abinda yasa take buɗewa kamar abinda wani ke sarrafawa shine...Wato aƙa'idar wannan masarautar duk wanda zeyi tafiyar daze fita daga garin MAHAR doline seya shigo gadin yashiga cikin wannan bishiyar ta gamji tukunnah yafito yayi tafiyarshi, idan ba hakanba kuwa daƙyar kadawo lafiya qalau idan katafi, shikuwa wannan shurin aduk lokacinda wani jinin sarautar zeshigo cikin gadin ɗin to seya yimasa maraba tahanyar sakin algaita, inkuwa barene dayashigo get ɗin ze ƙara girma ya buɗe ta yadda ze ƙara komawa abin tsoro kana daga ƙarshe ya haɗiye ka tamkar anshafeka ajikinshi sa'annan yakoma mazaunin shi, kuma duk wanda yayiwa hakan tofa idan har wani daga cikin masauratar yasani ko aka sanarda sarki tun kafin ma sarki Habibullah tun magabatanshi to tabbas se ankai ruwa rana tukkunna shirunnan ze aminta yafoto dakai kuma daga lokacinda kafito bubaka babu komayin lafiya harka komawa mahaliccinka, wannan dalilin ne yasa basa taɓa bari baƙuwar fuska tashiga gadin ɗinsu koda kuwa matansune Indai bajinin sarautar MAHAR bane sedai sushiga tareda kai domin idan tareda wani daga cikin jinin sarautar kashiga ba abinda zesameka harka fito. Wannan kenan, shine kaɗan daga cikin tarihin gadin ɗin gidan sarautar MAHAR. Kafin su ƙarasa tuni gamji yabuɗe ganyenshi sunyi sama tamkar yayi lema, suna ƙarasawa ciki yasauko da gayen yarufesu rub kamar babusu awurin kana yarinƙa matsawa harya haɗe da jikinsu, kafin kuma yabuɗe kamar yadda yayi aɗazu yayi musu lema, sekawai suka fito, shikuwa yakoma yadda yake,,,Hakan suka fito cikin gadin ɗin suka nufi harabar inda motocinsu suke, suna zuwa aka buɗe musu wata katuwar mota mekamada jirgin ƙasa fadawa nata kakkaresu har suka shiga ciki su duka ukkun kana aka rufe motar, dasauri wasu dogarai suka shiga wasu motoci biyu, biyu kuwa na excout ɗinshi ne dayazo dasu daga US Hakan yasa motarsu takasance a tsakiya, ta dogarawa agabanta kana ta excout ce agaba baki ɗaya, hakama bayan tadogarawa kebin tasu seta excout takasance abaya, ahakan suka harba akan kwalta sukabar masauratar. Acan gidan kuwa pert ɗin memartaba jekadiya ce tashigo tana jerawa memartaba kayan abinci shi a ƙaramin parlor shi,,,shikuwa yana cikin turaka shida me babba ɗaki yana ƙimtsawa kafin yafito cin abinci.....ita kuwa jekadiya tanagamawa tafice bayan tasanar Mishi tagama, aiko tana fita sega wata mata ta bayyana awurin tayi wata irin shiga wadda duk tarufe mata jiki ko ina, hannayenta kawai zaka iya gani wanda tafidda wani abin ɗaure a ƙyalle tana zubawa cikin abincin memartaba, cikin sauri sauri take komai sedai ayadda jikinta keyi da yanayin Fatar hannunta zaka gane cewar dattijuwa ce bayarinya ba, tana gama zubawa taɓace ɓat kamar bata wanzu awurinba. ɗagawarta keda wuya suka fito parlor suka zauna me babba ɗaki tace "takawa mizan zubama ne? Ɗan shiru yayi kamar bazeyi magana kusan minti biyar kana yabuɗe baki cikin kamalarshi yace "banajin cin komai me babban ɗaki kawai ruwan bunu nakeso kuma wanda kika dafa da hanunki sekuma fura kitura gum gimbiya khadija akarɓomin. "To ranka yadaɗe yadda kace Hakan za'ayi tafaɗa tareda Miƙewa tsaye dudda kasan cewar ta manyanta amma Hakan besa tagazawa dawai niya da mijintaba...tana fita pert ɗinta takoma inda ta haɗa Mishi ruwan bunun kamar yadda yabuƙata dakayan kamshi masu tadawa mutum gwaɗayi wanda ko beyi niyyar shaba zeji sha'awar shanshi...hadima suwaiba tasaka aka kira mata kana taturata gun gimbiya khadija wato matar abbey muneer mahaifiyar yarima sameer, akan tanasar da Ita saƙon memartaba, aiko ciki ƙanƙanin lokaci mammi tahaɗawa surukin nata furar tabawa hadima suwaiba batareda kowacce irin fargaba ba domin da watace me babban ɗaki taturo to ba abinda zesa tabada saƙon sedai takaishi da kanta sabida tasan kafa kaɗan ake jira asamu damar illata wani acikin gidan...hadima suwaiba kuwa itace tariƙawa me babba ɗaki kayan har perlor memartaba kana tayi musu sallama tatafi bayan ta ajiye musu kayan, amin tacciyar hadima kenen me siffar salihan bayin Allah....shikuwa memartaba cikin Farin ciki yasha furarshi seda yaƙoshi bayan ya idar sukadan yi fira shida me babba ɗaki kafin yatafi masallaci sallar azahar seda yadawone yasha ruwan bununshi hankali kwance.. Azabure tamike tsaye tana faɗar "Wlh bazeyuba miyasa zakamin hakan wai wannan tsohon mikake nufi danine? ai Wlh bazata saɓuba doline kaci wannan maganin domin tahakanne kawai zakayi murabus kuma kabawa yarona sarautar bawai kaɗora wancan ɗan iskan jikan nakaba, ina sam Wlh bazeyuba to minene mafita? Tayaya zansamu yaci wannan maganin? Tayiwa kanta wannan tambayar...kamar daga sama taji wata murya marar daɗin sauraro ana faɗar "aikuwa idan so dubu zaki zubashi to bazeciba indai da hanunki kika zuba domin mutanen masarautar nan bazu barshi yaciba, sedai kisaka wani yazuba Miki domin samun cikar burinki, ana gama faɗar Hakan bedroom ɗin nata yayi tsit kamar ba'ananne ake wannan hargaginba...ajiyar zuciya tasauke akaro na ba adadi kafin tace "aikuwa doline nasaka azuba maishi Wlh, daga hakan tashige wani lungu dake cikin bedroom ɗinta. Humm wa'iyazu billah antsufa shekaru sunja memakon akoma ga Allah anemi yardarshi a'a se neman duniya kuma akeyi kamar baza'a mutu ba, Allah yasa mufi ƙarfin zukatanmu. Taraba State Tunda suka isa taraba suke yawo acikin jalingo ababban company da Abbanshi ke gini sunyi yawo sosai domin company nada girma sosai seda sukaga komai yayi Dede inda beyiba suka bada umurnin gyarawa su Anwar domin shidai yarima sameer biye kawai yake dasu, bayan sun kammala suka nufi wani tsadadden hotel suka sauka da zimmar gobe sukai ziyara makarantinnen da abbana nashi yayi na isilamiyya dana boko..Hakan suka kwana gajiye washe gari da sassafe suka nufi makarantinnen, sukayi musu zuwan bazata sedai ayadda suka samu komai lpy qalau ana koyarwa yadda yadace ya tabbar musu da Cewar malaman na aikinsu, kuma sunyi musu tarba me kyau sam basuji rashin daɗiba akan bazatan dasuka musu, seda suka ɗanyi zagaye makarantu da dama kana ɗaya daga cikin yaran abbanshi dakenan taraba yaƙaraso wurinsu tareda russunawa yace...! Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp. Autar alheri ✍️ 🪐🐦‍🔥🪐 *AL' AJABI*🪐🐦‍🔥🪐 🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Dr Yasmeen Ahmad😚 Autar alheri ✍️ Al'ajabi, hummm Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI. ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃 Book 1 Page 15 & 16 "Yace "ranka yadaɗe inada magana please idan ba damuwa. "Okay munajinka Cewar ameer. "Yallaɓai Wlh dama wata makarantace acikin garin Adamawa wadda Alhaji yasiya yo yace duk lokacinda yaranshi sukazo akaisu suga wurin sabida kusan yaza'ayi aikin, shine nace kozakuzo mujecan kuga wurin? Yaƙarasa zancen cikin ladabi agaresu. Kallon princes sameer sukayi atare dominjin amsar daze bada sabida shine kawai ze iya kawo matsala tafiyar, amma se sukaga bece komaiba, dudda hakan basuyi mamaki sabida sunrigada sunsan wayeshi, juyawa Anwar yayi gun wannan matashin kamin yace "shikenan badamuwa amma bazamu samu damar zuwa yanzu ba sedai idan mun ƙara dawowa sabida yanzu daganan gida muka nufa. Dasauri wannan matashin yace "please yallaɓai Dade anduba lamarin domin Wlh mutanen wannan yankin suna matuƙar buƙatar tallafin ilimi acikin rayuwarsu gabaki ɗaya akan duhun jahilci suke rayuwa wannan dalilinnema yasa Alhaji siyan wurin domin kawo musu hasken addini, yaƙarasa zancen cikin alamun riƙo. Ido yarima sameer yaruntse daƙarfi yanajin wani irin zafi aranshi domin aduniya yatsani yaji Cewar wata halitta narayuwar rashin ilimin addini domin koba nazamani dai bazaka rasa abin kusantar uban gijinkaba. Shi kuwa Anwar ajiyar zuciya yasauke tareda buɗe baki zeyi magana kenan yaji ɗaukar cool voice ɗinshi yana faɗar "it's okay we will going to Adamawa state now. Yana gama faɗar Hakan yajuya zuwa motarsu cikin takonshi na ƙasaita wadda kallo ɗaya zakamishi kasan cewar shiɗin jinin sarautane.... murmushi dukkansu sukayi kana suka mara Mishi baya, seda suka shiga motarsu duka kana Ameer yaleƙo tareda baya ɗaya daga cikin hadiman su umurnin anunawa wannan saurayin me suna imam, motar daze shiga sutafi tare tunda shine yasan wurin. Aiko cikin sauri yacika umurnin shi kana sukaja motocinsu sukabar wurin, tareda nufar garin Adamawa state. MAYE BALWA "Danejo danejo wai kina inane? Kikabarni inata famar kiranki sekace wata sa'arki. Innawuro ce keta famar dokawa danejo kira kamar zata tsaga gidan....Ita kuwa danejo tana bayi ne shiyasa bata amsaba har seda tafito domin pappi ɗinta yahanata amsa kira abayi yagaya mata ba kyau Hakan shiyasa koda innawuro zata dafata bazata taɓa amsawaba se lokacinda tafito, to yanzumu hakance takasance, fitowa tayi dabuta ahannunta tana faɗar"na'am ganin Anan innah ina bayine...wani banzan kallo tawatsa mata kafin taja tsaki cikin takaicin yarinyar tace ungo maza jeji hayin barmo ki kaiwa hansai kuma kitsaya tagama ki karɓomin saƙona tukkunna kidawo, tafaɗa tana dungurawa danejo nera ɗari ahannu. Tokawai tace mata kana ta ɗauki ƴar sandarta tafice daga gidan, tafiya takeyi ahankali ita kaɗai tana wasada sandarta kuma aranta tana tunanin pappi ɗinta domin yau kwana biyu kenan bezoba kuma idan yayi wannan kwana biyun jitakeyi kamar shekara biyu ne yayi, amma tasan tunda har yacika kwana biyu yau to tabbas yau zezo ko gobe, Hakan dai take tafoyarta hankali kwance ita kaɗai kuma gashi wurin nada nisa sosai amma ahakan take tafiya batareda tasakawa ranta ganin nisan wurinba domin tabbas datasa Hakan aranta toda anyanke mata tafiyar sedai ahakan ma anayi ana ɗan kusantota da unguwar sabida se anfita rugarsu gabaki ɗaya anwuce ruga har biyu kana akai inda innawuro ta aiketa, kuma tasanda Hakan ammata turata sabida mugunta. Matafiya Tsaye suke acikin babban filin makarantar MAYE BALWA wadda tajima dawatsewa bakowa aciki kuma ba komai na anfani takoma tamkar kango, sunjima suna zagayen makarantar kafin su samu wani wuri daga gefen makarantar suka zauna suna tattaunawa da hakimin garin, bayan suyi magana da wani company gine,gine dake cikin garin Yola, suna jiran ƙarasowarsu domin suɗamƙa kwangilar gyaran makarantar hannunsu..basu jima awurinba manager company yazo, Hakan yake nuna musu tsare tsaren ginin makarantu dasuke dashi a laptop ɗinshi suna dubawa..shikuwa yarima sameer ya lumshe kyawawan idanuwanshi masu launin ruwan madara, yana sauraren bugun zuciyarshi dayakeji tamkar zata tsinke wani irin fargaba da faɗuwar gaba yakeji wanda besan daliliba kuma abin seƙara kusantoshi yakeyi...sukuwa sunacan suna aikinsu hankali kwance domin nema sukeyi suyi sugama subar unguwar domin babu alamun ko sunsan miye hotel balle suyi tunanin samunshi Anan kusa, sesun koma cikin gari tukkunna. Danejo Taje inda innawuro ta aiketa tadawo tana tafe tana tana tsilla sandarta sama gaya duk tazubo sumar kanta tarufe mata rabin fuska da ƙirjinta ɗaya har zuwa cibiyarta sabida tsawon sumar dakuma tsantsinta, tafiya takeyi ita kaɗai awurin domin kamar jeji hakan wurin yake sabida anfita daga cikin gari kuma ba'a ƙarasa cikin rugar Fulanin dake maƙwabtaka fawirinba,tayi tafiya menisa kafin tazo Dede inda motocinsu suke, da mamaki take kallon motocin bawai ɗan bata taɓa Ganin mota ba a'a kawai de tayi mamakin ganinsu awurinne, ahankali taƙarasa wurin cikin sanɗa tana leƙensu....Sukuwa basuma sanda akwai mutum awurinba. Tajima tana kallonsu basusaniba harta juya zata tafi sekawai idonta yasauka akan yarima sameer dake lumshe da Ido yasaka hannu ɗaya yaɗage setin zuciyarshi dayakeji kamar zata ɓalle tafoto waje...ido tawaro cikin tsananin fatin ciki dajin daɗi taƙarasa gunshi sam bata damu da mutanen dake wurinba cikin ɗauki tariƙo hannunshi tana faɗar "pappi cikin sweet voice ɗinta me daɗin sauraro...wani irin zabura princes yayi sabida wani mugun shuck dayaji lokacinda hannunta yasauka anashi, tareda buɗe lulu eyes ɗinshi akan kyakkyawar fuskarta, wanda yayi sanadiyyar tsanantawar bugun zuciyarshi. Sukuwa duka ido suka waro musamman brothers ɗinshi dasukasan waye yarima sameer dakuma yadda yake ƙyamatar mata, amma imam, Hakimi, da manager company duka kallon mamaki ne suke mata gatadai kallo ɗaya zaka mata kasan cewar ƴar fulanice ta asali wanda akasani da kunya da kawaici amma gaya tariƙe hannun namiji kuma babban mutum me daraja irin yarima sameer agansu batareda taji kunyarsuba. Shi kuwa wani mugun kallo kawai yakebinta dashi amma kasa cewa komai kowani dogon motsi yakasayi...cikin mamaki danejo kebinshi da kallo tunda tabuɗe ido aduniya take Ganin pappi ɗinta bata taɓa yimai maganaba yashareta se yau, atake gabanta yafaɗi tsoro da fargaba duk suka rufeta dara daran idanuwanta masu masifar haske suka canja kala atake suka cikoda ƙwallah, dasauri ta russuna wurin ƙasan ƙafafunshi taƙara kamo hannunshi ɗaya muryarta na rawa take faɗar "pappina bakada lafiya ne? Miyasa kayi shiru? Ko wani abun wannan mutanen sukayima? Miyasameka pappi? Kayi magana dan Allah. Taƙarasa zancen tana saka Mishi kukan dake fita har zuciyarta.. "Ikon Allah ke baiwar Allah sakeshi mana aina kika sanshi dazakiga mutum kawai kizo kiriƙeshi kinamai kuka? Cewar imam cikin mamaki...banza tayi dashi domin burinta kawai pappinta yayi magana amma shiru se ido kawai dayake binta dashi...shikuwa imam agarzuƙe yayo kanta yana masifa "waifa wannan wani lokacin Fulanin nan naruga ba hankaline dasuba tashi kibarnan kona tattakaki yanzu Wlh. "No karka daketa Cewar Ameer yana tasowa daga inda yake zaune yaduƙo kusan inda take gurfane riƙeda hannun yarima sameer yace "ƙanwata sakeshi muyi magana kinji, Yafaɗa cikin alamun rarrashi...dagowa tayi da jajayen idanuwanta masu masifar girma tawatsamaisu tareda girgiza kanta duka sumar data rufe rabin fuskarta tayi baya atake asalin fuskarta ta bayyana. Azabure ameer yayi baya sedai yayi ƙarfin halin hana kanshi faɗuwa, hakama duk wanda ke wurin seda yarazana Ganin tsananin kyawun wannan yarinyar gakuma gashi har gadon baya kana ƙwatar idonta kaɗai ta isa tashedama tabbas aljanace sabida kasan cewar ƙwayar idonta lite blue sedai acikin ido farine ƙal amma yanzu yakoma ja sabida kukanda tayi. Duk wanda ka kallah awurin natsuwa ta ɗauke Mishi amma Banda zaratan samarin dasukayi ta maza suna kallonta... ɗan seta kanshi yayi kana yaƙara cewa a'ina kikasanshi ƙanwata? Domin yaga dai taƙi ta sakeshi kamar yadda yabuƙata...ƙwallar dasuka cika idonta ne suka ƙara zubowa kana tace "pappina ne...! Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal complete ga duk me buƙata domin a complete yafito duk wanda keson posting kullun 700 ne zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp. Autar alheri ✍️ 🪐🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥🪐 🪐🐦‍🔥 *MASARAUTA*🐦‍🔥🪐 🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Dr Yasmeen Ahmad😚 Autar alheri ✍️ Al'ajabi, hummm Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI. ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃 Book 1 Page 17 & 18 "Kana tace "pappina ne kuma inasanshi banaso wani abun yasameshi, kace yayi magana dan Allah kowani abun kuka masa ne? Tafaɗa cikin yanayin tausayi domin duk zuciyarta ta karaya Ganin pappinta yaƙi cewa komai...ajiyar zuciya Ameer yasauke kana yadubi yarima sameer daya lumshe kyawawan idanuwanshi tun lokacinda kalamanta suka fara dukan dodon kunnenshi, kana yace "princes kasan wannan yarinyar ne? Yatambaya badan abashi amsaba domin yasan ba abinda yarima sameer zece Mishi idan kuwa zasu kwana awurinne, sedai ga mamakinshi yaji cool voice ɗinshi yana faɗar "I no her, yafaɗa kamar meciyon baki, kafin yaƙara motsa laɓɓansa cikin gajiyawa yake faɗar "please just sey her get from my saint, Yafaɗa, zuciyarshi ada gule. Ido danejo tazuba Mishi kawai tana kallonshi yayinda idon ke ƙara cikowa da ƙwallah...shikuwa Ameer jin kalaman ɗan uwan nashi yasa yadubeta kana yace "please ƙanwata inaga wannan Bashine pappin dakike magana akaiba kiyi haƙuri kije gida kinji zakiga pappinki acan yana jiranki amma wannan bashi bane, yaƙarasa zancen cikin rarrashi. Ita kuwa tunda taji saukar kalamanshi idonta suka ƙara zuba tamkar panpo, cikin kukanda keson kuɓuce mata tasaki hannayenshi wanda yaji tamkar lantarki ce tarikeshi amma yanzu tasakeshi sewani zutt,zutt yakeji acikin lallausan tafin hannuwan nashi. "Ni zakace akora my pappi ni HUSNAR KA? danejo ce fa? yau nikake kora? minayima dazafi Hakan? Ni pappi? Humm sabida kaga banada kowa danake raɓa naji sanyi sekai? Karka manta pappi kaine uwata, kaine ubana, kaine yayana, kaine ƙanena, kaine abokina, amma yau kaida kanka kake korana? Hum shikenan I'm going to all your life my pappi sedai zan zauna zaman tsimayen "When you're call me "when you're missing me😥 "When you're coming back to me my happiness "When you're coming back to me my everything all my life, I'll waiting for you any time my pappi. Tana gama faɗar Hakan tamiƙe tsaye tareda saka bayan hannunta tashare ƙwallar idonta, kana tajuya kawai tabar wurin. Sukuwa gabaki ɗaya sunyi mutuwar zaune tunda tafara magana domin sam basuyi tunanin zataji abinda princes yaceba balle har ta iya maida Mishi amsa da turanci ba, hartabar wurin basu saniba, sunlula duniyar tunanin ya akayi ƴar fillo ta iya Turanci kuma ƴar cikin ruga Fulanin jeji? Amma ba wanda ze basu amsar wannan tambayar tasu Hakan yasa suka ƙara gaskatawa ransu Cewar gamo sukayi da aljana... firgigit Hakan Anwar yayi yana kallon inda take gurfane da zimmar yabata haƙuri amma seyaga wayam bakowa Hakan yasa gabanshi ƙara mugun faɗuwa cikin kaɗuwa yake faɗar "kai ameer taɓace fa Wlh ajanace innalillahi wa'innailaihiraji'un...arazane Ameer ɗinma yamiƙe tareda riƙo hannun yarima sameer daya koma tamkar wanda aka zarewa lakka ajiki yamiƙar dashi tareda janshi suka fara tafiya gun motocinsu sedai duk yadda Ameer yaso sutaka dasauri abin yaƙi samuwa domin yadda yake tafiyarshi yanzuma Hakan yakeyinta cikin izza da ƙasaita tamkar yadda yasaba yin abarshi ga dukkan alamu dai hakanne tafiyar take bawai yanayi bane sabida kuɗi ko mulkinsu ba... hakama su imam tuni sun mara musu baya...hakimi kan se haƙuri yake basu domin ya ɗauka sun fasayin aikinne tunda yaga Manager company gini yacika bujenshi da iska, aranshi kuwa se tsinewa wannan aljanar yarinyar yakeyi...sukuwa dogaransu nahangosu tafe sukayi saurin buɗe musu motar, suna isowa suka shiga hakama excout ɗinsu suka shiga cikin sauri aka tada motocin sukabar yanki baki ɗaya. DANEJO Tafiya kawai takeyi batamasan ina take jefa kafartaba wani irin ɗaci takejin zuciyarta namata wanda bata taɓa jin irinshiba,,,yau ta ɗanɗani baƙin cikin dabata taɓa tunanin samuba, wai itace pappinta zece akora wai besantaba wannan wacce irin ranace me muni tazo acikin rayuwarta? tabbas wannan abin yayi mata zafi bakuma dan bata taɓa fuskantar Hakan bane a'a kawai dai ɗanta riski hakanne a inda batayi tunaniba, domin koda mutanen duniya zasu mata Hakan bazataji zafiba, amma agun pappinta kam bazata iya juraba, Hakan taketa zancen zuci harta isa gida tafaɗa babuko sallama gabaki ɗaya a hargitse take kamar wata zararriya... innawuro naganinta tataso cikin bala'i tana faɗar "ke dan ubanki nizaki wulaƙanta, tunyoshe nake jiranki amma kikayi zamanki seyanzu zaki dawomin kuma hannu rabbana, tukkunna ma ina aikenda namiki? Ko kina nufin ƙin tsayawa kikayi ki ƙarbo kika dawomin Hakan hannu rabbana? Taƙarasa zancen tana zuwa inda danejo take tsaye....Ita kuwa sema yanzu da innawuro ta tambe aikenta tatuna, dan ɗaukin Ganin pappinta yasa tayasarda saƙon. Cikin tsawa taji saukar muryar innawuro tana faɗar "wai badake nake maganaba kinwani shareni sekace wata sa'ar uwarki....ɗib tayi tare da haɗiye sauran kalamanta Ganin yadda danejo taɗago azabure tana watsa mata waƴannan idanuwan nata dasuka gama komawa abin tsoro sabida ɓacin rai wanda yanayinta yamaidata aljanar ƙarfi dayaji. Tsorontane yashiga innawuro lokaci ɗaya Hakan yasa tazuba mata ido kawai tana kallonta domin inda ada ne dasedai taji saukar ruwan duka tako'ina ajikinta amma yanzu kam tana shakku...iskace tafara kaɗawa tayi baya da sumar kan danejo tana kaɗata sama, Hakan yaƙara ta azzara sauyawar halittarta daga mutum zuwa siffar aljanu...dasauri innawuro tanufi ɗakinta tareda maida ƙyauren tarufe gam tana faɗar "aikin banza wannan yariya ko dangin ibilisai ni wuro inaganin jarabawar duniya mlm yaɗauko mana jaraba dabe ɗauko uwar aljanar nanba daba abinda zesa tazame muna fitina kataɓa ta kuma wani bala'in yabiyo baya, Hakan innawuro keta mitarta ita kaɗai acikin ɗakinta. Danejo kuwa nasu ɗakin tashiga tareda zubewa akan katifarta tana rushewa da matsanancin kuka metaɓa zuciya, sam takasa danne abin aranta Wani irin ɗaci ke taso mata azuciya, tarasa ina zata saka kanta, taɗauki tsawon lokaci tana kukan kafin taji ana shafa lallausar sumar kanta....dasauri taɗago tana kallonshi cikin mamaki domin tasan dudduniya mutun ɗaya kemata Hakan kuma sam batayi tunanin ganinshi ba yanzu..aiko sukayi ido huɗu dashi yana sakar mata lallausan murmushi wanda yaƙara fitoda asalin kyawun fuskarshi ga dimple ɗinshi duka biyu sun lotsa abinda ke bala'in ɗaukar hankalinta gareshi kenan...dasauri tajuye fuskarta tana turo baki gaba kawai taƙara rushewa da matsanancin kuka. "Ya salam shine abinda pappi yafurta ahankali yaname dafe kanshi, kafin yariƙo hannunta cikin sigar rarrashi yake faɗar"please my husnah stop crying mana, sata kigayamin miyasaki kuka, yafaɗa cikin Cool voice ɗinshi sak irinna yarima sameer domin basuda banbanci ko ƙwayar zarra ne tsakaninsu daga murya har kamanni na fuska da jiki har yanayi komai nasu iri ɗaya ne. Hakan yasa danejo keyiwa yarima sameer kallon pappinta. Shiru tayi taƙi Magana kusan minti ukku, kana tabuɗe baki cikin muryar kuka take faɗar "nikatafi bayan ɗazu ka wulaƙantani kakoreni daga wurinka dan kawai kana tareda wayancan mutanen shine yanzu zakazo min, haba pappi miyasa zakamin Hakan dan Allah? Karka manta fa Kaine ummana yayana kuma malamina idan kagujeni yazanyi? Tafaɗa tana ƙara sakin wani sabon kukan me tsima zuciyar mesauraro. Tunda tafara magana yake kallonta tamkar yasamu tv aranshi yana ayyana Cewar ta haɗu da princes Sameer ne kenan duk yadda akayi domin duk faɗin Afirca shine kawai keda kama dashi wanda za'a iya gani ayi tinanin shine, bece mata komaiba harta gama zancenta taɗora da kuka..hannunta kawai yariƙa tareda hura mata iskar bakinshi a ido domin bayaso wani daga cikin gidan yazo yaji abinda suke magana akai, aiko suka ɓace bat kafin su bayyana bakin wani ƙaton teku, buɗe idonta tayi taga inda suke, amma batace komaiba kuma bataji tsoroba kasan cewar sun saba irin wannan tafiyar da pappi, kusan minti 15 suna ahakan kafin yajiyo gareta cikin tausasa harshe yace "My husnah kitsaya kinutsu ki saurareni kinjiko..kai kawai taɗaga Mishi amma batace komaiba...Hakan yasa yaci gabada faɗar"kiyi haƙuri abisa korarda yarima sameer m habibullah yayi Miki, domin banine na korekiba yarima sameer ne, Shima kuma ba'ason ranshi yakorekiba sedan kasan cewarshi yatsani mata suraɓeshine da irin halayyar Ameer M habibullah yakeda Ita sam baze korekiba sabida Hakan kidena fishi da pappinki kinjiko ƙanwata, yaƙarsa zancen cikin kwantarda kai yadda zata fahimta....amma ina tun lokacinda yace bashi bane yakoreta ƙwaƙwalwarta tadena gane komai, tunani kawai take aranta to bashi bane waye? Waye takeda kama irinta pappinta? tayaya mutun biyu zasu kasance iri ɗaya? Kodai su ɗin twins ne? To koma twins ne aikamarsu tayi yawa kuma miyasa shi batasanshi ba se pappi kawai? Miyasa kuma bayason mace taraɓeshi? Miyasa ze koreta bayan ita batasan ba pappinta bane? Kuma tayaya ma zata yadda ba pappi bane? Hakama tayaya zataƙi yadda bayan pappinta betaɓa mata ƙarya ba...duk acikin ranta take jerawa kanta waƴannan tambayoyin da batada amsarsu, sedai abinda batasaniba afili take zancen zucin nata kuma koda azuci tayi pappinta ze iya sanin abinda take saƙawa....muryarshi ce takatse mata tunani inda yake fadar "duka zaki samu amsoshin wannan tambayoyin naki my husnah sedai bayanzuba dasannu Zaki fahimci komai, abu biyu saki sani ayanzu sune na ɗaya muba ƴan biyu bane hasalima bajinsinmu ɗaya ba inafatar kinsan Hakan, Sena biyu zaki bawa zuciyarki nutsuwa da bani bane kika gani ɗazu sabida zankaiki har inda yake kiganshi amma bazan bari yagankiba kin yadda? Yaƙarsa zancen yana kallonta...kai kawai ta iya ɗagawa amma takasa cewa komaiba sabida mamaki da al'ajabi. Sunjima aruwin yanata rarrashinta kafin yasamu zuciyarta taɗan nutsu yamaidata gida. MASARAUTAR MAHAR Sedare lis suka dawo garin MAHAR sedai agajiye liƙis suka dawo domin daga Adamawa ko ina basu tsayaba se masarautarsu, motar data ɗauko imam ce kawai tatsaya taraba ta ajiye shi kana suka ƙaraso..suna fitowa daga cikin motocin kowanne pert ɗinsu yanufa domin dare yayi sosai, koda yashigo general parlor gidansu bakowa kuma duka ankashe fitilun parlor, Hakan yasa ya haura kawai pert ɗinshi batareda yanemi mammi ba, yana shiga tun a perlor yafara fatali da kayan jikinshi harya shiga bedroom ɗin ƙarasa cirewa kawai yayi yafaɗa bathroom yasakarwa kanshi ruwa tareda lumshe kyawawan idanuwanshi, sedai arazane yabuɗe su jin saukar sweet voice ɗin danejo inda take fadar "kaine uwata, kaine ubana, kaine yayana, kaine ƙanena, kaine abokina, amma yau kaida kanka kake korana daga gareka, "when you're coming back to me my everything. Wani irin mugun faɗuwa gabanshi yayi yana ƙara ganin kyakkyawar fuskarta me ɗaukar hankali a ƙwayar idonshi, "hasbinallah "innalillahi wa'innailaihiraji'un wannan wacce irin yarinya ce ? Yafaɗa asaman lips ɗinshi kafin yayi sauri yayi wankan shaf'shaf yafito, kayan bacci shi kawai yazura taredayin addu'a yakwanta, sedai baccin yaƙaura cewa idonshi sam muryarta kawai yakeji tana mishi gizo idan kuma yarufe idonshi ita yake gani, yaɓata tsawon lokaci ahakan yarasa abinda yake mishi daɗi daƙyar bacci ɓarawo ya ɗauke shi, sedai ko minti 40 beyi dayin baccinba yafarka arazane yana salati, saka makon danejo dayariƙa gani acikin baccin shi tana kuka kamar ranta ze fita akan korar daya saka ayimata ɗazu, cikin wani irin yanayi yadafe kanshi yana maimaita....! Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp. Autar alheri ✍️ 🪐🐦‍🔥🪐 *AL' AJABIN*🪐🐦‍🔥🪐 🪐🐦‍🔥 *MASARAUTA*🐦‍🔥🪐 🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Daga💪Alƙalamin👇🪸🪸🪸🪸🪸🪸 Dr Yasmeen Ahmad😚 Autar alheri ✍️ Al'ajabi, hummm Book ɗin al'ajabi wani sabon kabcene me matuƙar al'ajabi da ban mamaki, kabcene wanda ya banbanta da sauran books na masu ban al'ajabi kamar irinsu ( MEJO NAJEEB,,, SOLDIERS FAMILY,,,,IZZAR MULKI,,, JEJI GIRL,) inaga sune Books masu ɗauke da abin al'ajabi to wannan kabcen dabanne sam ba irinsu bane, idan kuna so kukashe ƙwarƙwatar karatu to kigarzayo domin samun damar karanta book ɗin AL'AJABI. ROMANTIC LOVE STORY 💋 KAMAR YADDA AKA SABA HUMMM MY LOVELY SISTERS ABUNFA BA'A MAGANA KAWAI MUTSUNDUMA ACIKIN WANNAN LABARI ME TAKEN AL'AJABI 💃 Book 1 Page 19 & 20 "Yana maimaita innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, yanajin gabanshi na tsananta faɗuwa, yajima zaune kafin yamiƙe yanufi bathroom yaɗauro alwala yafito yatada sallar nafila domin ayanzu kusanci da mahaliccinshi kawai yake buƙata yarigada yagama gasgata cewar gamo yayi, hakan yaraya wannan daren har aka kira asuba kana yafice zuwa masallacinsu dake cikin masarautar, yana fitowa yasamu yan uwanshi duka sun fito domin wannan al'adace agun ahalin wannan masarautar muddin kana cikin masarautar to doline da asuba kafito ahaɗu domin shiga masallaci, daga iyayen nasu maza har memartaba sarki habibullah dawazirinshi kuma ƙane agareshi, baba tsoho kenan, har galadima wanda yakasance shima ƙane ne agunsu, kuma dukansu sun manyanta, kowanne datashi zuri'ar,,,ahakan suka nufi masallacin dukkansu. Bayan an idarda sallah kowa yafito ananne suka fara gaisawa da juna wato samarin gidan dakuma yayunsu domin memartaba da tawagar ƴan uwanshi tuni sunyi gaba. "Good morning yaya Naseer, cewar yarima sameer domin duk acikin yayunsu yafi ƙaunar yaya Naseer wanda baya iya shareshi kamar yadda yake share sauran. "A a morning my lovely bro yoshe agari? Naseer ɗin ya amsa yana rungumeshi. Bece komaiba yadda shima Naseer ɗin yasan bazece wani abinba, daga wannan gaisuwar, hakan duk suka gaisa da junansu kana kowa yanufi pert ɗinsu amma ameer da anwar pert ɗin mammi sukabi princes. Bara nabaku ɗan bayani kaɗan daga cikin wannan ahalin yadda zaku fahimta. Sarki habibullah yanada yara biyar kamar yadda kuka sani, Mansoor shine babba wato baba wanbai, yanada yara ukku Naseer, Abdul, kabeer, kuma kusan sune manyan yara agidan wato Abdul wanda suke kira yaya Abdul, sekuma yaya Naseer, da yaya kabeer, Muneer, shine kebinshi shine suke kira abbey, yanada yara ukku, Yarima Sameer, affan, Safnah, jabeer kuwa shisuke kira dady, yaronshi ɗaya Anwar, sekuma Mubarak, wanda suke kirada abba ciroma, yanada yara biyu, Ameer da Amerah, sekuma Autansu Abdullah, wanda sunanshi yaya Abdul yaci, shi bemada aure ayanzu hakan tun shekarun baya da matarshi tarasu beƙara aureba, hakanan yake zaunenshi, kuma bayama zama ƙasar yana US acan yake aikinshi, kuma shine suke kirada abban yarima ko abban princes domin tunda aka haifi yarima Sameer ahannunshi yataso shine yake kiranshi da yarima har Sunan yabishi to acan US basa cewa yarima sedai suce princes shine sunayen suka haɗe mishi...sarki habibullah kuwa matanshi ukku mebabban ɗaki itace uwar gida yaranta ukku, mansoor da jabeeer, se abdallah, se Fulani abu itako yaranta biyu mubarak da muneer, sa'annan Fulani huraira itako bata taɓa haihuwa ba, Kunji yadda suke barana barku hakan zuwa gaba saku fahimci komai domin akwai waƴanda se gaba sunayensu zasu fito dakuma rawarda zasu taka aciki. Suna isa general parlor mammi suka samu abbey zaune yana aikin a laptop ɗinshi, mammi kuma nagefenshi tana zuba mishi coffee, dukkansu rusunawa sukayi suna gaida iyayen nasu bayan sun amsa ne abbey yace "yaran abbey yagajiyar tafiya? Naga kunyi saurin dawowa kwana ɗaya duk nisan wurinnan. Murmushi Ameer yayi kana yace "wlh kuwa abbey domin akwai abubuwan damukeso muyine idan mundawo kafin bro yakoma US shiyasa muka dawo karmu ɓata lokaci acan. Jinjina kai abbey yayi kana yace "shikenan badamuwa sedai babu zancen komawa US ayanzu domin memartaba yabada umurnin dukkanku kufitarda matan aure kafin yatafi sabida akwai muhimmin abu dayakeso aiwatarwa agareku kuma acikin wannan lokacin yakeso kuyi aure, yaƙarasa zancen yana kallon yanayinsu. Seyaga Anwar ne kawai yaɗago aɗan razane yana dubanshi sekuma Ameer dayace "aure kuma yanzu abbey? Amma shi gogan ko ɗagowa beyiba ga dukkan alamu bemasan akanme ake maganarba domin yalula wata duniyar, fuskar waccan aljanar kawai yake gani a idonshi hakama muryarta kemishi gizo acikin kunnenshi kuma cikin sautin kuka....da mamaki abbey ke kallonshi yana karantar yanayinshi, hakama yan uwan nashi, kusan minti 15 suna ahakan domin abbey zuba mishi ido yayi koda zece wani abu. Amma shiru, hakan yasa yataɓoshi yana faɗar"Muhammad lafiyarka kuwa? Yatambaya da mamaki kwance akan fuskarshi. Mammi ma shitake kallo mamaki fall ranta..arazane yaɗago yana faɗar "na'am abbey. Dukkansu zaro ido sukayi yadda sukaga idonshi suyi luhu,luhu kamar wanda yasha kuka yagaji kokuma wanda beyi bacciba, abinka ga me manyan idanuwa. Dukkansu shiru sukayi suna kallonshi kafin abbey yace "Muhammad Mike damunka? Bakada lafiya ne? Kakoma hakan? Damamaki shima yake kallon mahaifin nashi jin tambayar dayake mishi amma yakasa cewa komai, cikin ɗan tsawa abbey yace "ya inama magana kamin banza wai yoshe zaka ajiye wannan miskilin nakane Sameer? Humm toni bazan juri wannan sakarcinba kaji da kyau ina buƙatar kakawomin matar aure acikin wannan watan kafin ka koma US kuma umurni ne yanzu yajanye daga umurnin memartaba nawane kuma doline kowa yakawo idan ba hakanba toni zan nemawa mutun dakaina, yana gama faɗar hakan tamiƙe kawai yabar parlor sefamar faɗa yakeyi domin aganinshi duk laifin Abdullah ne dake biyewa shirmen sameer ɗin shiyasa yake yiwa mutanen renin hankali. Shikuwa gabaki ɗaya mutuwar zaune yayi tunda yaji kalimar aure jinshi ya ɗauke, auren kawai kemishi amsa kuwa cikin kunne..mammi ma batace musu komaiba tamiƙe warta domin idan tatsaya zata tausaya musu ne awannan gaɓar kuwa basa buƙatar tausayi domin kuwa inba hakan aka musuba bazasuyi aurenba duka yaran gidan maza sunyi aure sune kawai sukaƙiyi dan sunga anzuba musu ido...mammi na ɗagawa suka Miƙe jiki asanyaye suka nufi pert ɗinshi kowannensu zuciyarshi na luguden tara,tara musamman princes da babu zancen aure yanzu atsarinshi. A parlor suka zube cikin tashin hankalin da yakasa ɓoyuwa agaresu anwar yace "brother's yazamuyi da wannan zancen na abbey plesse aure fa, yafaɗa cikin alhini..."humm aini namarasa abin faɗa wlh dan banmasan ta ina zamu faraba, amma ni inaga Indai abbin yazo da hakan to kawai Nawwara zanfitar dama ita nakeso kawai banyi niyyar yin auren bane ayanzu, cewar ameer...dasauri duk suka kalleshi sedai kuma zancen ameer ya sanyaya ran anwar hakan yasa yasaki wani lallausan murmushi kawai yana shafa sumar kanshi. Da mamaki ameer yace "yadai bro? Ko kaima abin yazo maka dasauƙi ne? Humm kawai Anwar yace amma bebawa ameer amsaba, balle shi gogan dagabaki ɗaya baya cikin nutsuwarshi, fahimtar hakan yasa suka sakashi agaba da tambayar Mike damunshi amma yakasa cemusu komai, ahakan sukawini ranar a pert ɗinshi sallah kawai ke fidda su sedai yanayinda princes yake ciki yaƙara tada musu hankali hakan yasa suka yanke shawarar kiran abbanshi su sanar dashi. DANEJO Tunda abbey kemusu zancen aure har kawo firar dasukeyi tsakaninsu tana tsaye itada pappinta tana kallonsu cikin mugun mamaki ta kalli yarima sameer kuma ta kalli pappi, tabbas ba pappi bane amma ba wanda ze yadda da hakan idan ba yagansu hakan tadata gansuba. Seda pappi yaga tagamsu dacewar wanda tagani dai bashi bane kana yasake ɗauketa yamaidata rugarsu, shikuwa yayi tafiyarshi, amma hakan danejo takasa samun saƙat domin kuwa tunanin abubuwan datagani acikin wannan masarautar da pappi yakaita yahanata sukuni gakuma wannan dake Kamada pappi datake ganin kamar yana cikin tashin hankali kuma duk yadda taso tayiwa pappinta tambaya akan abubuwan data gani yaƙi bata damar hakan, wannan lamarin shine yamayarda danejo wata irin sukuku. Su jauro Tun lokacinda suka tare danejo suka shiga taitayinsu domin seda sukayi kusan mako ɗaya akwance suna jinyar abinda idonsu yagane musu sedai daga lokacinda suka tuna kalaman danejo agaresu inda take cewa duk wanda yaƙara aikata irin abinda suka mata agarin to sune dalaifi, suka ware, atake ciwo yaƙare, daganan suka koma sojojijon dole acikin rugarsu masu gadin ƴammata, Hakan yasa kowacce budurwa tasamu inci acikin rugar tasu. MASARAUTAR MAHAR yau dai wannan matar samu damar aiwatarda mummunan ƙudurinta akan sarki Habibullah domin tabawa wata baiwa maganin datakeson ayiwa sarkin anfani dashi tasaka acikin abincinda jekadiya zata kai masa, wannan hadimar kuwa bakowa bace face amin tacciyar hadimar me babban ɗaki wanda ita kaɗai jekadiya ta yadda da Ita kasan cewarta dattijuwa kamarsu, hadima hajjo kenan munafukar tsohowa me fuska biyu... lokacinda tazowa da matarda tasaka aikin da labarin ta aiwatarda saƙonta kuma har memartaba yaci baƙaramin Farin ciki tayiba, atake tafaɗa turakarta tareda ɗauko wani walki ta ɗaura kana tarufe idonta tana karanto wasu laziman tsafi kawai taɓace daga wurin segata ta bayyana acikin wannan ƙugurumin jejin memasifar tsoratarwa...tana sauka wurin ya ɗauke da wata mahau kaciyar dariya cikin ɗaga murya me dariyar ke faɗar "aikinki na kyau Fulanin sarki habibullah yanzu Seki zuba ido kiga yadda komai ze kasance. "Murmushi tayi cikinjin daɗi tace "godiya nakeyi yakai wannan dodo, sedai inada tambaya wadda nakeyima kullun koyanzu itace zanyi, akan babyn da gimbiya halima tahaifa shekarun baya, wai haryanzu baka gano muna wanda yaɗauke shiba dakuma inda yake? Tafaɗa cikin damuwa...ɗan shiru wurin yaɗauka nawani lokaci kafin taji saukar mummunar muryar dodo yana cewa "tabbas bamu gano komaiba gameda wannan baby domin bamuma samu tahanyar dazamu gano wani abinba atare dashi abu ɗaya nasani shine duk inda yake yana raye kuma acikin aminci da kariya ta musamman tabbas kinrigada kinyi sake Fulani dama tarigida tawuceki, yanzu sedai kishiryama yaƙarshi aduk lokacinda ze bayyana agareki domin tabbas dashirin yaƙarki zeshigo masarautar MAHAR, hhhhhh, hhhhhh,,hhhhh Hakan yariƙa ɓaɓɓaka wannan dariyar merazana duk wani meji alokacinda yakeyinta kafin kuma wurim yayi tsit kamar ba'abinda yafaru, Hakan itama Fulani taɓace kamar yadda tazo takoma turakarta sedai duk kwakwata nakasa gane wacce Fulani ce acikin matan sarki domin taƙi bada damar aga fuskarta. US Zaune yake acikin tangamemen office ɗinshi yasaka computer agaba yana aikinshi cikin mutsuwa da kamala, kyakkyawan dattijo mecikar haiba dakuma kamala fari tass kamar ka kwanta shi jini yafito, ahankali yake aikin yanayi yana kurɓar tea ɗin dake gefenshi, wayarshice tayi ƙara wanda yasakashi saurin dubawa domin wayar family shi daban take sabida be haɗa komai da ahalinshiba dudda baya taredasu amma yanajin sonsu harcikin ɓargon jikinshi, dubawa yayi yaga me kiran nashi afili ya furta "Ameer sekuma yayi picking yakara wayar akunne tareda sallama, "Abba inawuni. "Murmushi yayi wanda yaƙara Mishi kyau kana yace "lpy qalau Ameer sedai fa nan kam hantsine ya kuke y gidan ya memartaba? "Duka lpy qalau alhamdulillah Abba. "Masha allah, miyake faruwane Naji muryarka wani iri? Yajefawa Ameer tambayar..ajiyar zuciya Ameer yasauke kana yace "Wlh Abba akwai matsala ne, Anan yashiga bashi labarin yadda sukayi da abbey dakuma yanayinda princes keciki sedai yaƙara da Cewar amma yana Ganin ba wannan maganar ce tafi ɗagawa princes ɗin hankaliba domin tun kafin abbey yayi zancen suka ganshi wani iri....cikin tashin hankali Alhaji Abdallah yamiƙe tsaye yana faɗar "subhanallah inayake shi Sameer ɗin? "Yana bedroom Abba. "Okay bashi wayar yafaɗa aƙagare. Aiko Ameer yamiƙe zuwa bedroom ɗinshi koda yashiga yana zaune ya jingina kanshi dajikin bed sedai ba bacci yakeyiba, bece mishi komaiba yaƙara Mishi wayar akunne domin yasan koyayi magana ba tanka Mishi zeyiba... ɗagowa yayi yana hararar ameer ɗin kafin yayi wani motsin yaji saukar muryar abbanshi yana faɗar "Sameer Mike damunka? Yafaɗa hankalinshi duk atashe, jin muryar abbanshi ne yasa yariƙe wayar tareda lumshe kyawawan idanuwanshi, yana sauke ajiyar zuciya...Ganin Hakan yasa Ameer ficewa daga bedroom ɗin...shikuwa shiru yayi bece komaiba kusan minti 5 seda yaƙara jin muryar abban nashi yana faɗar"kanajina kuwa sameer waimike faruwane a,nan? Yaƙara jefo wata tambayar. Daƙyar ya haɗiye Yawun dasuka tokare maƙoshinsa kana yabuɗe baki daƙyar yace "Abba, sekuma yayi shiru. "Na'am yarona miyasameka? Naji muryarka Hakan? Mi akayima? Wani abunne yafaru? Duk ajere yake jefomishi tambayoyin. Yarima Sameer kam yakasa bashi amsa ko ɗaya daƙyar ya iya buɗe baki yace "Abba aljana gamo nayi Abba Wlh aljanace, yafaɗa yanajan wani irin numfashi wanda yakeji kamar zuciyarshi zata fasa ƙirjinshi ne tafito....ido Alhaji Abdallah yawaro cikin mugun tashin hankalin daya ƙara yimai dirar mikiya yace "aljana dai Sameer a'ina? Kai baradai ganinan zuwa zanshigo Nigeria nanda ƙarfe 6 nasafiyarku, daga Hakan ya yanke wayar tareda kwashe takashenshi ko kashe computer ɗin beyiba yabar office ɗin hankali amatuƙar tashe....! END BOOK 1 kuma Anan free page yaƙare semun haɗu a book 2 wanda yakasance paid ne. Humm yanzune za'afara asalin wasan acikin wannan book ɗin metaken👉 *AL'AJABIN MASAURATA* Shin wacece HUSNAH? Miye alaƙarta da pappi? Wacece wannan Fulanin dake neman mutane da sharri acikin masarautar MAHAR? Shin ina labarin jinjirin da aka sace? Miyasa aka kashe gimbiya halima? Mi zuwan abban princes ze haifar? Miyasa PAPPI kezuwama HUSNAH da kamannin yarima sameer? Minene yatadawa HUSNAH hankali acikin masarautar MAHAR? Shin minene asalin faruwa wannan abubuwan al'ajabi dake cikin masauratar MAHAR? Humm duk kobiyoni semun haɗu a page nagaba in sha Allah. Book ɗin AL'AJABI Paid book ne akan 1k kacal 👌 zaki iya tura kuɗinki ta wannan account ɗin 👉2276776261 sha'awanatu ƙasim UBA bank, kana kitura Shedar biyanki a wannan nomber 👉 07037092176 on whatsapp. Autar alheri ✍️