An dauko wannan littafi daga shafin https://gistrog.com.ng ku ziyarci shafin na https://gistrog.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348141702912 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://gistrog.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348141702912 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://gistrog.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.gistrog.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/SuleimanUsmanKurya Twitter : https://twitter.com/Kuryaloaded_Ng Telegram : https://t.me/+Um7CIRmWSIU2NTg8 ๏ปฟ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA NA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) Gargadi........ Wannan littafin mallaki Na ne kuma bana yi shi don cin zarafin wani ko wata bane hasalima duk wanda ya ga ko ta ga labarin yayi daidai da tsarin rayuwar ta ko makamancin hakan to ina me bada hakuri, Sannan ban yarda wani ko wata su juya mun labari Na ko su canza ba tare da neman izini Na, Da sunan Allah me rahma me Jin kai,Allah yanda Na fara rubuta labarin nan lafiya Ubangiji ka sa Na gama shi lafiya, .............. Page one **********Bauchin Yakubu GRA Karan hayaniyan mutane tare da bugun gate in wani tangamemen gida ne yayi alarming securities in gidan kan bakin da me gidan ke expecting tun safe sun iso, Sunday ne ya mike tare da kallon mal Iro yace Iro I think they are here already make I do quick and open this gate before oga change am for me,dariya mal Iro yayi tare da bantaran goron sa domin shi Sam ba gane wanga turanci na Sunday yake yi ba,normal turanci ma ya ya kare da shi balle wata broken, Shi ko Sunday cikin sauri ya tashi tare da nufan black gate in saida ya bude kofar ya leka ganin dandazon yan jarida ne ga sanya shi saurin bude gate in gaisuwa suka yi exchanging bayan sun shigo cikin premises in gidan, Masha Allah Na fadi sakamakon karewa gidan kallo da nayi,wata gida ne Wanda ya amsa sunan sa gida babban duplex building ne wanda aka kawata wajen gidan da flowers kaloli daban daban,kallo daya za ka yi wa gidan ka san mamallakin sa ba karamin attajiri bane domin duk layin zan iya cewa gidan Sen RILWANU AUDU WAZIRI .... Ya fi Na kowanne kyau, Sa'eed ne ya fito daga cikin main house in gidan sanye da black and white uniform, shine mafi kusanci da Senator Rilwan, Cikin fara'a ya karasa gurin yan jarida domin an riga an San da zuwan su,sun zo ne domin tattaunawa da Sen RILWANU AUDU WAZIRI wanda aka tsayar a partyn su domin yin Takaran Gwamnan jahar Bauchi,ganin zabe ya karato ne ya sanya ya hada zaman shi da kanshi domin bayyanar da wasu raayoyin shi tare da amsa wasu yan tambayoyi da suke ta son masa, Ba karamin lucky da dadi yan jaridan da suka samu zuwa suka yi ba domin sun San ko banza bara su koma hannu Na dukan cinya ba domin Sen RILWANU an san shi da halin kyauta da son jamaa ka'ida ne duk wani Wanda ya zo ganin shi to baya zuwan banza, Iso Sa'eed yayi musu zuwa ga wani babban Hall dake cikin gidan Wanda an yi shi ne daman domin taro, Hall ne babba me kyau dauke da kujeru da Dan karamin tables Wanda ke dauke da snacks and drinks a kai, Bismillah have a seat Sa'eed yace yana murmushi su din ma murmushin suka yi tare da fara kokarin zama,baran sanar da Sen zuwan ku kafin nan ku fara shan ruwa, Ya wancin gurin ba karamin dadi suka ji ba domin ka je inda za a karbe ka a mutunta ka har a baka abun makulashe ma wani abu ne,nan suka hau Dan ciye ciye da dan shaye shaye kun san mutanan mu ba a ganin bati a bari lol.... Kusan 15 mints da fitan Sa'eed suka fara Jin alamun tafiya tare da magananganun mutane Wanda ya tabbatar musu gwamman goben su ne ke tafe,da sauri suka yi arranging kansu tare da kokarin setting cameras in su domin kowa so yake ya fara daukan sa a hoto, Kofar aka bude Wanda securities in sa ne kusan su biyar a gaba sanye da irin same kayan da ke jikin Sa'eed sai wasu biyar in a baya sai kuma wasu mutane su uku a tsakiya ko wannan su ya hade cikin dakkakiyar shadda sai kyalli kawai suke zuba wa da kamshi, Da sauri yan jaridan suka Mike suka fara daukan su a hato,daya daga cikin mutanan ke kirarin Senator Rilwan sai kayi gwamman mu Na gobe insha Allah sai ka mulki jahar Bauchi... Wanda ake kira da Senator RILWANU AUDU WAZIRI Na bi da kallo,masha Allah na furta sakamakon ganin babban mutum me kamala sanye yake cikin farar shadda Wanda ta ji aiki da brown zare ta ko xauna masa damas a jiki duk da shi din ba ramamme bane ba kuma za a kira shi da kato can ba, Brown hula takalmi tare da links ne a jikin sa,saidai duk gayun nan da ya ci yayi lacking Abu daya shine murmushi, A cikin yan jaridun ne daya ya kalli daya yace Salman ya haka yau kamar abunda ke damun Sen domin daga fitowan sa jikin shi a sanyaye and ka dubi fuskan shi ko digon faraa babu bayan kuma shi mutum ne me yawan faraa, Hmm Tahir manta kawai ni kaina jiki Na yayi sanyi domin tun duban farko da nayi masa na gano damuwa lulube a fuskan sa,ni dai ko ma miye ke damun shi Allah ya sa kar yayi affecting Alkhairin da zai mana, Daya daga cikin yan jaridan ne ya tashi tare da mika gaisuwa bayan Alhaji Rilwan ya zauna tare da manyan Aminan sa guda biyu,Alhaji Salis da Alhaji Kabiru, Nan suka shiga masa tambayoyi akan zaben da ke tahowa ya yake ganin abun zai kasance tunda yana da abokan hamaiya dukda ma shi din mutum ne me Alkhairi hannun sa a bude yake ya sanya mutane ke kaunar sa sosai, Mikewa yayi sai a lokacin Na ga yayi murmushi farko dai da sunan Allah ya fara sannan ya mika godiya sai kuma ya fara jawabin sa kamar haka...... Hakika farin jini da soyayyan da ya samu a gurin mutane daga Allah ne domin in za a tuna sanda ya fito neman senator haka nan mutane suka yi ta kauna shi,ya gode wa Allah da irin daukaka da nasarorin da ya samu a rayuwar sa sannan ya Na mika godia ga dumbin jamaar garin Bauchi bisa yadda da kaunar da suke nuna masa kuma in sha Allah muddum ya zama Gwamma to zai yi mulki bisa tsoron Allah zai kaunaci talakawan sa zai.nan dai yayi ta jero irin cigaban da zai kawo wa garin Bauchi, Nan ko aka sanya tafi ana fadin sai kayi Gwamma in sha Allah uban marayu kuma gatan Bauchi, Dan gurban ruwa yayi sannna ya cigaba da jero jawaban sa ,yanda Hall in yayi tsit baka Jin muryan kowa sai nashi, Kamar daga sama suka ji an banko kofar Hall in kafin securities su kai ga sanin waye har ta shigo, Sanye take da ash in dogon rigan material kanta ko dankwali babu dogon bakin suman kanta ya kwanto har kafadun ta,kafafunta ko slippers babu,da gudu ta hayo kan stage in, Kallon Sen Salis yayi yace Alhaji kamar Princess nake gani lafiyan ta kuwa?? Wata kallan gumi ne ya tsattsafo wa Sen a fuskan shi wanda ya sanya bayan hannun sa ya goge ji yayi wani irin balain ciwon ciki da zafi ya durnuke shi lokaci daya duk da uban AC's in da ke cikin Hall in, Tafi ta shiga yi hannuwa bibiyu tana yi tana fadin wow wow nice one, so tsayawa kuka yi don kuma baku da aikin yi irin sa yana cika ku da maganganun karya da yaudara ku kuma kuna saurara kuna cewa sai yayi sai yayi me.ta kare cikin murya me karfi idanun ta jajjawur hawaye Na zuba, Wannan mutumin ne wai har kuka tsayar matsayin Dan Takaran ku wai wannan mugu mara mutuncin mutumin Wanda babu ko dikon tsoron Allah a tattare da shi kuke so yayi mulkin jahar Bauchi inalilahi wa ina ilaihi raju'un da kuwa masifa da bala'i ta afku a garin nan, Cikin sauri Alhaji Kabiru ya tashi yace keeee NADIYA kina da hankali kuwa wani irin shashanci da iskancin banza ke damun ki ko dai kin yi shaye shaye ne in to hauka kike to kiyi maza ki dawo hankalin ki uban ki mahaifi kike jefa da irin wanna kalmomin, Cikin sauri ta katse shi da ka dakata mun karamin Dan iska ai ba da kai nake ba sarai Na san waye shi, Dan juyi tayi tare da nuna SEN in tace wai ko ba the greatest SEN RILWANU AUDU WAZIRI ba the most richest man in Bauchi ko ba shi ba,Wanda a idanun duniya yake Na Allah amman a badini fa,Allah Ubangiji ya tsine maka Daddy ya Allah Na roke ka,ka hada shi da masifan duniyaa da ba lahira babu masifa kamar kasancewa yar ka da nayi I regret being Ur daughter you are indeed a disgrace to all fathers around the world da yardar Allah bara ka taba samun mulkin jahar Bauchi ba yanda ka tarwatsa mun farinciki Na Allah ya tarwatsa naka I hate you so beyond word, Da sauri Sen ya runtse idanun sa Wanda hawaye suka taru a ciki, Alhaji salis ne yayi alama da hannu wa Sa'eed su fita da ita mana domin ganin yan jaridan attentions in su duka Na kanta,da sauri suka nufe ta,don't touch me wawaye jakuna kun saida wa imanin ku da lahiran ku ga wannan mugu Azalumin mutum,ta nuna Sen, Kama ta suka yi da karfi tana tirjewa tana kuka tana aunawa Sen zagi tare da dibe masa Albarka zagin sa take ta uwa ta uba tana kiran sa da mugayen sunaye Wanda duk Wanda ke gurin sai da jikin su yayi sanyi, Ku tashi ku bashi guri dumin associating da irin wannan wlhy kan jawo talauci da kassanci ni dai shawara Na baku shine kalman NADIYA Na karshe kafin su Sa'eed suka fidda ta, Wato yanda ka san anyi ruwa an dauke haka cak jikin kowa ya koma a cikin Hall in baka Jin komai sai sheshekan SEN RILWANU AUDU WAZIRI wanda ya kifa fusakan shi bisa tafukan hannun shi yana kuka, Ba shi kadai ba jikin gaba daya yan jaridun yayi laasar domin wannan ba karamin abun girgiza da alajabi bane,ace 'Ya daya dilo a gurin Sen RILWANU ne ta fito ko Dan kwali babu tayi masa irin wannan mugun diban Albarkan kan kowa ya kulle, Da kyar daya daga cikin yan jaridan ya mike tare da cewa yallabai ko za ka iya mana karin bayani game da abun da Hajiya NADIYA ta gama fadi, Mikewa yayi ya kalli Dan jaridan idanun shi yayi jawur har ya bude baki kawai ya girgiza kai tare da Saurin fice wa daga Hall in domin ya cigaba da zama zai iya fashe wa da kuka bin shi suka yi suna yallabai yallabai ina ko sauraran su be yi ba,ya fice cikin sauri yana baza babban Riga Adduar shi daya Allah sa ba a dauka abunda Nadiya ta fadi ba in ko an yi hakan shike nan tashi ta kare magauta sun yi nasara a Kansa, Duk yanda suka so su ji wani abu daga bakin Aminan sa kala basu ce musu ba domin har yanzu cikin shock suke,Sa'eed ne yanda ta musu jagora suka shigo haka yayi musu suka fice daga gidan zuciyar kowa da abunda ke sakawa game da abunda ya faru duk yanda aka yi akwai boyayyan alamari a kasa ammann babu me basu wannan amsoshin sai shi kan shi SEN in ........ Toh fa wannna alamari da daure kai yake ace ya ce ke jifan uban ta mahaifi da irin wannan kalomin.. Ku biyo ni a sannun cikin wannan tafiya me cike da sarkakiya ,Na San ko wannan ku zai cika da tambayoyi Wanda Na tanadi amsoshin shi tsaf,๐Ÿ˜ Ga masu son a tallata musu hajojin su za su iya tuntuba ta ta wannan layin: 08100046388. ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA NA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) I Dedicated this whole book to you my dearest ummu Mansur (uwar daki na๐Ÿฅนโค๏ธ),I love you so beyond words ........ My What's app group https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK .............. Page two *************** Falmata!! Falmata ihun kiran sunan ta Sen ke yi daga ganin yanayin sa kasan yana cike da tsantsan bacin rai, Jiki Na bari Na ga wata yar dattijiwa ta fito tana goge sauran ruwan dake hannun ta a jikin zanin da ke jikin ta alamun daga kitchen ta fito, Gaban Sen ta zo tare da zubewa jikin ta Na rawa domin ko be fada ba ta san yau ta kade, Kallon ta yayi Na yan seconds sannan ya ja tsaki ya watsar,cikin bacin rai da hargagi kamar ba shi ne mutumin ya gama magana cikin tattausan murya a gaban yan media dazu ba, Da yatsar sa manuniya ya nuna ta sannan yace Ashe Falmata baki da mutunci ban sani ba,jikin ta Na rawa tace tuba nake uban gida Na wlhh tallahi ban san lokacin da uwar daki Na ta mike ba zato Na duk tana bacci Na shiga kitchen domin samar ma abun da za ka ci in kun gama taro sai kawai shigowar ta Na gani da su Sa'eed, Dallah rufe wa mutane baki yar iskar mata kawai one task kawai Na baki shine lura da princess tunda Na sanar da ke ina da taro yau Amman kin shiga wai kitchen dafa abinci ai ko kin dafa abincin karshe ke nan domin yau din nan zaki bar gidan nan ya kare kamar zai duke ta, Nan take ta hau kuka tana rokon shi Allah Annabi kar ya daga ta daga gurin neman Halal inta shekaru kusan nawa tana masa aiki yayi hakuri yayi over looking mistake in nan da tayi wlhy ta dauka NADIYA bacci take har yanzu duba da kwanan ta biyu tana bacci bata farka ba so bata dauka za ta tashi yanzu ba, Alhaji Salis ne yace ya isa haka Sen is of no use ka tsaya kana venting anger in ka akan wannan worthless matar,let's go and face our problem ya fada calmly, Tirjewa SEN ya ke yi while Salis Na jan shi domin barin gurin don ya ga alaman ranshi yayi kololuwa gurin baci, Da kyar dai ya samu suka bar gurin bayan Salis ya ce da Falmata dake ta faman rokon SEN ta tashi ta koma kitchen ta cigaba da aikin ta, Har sun kai ga shiga part in shi ya hango Sa'eed,kamar Wanda aka tsikara yace Salis kira mun wancan useless boy in, daga gurin Alhaji salis yayi wa Sa'eed magana kan ya zo SEN Na son ganin shi, Da sauri kuwa ya karaso yanda suke tsaya cike da girmamawa ya dan rusuna yace Allah ya ja da ran ka gwamman mu Na gobe, Gwamnan uwar ka SEN yace cikin tsantsan bacin rai bayan ya wanke Sa'eed da wata zazzafan Mari,da sauri ya dafe kuncin shi don ba karya Marin ta shige shi, Don uban ka Sa'eed me kuke yi har NADIYA ta samu damar shigowa cikin press confirence ina,nace uban me kuke yi , Kan shi Na kasa yace yallabai wlhh ba laifi Na bane laifin Muktar ne tunda su na bari a waje ni kan ba ina tare da kai a ciki ba, Cikin bacin rai SEN yace Salis ka duba ka ji wannan wawan yaro yake fada mun waye chief security ina ba kai bane ya ci ace duk kai za ka kula da komai wlhy in har wani abu ya samu kujera ta wlhy tallahi gaba dayan ku baran raga muku ba shashashu kawai Wanda basu San yanda ke musu ciwo ba, Jan hannun shi Salis yayi yace don Allah RILWANU stop all this is not that necessary ta ho mu shiga ka samu ka sha ko ruwan sanyi ne, Bayi da option sai bin bayan Alhaji salis in Wanda ke matsayin Aminin shi kuma mataimakin shi domin shi ya tsayar as deputy governor in shi,ko ba don komai ba ya ci ya jiga makoshin Na shi don ba karamin bushewa yayi ba, A tangameman parlor in shi da ya gaji da tsaruwa suka ya da zango,fridge ya bude tare da dauko bottle water me sanyi ya zuba masa a glass cup tare da mika masa have a sip yace da shi calmly, Ba musu Sen ya karbi cup in ruwan tare da nufan bakin shi sa cup in Sai kuma ya tsaya kallon Salis yayi yace Salis wat will happen in har shegun yan jaridun nan sun yi recording scene in da princess ta gama yi, Numfashi Salis ya ja tare da zama kusa da shi yace kai I don't think za suyi shooting because gaba dayan mu are shocked am sure harda su ina za su samu daman dauka, Allah sa ba Wanda ya dauka domin in har an dauka yadawa za suyi a duniya and muddum aka yada shike nan makauta sun samu nasara akan mu, Da yardar Allah bare ma faru that way ba just be faithful my friend,dan shiru suka yi duka kafin yace yanzu ina ita princess in, Cup in hand in shi ya aje tare da furzar da iska yace an mata alauran bacci, Gyara zama salis yayi sannan yace wai ni kam me ke damun NADIYA ne lfyan ta kuwa ni dai sani Na da ita bata da wata cuta da ya shafi brain inta balle nace shine ya tashi mata, Ajiyar zuciya SEN ya sauke sannan yace wlhy Salis karan shigowar waya ce ta katse mishi abun da yayi niyan fada,tare da zaro wayar tasa daga aljihu, Ganin Wanda ke kiran sa saida gaban shi ya fadi ba kowa bane illa shugaban party in su,Na shiga uku shine kalman da ya fadi be ma San ya fada ba,dafa shoulders in shi Salis yayi yace ka dauka komai zai tafi daidai, Dauka yayi jiki ba kwari,gaishe shi yayi inda yayi sauran tsayar da shi ta hanyar cewa SEN RILWANU shin ka shiga social media kuwa yau,idanu ya runtse yana fatan ba dai video in abunda NADIYA tayi masa ke trending ba, Cikin sarkewaan murya yace aa ranka ya Dade ban shiga ba wa niiii abuunnn ne ya faruuuu ya fada da kyar, Lalle RILWANU au baka ma San me ke faruwa ba ko to gaba daya kafofin sadarwa Na duniya kama daga kan Twitter Facebook YouTube Instagram video in ka ne kawai yake trending wani irin shirme ne haka ace a dauki yarinya ka tana maka zagin tsamen nama a gaban media Inalilahi,Anya ba muyi zaben tumin dare ba kuwa za ka jawo bacin sunan party in mu daman can kai ba mutumin kirki bane wai, Cikin tashin hankali yace yallabai kar ka ce haka wlhy tallahi nima yanda kake cike da mamaki haka nake Sam ba haka princess take ba duk Wanda ya sanni yasan akwai kyakkyawan soyayya da kauna tare da shakuwa tsani na da tilon yarinya ta,wannan definitely sa hannun magauta ne an ga nasara da daukaka Na tattare da ni,but don Allah sir kayi hakuri a kuma bai wa yan party hakuri in sha Allah I got this I can control it duk me nema Na da sharri Na fi karfin shi, Hmm shike nan gaskia try your best ka wanke kanka domin wlhy banda maganar ka babu abunda ake yi a media kowa da irin abunda yake fadi son ranshi ka ga kuma kujeran gwamma ba karamin kujera bane, Hakuri ya bashi tare da bashi assurance zai kawo karshen matsalan gobe in sha Allah,suka yi sallama tare da kashe wayan, Wata irin wawan jifa yayi da wayar ta bugi bango nan take kuwa ta tarwatse,cikin ihu yace damn it meyasa haka zai faru da ni why za a yi using NADIYA ta domin bata mun siyasa ta why my baby ,rike shi Salisu yayi yace calm down in sha Allah za muyi coming over this, Shiru yayi yana ta Dan nazari kusan Na mintuna sannan ya mike yace Salisu thank u so much you can take za ka iya tafiya,kace da Kabiru ina son ganin shi in ka fita,okay Ranka ya Dade a huta lfy Allah ya kyauta Na gama yace tare da barin parlor in cike da mamakin me ke damun Nadiyar har haka, A hanyar fita daga gidan ya hadu da Kabirun sanar da shi yayi ya je part in Senator yana son ganin shi,da toh ya amsa suka yi saying good bye in su don shi Salisu gida zai koma, Shi ko Kabiru kai tsaye part in Senator ya nufa inda ya tarar da shi ya kasa zaune ya kasa tsaye, Dafa shi yayi yace SEN take it easy sanin kan ka ne dai over thinking baya solving problems, cikin murya me rauni yace Kabiru ya kake son nayi dazun nan shugaba party ya kira ni har yana ce mun sun yi Dana sanin tsaida ni zaa iya kwace ma kujera na a tsaida wani, Calm down ba wanda ya isa ya kwace ma kujera yan gari ai suna bayan ka,wani irin baya Kabiru bayan an samu Dan iskan da ya yada video in nan yanzu haka shike trending a duniya, Whattttttt Kabiru yace yana zaro idanu shegu tsiyan yan jarida ke nan munafurci Amman ba komai we got this in control zauna ka ji yanda za aka yi, Nan ko SEN ya zauna shima Kabirun zama yayi suka shiga tattaunawa game da yanda za a yi,sai ga SEN har yana dariya suna tafawa da Kabirun ganin sun kawo karshen matsalan nan,Kabiru be bar gidan SEN ba sai dab Magriba akan gobe yana so ya kara gayyato masa yan jaridun zai Kara tattaunawa da su a haka suka rabu ya tafi gidan shi akan sai zuwa goben, Around 10 Na dare Senator RILWANU ne zaune a bakin gadon da NADIYA ke kwance kallo daya za ka mata ka gano baccin wahala kawai take yi,hannun ta Na cikin nashi ya tsurawa fuskan ta ido yanda take sauke numfashi a hankali, idanu ya damke da karfi tuno irin munanan kalmomin da ta jefe shi da su dazu da safe, Hawayen idanun sa ya goge da hannun daya Allah ya isa miki princess ita an cuce ni wlhy dake an ga ba yanda aka iya da ni shine aka biyo kan abunbda Na fi kauna duk rayuwa ta,shiru ya dan yi tare da shafa kanta don't worry my love you will get well in no time,am so sorry baby but I have to do this I got no option ki yafe ni princess ita ya kare yana hawaye tare da daukan wayan shi tare da danna wata lamba, Ringing uku aka dauka cike da girmamawa doctor Bashir Ubaidullah ya gaida Senator,amsawa yayi yace yauwa Doc kana jina make sure gobe karfe 11 Na safe ku iso gida Na ku tafi da ita domin haukan da ta mana yau ta baki ma bare iya fadan shi ba ya kare yana breaking down into tears........... Kar amanta ana sharing sabida da Allah Gama su son a tallata musu hajar su za su iya mun magana ta wannan no in 08100046388. ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA NA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM ......... My what's app group https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Don Allah duk wanda ta san bara tana yin comment ba to don Allah kar tayi joining, sannan wannan group in Na mata ne zallah banda maza don Allah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga ma su son a tallata musu hajojin su, za su iya mun magana ta wannan no: 08100046388 ............. Page three ************* Karfe goma daidai doctor Bashir ya iso cikin gidan SEN shida workers in shi a cikin motan daukan marasa lafiya wato (Ambulance), A zaune suke a parlor in SEN daga ganin alamun su tattaunawa suke me matukar mahimmanci, Doctor ne ya dago tare da kallon SEN yace ranka ya Dade ban ki ta taka ba saidai ina Jin tsoron abunda ke iya zuwa ya zo, Look Bashir we do trust u ne ya sanya har muka damka amanar princess a hannun ka so pls don't let us down,Kabiru ya fadi yana kallon cikin idanun doctor, In sha Allah Alhaji I will not let you down yanda kuka ce hakan za a yi,cike da alhini Sen yace I still can't believe this wai Nadeeya Rilwanu audu waziri ce tayi hauka ya salam,don Allah doc do take care of my princess for me I don't mind spending ko nawa ne ni dai all I want shine ta dawo normal ya kare kamar zai yi kuka, Patting bayan shi Kabiru ke yi yana haba my friend be a man mana Na san da ciwo sosai ko dan kasancewar ta ya daya tilo a gurin ka ammman we are doing this for her own good,so allow the doctors to do their job pls, Numfashi ya sauke sannan yace yeah haka ne you gat some point ne dai all am saying here is Bashir ka kula mun da princess kar a samu wata matsala make sure duk abubuwan da Kabiru ya sanar maka ka gane ko, Da sauri Ubaidullah yace yeah sir Na gane in sha Allah bara a samu ko wani matsala ba ai mun sha dealing da cases in da ya fi Na princess ma in no time za ka ga ta samu lfy, Nan take Kabiru ya ciro wayan shi tare da masa transfer in mil 5,debit alert ya nuna masa sannan yace ga shi for a start mu dai fatan mu komai ya tafi daidai and ta samu lfy make sure a siya mata duk abunda take so extra kula nake so ku bata, Nan take ya washe baki tare da zaro idanu Jin huge amount in da aka ambata hakan ma wai for a start wow harka da gidan gwamnati akwai samu ya fadi a can kasan ranshi,while a fili kuma godia yake ta zuba wa tare da Kara jaddada musu kan cewa babu wata matsalan da za a samu daga Gare shi his daughter will be safe and sound, Mikewa SEN yayi yace okay in dai haka ne ai no need of wasting time mu je ku tafi da ita kawai, ............... Nadeeyah Ba yanda Falmata bata yi da Nadeeya ba kan ta tashi daga kwanciyan kukan nan da take yi tayi wanka ta sauya kaya ko itama ta ji dadin jikin ta domin Sen ya aiko ace da ita ta sanya Nadeeyan wanka za a tafi da ita,tayi kuka sosai tare da tofin Allah tsine ga duk me sa hannu a samun rashin lfyn Nadeeyan, Kallon ta Nadeeya tayi da red eyes in ta tace wai Inna Falmata ke ma kallon mara lfy kike mun,wai me yasa kun kasa gane wancan mugun mutumin azzalumi ne,I thought in duk duniya sun kasa fahimta ta ke za ki fahimce ni duba da irin shakuwar da ke tsakanin mu,ta kare tana kuka don Allah Inna Falmata kar ki bari a kai ni ko ina tunda ke ma kin ce baki San yanda za a kai ni ba ni fa lafiya ta lau ta kare tana share hawaye, Ita din ma Inna Falmata hawayen take yi tana Allah ya baki lafiya uwar daki Na tabbas an cuce mu an zalunce mu,in ba haka ace duk irin shakuwa da soyayyar dake tsakanin ki da Ranka ya Dade ace ki masa irin wannan diban Albarkan??, Jin knocking in kofar da aka yi ne ya sanya ta mike wa da sauri Nadeeya ta riko ta tana rokon ta don Allah kar ta bar ta,jiki a sanyaye tace yi hakuri uwar daki Na ina zuwa da sauri ta bar gurin don ta cigaba da zama kuka za suyi ta yi,hakika ciwon nan Nadeeya ke yi amman har cikin Jinin jikin ta take Jin zafi da radadi, Bude kofar tayi ganin SEN ne da kanshi ya sa ta zube tana gaida shi ko amsa wa be yi ba yace ya Falmata ta shirya don za su tafi ne,aa ranka ya Dade tun safe nake binta tayi wanka amman Sam taki yi ko tashi taki balle tayi wankan sai kuka da sumbatu kawai take yi marasa dadin ji, Goshin shi ya shafo sannan yace kai Nadeeya ina ba dai taurin kai ba,daman can ya balle yanzu ya hadu da lalura,matsa baran shiga da kaina, A hankali ya shiga cikin dakin zuciyar shi Na bugawa domin daga jiya zuwa yau yar ta shi tsoro ta koma bashi, A kwance ya same ta ta kifa fuskan ta a cikin hannuwan ta yana jiyo sheshekan kukan ta, Zuciyar shi a karye ya zauna bakin gadon tare da dafo kafadunta da hannun shi,yace Nadeeyan Daddyn ta, Da sauri ta buge hannun nashi tare da Saurin Mike wa ido cikin ido ta kalle shi tace kar ka kuma taba ni da wannan kazaman hannayen naka mara tsoron Allah, Baki a bude yake kallon ta yace princess yau ni kike kiran hannaye na masu datti ,hannun da ya Raine ki ya koya miki tafiya ya ciyar da ke ya wanke ki,haba Nadeeya ta, Cikin tsawa tace I beg u in the name of Allah to drop this act ai wlhy an yi walkiya Allah ya tona ma asiri zan so duniya su San kai wani irin mutum ne wlhy ka sanya fuskan mutunci kana yaudara da zalumtar bayin Allah,in sha Allah Allah bare bar ka ba yanda ka tarwatsa mun rayuwa kai ma,dakatar da ita yayi saurin yi domin ji da yayi zuciyar sa Na kokarin bugawa,ya isa haka ko ma miye za ki ce baran ga laifin ki ba domin ba a cikin hankalin ki kike ba Allah ya isa an cuce ni,Allah ya baki lafiya my baby girl am so sorry I have to do this ni ma ba don raina ya so ba ya kare a raunane tare da cewa doctor you can come in, Nan ko doc Bashir da wasu murdaddu majiya karfin mataye sanye da uniform su biyar suka shigo dakin, Go get her shine abunda Bashir yace da Matan, Jin haka ya sanya Nadeeya birkicewa ta dauko bed side lamp in ta ta rike tana rantsuwa akan duk Wanda ya taba ta sai ta kashe shi ita she is not mad,juyar da kai SEN yayi cause his heart bare iya daukan hakan ba, Tsayawa cak suka yi matan suna kallon ta,tsayawa kallon ta za kuyi ko za ku dauko ta kun taba ganin mahaukacin da ya amsa kan cewa shi mahaukaci ne?dallah kuyi sauri kar ku bata mana time, Nan fa aka shiga kokuwa inda Nadeeya Sam taki yarda su kama ta banda ihun neman ceto da kwala wa Inna Falmata kira babu abunda take yi,a garin haka har ta fasawa biyu goshi,ganin tana bata musu lokaci ne ya sanya doc bashir tsikara mata Alluran kashe jiki,in da a take ta kwalla ihu tare da zubewa a kan gadon, Nan take jikin ta ya mutu in da ba wasting time suka dauko ta tare da fitowa da ita daga dakin, Duk Wanda ke gidan saida ya zubda hawayen tausayin hajiya Nadeeya kar Inna Falmata ta samu labari tana ji tana gani aka sanya ta a bayan Ambulance, Kusa da ita SEN ya zo tare da mata kiss a goshi sannan yace am so sorry my love,in sha Allah za ki samu sauki zan Na zuwa duba ki take care of your self for me I love you so much,ya kare yana hawaye Ji take wata wutan tsanan shi Na Kara ruruwa a ranta tabbas da da akwai wuka a gefen ta sai ta luma masa, Doctor make sure to take care of my daughter ita kadai Gare ni ina matukar kaunar ta,in sha Allah kar ka samu damuwa Alhaji shine kalman doctor Na karshe kafin ya shiga mota, Ina ji ina gani aka rufe ni tare da Jan motan aka bar gidan mahaifina da ni,ban San ina yace su kai ni ba kila ma kashe ni za ayi halan yau ne Jan numfashi na Na karshe a duniya, tabbas da da yanda zan yi da Na gudu Na tafi wata nahiyar daban Na fara sabon rayuwa ta yanda babu Wanda ya sanni Amman kash ni tawa kaddaran da haka ta zo mun, Fitan su yayi daidai da isowan yan jaridun,Wanda cike da mamaki suke bin motan ambulance in da kallo zukatan su fal da tambayoyi, Kai tsaye Sa'eed ya wuce da su confrence Hall in SEN yanda suka yi taro jiya zaman su da be fi da 5 mints ba sai ga SEN ya shigo da makarraban sa, Sai da suka zauna yan press suka mika gaisuwa sannan SEN ya mike da kanshi, Gyaran murya yayi daga kallon yanayin sa kasan ranshi a tsantsan bace yake domin babu ko dikon faraa a fuskan shi, idanun shi sun yi jawur alamun ya sha kuka har ya gaji, Kamar kullum da sunan Allah ya bude taron sannan ya fara magana kamar haka, Hakika nin gaskia ina kara gode wa Allah da ya bani adon rai da lafiya har nake tsaye a gaban ku,nasan daga ku har aluman gari gaba daya kun zaku ku ji kundin labarin game da abunda ya faru jiya a gida Na,Wanda ko a tarihi ban taba Jin makamancin hakan ba har wasu Na tantaman Anya wannan yarinyar sa ce ko wasu suce Anya wannan asalin uban ta ne, Numfashi ya sauke sannan yace tabbas Nadeeya yarinya ta ce ita ce ya daya tilo Wanda Allah ya mallaka mun Wanda nake son ta fiye da rayuwa ta, Tabbas mulki daukaka arziki suna da shahara duk Na Allah ne,shi ke azurta bawan sa a sanda ya so kuma ya talauta shi sanda ya so,shi ke bada mulki kuma shi ke hanawa, Soyayya da daukaka ta da kuma farin jini Na duk daga Allah ne,ni Na yarda da hakan, Sannan duk Wanda ya sanni ya San ni mutumin arziki ne ba wai yabon kai Na nake ba,Amman an sani ina da kyakyawan muamala tsakanin Na da mutane Na,Wanda gama daga iyalan gida Na,abokai Na maaikata na, makota Na kai da ma sauran mutane baki daya, Hakikanin gaskia duk musulmin da yace yana zaune Allah be jarabban sa to ya duba imanin shi,ni Na yarda da jarabawa kuma a shirye nake Na karbe ta ko ya yake, Ni ban taba nufan kowa da sharri ba a rayuwa ta hasalima duk Wanda nake tare da shi da zuciya daya nake zama da kowa,sai dai kash an samu wani mara tsoron Allahn mara imani da ya jefi yarinya ta, Woto an yi anyi a kassarani Allah be bada saa ba sai aka biyo kan abunda nafi kauna a rayuwa ta sabida an san cewa Nadeeya ta ita ce weak point ita, Tabbas Nadeeya ce rayuwa ta kuma duk Wanda ya San ni ya San akwai tsantsan soyayya da muguwar shakuwa me karfi tsakani Na da tilon diya ta,wanda wasu ke cewa tun bayan rasuwar mahaifiyar ta yau fiye da shekaru 20 Na kasa Kara aure sabida gudun kar a cutar mun da ita, Hawaye ya kuma sharewa sannan ya daura da fadin ban taba expecting akwai Randa ko Nadeeya giyan wake ta sha zata iya sauraran wasu Na zagi Na bata dau mataki ba balle ace ita da kan ta,tabbas ba cikin haiyacin ta take ba,domin am her role model, Tabbas an cuce ni an kuma zalunce ni an yi hakan ne domin bata mun siyasata Wanda sun manta Allah shi ke bayar da mulki ga Wanda ya so, Ni muslmi ne Na yarda akwai kaddara sannan baran zargi kowa ba ,saidai na bar duk Wanda yayi aikin nan da fitowan Rana da faduwar sa domin an cuce mu my innocent baby dole Na kira kwararan likitan brain don ya zo ya tafi da ita asibitin mahaukata,domin bata taimako don she is mentally unstable, ya kare yana kuka sosai, Riko hannun shi Salis yayi yace is okay ba komai akwai Allah suna ganin sun karya mu ne don sun haukatar mana da yarinya Amman sharrin su kan su xai koma da yardar Allah, Ba su kadai ba hatta ni jiki Na sanyi yayi,domin ganin yanda Sen ke kuka yana maimaita kalman an cuce shi ba zai taba yafewa ba in takarar ne ba a so yayi ai da ba a biyo ta wannan hanyan ba, Gaba daya yan jaridun nan tausayin shi nee ya kama su,haba daman saidai in jifan Amman duk wani xan garin Bauchi ya San waye Senator RILWANU AUDU WAZIRI mutum ne me tsoron Allah da kuma mutunci,Sam kallmomin da yar sa ta jefe shi da su basu yi daidai da shi ba,kawai magauta ne suka yi hakan domin bata mishi siyasan sa kai mutane ba a tsoron Allah akan neman duniya ace a jefi yar mutum ta zo cikin bainan nasi ta kwashe masa Albarka haka,gaskiya Allah ya zaka maka shi ne abunda wasu ke ta fadi, Wani daga cikin yan jaridun ne ya mike tare da cewa ran ka ya Dade in har da gaske ne jifan Hajiya Nadeeya aka yi,to ai magungunan gargajiya ya kamace ta ba wai asibitin mahaukata ba..... Assalamu Alaikum mutanan arziki, ina yi wa kowa fatan Alkhairi da kuma fatan anyi zabe lafiya Ubangiji ya zaba mana shuwagabannin kasa Na gari, Hakikanin gaskia ina matukar godia ga irin karba da kuma soyayyar fa kuke nuna wa littafi Na,Ubangiji ya sakar wa kowa da Alkhairi, ina kaunan ku fisabillah, A cigaba da sharing pls, Sai ranar Monday kuma in sha Allahu. ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA NA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ......... My what's app group https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Kofa a bude take ga duk me son joining saidai duk wacce ta san bara ta Na sharhi ba to don Allah ta zauna ba sai tayi joining ba,and don Allah maza should stay away from this group domin Na mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su kofa a bude take,suyi mun magana ta wannan no: 08100046388 ............ Page four *********** Ranka ya Dade in har da gaske Hajiya Nadeeya jefan ta aka yi to ai magungunan gargajiya ya kamace ta ba Asibitin mahaukata ba?? Tambayan da wani Dan jarida ya jefo wa SEN ke nan, Madadin ya amsa shi da kanshi Alhaji Kabiru ne ya mike ran shi a Dan bace yace wai why are you people after rayukan mutane ne,can't you see irin stage in da yake and you guys are trying to rub salt on his wound,da wannan silly questions in naku, Dafa shi Sen yayi domin ya san halin Aminin nashi da Saurin hawa and hakan ba karamar barazana bace ga siyasan sa, Cikin calm voice yace allow them su tambayi duk abunda suke son tambaya,tunda ai ni daa kai Na Na gayyato su,beside ai ba wani tambayan ban haushi yayi ba,yana da gaskia don kowa ya ji statement ina ya kuma ji gidan mahaukata aka aika princess dole yayi mamaki, Pardon my friend's behavior kasan ance,abokin da zai taya ka kuka yayin da wani abun rashin dadi ya same ka shine Aminin ka Na ainihi, Kamar yanda ka tambaya yeah jifan Nadeeya ta aka yi Wanda duk mun sani Asiri gaskia ce tunda har fiyayyen halitta ma an masa ta kama sa,and kamar yanda ka fada haka ne maganin gargajiya ya kamaci Wanda aka jefe,saidai wannan jifan ta sha banban, Domin a sanadin haka brain in Nadeeya ya tabu tabi Me girma ma,ya kare yana share hawaye,Wanda bani da option sai dai dole a kaita asibitin su fara magance wannan matsalan domin wani jijiya da Is connected to her brain yaa samu matsala Wanda ya ci a gyara shi domin ceto ranta,bayan nan sai a koma Na gargajiyar ganga ganga,duk da yanzun ma ba zama za a yi ba har sai an jira likita, Wani ne ya kuma tashi domin yin wani tambayan, Hannu Sen ya daga mishi tare da cewa don Allah ku bar Ni haka,bana cikin Jin dadi zuciya ta zafi take mun,ya ci Na sha magani Na kwanta ko zan samu hutu,domin yanda Na ga daran jiya haka Na ga Rana ko rintsawa ban yi ba,na gode sosai da zuwan da kuka yi,ina me bada hakurin rude behaviors in Nadeeya Na jiya,domin ba a cikin haiyacin ta tayi ba,Na yafe mata duniya da lahira Allah ya baki lfy princess ita, Don Allah duk Wanda ya kalli video in nan make sure ya sanya Nadeeya Rilwanu Audu Waziri a addu'a,ya kare with pleading hands,yana cewa mu je Kabiru, make sure Sa'eed ka sallame su,da haka suka bar cikin confirence Hall in, ..........NADEEYAH Ni dai tun ana tafiya ina tunanin ina wannan mutanan mara sa imani za su kai ni,har idanu Na suka lumshe bacci barawo ya kwashe ni, Sun yi tafiyan mintoti kafin suka iso Teaching hospital dake nan garin Bauchi wato Specialist, Direct Psychiatric clinic suka nufa(wato bangaran masu tabuwan kwakwalwa), Parking driver yayi a bakin clinic in,inda nurses in da Doctor Bashir yayi waya da su akan su fito da stretcher (gadon daukan marasa lfy),suna bakin gurin suna jiran isowan sa, Bude kofa yayi yace where is Sister Kareematu,am here sis wata mata ta amsa tana daga hannu, Maza ku dauke ta ku kai ta ku kai ta Isolated room in da Na miki magana akai,I hope an kai komai da komai da za ta bukata ko,domin wannan ba kamar regular marasa lafiya bane,wannan daban ce,don yarinya ce daya tilo a gurin SEN kin ga kuwa dole mu kula da ita yanda ya kamata, Da mugun mamaki duk yan gurin ke kallon Nadeeya da ke kwance alamun bacci ma take abunta saidai daga yanda take baccin kasan Na wahala ne, Mamaki suke yi me zai Kawo Hajiya Nadeeya Rilwanu Audu Waziri wannan asibitin a hakan ma wai mara lfy,rashin lfyn ma Na cutar brain,to wai yaushe ta haukace ne ma and miye silan haukan nata,shine tambayan da yawancin nurses in gurin ke wa kan su, Tsawan da ya daka musu ne ya sanya suka ja ta a sukwane,kallon Sister Kareema yayi yace in kun kai ta meet me in my office, da toh kawai ta amsa shi sannan suka wuce, Daki ne Na Alfarma Wanda saida nayi mamakin ganin dakin domin maraban shi da dakin gidan yan gayu kadan ne,domin harda T.v,Air con,table and resting chair,ga wata lafiyyar gado dauke da lallausan blanket akai color white and blue ga kuma drower in jera kaya tare da mini fridge sai kuma da toilet a cikin dakin, A gefen gadon kuwa chain ne daure(wato Ankwa), A kan gadon suka aje ta tare shimfida ta,ido doctor Kareema tayi musu duk suka fice daga dakin banda,nurse Zaituna, Kallon ta tayi tace Zaituna dauko mun uniform in ta a cikin drower muyi mu sa mata in yi sauri in je gurin wancan Dan tijaran kafin ya yi mun hayaniya nayi late, Drower ta bude tare da dauko daya daga cikin jerin uniforms in da ke cikin gurin wanda Riga da wando ne kalan blue da fari, Without waste of time suka tube Nadeeya tare da sanya mata uniform in suka gyara mata kwanciya tare da ja mata barko, Shegiya Kareematu wato kwadayin ki ke hada ni da ke dake kin ga yar gidan maiko shine ke da kan ki kika sanya mata kaya ko??Zaituna ta kare tana dariyan shakiyanci, Yo Zaituna ba dole Na ba kina ji dai yace mana yar gidan SEN RILWANU ne ai wlhy dole Na shege mata ko da zata kashe ni da duka Na samu Na yagi rabo Na halan in uban ta ya ga yanda nake kula da ita har kyautan gida da mota ya bani,ina dalili in cuci kai Na akan wayancan mahaukatan mutanan,da ba komai kake samu in return ba sai duka,ta kare tana dariya,daga haka suka bar dakin tare da rufe mata kofan, Nan suka rabu ita Zaituna ta koma bakin aikin fa while Kareematu office in Doc Bashir ta nufa, .......... SEN RILWANU Amman Kabiru kana ganin karshen matsalan me nan ko,haba Amini na don Allah ka saki ranka bana son kana sanya wa kan ka damuwa am very sure by the time aka saki video in nan karshen matsalan mu ta zo sai dai mu fuskanci gaba,am very sure kiran wayan party chairman ne zai daga ka daga bacci gobe, Ai tun farko ma mistake ne da wancan dan iskankan Dan jaridan ya dauki abunda ke faruwa,gashi gulman shi ya ja masa Na sanya a kamo mun shi sai Na ci uban sa daga yau bare Kara aikin jarida ba, Da sauri SEN yace aa Alhaji Kabiru kar kayi masa komai don Allah ka bar abun nan kawai ya wuce kar mu kira damuwa wa kan mu,ba gashi komai ya tafi daidai ba,dadi Na da kai wlhy anger shi fa zaman duniya yar siyasa ce, Hmmm ni kuma wannan sanyin kan ke bata mun rai wlhy ya kare yana girgiza kafa,but tunda kace haka shike nan bazan masa komai ba, Hmmm Allah sarki Nadeeya ta ko tana wani hali yanzu sai Allah ya kare kamar zai yi kuka, Dariya Kabiru yayi yace ni kan Anya na taba ganin mutum me son yarinyar sa irin ka kuwa, Hmmm Kabiru bara ka gane bane wlhy Nadeeya rayuwa ta ce,saisa kiran wayan shi da aka yi ne ya katse mishi me yake shirin fada,share wa yayi ba tare da ya dauka ba domin wlhy ba karamin gajiya yayi ba,bacci yake son yi ma jira yake Kabiru ya tafi, Jin an Kara kira ne ya sanya Kabiru yace ka dauka mana kila important call ne,be so ba ya dai dauki wayan, Ganin No in United state of America ne ya sanya shi sakin murmushi domin ya San ba kowa bane Ila Afzaal,cike da shaukin ya dauki wayan,tare da cewa hello son, A can bangaran ma Afzaal din cike da kauna yace Hi Daddy ya kake,ina lfy klau my son hope dai ba wata matsala ko, Numfashi Afzaal ya sauke yace eh babu for now kam don kudin da Na tafi da su suna nan jibge,sai dai ina missing in ka ne sosai,ya kare kamar zai yi kuka, Dan dariya SEN yayi yace ohhh Afzaal fitina ko Nima nayi missing in ka yaro Na,saidai abubuwa marasa dadi sun faru bayan tafiyan ka,domin Nadeeya hauka ne tuburan ya kamata yanzu haka ma Na kira doc bashir ya tafi da ita, Oh good Ashe abun babba ne,ai ya wuce yanda kake zato,kai to Allah bata lafiya,ni dai yaushe xan dawo don Na fara gajiya da zaman USA?? Numfashi SEN ya sauke sannan yace not now son ka cigaba da zama har sai wannan kuran ta lafa tukun Na,zan sanya manager yayi maka transfer in 5mil make sure to take care of yourself bye,be jira amsan sa ba yayi ending in call in, Kallon Kabiru yayi da ke cin abinci yace kai ka ji mun yaro ana ba guri yana ya kwanta wai dawowa yake son yayi, Dariya Kabiru ya sheke da shi sannan yace ka ji Dan nema to ya dawo yayi me ana tsaka da wannan halin,oho fa ni kan zan shiga ciki Na huta mayi waya kawai,in ka fita kace da Sa'eed duk Wanda ya zo nema Na ace Na sha magani Na kwanta,kai kawai Kabiru ya gyada masa don ya cika shinkafa a bakin sa, ............Kaduna State 44 barrack hospital , Zaune yake shi kadai a cikin office in sa,sanye yake cikin white and black dress,shiru yayi tare da kura wa guri guda ido alamun he is lost in thought, Ko karan bude kofan da shigowa doctor Mujaheed be ji ba,sai da ya taba shi tare da cewa Helllooooo wai tunanin me kake yi ne haka har baka ji shigowa ta ba, Dago idanun shi yai masha Allah Na furta domin mutum ne me cikan halitta da haiba kyakkyawa dashi bara a kira shi fari ba haka zalika bara ace da shi baki ba,yana da long nose ba wai can ba kai in fact dai he damn cute and handsome,(domin duk creation in ubangiji banu munana), Kallon Abokin Na shi yayi for some seconds sannan yace wlhy Mujaheed ya tabbata mutanan nan transfer za su mun hakan ma wai within 2 weeks,Doctor NAMEER ABDALLAH ya kare cike da bacin rai, Numfashi Mujaheed ya sauke sannan yace ikon Allah kuma ina suka aika ka, Dan guntun tsaki ya ja sannan yace wai Bauchi fa wata Teaching hospital nan aka jefa ni........ Aradun Allah Na gaji๐Ÿคช, Don girman Allah Arin ga yi ana kankaro mutunci gurin yin sharing and commenting๐Ÿ™๐Ÿป, Ina mika godia Gare ku masoyan littafin nan da kuma ni Na gode sosai Allah saka da Alkhairi, Sai kun ji ni gobe in Allah yayi muna cikin masu rai da lfy, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi๐Ÿ™๐Ÿปโค๏ธ ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHI TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ......... My what's app group l https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Ina maraba da duk me son shiga wannan group in saidai in har kin San ba sharhi zaki nayi ba toh don Allah kiyi zaman ki kar ki shiga,haka ma Na miji Na roke ku da sunan Allah kar Na mijin da ya yi joining group in nan domin akwai matan aure a ciki,Na mata ne xallah๐Ÿ™๐Ÿป Ga masu son a tallata musu hajojin su kuwa suna iya tuntuba ta ta wannan layin: 08100046388 ........... Page five ********** Dan guntun tsaki ya ja sannan ya ce wai Bauchi fa wata teaching hospital nan aka je fa ni, Murmushi Mujaheed yayi sannan yace but Bauchi is a very nice city mutumi Na domin I have been there twice or thrice haka nan,duk da ba wata girma can Gare ta kamar nan ba and nan mun fi su yawancin abubuwa,but am very sure za kayi enjoying zaman ka a can,domin sun iya masa sosai,and ka ga kuma kai kana son masa,saidai fa mutanna Bauchi akwai Dan banzan rowa ya kare yana dariya, Saisa ake musu kirari da yan Bauchi naman keya,ya kare yana Kara dariyan shakiyanci, Tsaki Doc Nameer ya kuma ja sannan yace ni ina ruwana da Rowan su sai kace karamin yaro kawai daga zuwa Na gari sai Na hau roko haba dallah, Ni fa ba fa kyan garin ko kyan mutannan garin bane a gaba na, duk abunda ke garin ni bana so Na fi son a bar Ni cikin family Na, Hannun shi Mujaheed ya dafa sannan yace haba mana Nameer sai kace ba Na miji ba duk wani maaikaci ai ya kamata ya zama a cikin Jinin jikin shi yi masa transfer, don Allah kar ka bar Dan wannan abun ya Dame ka ka ji, Hmmm Mujaheed bara ka gane bane wlhy duk abun da zai sanya ni nisa da Angel to wlhy Na tsani wannan abun with passion, ko kadan bana son nisa da ita,and sanin kan ka ne babu yanda za a yi Mama ta bari Na tafi da ita har Bauchi ni fa shine damuwan da nake yi, Zama Mujaheed ya gyara sannan yace haka ne kam Mama ba bari za tayi ku tafi ba kam amman be faithful my friend in sha Allah komai zai zo maka da sauki am very sure sai ka bani labarin irin dadin da Bauchi ta maka domin garin akwai dadin zama, Dan kallon shi Nameer yayi sannan yace ni kam dai ko yar bauchin nan kake son Kara ta biyu ne Na ga yanda kake backing up in garin nan bil hakki, Dariya me Dan sauti Mujaheed yayi sannan yace kai mutumi na, shi din ma dariyan yayi kafin yace in tayi tsami ma ji ai, Duk shiru suka Dan yi kowa Na dan danna wayar sa kafin can Doc Nameer ya dauko tare da cewa yauwa ni kam friend ka ga wani video kuwa dake ta trending daga jiya zuwa yau, Hmm wlhy Na gani Nameer abun ya matukar daure mun kai wlhy ohhh duniya wlhy ina tsoron wannan rayuwan yanzu tsaban dibewan Albarka ai ubanka ko Dan giya ne bara ka fito bainan nasi kana masa irin wannan zagin karan dagin ba,balle ace mutum me tsoron Allah me dattaku irin SEN ace wai yau yar shi kwaya daya tilo ta fito cikin media ta masa zagin fitan hankali sabida bat ta kunya,daman tsiyan ka nuna wa yaro kana mugun son shi ke nan nan zaka ga yana fallin iskanci ya kare cike da Jin haushi, Goshi Nameer ya dafe sannan yace dadi Na da kai ke nan Mujaheed yanke hukunci ba tare da kasan cikkkaken me ke faruwa ba, Ka san me ya mata ne tayi masa hakan?a yanda aka ce akwai shakuwa da soyayya me karfi a tsakanin ta da shi meya sa for all past years in da suka yi spending together bata taba masa hakan ba sai yanzu dole akwai wani abu a kasa, Miye a kasan iskanci ne fa irin Na yaran masu kudi wai su suna koyi da dabiar yahudawa,domin ita kanta Nadeeyan an ce bata cika zama a nan gida Nigeria ba sai da ta kammala karatun ta tsaf da aikin ma an dauka a can turan za ta yi,wlhy Nameer ba komai bane fa kawai iskanci ne fa da samun guri,Amman ace mutum kamar Audu Waziri wlhy duk duniya an sheda mutum ne me son aluma da kuma tausayin talakawa,ni in ba don yar sa bace sai nace tayi ne don ta bata masa siyasan sa, Da ido kawai yake bin Mujaheed domin shi fa haka yake magana ce da shi har ta Allah tsine mamaki yake me ya Hana shi karantan Mass com ko wani law sai kuma ya kare da karatun malamin jinya, Kayi shiru kana kallo na ko kai goyon bayan yarinya kake yi ne ya kare yana tsare shi da ido Wanda hakan ya baiwa Doc Nameer dariya, Dan darawa yayi sannan yace ba ka da dama wlhy Mujaheed ni a ina Na san ta da har zan bi bayan ka,kawai dai ina magana ne daga abunda nayi tunani,yau da ace kamar daga waje ne wani ya shigo yayi masa irin wannan zagin sai muce daga magauta ne don ba a so ya ci,amman fa yar sa ce ta cikin sa, Allah Na tuba duk da ance sanin mutum sai Allah amman ya ci ace ta san halin uban ta ciki da waje,kai ni fa sai sa Sam bana son politics kila ma hadin baki suka yi da yar ta shi tayi masa hakan domin ya samu sympathy in mutane a kuma Kara ganin kima tausayi da kuma mutuncin shi,ka zo ka tsaya kana kare shi kamar muna court room ya kare tare da mikewa, Mujaheed in ma mikewan yayi sannan yace ai daman politics in ko hakan ne da Sen ya ban mamaki wlhy,kar wani abun da Dan Adam zai yi ya baka mamaki Mujaheed domin yanda ka ga mutum ka bar shi kawai,fatan mu dai shine Allah yasa muyi kyakkyawan karshe ya kare tare da fita daga cikin office in,da Ameen Mujaheed in ya amsa sannna ya bi bayan sa yana me yi masa wani hiran daban, Nadeeya....... Ba ita ta farka ba sai karfe 10 Na safiya sakamakon Aluran baccin da doctor Bashir ya shigo ya tsikara mata, A hankali ta fara bude idanun ta Wanda sun riga da sun kumbura tsaban kukan da ta ke ci kwana 3 da suka wuce,a hankali ta ji kanta Na juyawa Wanda ta sanya hannu tare da dafe kan tana kokorin bude idanun ta Tas ta samu ta sanya wani abu a cikin cikin ta domin ba karamin yunwa take ji ba,don rabon ta da cin abinci tun shekaran jiya, Hamdala take yi wa ubangiji a ranta da ya kubutar da ita SEN be sanya an mata komai ba domin har ga Allah ta tsorata time in da doctor Bashir suka zo daukan ta, ganin she is still alive ne ya sanya ta fara bin damin da take jiki da kallo, Mamaki take yaushe aka kawo ta cikin dakin nan ina ne ma nan gidan waye and be take yi,ko dai ya sanya an kawo ta nan ne don ya ji dadin kashe ta, Mamaki ne ya kamata tare da bude baki sakamakon ganin uniform sanye a jikin ta,Wanda harda no a jikin rigan domin ita ce no 354, Hasbunallahu wa ni imal wakil,shine kalman da take Nana ta wa,in har ta canka daidai nan dai asibiti aka kawo ta ,saidai no in da ke jikin ta ne bata san Na miye ba,a hankali ta sauko daga kan gadon duk da ba wani karfi bane a jikin ta ta fara bin dakin da kallo, Sam brain in ta yaki responding balle ta samu ta fahimce inda aka kawo ta,saida idanun ta suka sauka akan chains in da ke jikin gadon, A mugun tsorace tayi baya tare da furta kalman Na shiga uku ni Nadeeya kar dai abunda nake tunani ne,kar dai gidan mahaukata wannan mugun ya sanya aka kawo ni,shike nan Na kade shine kalman da take fadi tana kuka, Ganin in ta zauna kuka ba inda zai kai ta domin burin ta be wuce ta ga ta tona wa SEN asiri ba,tana son duk duniya su san shi wani irin mutum ne,Amman abune me matukar wahala, Kamar Wanda aka zabura tayi saurin mikewa domin bara ta zauna da hankalin ta a maida ta mahaukaciya ba, Tunanin guduwa ne ya fado mata a rai, da za ta samu ta gudu daga kasar nan ma baki daya ta koma can wata kasan ta faro rayuwar ta daga farko yanda SEN bare ma San yanda take ba, Da Sauri ta nufi bakin kofan saidai duk yanda ta so ta samu ta fice kasawa tayi,tayi kuka kamar ranta zai fita ta kuma ja wa SEN Allah ya isa ya fi 10 basket, nan kasa ta kwanta looking so very helpless tun tana kuka,bar tayi shiru tana tunanin mafitan da za ta samar wa kan ta, ..............Kaduna Shigowan shi ke nan parlor in hajiyar sa,bakin shi dauke da sallama,da gudu gudu sauri sauri wata yar cute baby Wanda bara ta wuce 2 and the half years ba ta nufo shi tana ware hannaye,ta fadi ta mike tana fadin Papeee daga ganin yanda take masa kasan murna take da zuwan shi, Nufan ta yayi da sauri yana dariya domin yanda take gudun tana talle yan tiny legs in ta abun dariya ne, Daukan ta cak yayi tare da juyi da ita sannan ya rungume ta tsam a kirjin shi yana Jin kaunar yarinyar ta shi har cikin Jinin shi, Lallausan suman kanta ya shafa sannan yace my Angel wa ya bar miki suman ki a bude??, Mama ne ta fadi cike da gwarance,mama ce ta bar mun kan Angel ita a bude haka,kai ta daga mishi tana dariya tare da tsale a kan jikin shi, Lalle Haanan wato ni za ki yi wa Shari don kin ga Papan ki ko,ai ko zai ta fi ya bar Ni da ke a cikin gidan nan wata yar kyakkyawan dattijiyar mata ta fadi tana fitowa daga cikin kitchen, Fuskan ta ta boye a kirjin shi tana dariya domin yarinyar ba dai wayo ba, Shi kan shi Nameer dariyar yake domin drama in Mama da Haanan Sam baya kare wa,domin mama maida ta take kamar wata babbar mata tayi ta tsokana ta tana kiran ta Tsohuwa, Dan risina wa yayi tare da cewa an wuni lafiya Mama, cike da faraar ta ta amsa shi da Alhamdulillah my son ya gurin aiki kuma, Kai ya dan Sosa sannan yace wlhy mama gurin aiki ba dadi don maganar ma da nake miki yanzu sun yi mun transfer zuwa garin Bauchi, Kai mama ta jijiga irin Na nuna alhini sannan tace ayya Abu be yi dadi ba Sam wlhy Amman ya aka iya toh,haka xa muyi hakuri ka tafi,gashi ni ba kowa Na sani a garin Bauchi ba,Amman ba komai Ubangiji ya sanya hakan shi yafi zama Alkhairi, Ameen thuma Ameen Mama hope dai babu wata matsalan,aa Sam babu matsala Babana Allah yayi maka Albarka ta kare ka a duk inda kake,Ameen ya Allah mama ta,ya kare yana jan yatsan kafan Angel, Kuma yaushe ne tafiyar taka ,wlhy mama within 2 weeks suka ce, Kai da wuri haka,toh Tsohuwa sai ki Bini a sannu don papa dai Bauchi zai tafi ya bar Ni daga ni sai ke, Dariya ya sanya sannan yace aa mama da Angel ita zan tafi,hararan wasa tayi masa sannan tace ka ma isa,ai tun da kaki Kara auran nan to ba yanda za ka da ita, Ace magana kullum mun yi tayi ke nan haba Baba Na yau margayiya shekarun ta biyu da rabi da rasuwa da ya ci ace ka Kara aure wlhy ko don yarinyar nan kar ta taso babu uwa a tattare da ita, Numfashi me zafi ya furxar,domin har Ila yau in aka yi maganar mutuwar RA'ISAAH ji yake kamar jiya ta bar shi s doran duniyar nan shi kadai da little Hanaan in shi, Nan take idanun shi suka kafa a hankali yace kiyi hakuri mama wlhy ba wai naki jin maganar ki bane ko auran ne bana son karawa, wlhy mama tunda Ra'isaa ta rasu ta tafi da duk wata soyayya ta,bata raye Amman har yanzu bugun zuciya ta tata ce bana Jin akwai wata macen da zan kalla har ta burge ni balle har Na ji shaawar auran ta ,ya kare kamar zai yi kuka, Numfashi Mama ta sauke tana me tsananin Jin tausayin Nameer in domin ita kanta sheda ce ba karamar kauna yake wa margayiya ba, Shike nan my son Na fahimce ka Allah ubangiji ya cigaba da yi wa Ra'isaa rahma ya sanya ta huta in namu ya zo ya sanya mu cika da imani, Ameen thuma Ameen ya amsa tare da mikewa ya shimfida Haanan da already tayi bacci akan sofa yace Mama bari na Dan shiga Na rintsa zuwa la'asar zan tashi, toh son abincin fa,bara ka bari ka ci abinci ba ka ji dadin kwanciya,aa mama abincin nan zai n tashi ya kare tare da shigewa daki,da kallon tausayi mama ta bishi domin ta san ba wani baccin da yake ji kawai hiran margayiya da aka yi ne ya tado mishi inda yake Mai kaikayi, ............Doc Bashir Tsaye yake da waya a kunne alamun waya yake yi hakan ma da mutum me mahimmanci,ranka ya Dade tana nan a cikin koshin lafiya duk wani abun bukata da kace duk mun sanya mata, yanzu haka ma bacci take yi, Ban ji abunda aka ce daga can bangaran ba sai ji nayi Bashir Na cewa aa ranka ya Dade ba a riga an fara ba, Sorry ranka ya dade,injections in ne bamu da shi a nan Amman Na aika yana kan hanya gobe ko jibi za mu fara mata in sha Allah ka kwantar da hankalin ka yanda kake so haka zai faru ,Dan dariya yayi sannan yace godia nake ranka ya Dade Allah Kara girma...... Ayi mun afuwa da typing errors pls am trying all my best ban yi edit ba kuma typing in dare ne and keyboard ina yana bani matsala wlhy, Masoyana ina Jin dadin irin karfin gwiwan da kuke bani,Allah saka muku da Aljannah, Sai kun jinu gobe in sha Allah, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ......... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Kofa a bude take kowa Na iya joining Amman,in har kin gan ba sharhi bane zai kawo ki don Allah to ki yi zaman ki ba sai kin shigo ba,and don Allah wannan group in mata ne xallah domin akwai matan aure a ciki,maza Na hada ku da Allah stay far away from this group please๐Ÿ™๐Ÿป, Gama su son a tallata musu hajojin su kofa a bude take har yanzu za su iya mun magana ta wannan layin: 08100046388 ........... Page Six ********** A week later, Nadeeyah na hango kwance a kuryan gado ta zuba wa guri daya ido alamun tunani take yi, Hawaye ne ke zubowa daga cikin idanun ta,domin yau kimanin sati daya ke nan da kawo ta dakin nan aka rufe ta,bata cika ganin mutane ba sai doc bashir yakan shigo ya duba lafiyar ta a ce war sa wai tana da ciwon hauka,Wanda ta Riga da ta san sam ita lafiyar ta klau,sai sister kareematu da ke shigo mata da abinci Wanda sai ma an tambaye ta me take so ta ci, SEN ya zo gurin ta har kusan sau hudu Amman sam taki ma ta bashi daman ganin nata domin toilet ta shiga ta rufe kan ta a ciki,in akwai hallitan da ta fi tsana a doran kasa toh bayan SEN ne, Shiru kawai tayi tana juyayin yanda rayuwar ta ta kife lokaci guda,ace wai for all people yau ita ce Nadeeya Rilwanu Audu Waziri ke kwance a kan gadon asibiti da sunan wai ta haukace,ga shi wani abun haushin ta sha attempting guduwa saidai sam kasawa take because shi kanshi dakin da take ciki akwai security pin code Na bude shi da rufe shi,Wanda har Ila yau bata san miye pin in ba, Jin alamun bude kofa ne tare da Dan magananganun mutane ya sanya ta gane dakin ake kokarin shigowa,kila doc Kareematu ce ta kawo mata abinci, Yau dai by all means sai ta bi bayan ta a boye ta ga numbers in da take dannawa kofar ya bude,ko tayi mata Alkawarin kudi in har ta taimaka mata ta gudu domin ta ga alama ita mata ce me kwadayi da son abun duniya, Saidai fuskan SEN da doctor Bashir da ta gani ne ya sanya ta ji ranta ya kuma baci,da sauri tayi kokarin mikewa don shigewa toilet coz ita dai bata ga amfanin zama tayi magana da wannan mara tsoran Allahn ba, Cike da raunanan murya ta ji ya kira sunan ta princess,bata dago ba haka zalika bata ce da shi uffan ba, A hankali ya taka tare da nufar inda take ya kamo hannun ta tare da cewa am sorry my love jiya ban samu Na zo ba wlhy kina rai Na meeting ne ya rike ni, Dago da kanta tayi tare da watsa masa wata irin kallon tsana,sannan tace can you pls take off your hands a jiki Na,I told you to stop touching me da wannan hands in naka ko ka manta ne, Murmushi yayi tare da cewa Allah sarki Nadeeyan daddy wlhy mutanan nan da suka miki wannan abun ba zan taba yafe musu ba, Wow SEN shine abunda ta katse shi da shi wai was all this drama necessary I mean all the tears all the lies all the stories da kayi cooking up, har wai da kan ka ka sanya a kawo ni gidan mahaukata Daddy are u for real,ta kare tana kallon shi, Daga ni har kai har wannan mugun doctor in mun san I am not mad lafiya ta kalau,me yasa bara ka bar Ni nayi tafiya ta ba,okay kana Jin tsoron zan tona ma asiri ne right ,fine SEN I promise you baran ce wa kowa koami ba I will hold my mouth to my self,all I want from you is my freedom wlhy am sick tired of all this game da kake playing ta kare tana kuka, Tsunguna wa SEN yayi shima yana hawayen tare da kallon ta,yace haba Nadeeya do u think ina enjoying kallon ki haka ne??God knows irin rashin baccin da nake samu kullum akan ki, Nadeeya I love you so much ke ce rayuwa ta and duk abun nan da kika ga ina yi sabida ke ne wlhy, Kallon shi tayi da sauri sannan tace sabida Ni fa kace tana nuna kanta da yatsa,murmushi tayi Wanda ake kira ya fi kuka ciwo sannan tace kana yi dai sabida siyasan ka da kuma mutanan gari, Daddy in har kana sona kamar yanda kace why not bara ka kawo karshen wannan abun ba,I won't you let me go, Na fada ma I will surely hold my lips, Kai ya girgiza sannan yace doc ni yana ke ga kamar ciwon nata dada karuwa yake yi kuma kace da ni tana samun sauki, Stop changing the topic pls ka tsaya muyi magana wlhh ma gaji shine abunda Nadeeya ta fadi tana kuka,hannun ta ta hade guri biyu in a pleading way tana fadin Na roke ka pls SEN set me free I want my freedom, I promise you in Na fito zan tafi can inda bara ka sake gani Na ba don Allah ka ji, Kai ya girgiza sannan ya kara da wlhy an cece ni sanin kan ki ne Nadeeya bara iya jure zama babu ke ba,ni dai nawa kaddaran ke nan,ba komai akwai Allah in sha Allah zai saka mun akan abunda aka miki,Na sanya ana saukan qurani da sunan ki,sannan ni da Alhaji Kabiru kullum muna tsayuwar dare da sadaka tare da rokan Allah ya baki lafiya,ga Doc bashir ma is trying his best day and night don ya ga kin samu lfy in no time,kar ki damu Nadee dee ta you will be fine in no time zai zamo kamar ba a yi ba,za mu cigaba da rayuwar mu kamar da ko Doctor SEN ya kare yana kallon Bashir, Da sauri ya daga kai yana fadin yes haka ne,hakuri kawai za ki kara Hajiya Nadeeya domin mu samu mu kawo karshen problem in ki ki koma gida, mutane Na haukan da ya fi naki ma su warke balle naki ai me sauki ne, Dariya ta kwashe da shi sannan tace wlhy Doc bashir kai ma baka tsoron Allah wai ni kam nawa wannan mugun ya baka ne ka dage lalle sai ka lagaba mun cutar da bani da,1 mil,5mil,10 mil 20 or 50 mil,ta kare tana tsare shi da idanu, Kame kame ya soma yi yana uhmm ahhmmm wani irin magana ke nan nawa kuwa zai bani bayan kuma aiki Na ne kula da marasa lafiya, Wani darinyan ta kuma sannan tace it shows akan face in ka baka da gaskiya ka karbi kudin Senator,look doc wlhy I promise u in har ka sake ni Na fita I will double the amount in da ya baka, Jin hakan ne ya sanya SEN cewa doc ka ji ko wlhy Nadeeya ta,ta tafi shike nan ya tabbatan dai princess ita hauka tayi,ya kare yana share hawaye,baran iya cigaba da zaman dakin nan ba doc mu je ka raka ni akwai abunda nake son fada maka, Karasowa yayi gurin Nadeeya tare da shafa kanta sannan yace my baby girl ni zan tafi sai jibi in sha Allah ga shi fav chocolates in ki ne Na kawo miki,take care of yourself ko,yanzu zan ga doctor game da case in ki ko xa a canja miki treatment ne don Na ga jikin naki sai Kara rashin dadi yake yi, Hawaye ke zuba a idanun ta, tana ji tana gani suka fita daga dakin ba tare da sun saurari ko sun tausayawa irin rokon da take musu ba,hurgi tayi da ledan chocolates in suka zube,tana kuka tana I don't want your money or chocolates freedom ina nake so,tunda Na bika ta lallami kaki yarda SEN mark my words sai Na tona ma asiri shine ihun da tayi Wanda am very sure daga shi har doc sun ji, Kai kawai ga girgiza ba tare da yace komai ba suka nufi office in Doc bashir, Suna shiga ya daga hannu cikin zafin rai tare da kwada wa Doc bashir wata irin Mari me zafi da Kara,tassss kake ji, Da sauri ya rike kumatun sa da yake ji suna masa radadi,yace Yallabai lafiya, Cike da bacin rai SEN yace lafiya kake tambaya ta Dan uban ka,ni za kayi wa karya Bashir ni?ya nuna kansa, Na gani jiyan nan sai da Na sanya aka kawo maka 5 mil duk za to Na kayi nisa akan aikin da na baka ace one simple job ka kasa mun sai cin kudi Na kake sabida gani Dan iska me kudin banza ko, Da sauri ya ce a a yallabai wlhy sam ba haka bane, aluran ne har yanzu basu iso ba sun dan yi wahalan samu ne, Dallah ka mun shiru yau abu kusan sati har yanzu ace Alura ya kasa samu,kasan baka shirya ba kace we can trust you with this iyeee ya kare cikin fada, Shi dai doc be da baki da ya wuce hakuri don hakuri ya ringa ba wa SEN yana mishi Alkawari kan in sha Allah gobe za a kawo, Da kyar ya samu ya sauko sannan yace da shi and wlhy Bashir Na ga alaman kana da son duniya muddum Nadeeya tayi maka wani offer a cikin haukan ta ka karba sai Na ci uban ka,sai Na daure ka tas kai da zuriar ka in har Na shigo ban ga yarinya ta ba,am doing this for her on good so bana son Jin wata bad news daga gare ka shine abunda SEN yace babu wasa a tattare da shi, In sha Allah bara a samu ba baran baka kunya ba sir ,daga haka SEN be Kara cewa komai ba ya fice daga office in,duk Wanda ya gan shi sai ya kwashi gaisuwa inda duk wanda ya gaishe shi sai ya mai kyautan kudi, saisa yake kara siye zukatan mutane,domin video in da ya sanya aka yi Na biyun ba karamin sympathy ya samu a gurin mutane ba,domin haka aka din gi zuwa masa gida jajje wasun ma da yawa be san su ba,daga masu zuwa jajje sai masu zuwa kan sun san malami me karya sanmu,sai masu zuwa kan cewa sun fara yi wa Nadeeya sauka,ba karamin tausaya masa mutane suka yi ba,wanda hakan ya kwantar wa party hankali suka bar shi ya cigaba da Takaran sa, Da harara Doc bashir ya bi bayan SEN tare da Kara susa kumatun shi sannan yace Allah ya isa na,haka kawai ni na san miye tsakanin ku da yar taka,nasan me ka mata kana neman maida komai kaina,(ni ko nace madallah ai kadan ka gani ko ba son kudi ba ), Tsaki ya ja tare da kiran Wanda yayi order in aluran a hannun shi,nan fa ya hau surfa mishi tijara,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,hakuri mutumin ke bashi kan gobe da sassafe za a kawo mishi,da haka yayi ending call in, Kamar yanda mutumin yayi alkawari kuwa sassafe aka kira doc bashir kan ya zo ya karbi order inshi,abun da yake ta jira ke nan tun tuni,be bata time ba ya je ya karba Wanda aka sako masa a cikin box,kai tsaye hospital ya nufa don so yake yanzu yanzu ya fara mata aluran don ya ga alaman SEN zai iya cin uban shi in be yi ba, A hanyan shi ta shiga hospital in ne ya ga isowar doc Kareematu wanda daman shi ya kira ta tun yana hanya,a tare suka yi parking sannan suka shigo, Kareematu aluran fa sun iso Na sanya wada ya kai mun office ina kuma yau nake son Na fara mata, Kallon shi tayi sannan tace kai doc gaskia ni ina Jin tsoro kasan fa wannan aikin na da hatsari za a iya kwace mana lasisin mu muddum asirin mu ya tonu, Ke dallah dadi Na da ke tsoro,ga dai ki da son abun duniya Amman akwai tsoro, taya asirin mu zai tonu daga ke ne fa sai ni muka San wannan batu, Ke din ma don ina kaunar ki da arziki ne ya sanya Na fada miki,don ko banza ai ina moruwa da ke ya kare yana kashe mata ido daya, Ni dai gaskia Bashir ina Jin tsoro wlhy Baban ta fa babban mutum ne,in ya sani baka tunanin mu kare rayuwar mu a prison, Oh shit Kareematu wlhy Sam baki gane wa nace miki ki saki jikin ki,aluran nan ma fa bake za ki Na mata ba ni zan nayi are u happy now,ya kare yana kallon ta Gaskia ni kam Bashir ina Jin tsoro, Dan kakai ya girgiza sannan yace na gane matsalan ki bani account details in ki,ko da yake ma bar shi ina da shi I think, Dan wayan shi ya daddanna sannan yace da ita,Na miki transfer in 1.5mil are u in for this or no, Idanu ta zaro jin amount in da ya ambata,bakin ta har rawa yake tace are are you seri ous Bashir, Dan dariya yayi sannan ya nuna mata debit alert in da aka masa,wanda take ta ji karan shigowan message, Haba dan ihu tayi tare da rungume shi tana wlhy ya shigo Bashir kai 1.5 fa,shafo bayan ta yake yi cike da iskanci yace wannan somin tabi ne my love,in har kika bani goyan baya har mota sai Na canza miki, Cike da murna tace wlhy har goyan jiki ma na baka Doc Bashir ina, Shegiya kareema yaushe rabon da ki kira ni da haka,fari tayi irin Na yan bariki sannan tace ai yau a guest house in ka ma zan kwana, dariya ha kwashe da shi sannan yace to shi mijin naki fa,dallah ya tafi can ce masa zan yi night gare ni domin yanda ka faranta mun din nan sai Na jiyar da kai dadi Na musamman, (wa'iyazu billah, wannan rayuwa da muke ciki yanzu abun tsoro ne ace mata da auran su suna zina,Allah ka dada kare mana imanin mu da mutuncin mu), A tare suka shiga dakin Nadeeya a kwance suka tarar da ita kamar me bacci, Kan gadon Kareematu ta hau tare da shafa kan Nadeeyan sannan tace sannu maza tashi lokacin magani yayi,Nadeeya bata ko kula ta hasali ma ko ido bata dago ta kalle ta ba, Kareematu tashi ki dauko drip in da muka shigo da shi ki daura mata domin she looks very weak and pale am sure taki sake wa ta ci abincin kirki, Tashiwa kareematu tayi tare da dauko drip in,hannun Nadeeya ta kama tare da fara neman jijiyan ta,ko motsi Nadeeyan bata yi ba domin ita kanta tana bukatan karin ruwan,don gani take tsaban kukan da take yi ruwan jikin ta Na gab da kare wa, Cike da nutsuwa, Kareematu ta samu ta huda Nadeeya tare da daura mata ruwan, A hankali ruwan ya fara shiga jikin ta wanda ta lumshe idanu ,domin ji tayi kamar kanta Na juyawa,a sannu bacci yayi awun gaba da ita sakamakon aluran baccin da Kareematu tayi a cikin drip in, Kallon Bashir tayi da ya gama hada aluran a sirinji guda biyu yana nufo Nadeeya ya sanya tace Doc anya kuwa wannan doss in basu mata yawa ba ,Na ga aluran nan duk masu karfi ne and biyu Na ga kana shirin yi mata, Dan dariya yayi sannan yace my Kareematu ke nan,ai da uku ne ma soke dayan nayi domin zai iya zamo mata matsala nan gaba,sabida in no time nake son ya fara aiki ya sanya zan Na mata biyu daya a cikin drip while daya a jijiya,ya kare yana juye ruwan aluran a cikin drip in, While dayan a nutse ya kama hannun ta tare da tsikara mata a jijiyan ta,yauwa kin ga an gama Na yanzu saura kuma an jima da yamma in sha Allah, Da mamaki ta kalle shi bayan ya ja wa Nadeeya bargo tace kana nufin sau biyu za a Na mata a Rana,yes sau biyu ne hope dai kin kalli yanda Na dama aluran da yanda nayi mata don in bana nan ke za ki Na mata, Da kai kawai ta amsa shi sannan suka baro dakin yana cewa yi sauri ki karasa abunda kike yi nima Na samu Na gama aikin gaba Na mu samu mu tafi don wlhy tun dazu da kika di ga mun Zuma a baki hankali Na ya fara barin jiki Na........ Na san akwai lots of typing errors hakan kuma ya faru ne sabida rashin edit in da ban samu nayi ba,so ana mun afuwa pls๐Ÿ™๐Ÿป, Hakikanin gaskia bani da bakin da zan gode muku yan group ina bisa irin goyan baya da kaunar da kuke nuna mun saidai nace Allah ya saka da Alkhairi ya kuma bar kauna๐Ÿฅนโค๏ธ, Ina mika sakon gaisuwa da kuma godia Gare ku masoyan book in nan Wanda Na sani da Wanda ban san su ba,Allah dai ya bar zumunci, Sai kuma gobe in Allah me komai me kawo ya so, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ........ My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Ina marhaban da duk me son shiga wannan group in saidai in har kin san ba sharhi za ki Na yi ba toh don Allah kiyi zaman ki kar ki shigo, haka zalika maza na roke ku da Allah kar kuyi joining in group in nan domin Na mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ......... Page seven ********** Tabbas rayuwar duniyar nan abun tsoro ce Na kuma Kara yarda in har kana raiye to kana da sauran kallo,domin lokaci daya Nadeeya ta koma abun tausayi,duk wani me imani in har ya ganta sai ya zubda mata hawayen tausayi, Yau kusan kwana biyar ke nan doc bashir nayi mata injections in nan ba daga kafa kullum biyu safe da yamma,irin yawan doss in da yake bata ya sanya ya fara nuna effect in shi akan ta, Domin a halin da Nadeeya ke ciki yanzu ita kanta ba gane kan ta take yi ba,haka kawai cikin dare za ta fara ihu tana tsigan gashin kanta tana kuka tana surutai,ko kuma ta mike tayi ta rawa tana tafi ita kadai, Sai abun yayi kamar ya lafa da ya kuma mata aluran shi ke nan sai kuma ta burkice ta fara behaving abnormal, Ba karamin dadi doc bashir ke ji ba ganin aikin sa is working domin Jinin Nadeeya Sam be da karfi ya sanya within no time injections in ya fara aiki,kila da ukun yake mata,wataran saidai ta buge kowa ta fita da gudu tsirara kan titi tayi hauka tuburan, Nadeeya brain inta ya fara samun matsala, don ita kadai sai ta dauki fiye da awa tana hira da iska,ko kuma ta tashi da gudu tayi ta zagaye dakin tana tsalle,abun dai gwanin ban tausayi, Yana da assurance tunda har ya fara aiki haka in har ya cigaba da bata to burin su zai cika zata yi hauka Na har gaban abada bara ta taba samun lafiya ba, ........... Kaduna Doctor Nameer ko tsaf ya hade kayan abun bukatun sa domin a gobe Sunday yake son shiga Bauchi Monday yayi reporting ya fara aiki, Zaune suke da Mama suna Dan taba hira Haanan Na jikin shi yana mata wasa, Hope dai ka dauki yajin da Na zuba maka a roba dai ina,Dan murmushi yayi sannna yace eh mama Na dauka,ai ko kin taimake ni domin ban San ko abincin restaurants in su Sam ba dadi, Dariya mama ta sanya sannan tace Amman kam Babana baka da dama wai ni kam me ka maida Bauchin ne,yanda kake ganin Kaduna city ne haka ma bauchin take fa,garin Sam ba laifi ai nan muka kai yar gidan Aminiya ta hajiya Salma, Shi dai be ce da ita komai ba domin Allah ya gani ba son zuwa garin nan yake ba, Can kuma sai ya kalle ta yace Maama ko dai za ku shirya mu tafi tare ne, Ai nan ma dariyan ta kuma sanya wa sannan tace yau kun ji mun Babana wai sai kace wani karamin yaro,kawai sai Na shirya mu bika gurin aiki,ni ba matar ka ba ina mahaifiyar ka,ai ka ga ranar aure yau da da matar ka ce ai ba sai ka tsaya neman shawaran ta ba, Fuskan tausayi ya sanya sannan yace ayya Mama na yanzu don Allah bara ki Bini ba zan dai siya miki Sheraton wannan sallan a dinka miki, Dakuwa tayi mashi da hannu sannan tace kaci gidan ku Babana to rike kayan ka in dai sai Na bika Bauchi ne kai sanin kan ka ne sarai tun kafin Na Auri Alhaji Allah ya jikan shi nake sanya kaya masu tsada,dariya ya kwashe da shi domin shi din ma ya fadi ne don Jin bakin mahaifiyar ta shi, .......... Alhaji Abdallah Mai nasara Dan haifaffen garin Kaduna,daga shi sai kanwar shi guda daya tal me suna Hajiya Bilkisu iyayen su suka haifa, Baban su me rufin asiri ne sannan ya yi kokarin wadata su da duk wani abun da yaro xai bukata na rayuwar yau da kullum,haka zalika mahaifiyar su mata ce jajirtatciya akan yaran ta domin sun samu tarbiya daidai gwargwado, A haka har suka girma Abdallah ya samu gurbi a makarantar ABU inda ya hada degree in shi, dake mutum ne me son kasuwan ci sai ya fada kasuwa inda Allah ya sanya wa harkan Albarka budi sai shigo masa suke yi ta ko ta ina, A haka ne watarana ya je garin Yola ya ci karo da matar sa kyakkyawan bafulatana in da a take ya nuna yana bidan auran ta,ba tare da bata lokaci ba aka tsaida musu Rana,domin an yi dace itan ma tana kaunar shi sannan yana da gida aiki har da abun hawan sa, Ba tare da an ja lokaci me tsayi ba aka daura auran Abdallah da Amaryan sa Aishatu in da aka kawo ta unguwar badarawa anan cikin Kaduna, Akwai shakuwa soyayya hakuri da kuma tsantsan biyayya a zaman Aishatu da Abdallah domin mata ce me kawaici da sanin ya kamata,ya sanya yan uwan shi suke Jin dadin zama da ita, auran su da wata bakwai lokacin ma har an samu rabo a tsakanin Allah ya dauki ran mahaifin Abdallah, Wanda ba karamin taba su yayi ba,an ci kuka kam domin sun yi babban rashi kafin suka fauwala wa ubangiji komai, Allah ya Albarkaci Abdallah da Aishatu da samun yara uku biyu maza sai Autar su mace, Dan su Na fari sunan shi Abubakar Sadiq Wanda a yanxu Baban Engineer ne,yana da aure harda yara uku suna xaune ne a garin Lagos,sai Na biyu Nameer,sai kuma Autar su Nana Khadija Wanda tai aure ita ma tana zaune a garin Abuja harda Dan ta Na miji guda daya, Nameer Abdallah matashin saurayi ne me ji da jini a jika,akwai shi da cikar halitta da kwarjini tare da saukin kai, Likitan mahaukata yake da burin karanta tun yana yaro ya sanya Baban shi biya masa kudi ya tafi Cairo don samun gurbin karatu a can, Mutum ne me taka tsantsan da Rayuwar sa hakuri rashin magana da kuma tsananin tsoron Allah,mutum ne me yawan ibada tare da tsarkake da kuma mika alamuran sa ga Allah,ya sanya ya kasance mafi soyuwa a cikin yaran su domin shi Sam be da hayaniya ko matsala,mutum ne me balain kokari,sannan in dai abu be shafe shi ba to Sam baya sanya baki ciki, Allah ya tsare shi baya shaye shaye balle neman mata,yana aji uku ne Allah ya hada shi da Ra'isaah Abdul Aziz,Wanda balarabiyar Egypt ce, soyayya ce me karfi tare da shakuwa ya shiga tsakanin su a kan kanin lokaci,ta zamo wani jini Na jikin shi,tunda yake be taba so ba sai akan Raa'isah Wanda yake Jin ta har cikin zuciyar sa, A nata bangaran ma hakan take,ba tare da bata lokaci ba ta gabatar da shi wa mahaifin ta ganin kamalan sa ya sanya kai tsaye mahaifin nata yarda da batun soyayyar ta su,ganin ya kusa gama wa ya sanya aka bar bikin sai bayan ya gama karatun shi, Cikin ikom Allah kuwa gamawan shi da wata guda aka daura masu aure wannan ranar kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha don murna haka yake ji,domin shi kan shi mamakin irin yanda yake tsananin kaunar Raa'isaah yake yi, Hidiman biki aka yi aka gama sannan aka bashi Amaryan sa domin ya sanar da ita shi bare iya nisa da iyayen sa ba,a malali Baban shi ya Gina masa gida me kyan gaske inda nan aka sanya Amarya, Rayuwar auran su rayuwa ce me cike da tsantsan soyayya da fahimtar da kuma tattalin juna,ko wannan su rige rigen faranta ran Dan uwan shi yake yi,duk Wanda ya ga yanda suke gudanar da Rayuwar auran su to tabbas sai yai shaawa, domin Raa'isa mata ce ta kwarai me tsaninin biyayya, babu abunda daya ke boye wa daya,Raa'isah ta zo Nigeria bata Jin ko zo a yaran Hausa Amman bata dauki wata uku ba aka fara koya mata hausa, Watan su uku da aure Allah ya azurta ta da samun ciki,tattali kula da soyayya take samu daga gurin Nameer, Wanda hakan yayi daidai da rasuwar Mahifin su Alhaji Abdallah me Nasara sakamakon hatsarin jirgin sama da suka samu, Ba karamin jijiga Nameer yayi da Jin mutuwar mahaifin shi ba domin akwai shakuwa me karfi tsakanin su,sun yi kuka sun ji ba dadi Amman hak a karshe dole suka hakura suka fawala wa Allah komai suka cigaba da yi masa addua, A hankali rayuwa ta cigaba da tafiya cikin Raa'isah yana dada girma hutu Nameer ya dauka a gurin aiki domin bata cikakken kulawa,kama daga kan girki wanki,wanke wanke shara duk shi yake mata,ganin ta yi nauyi already, Duk wani abun da zai faranta mata shi yake yi,haka zai kashe Rana daya ya zauna kawai yana yabon irin kyan da ta Kara sakamakon samun cikin nata,Wanda ita har mamaki take yi domin muni ta ga ta yi tare da kumbura Amman kullum Nameer kyau yake cewa tana masa, Tabbas Nameer da Mama sunyi playing role me girma a rayuwar ta more especially ma lokacin cikin ta,domin duk wani kula da soyayya gata ta gani a gurin su,a haka har cikin nata ya shiga watan haihuwa,ba yanda mama bata yi da shi ba kan ya dawo da ita gurin ta zata fi kula da ita Amman Sam yace aa shi zai kula da Noor in sa,sunan da yake kiran ta da shi ke nan, Suna zaune ranar Alhamis da safe yana matsa mata kafa yana mata hira akan in ta haihu bayan suna in sha Allah zai kai ta gida ta je ta ga family in ta,ba karamin dadi ta ji ba nan tayi ta murna tana she can't wait ta haihu, Wannan daran haka suka raya shi cike da soyayya da shaukin juna,Wanda cikin dare naguda ya tashi mata gan ga gan ga,daukan ta yayi cak sai hospital, saida suka isa sannan ya samu ya kira mama, Suna nan tsaye har asuba Amman Allah be yi ta sauka ba,har suna shirin shiga da ita tiyata cikin iko Na Allah sai ga kan jinjira a nan ta samu ta haife santaleliyar baby girl in ta fara me kyau da ita,in da ita kuwa Raa'isah ko shurawa bata yi ba tace ga garin ku nan rai yayi halin shi, Ko da sakon mutuwar ta riski Nameer yankan jiki yayi ya fadi ya suma kwanan shi uku be San yanda kan shi yake ba,kafin ya farfado, Da kyar da addua aka samu ya dawo cikin haiyacin sa domin kusan zare wa yayi,don ko kadan be yi tsakanin wai mutuwa Noor in shi za ta yi ba,ko ana gobe za ta mutu zama suka yi tare da tsara irin yanda zasu yi rayuwa tare da babyn su ashe rashin sani tafiya za tayi ba tare da ko ta san me ta haifa ba,babu ruwan Allah baya barin wani Dan wani ya ji dadi,Alhamdulillah Raa'isaah tayi mutuwar shahada,(ya Allah kar ka dauki ran mu sai kana farin ciki da mu), Kwanan su 5 a Asibiti sannan aka sallame shi,gidan ta mama ta wuce da shi domin ganin lamarin Nameer in dai da ayoyin Allah, A haka aka yanka wa yarinya rago tare da maida mata sunan mahaifiyar ta suna kiran ta da Haanan,Wanda Sam ba a yi taron suna ba sabida rasuwar da aka yi, Da kyar da nasihohi aka samu Nameer ya dawo haiyacin sa domin ko kadan ya kasa jure rashin mahaifin shi da LOML a cikin shekara guda, Tun da aka samu ya dawo hankalin shi ya kara komawa wani shiru shiru,kullum yana zaune shi kadai yana tunanin Raa'isaah,tare da daukan soyayyan duniya ya daura wa Haanan,ba ya shiri da abunda zai taba ta ko kadan, Ba yanda ba ayi da shi akan ya kara aure ba,Anty Bilki har gida ta kawo masa tayin diyar ta Amrah kan ha aura ,Amman Sam ya nuna baya so, Domin gani yake bare taba samun mata kamar Noor ba ta so shi tun bayi da komai Allah ne yi za ta more shi a yanzu da samu ke ta xuwa masa ba,saisa ya dagr duk wasu kudadan shi daga Maman sai Haanan yake wa spending, Kwata kwata yaki bude zuciyar sa yau fiye da 2 years balle har ya sanya wata diya mace a ciki domin a cewar sa tun bayar rasuwar noor to be ga wata ya macen da ta yi masa ya aura ba,and da aka Dame shi yayi aure ko Dan angel in sa,shi he can take care of her alone, bare juri ganin ya auro mata tana cin uban Haanan in sa ba,ya sanya Sam be ma da raayin Kara auran, ..........Back to story Har bakin mota Mama da Haanan suka rako shi sai kuka take tana mika masa hannu kan ya dauke ta ya tafi da ita, Jin kukan nata yake har ranshi domin ya San Mama sam bara ta bashi Angel su tafi can uwa duniya kam, Addu'oi sosai Na tsari da fatan saa mama tayi masa sannan suka rabu ya ja motar shi tare da barin gidan zuciyar shi Na zafi,don kukan da angel ke yi har ransa yake ji, Sai da ya biya 44 yayi wa mujaheed sallama tare da daukan sauran abubuwan shi har mota mujaheed ya rako sa yana masa tsiya kan in ya je Bauchi pls ya duba mishi ya SEN da wannan mara ta idon yarinyar ta shi suke ciki,da toh kawai doc Nameer ya amsa shi domin shi miye hadin shi da Sen balle wata yar sa,shi da da xai je asibiti ko ina zai gan ta har ya San ya suke ciki oho, da haka ya shige motar shi tare da daukan hanyan Bauchin Yakubu,sai mu ce Allah ya kiyaye hanya Doc Nameer..... Keep on sharing and commenting pls, Ina matukar godia da irin kaunar da kuke nuna mun,Allah saka da Alkhairi, Sai kuma zuwa Monday in Allah me komai me kowa ya so. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Ina maraba da duk me son yin joining Amman in har kin San bara ki Na yin comment ba toh don Allah kar ki shiga,haka zalika don Allah maza kar su shiga,domin group in mata ne zallah kuma mafi yawan su matan aure ne๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 .......... Page eight ********* Tafiya good five hours ne ya shigo da doctor Nameer cikin Bauchin Yakubu,ba karamin gajiya ya taro ba domin shi ya tuko motan da Kansa,it's been a while since da yayi long journey haka nan, Tunda ya iso yake bin tsarin garin da kallo,shi ba kowa ya sani ba balle ya ce zai nufi gidan wani ya sauka,gashi yamma ta fara yi domin be yi iso wan wuri ba sabida tsaye tsayen da ya ringa yi a hanya, Ganin be da option in da ya wuce ya nemi hotel ya kama,domin ya samu gurin kwana,Dan tsaki yayi tare da cewa tsiyan ka zo guri baka san kowa ba ke nan wlhy duk sai ka bi ka zama wani bako, A ZARANDA HOTEL,ya yada zango inda ya shiga tare da biyan kudin dakin kwana uku, dole ya dan tsaya Na kwanakin kafin ya samar wa kansa,mahallin da zai zauna,domin Sam be kaunar zaman hotel, A reception ya tsaya tare da biyan kudin daki Na kwana uku,aka ba shi key in dakin sannan masu aikin hotel suka dauko jakar kayan shi tare da nufar dakin Na shi da shi, Godia yayi musu bayan sun aje sannan suka wuce,dakin ya bi da kallo,wow daki ne me kyau kamar mutum yana gida, domin komai akwai a ciki,gado kujera harda fridge, Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya fada kan gadon,oh my god am damn tired wlhy,ya kare yana shafe goshi,so yake ya dan huta kafin ya samu yayi wanka ya sanya wani abu a cikin nashi ko zai samu gajiyar jikin shi ya bar shi, Ringing in da wayar sa ke yi ne ya sanya ya bude idanun shi a hankali tare da janyo wayan domin ya San ba kowa bane ila Mama, Saidai ganin bakuwar no ne ya sanya shi mamaki,har ya yanke be dauka ba,sai da aka kuma kira sannan ya dauka, Hello brother ya ji muryan ta ya doki kunnan sa,a hankali yace shit ba dai yarinyar nan ba, Haba Brother yanzu kana ji Na ka share ni,ta kare cike da shagwaba,gashin kan shi ya shafa sannan ya ce Amrah yaushe kika shigo Nigeria and ina Maman ki, Hmmm ai Yaya Nayi fushi kana tafiya Ashe jirgin mu yana landing I wanted giving you a surprise ya sanya ban sanar da ku zan zo ba,saidai am not lucky Ashe ka tafi Bauchi ta kare a shagwabe, Hmm Amrah Na tafi ban ma Dade da isowa ba ya amsa ta da kyar, ayya sorry brother Na Na san ba Wanda ka sani a Bauchi you will be so very lonely ko dai in zo ne, Idanu ya zaro a kasan makoshi yace what,a fili kuma sai cewa yayi kee Amrah are you okay kuwa,an ce miki ko ina ne irin Manchester ehyeee taya za ki biyo ni Bauchi, Hey common sweetheart nima dai wasa nake maka,ko kace Na zo am not coming ta kare tana dariya, Tsaki yayi a hankali domin shi fa haukan wannan yarinyar ke hada ta da shi sam bata da kan gado, Ina Mama shine abun da ya tambaye ta Jin tana son kamo wata shirmen nata daban, Ga ta nan kusa da ni in bata,idanu ya zaro Jin wai mama Na gefen ta take wannan haukan sam rayuwar turai be yi ba wlhy,hello are you lost again ta tambaya tana fari da ido kamar yana ganin ta, Bata shine abun da kawai ya ce da ita,ba musu kuwa ta mika wa mama wayan, Sallama ya fara mata sannan ya gaida ta,ta amsa cike da kauna sannan ta tambaye shi ya hanya ya sauka lfy,wlhy Alhamdulillah mama saidai gajiya gaskia Bauchi da nisa,dan murmushi tayi sannan tace ai ka dade baka yi tafiya bane Babana ya sanya kake ganin nisan Na shi har haka, Gaskia kam baki ji jiki Na ba wlhy mama kamar an mun duka,dariya ta Dan yi sannan tace haba dai son to waye zai buge ka din,shima dariyan ya dan yi sannan yace Ashe Amraah ta zo? Eh wlhy kana fita ko 30 mints baka yi ba sai ga shigowar ta,basu ma dade da dawowa da Haanaan daga Havilla sun je shan ice cream ba, Nan take yayi kicin kicin da fuska yace haba mama nawa Angel take da za a wani kaita shan ice cream in mura ya kama ta fa,gaskia a ce da ita kar ta kuma fitar mun da yarinya wani wai yawon shan ice cream,ya kare da iya kar gaskiar sa, Baki mama ta bude tana mamaki irin wannan rashin kunya ta Nameer,sannan tace zan iya bata sai ka fada mata da kan ka,uban da ya fi kowa son yar sa, Ayya Mama Na ga dai har yanzu Haanan baby ce ko 3 years fa bata yi ba,ai ice cream is not good for her health at all,ya kare a marairaice, Hmmm son ke nan,ni kam a huta gajiya sai mun yi magana later hajiya Salma na kira na,da haka ta mika wa Amraah wayan tata, Jin abun tace ne ya sanya shi kashe wayar da sauri domin Allah ya gani bayi da energy in tsayawa Jin abubuwan da wancan wawiyar yarinyar za ta ce masa, Toilet ya fada kai tsaye bayan yayi placing order in abincin da zai ci,wanka yayi da ruwan zafi ya gasa jikin shi sosai yanda wahalan za ta warware sannan ya fito, Shafa ya gama yi tare da combing in gashin shi, sannan ya sanya light ash in jallabiya a jikin shi,yana fesa turare yayi daidai da knocking in kofar dakin shi, Ko da ya bude Waiter ne dauke da abincin da yayi order karba yayi tare da musu godia sannan ya koma daki, A nutse ya zauna bayan yayi bismillah ya soma cin abincin shi cikin kwanciyar hankali, wow Ashe dai mutan Bauchi an iya abinci ya kare yana murmushi shi kadan sa, Saida ya cinye abincin tas, yayi realizing ashe dai yana dauke da yunwa a cikin sa,a nan cikin dakin Na shi ya gabatar da Sallan Magrib da isha'i sabida rashin sanin masallaci da ke kusa, Around 9 ya gama komai tare da hayewa kan gado ya janyo laptop in shi tare da kunna wani American movie ya shiga kallo,ganin idanun shi Na ya ji ne ya sanya shi rufe laptop in tare da yin Azkar in bacci ya ja blanket sai bacci, .........Senator Shigowan shi ke nan a matukar gajiye cikin part in shi domin ba karamin gajiya yayi a meeting in party da suka yi yau ba,babban rigan jikin shi ya cire tare da mikawa Saa'eed yana cewa kai wlhy am really tired, Sannu yallabai ko dai sai an hada ma da tausa ne yau,aa Saa'eed in nayi wanka da ruwan dumi ma zan ji daidai,da haka suka kara sa shigowa cikin parlor in shi, Ido waje da matukar mamaki yake kallon shi,Afzal ya kira sunan shi a Dan tsorace domin ba karamin mamakin ganin shi yayi ba Sam be dauka zai dawo Nigeria yau ba beside jiya jiyan nan suka yi waya ya sanya a tura masa kudi kan ba nan kusa zai dawo ba, Cike da tsantsan farinciki Afzal ya taso tare da fadawa jikin SEN yana cewa Dad ya ka ga surprise ina? Fito da shi yayi daga cikin jikin shi yace Why are you back Afzal? Kallon Saa'eed Afzal yayi sannan yace Mal can you leave us alone,sorry sir shine abunda yace da sauri tare da ficewa daga part in yana mamakin me ya kawo Afzal gidan kuma, Afzal why are you back, ina ce I told u not to come back until I'm done with things over here, Fuskan yara Afzal yayi tare da narai narai da idanu kamar me shirin yin kuka yace but Daddy I have missed you ne,and kai ka ki bari Na in dawo,Na gaji da zama ni kadai a can USA and beside I thought you are done with things over here ne ai tunda kai da kan ka kace da ni I shouldn't panic za ka yi taking control in komai da komai, ya kare yana zumburo baki, Yeah Na sani but am not done working out things yet,bara ka gane ba Afzaal abubuwa sun cabe da yawa wlhy,SEN ya kare tare da zama yana dafe goshin shi, A kusa da shi ya zauna sannan ya dafa hannun shi cikin soft voice yace yeah Dad Na san you are doing all your best so relax pls don't be over stressing your self out, Numfashi kawai SEN ya sauke ba tare da yace komai ba,domin shi kadai ya San irin halin da yake ciki a yanzu, Duk shiru suka yi for so mints kafin can Afzaal yayi breaking shirun da tambayan,How is Nadeeya doing? I hope she's coping well? Hmmm Afzaal ke nan Nadeeya is not in a good shape at the moment, but Doc Bashir is trying his best, Can we go and see her right now pls? Aa Afzaal dare ya Riga da yayi yanzu, and ka ga yau ka dawo daga USA am sure akwai gajiya a jikin ka,and ni kai Na a gajiye nake ka dai bari gobe da safe sai mu je ka duba ta,bayi da yanda ya iya toh kawai ya ce da Sen sannan SEN ya wuce dakin shi domin watsa ruwa, .........Doc Nameer Tunda yayi asuba be koma bacci ba,wanka yayi bayan ya kammala Azkar in shi sannan ya fito ya shirya cikin black trouser and white shit Wanda ba karamin karban shi suka yi ba, Breakfast in da yayi order ya zauna ya ci cikin kwanciyar hankali, sannan ya tattara duk wani abun bukatun sa ya dau car key in shi tare da rufo dakin ya sauko kasa da key in, A reception in ya aje musu key,sannan yace da su ya fita sai ya dawo,Allah kiyaye suka mishi sannan ya fada motar shi,da taimakon Map location da yayi setting a wayan shi ya iso Asibitin da aka mishi transfer, inda yayi parking a inda ake parking motoci,bayan an nuna mishi fanin da yake wato fanin Psychiatric, Shiru kawai yayi a cikin motan yana me kare wa building in asibitin kallo tare da mutanan da kai kawo a cikin asibitin, yayi kusan mintuna yana zaune shi fargaban fitowa ma yake ji, Like ka je gurin da baka San kowa ba and ba wanda ya sanka ya fi komai ban haushi,be ma san ta ina zai fara ba ko wa zai fara samu ma oho, yayi kusan 10 mints a cikin motan yana ta nazari kafin can yayi shahada yana me buda kofar motan,bakin shi dauke da adduar ubangiji ya sanya ya fara a saa, Allah ya bashi ikon da zai amfanar da mutane daga ilimin da yayi masa,Allah ya Hana ni zalintar kowa kuma ka tsare kowa daga zalinta ta,shine addu'oin da yake bakin shi yayin da ya fito daga cikin motan... Ina matukar godia da irin so da kaunar da kuke nuna mun,Allah ubangiji ya bar mu tare, A cigaba da sharing and commenting pls, Ina yi wa kowa fatan Alkhairiโค๏ธ๐Ÿ™๐Ÿป. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin San ba sharhi bane zai kawo ki toh don Allah kar ki shiga, haka zalika maza don Allah kar suyi joining domin group in mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su,contact me via: 08100046388 .......... Page nine ********** Cike da takun nutsuwa fuskan shi Na kallon kasa har ya shigo cikin clinic in hannun shi dauke da takardu, Mutane daban daban ke kai kawo,Wanda yawanci nurses ne da kuma doctors sai workers, sai kuma tsirarun masu jinya da suke sanye da uniform a jikin su,don du samu su sha iskan safiya tare da hasken ranar hantsi, Da ido yake bin su da kallo abun tausayi ganin haukan da suke yi tuburan,adduar samun lafiya yake wa ko wannan su, Hey Mr Handsome in da ya ji an ambata ne ya sanya shi ja ya tsaya cak,domin tabbas ya san da shi ake yi,and duk Wanda ya kira shi da wannan sunan most be one of his old school friends and mate, Da mamaki ya juyo domin ganin waye haka,a tsaye ya ganshi yana zuba masa murmushi, Shi din ma murmushin ya maiyar masa tare da bin shi da kallon mamaki,tabbas ya gane shi, course mate in shi ne Wanda zai iya ce wa ma suna mutunci ba laifi domin har auran shi ya zo, canza wayar da ya yi ne ya sanya shi losing in contact in shi, Doc Habeeb long time no see,Nameer ya ce yana mika mashi hannu, Ka bari kawai mr Handsome I have been trying your no for a long period of time bana samun ka,har Na zo Na hakura, Ayya wlhy Habeeb line ina ne ya samu matsala Na canza sabo,sai kuma nayi losing contact in ka,how have you been,wai me ma ya kawo ka Bauchi, Dariya doc Habeeb ya sanya sannan ya ce see you ai kai zan wa wannan tambayan domin Bauchi kam ai garin mu ne,and wlhy a nan Na samu aiki,so ka ga am working here kai fa me kake yi a Bauchi, Hmmm bari kawai Habeeb ni ba Na manta ba Ashe kai Dan Bauchi ne wlhy transfer aka mun daga 44 xuwa nan hospital in jiya shigowa ta ma, Ayya toh ubangiji ya sa da abunda ya tare,where is madam ko ka bar ta a can masaukin ka,am very sure yanzu kam kuna da babies ko, Jin abunda ya fadi ne ya sanya annurin fuskan Doc Nameer daukewa cak,lura da hakan ne ya sanya Habeeb cewa am sorry friend ko Na fadi abunda be dace bane, Aa sam baka fadi abunda be dace ba ya daure ya ce,sannan ya kara da Alhamdulillah we are blessed with a little beautiful daughter, saidai unfortunately Noor ta koma ga me sama gurin haihuwar angel, Allahu Akbar am so sorry for your lost friend,Habeeb ya ce yana girgiza kai,domin ba karamin mamakin mutuwar Tata yayi ba,and ya tausaya wa Nameer in domin shi kanshi sheda ne da irin kaunar da ke tsakanin Nameer da Margayiya, Ubangiji ya mata rahma ya jikan ta sannan ya raya bayan ta,Ameen ya Allah Habeeb thank u so much, Haba babu komai Mr handsome, so ina angel in take,wlhy Na baro ta Kaduna a gurin mama jiya da zan taho, Allah sarki Allah ya raya ta bisa sunnah sannan yayi mata Albarka ya kuma baka mata ta kwarai Wanda za ta maye maka gurbin noor ta kuma rike Haanaan da amana,murmushi kawai Nameer yayi domin shi yana ji a jikin shi har ya koma ga Allahn sa bare kuma Kara soyayya ba balle har a kai ga batun aure, A fili kuwa cewa yayi me hali baya fasa halin shi Habeeb har yanzu dai surutun Na nan,na biye ka sai mu kwana kana mun zuba, Dariya Habeeb in yayi sannan yace ga ka kai kuma miskili ba baka kaunar surutu ko kadan saisa Sam bara ka iya zaman gida Na ba ashe domin daga ni har Madam da little boy in mu surutu gare mu, Wait Habeeb wai kana nufin kayi aure,dariya ya dan yi sannan yace getting to 2 years ke nan da aure Na har Allah ya kawo karuwa mun samu baby boy, Kai Masha Allah ubangiji ya raya shi da imani Allah ya kade fitina a zaman ku,ameen ya Allah doc Nameer ashe dai za mu Kara haduwa ikon Allah sai gashi guri daya za mu Na aiki,kai it was so nice seeing you again, Smile Nameer yayi yace it was nice seeing too,ni dai yanzu nuna mun office in senior Doc in da ke gurin nan nayi reporting don Na samu mu fara aikin da kake murna an hada mu guri daya, Dariya Habeeb yayi sannan yace bara ka gane bane,wlhy,Nameer haduwa da Wanda ka sani tun before dadi gare shi,mu je in gwada ma office in shi,sunan shi doctor Bashir sai kayi a hankali don mutumin Dan banza ne, Kai kawai Nameer ya girgiza domin in dai surutu ne da gulma Habeeb to ya iya shi kamar wata mace, Har bakin office in doctor Bashir Ubaidullah ya rako shi sannan yace da shi in kun gama da shi ma hadu a new office in ka ko nawa,da ki kawai ya amsa shi sannan yayi knocking in kofar bakin shi dauke da sallama, A zaune ya tarar da Doc Bashir bayan yace da shi ya shigo,seat ya nuna mishi alamun ya zauan,bayan ya zauna in ne,yake tambayan shi daga ina, Nan Nameer yayi masa bayani kan daga kaduna aka mishi transfer nan, Saida ya kare masa kallo sannan yace ina takardun naka, Akan table ya aje masa,sannan Bashir ya shiga dubawa a gadarance,ganin komai ya cika ne ya sanya shi dagowa yace well doc Nameer Abdallah Na ga takardun ka,komai normal ka koma gida daga gobe za ka fara aiki, Da mamaki Nameer ke kallon shi why zai ce ya koma sai gobe ya dawo bayan shi ya dauka ya zai fara aiki,sai sa ma yayi sammakon sassafe, Yana kokarin magana ne ya ji an bango kofan,a zuciye Bashir yace wannan wani irin Jaki ne haka zai bugowa mutum kofar office, ganin Nurse Kareematu ce tsaye tana watsa mishi kallon banza domin ta ji me ya ce wato ni ce jakar shine kalman da ta furta tana hararan shi, Dariya ya dan yi sannan yace dadi Na da ke saurin fushi wallahi ai ban San ke bane,tsaki ta ja sannan tace wai ka je kayi baki, Da mamaki ya maimaita kallman baki kuma ni kuma suka ce suna nema, Ji wani tambayan iskanci Bashir in ba kai suke nema ba meyasa zan zo Na fada ma,SEN da wani matashi, Jin sunan da ta ambata ya sanya da sauri Mike wa sannan yace haba Kareema why baki fada mun since ba kika sa zan bata masa lokaci ya kare yana gyara zaman lap coat in shi, Nameer ya kalla sannan yace I got important issues a gaba Na so see u tomorrow kawai,ah Doc kace sabuwar hannu muka yi,Kareematu tace tana me bin shi da wani irin mayen kallo, Jin abunda ta fadi ne ya sanya Nameer mikewa tare da watsa mata wani irin wulakantattcen kallo sannan ya bar office in,cike da mamakin wani SEN ne ya zo cikin asibitin nasu, Doctor Bashir kuwa yanda kuka san zai yi wa SEN sujjada tsaban dukawa yana gaida shi,fuska sake SEN ya amsa shi tare da tambayan ya aiki,domin ba karamin murna yayi ba da jiya ya kira shi a waya ya sanar da shi plan in su Na ta working out, Afzaal ya gaida wanda ya amsa shi cike da isa da gadara kamar Dan sarki,sannan suka nufi Isolated room inda aka killace Nadeeya, Tun daga waje suke jiyo ihu da dariyar ta da alamun surutu take da kanta take irin wannan mugun dariyan, Saida ya rubuta pin code in sannan kofar ta bude suka samu suka shiga kofar ta rufe, A dantamalin kasan tiles suka same ta tayi zaman yan daukan karatu gashin kanta ya sauko sun rufe mata har fuska,Wanda su take irgawa wai don ta ga yawan,su sai ta kai quarter in counting in Sai ta manta shine abun yake bata dariya, Da ido Afzaal yake bin ta da kallo domin ya kasa yarda wai Nadeeya ce wannan zaune a kasa hakan nan da sunan tayi hauka, Kusa da ita SEN ya zo tare da taba shoulder in ta yana fadin princes look who is here to see you, Juyowa tayi a razane don Jin an yi mata magana saidai Sam bata gane me yace ba,karaf idanun ta suka sauka a kan fuskan Afzaal, Wata iriyan ihu ta sanya me mugun Kara Wanda saida kusan rabi yan cikin clinic in saida suka ji a ciki kuwa har da Nameer Wanda ke Dan zagawa don ganin ya tsarin gurin yake kafin zuwa gobe ya fara aiki, Kamar Wanda aka tsikara ta mike da sauri har tana harde kafa tana kusan faduwa,flower vase in jikin gadon ta ta dauka kafin kowa yayi auni ta kwada wa Afzaal a goshi Wanda nan ya fashe kalban kuma ta yanka mishi fatan goshi nan take jini ya balle masa, Wata iriyan Kara ya sake sakamakon azaban zafin da yake ji da kuma yanda jini ke zuba masa yake yi,baki bude Doc da Sen ke bin ta da kallo domin tunda ta fara haukan nata bata taba duka Ko attempting in ji wa kowa ciwo ba in ba kanta ba, Kafin sukai ga mamakin ya sake su tayi wata super in Albarka tare da fitowa akan Afzaal Wanda saida ya kai kasa, Wuyan rigan shi ta cukumo Wanda ya baci da jini,idanun ta Na fidda hawaye tana ihu ta hau cizon shi tana Marin shi ta ko ta ina a fuskan shi, Ihu yake domin ba karya ba karamin azaba yake sha ba,domin in ta kama fatan yanda ka san ta samu fatan rago ko kaza yanda take ja ga shi zafin Marukan nata yake ji har cikin brain in shi, Ihu yake yana fadi Daddy help me pls zata kashe ni,ina Nadeeya bata ma San yana yi ba duka take mishi ta ko ta ina kamar Wanda Allah ya aiko ta,tana kuma kan ihu tana surutan da ni kai Na ban San me take fadi ba, Ganin tana kokarin kashe shi da duka ne ya sanya doc Bashir danna wani red button Wanda yayi alarming in nurses su taho da sauri akwai matsala, Ai ko cikin sauri sai ga su Sister Kareematu da kyar aka samu aka banbare ta daga kan Afzaal tana ihu tana cizon nurses in tana fadin su bar ta sai ta kashe wannan dan iskan mara tsoron Allah,a bar ta ta ga bayan shi,domin barin irin wannan mugayen shi da Sen a doran kasa masifa ne domin Jinin su ya Riga da ya halatta,shine irin ihun kukan da take yi,da kyar da sidin goshi aka tsikara mata aluran bacci tare da kwantar da ita,tare da sanya mata chain a hands inta,ganin tayi bacci ne ya sanya Doctor Bashir cewa Kareematu ta ja Afzaal a je a gyara masa ciwuwukan shi,in an gama ya same su a office in shi, Hannun SEN ya ja tare da fitowa da shi daga dakin har suka iso office in shi jikin SEN a mace yake da abunda Nadeeya ta aika ta, Zaunar da shi Bashir yayi tare da ibo mishi ruwa me sanyi a cup daga dispenser ya mika wa SEN,yallabai ga ruwa ka samu ka sha, Kofan SEN ya buge cike da tsantsan bacin rai Wanda yayi sanadiyar tarwatsewan cup in, In sha ruwan me Bashir ruwan uwar ka kake son Na sha ya kare tare da wanke fuskan doctor Bashir da Mari,(Sen irin mutanan nan ne da Sam basu Iya controlling anger in su ba,in ran su ya baci in ba duka suka yi ba basa Jin anger in zai fita ko in ce irin masu saurin hannun nan ne), Da hannu biyu Bashir ya dafe kumatun shi domin ba karya Marin ya shige shi, Cikin zafin rai SEN yace Amman wlhy Bashir ban taba ganin Dan iska da ya raina mun wayo ba irin ka,Dan uban ka kace da ni Nadeeya tayi hauka ita kanta bata san waye ita ba balle ta san su waye a kan ta ya kare yana tsare shi da ido, Ba karamin baci ran Doc yayi ba Amman haka ya daure yace ranka ya Dade kayi hakuri,wai hakurin uwar me zan yi kana nufin 50 mil in da ka karba a banza ne ko me? Aa sam SEN ba haka bane, wlhy Na rantse ma da girman Allah a halin da ake cikin nan Nadeeya is not in her normal senses, tabbas ta yi nisa a hauka sabida injections In da nake bata, In har ta haukace a taya ta gane Afzaal har tayi attacking in shi tana neman kashe shi,za ka fada mun gaskia ko sai Na sa an daure mun kai domin wlhy babu Wanda ya isa ya ci kudi Na ya kwana lfy Dan uban shi ba a yi shi ba, Zufan goshin shi Doc ya goge yana Jin radadi a kan kumatun shi har yanzu kafin yace, Ranka ya Dade maganar gaskia wlhy Nadeeya ta samu tabin kwakwalwa a yanzu haka,saidai one thing da nayi observing shine,har yanzu zuciyar ta ta kasa manta abunda kayi mata Wanda kila yana da hadi da wannan yaro da kuka zo tare,domin tun da muke da ita ko yatsan wani bata taba kamawa ba, Tayu mun tsayar da aikin brain in ta mun kuma sanya shi kamuwa da tabuwa sabida aluran da muke bata amman abubuwan da ke heart in ta fa,ranka ya Dade daga gani akwai abunda kuka mata kai da Azaal Wanda ta kasa manta shi har yayi motsa ciwon nata har tayi attacking in ta, Dan numfashi ya ja sannan yace sir zan iya sanin miye kuka mata da zafi har haka duk da tana cikin hauka ta kasa mantawa,domin ga dukkan alamu yarinyar nan zalintar ta kuka yi, Baki a bude SEN ke bin bashir da kallo kafin can yace,lalle Bashir ka mance da waye kake magana,yanzu don asaraa a zuriar ku ta kare ni ne zaka kalli tsaban idona kace Na zalunci yarinya ta Na sanar da kai me muka mata,Dan uban ka har kayi girman da za ka fada mun wannan maganar banzan,ya kare tare da nufo kanshi,Wanda tsoro ya cika basir dam domin har fitsari ya fara digawa a wandon Shi, don ya ga alamun bugun bura uba SEN zai yi masa a cikin office in nan, Afzaal ne yayi saurin riko shi Wanda shigiwan shi ke nan saman kan shi dauke da bandeji, Take it easy dad kar ka ji masa ciwo,sake ni son Dan bura uba ni wannan matsiyacin ke fada min maganar da ya zo masa,Dan uwar shi dan Kabiru ya kawo shi ya ci arziki,saisa ni Sam ban so nan din ba Amman Kabiru ya nace,ka sake ni in samu in fasa wa Dan iska baki, Gam Afzaal ya rike shi yana daddy pls try to control ur anger mu samu solution domin Na ga anya Nadeeya tayi hauka kuwa,I can see so much hate in da take mun daga cikin idanun ta, A gaban SEN doc Bashir ya zube yana me rogon SEN afuwa kan ya yafe masa yayi kuskure,da kyar aka samu SEN ya hakura bayan ya kafa wa Doc last warning kan ya tsaya iya inda aka aje shi, Duk shiru suka yi kowa Na tunanin ta ina ne mafita domin kan SEN gabadaya ya kulle gani yake da daga inda aka haukatar da Nadeeya matsalan shi ta kare,zagi da cin mutuncin da take masa zai kare,Amman me abun da tayi yau din nan ba karamin dada tsorata shi tayi ba ,although an ce tayi haukan but abun Na ranta wanda wat if wataran ta fada a inda be dace ba fa shike nan ta tona mishi asiri fa,kai ina bare yu ba shine abunda ya fada yana me girgiza Kansa, I got an idea shine abunda doc ya fadi,go on dad yace da shi,cike da farinciki kila treatment zai canza mata, Dan shiru yayi don be san yanda SEN zai karbi idea in nashi ba Hmmm ranka ya Dade duba da nayi Nadeeya barazana ce a cikin rayuwan ka why not kawai a kau da ita,wat I mean hers is why not a kashe Nadeeya kawai ka ga shike nan hankalin kowa zai kwanta, Ai ko be kai ga rufe baki ba ya ji saukan yatsu tassss a fuskan shi,wannan karan saida ya saki Kara sabida azaba, Both daddy maganar Doc Na kan hanya duk abunda zai baka ciwon kai kashe wannan abun shine zaman lfyn ka since ai Na fada maka ka bari a kashe ta kawai ko ma samu mu huta Afzaal ya kare yana turo baki, Tassss ya ji saukan Mari a fuskan shi Wanda cike da mamaki ke kallon Daddyn, Ku Ashe mutanan banza ne mutanan wofi ban sani ba,wai Nadeeya muke maganar a kashe ka,kai Afzal ka mance Na fadin maka Nadeeya ita ce rayuwa ta,ko nesa da ni baran bari ta je ba balle ace ta bar duniyar, Dole Nadeeya ta zama a raye,and wlhy wannan ya zamo Na karshe da za ku Kara yin irin wannan tunanin ko kuma wlhy ku kare rayuwar ku a cikin prison, wawaye Wanda basu da amfanin komai, shike nan ni da kai Na Na san mafitar da zan dauka,wuce mu tafi yace da Afzaal yana fita daga office in, Idanu taf da hawaye Bashir ya bi bayan SEN da shi Allah ya isa na,mutum yayi ta Marin ka kamar uban ka,ya San yana son yar tashi ya kawo ta nan in haukatar masa da ita,sannan yanzu ya zo yana ta faman marin mutane, akan me,(ni ko nace son duniyar ka ai duk me kwadayi yana tare da wulakanci, kadan ma ka gani), **************Doctor Nameer Sister don Allah ihun Ms nake ji ne hka,and daga ina ihun ke fita haka,ya tambayi wata nurse da ta zo wucewa, Hmm kila kai bako ne a hospital in nan,daga IR ne ihun nan ke fitowa, Kallon rashin fahimta yayi mata sannan yace pls miye IR kuma,Dan dariya tayi sannan tace Isolated room, mamaki ne ya kama shi shi sannan yace kar ki ce Na fiye tambaya waye a IR in, Baki ta Dan taba sannan tace eh wlhy Na ji dai an ce wai Yar gidan SEN ce a cikin dakin Nadeeya Audu Waziri,ta kare tare da barin gurin, Wani irin mamaki ne da al'ajabi ne suka Kama Doc Nameer, domin shi wlhy tun Randa suka yi hira da Mujaheed ga me da case in su be kuma matsa wa kan shi sai ya San abunda ke wakana,domin shi duk daukan abun yake akan acting ne don ya samu sympathy in mutane,a haka ya fito ya shige motar shi don komawa masaukin sa,zuciyar shi cike da tarin tambayoyi kan me ya kawo Nadeeyan gidan mahaukata...... A cigaba da sharing ana commenting ina yi muku son so fisabillilah๐Ÿ™๐Ÿปโค๏ธ [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ........ My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin San bara ki Na comment ba toh don Allah kar ma ki shigo,domin ko kin shiga zan fidda ki,haka zalika maza ma kar su shigo group in nan,domin group in mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ........ Page eleven & twelve ************ Odogwu Na shiga uku na lallace asiri Na ya dab da tonuwa a bai nan duniya,ka taimake ni in baka rufa min asiri ba ban San yanda zan yi ba,duniya za su yi mun tofin Allah tsine, komai da Na mallaka zai kare,sanin kan ka ne bani da burin da ya wuce na samu kujeran takaran gwamma na jahar Bauchi,SEN ya kare cike da kuka zufa duk ya wanke mishi fuskan shi kanshi a kasa ya hade Hannaye guri daya, Wanda ake kira da Odogwu ko pimmm be ce ba illa wata katuwar maciya da ke gefen shi da yake shafawa, Dago da idona nayi tare da kare masa kallo,ya subhanallahi Na furta domin wani irin mummunan halitta da nayi arba da shi,baki ne wuluk munannanne irin manyan mutanan nan Wanda kallo daya za ka masa kasan shi da tausayi da imani sun yi hannun riga, yana sanye da kaya kallan fatan damisa,fuskan shi a matukar daure daga ganin alamun sa kasan baya cike da farinciki sannan daga ganin shi bare yi tausayi ba, Ganin be ce da shi komai bane har na tsahon lokuta ya sanya SEN ya shiga mishi kirari da yarbanci,yana yabon shi yana masa kirari da nuna tsantsan mulki irin nashi,fadi yake ya taimake shi kar ya gaji da shi,in har be taimaka masa ba waye zai masa,shine me amsan dukka rokon shi sannan ya share masa dukkan hawayen shi,in har ya juya masa baya,toh tabbas rayuwan shi zai daidaice, (Waiya zu billahi,kai mutane mu ji tsoron Allah sabida neman duniya mu saida imanin mu har ka ji mutum Na daukan hakkin Allah yana baiwa wanin shi abunda Allah kadai ke iyayi Amman sabida jahilci ka dauka ka mika wa wanin shi,ubangiji ka tsare mana imani da mutuncin mu, Allah ka tsare mu da aikata shirka๐Ÿ™) A gadaran ce Odugwu ya dago tare da kare wa SEN da ke durkushe a gaban shi kallo,me cike da tsantsan bacin rai,kamar bare yi magana ba kuma sai Na ga ya bude baki, Cikin muryan mara dadin sauraro da hausan da bata ishe shi ba,yace RILWANU ya tabbata baka Jin magana,and Na ga alaman you are trying me ne wlhh, Cikin sauri yace Odugwu ba haka bane Na tuba wlhy ni kai Na ban san yanda aka yi Nadeeya ta ji mu ba, Wata irin tsawa ya daga wa SEN Wanda saida ya sanya shi kusan sakin fitsari,duk irin Dade war sa da irin kyautata wa Odugwu da yake yi a kunyar nan ba shi zai Hana in ya dan kuskure ya ci uban shi ba wani zubin harda punishment yake masa, Sau nawa zan yi warning in ka,akan kar ka kuskura kana kira mana sunan God anan,kasan da shi ka zo nan,ko ba bukatun ka muke biya maka Wanda shi ya kasa biya ma ba,(ya salam jahilci be yi ba sam wlhy), Cikin sauri SEN ya daga kai yana me bawa Odugwu hakuri, Tabbas kayi babban kuskure da ka bari yarinyar ka ta san halin da kake ciki,Wanda bata da buri da ya wuce ta ga tonuwar asirin ka,Wanda tonuwar asirin ka ya shafi duka yan kungiyar BROTHERHOOD gaba daya, Kuskure aka samu Na tuba Odugwu kai me rahma ne ka taimaka ka yafe ni sannan a san yanda za a yi kar yarinyar nan ta tona mun asiri, Wata irin dariya me karfi Odugwu ya sanya Wanda saida dakin gaba daya ya amsa sannan yace,dole kashe ta za a yi,yau cikin dare zan sanya aje a ibo mun Jinin ta in baiwa dodon tsafi zai yi farinciki da kai sannan ina maka albishir in kai za ka ci zabe,tashi ka tafi matsalan ka ta kau, Zabura SEN yayi tare da kwanta wa yana me rike kafafuwan odogwu cikin kuka da be ma san yaushe ya zo masa ba ya hau rokan sa,ka taimake ni Odugwu kar a kashe Nadeeya,yarinyar nan has suffered a lot,and kai kan ka kasan rayuwar ta shine cigaba Na, Dariya ha kuma yi sannan yace duk wannan ba matsala bane ko tana raye ko bata raye in har kana tare da mu,za ka cigaba da shahara da daukaka, Odugwu banda kashe Nadeeya ita ce rayuwa ta,ka mun rai ayi wani abun daban ba wannan ba, Wani irin hangade shi yayi saida snake in jikin shi ya fadi tare da nufan Sen rai a bace yana neman kai masa Sara,idanu SEN ya kamkame bugun zuciyar sa Na karuwa domin ya San muddum snake in nan ya sare shi shike nan ya rasa rayuwar sa, Hannu ya daga sai ga snake in ya tsaya,da kanshi ya sauko tare da daukan snake in,kanshi ya shafa tare da masa kiss a baki,sannan ya koma gurin zaman sa, Dan shiru ne ya biyo baya kafin can Odugwu yace ya kake so ayi yanzu,you are one of my favorite costumers,domin kana baiwa kungiya abunda take bukata,saidai at times kana bani ciwon kai Rilwanu,ya kare yana kada kafafuwa, Da sauri ya matso ganin shugaban nasu ya fara sauko wa,Na san tabbas in har Nadeeya ta bude bakin ta ko ta samu dama guduwa za tayi,sannan tonuwar asiri Na ya zo ke nan,duniya za tayi tir da ni ,ina so ayi mata aikin da baxa ta iya guduwa ba,sannan duk yanda za ayi bara ta iya magana ba,ya kare yana me addua a ran shi Allah ya sa shugaban nasu ya yarda da abunda ya ce, Dan dariya yayi me razanar wa sannan yace kai mutum ne ne tsatsan son kanshi a kowani irin hali,ya sanya da ka tashi zaban hukuncin da za a wa Nadeeya ka zabar mata ma fi sauki, Hmmm well tunda kai da kan ka ka zabi hakan Na yarda Amman dole kasan akwai paying price kafin aikin ka yayi right,and baka isa kace bara kayi ba, Cikin sauri yace Na yarda koma miye zan yi odugwu just say it,am ready in yi koma miye,ya kare zuciyar shi Na bugawa domin shi har yau ya kasa sabawa da irin abubuwan da shugaban ke Sanya su, Zama ya gyara tare da cewa well,this time around you have to make Sacrifice, And wannan karon blood muke bukata Na kuma new born baby boy wanda aka haifa kar ya wuce 1 hour da fitowa duniya,in har ka kaba za ayi farinciki da kai sannan aikin ka zai yi, Gumi ne ya karyo wa SEN yo shi ina zai samu new born baby boy har ma ya bada Jinin nashi wa dodon tsafi,ya shiga uku, Odugwu be jira cewan shi ba ya bar gurin yana taku kasan gurin Na amsawa domin irin dogaye manyanan mutane ne,kato ne sosai,kai tsaye cikin Hall in ya koma domin ganawa da sauran mutanan gurin, Jiki a sanyaye SEN ya mike tare da haurawa sama,wani daki ya shiga Wanda ba komai a dakin sai wani katon gunkin Na miji a tube, Faduwa yayi a gaban gunkin bayan ya gama maza kirari ya taba kafafun shi don neman Albarka, sannan ya kama private part in gunkin tare da tsotsa sau uku,sannan ya mike,bayyanar kayan shi a bayan gunkin ne ya tabbatar masa sakon gaisuwan da ya isar an karba,and ga dukkan alamu fushin da ake da shi ya sauka,dole yayi takatsantsan duk laifin shi ne da ya bari had Nadeeya ta san asirin shi, Cikin sauri ya dauki ja da bakin kayan da ya gani ya sanya a jikin shi,sanann ya sauko ,da Alhaji Kabiru suka ci karo a bakin stairs in,hope komai normal koh ya tambaya yana kallon shi, Mu je a gama taron nan Na baka labari, nan suka jero suka shiga gaisawa da mutane Wanda kowannan su,Na dauke da wata bakar zobe a hannayen su,hade babban yatsan su suke guri daya tare da murxa zoben juna haka ake gaisuwan, Guri suka nema suka zauna,nan masu bukatu da masu sacrifice suka fara gabatar da shi a gurin Odugwu, Kusan hours in su uku,sannan ya tafa hannu nan take maaikatan gidan suka fara fitowa da tray a hannayen su Wanda ke dauke da naman mutum akan plate da kuma Jinin mutum a cikin glass cup,nan suka shiga serving babu tsoron Allah kowa ya shiga ci hankali kwance,baka Jin komai sai karni jini da Hall in ke yi, Saida aka ci aka koshi sannan kowa ya shiga goge bakin shi,tashi Odugwu yayi tare da Kara karfafa su kan duk wani damuwar su da matsololin su ko wace iri ce zai magance sa,sannan kar su sake duk Wanda aka bashi aiki yahi a bayyane ko ha kuskure,domin tonuwar asirin daya kamar tonuwar asirin duka yan kungiya ne,kowa kuma yayi kokarin yin aikin da aka bashi ko kuma ya hadu da fushin shugaba, suna iya watsewa sai next month kuma in lokaci ya kai,daga haka ya bace bat bayan sun rusuna duka domin nuna tsantsan biyayyan su, Sama kowa ya hau tare da canzo kayan su,nan suka fito tsab kamar ba su ba, Mamaki Na yi ganin manyan fuskokin yan kasar nan a wannan gida,ikon Allah gaskia tsoron Allah yayi karanci a duniyar mun nan, mutum can go to any extend don ya samu abun duniya,Allah ka tsare mana imani da mutuncin mu, Nan da aka hau gaisawa da juna suna shigewa motocin su Na Alfarma, ana sai kuma an hadu next month, ana ficewa daga gidan,fuskokin su cike da faraa bara ka taba cewa wa'in nan responsible mutanan ne ke kungiyar asiri,coz dukkan njn su suna da cikar halitta,(babu kamar Na SEN ni duk ya fi bani mamaki ma,a fuska kamar mutumin kirki Bini Bini ya kira Allah Ashe Dan iska ne mushuriki), A mota daya suka taho da Kabiru sabida amotar shi ya bar wa Sa'eed a can wata expensive hotel me suna G_PINNACLE, Normally a hotel in suke sauka duk sanda suka zo meeting,sai ya bar Saa'eed su wuce da Kabiru, Suna tafe ne suna Dan taba hira, Abokina ya kuka kare da Odugwu ne,hmmm wlhy Kabiru ka mance kawai Odugwu yana gab da daina daga mun kafa,domin shi da kanshi fa yace a kashe Nadeeya bayan yasan irin mahimmancin da take da shi a guri Na, Dan dariya Kabiru ya sanya sannan yace kai kuma Nadeeya yar zinare ce ko da bara a kashe ta ba,Na ga ko baka baiwa dodon tsafi Jinin ga ba za ta dai mutu,ba ya fi ta mutun ba da irin wannan rayuwar da take yi mara yanci,mu yaran mu nawa muka bada,su ba ma son su su ne, Are you talking about sacrificing in blood,kai kan ka sheda ne ne abubuwa nawa nayi sacrificing aa kungiyar nan,abubuwa nawa Na rasa,yanzu haka Nadeeya ta fa ke kwance a gadon asibiti mahaukata sabida ga San wani abu daga sirri Na, Ganin ran SEN ya baci ne ya sanya Alhaji Kabiru maida abun wasa sannan yace to yanzu wat is the way forward ya kuka tsaya da odugwu, yace Na kawo mishi blood in new born baby boy ya San aikin da zai yi,kuma in yi making sure ban dau time ba, Tab wlhy odugwu yana son ka inda wani ne yayi abunda kayin nan toh wlhy da uwar shi mahifiya za a ce ya je ya kwanta da ita sannan a bashi kyelle ya goga mata ya kawo wa dodon tsafi, Baki SEN ya bude domin shi har yau in ya ji wani abun Na Brotherhood in nan sai zuciyar shi tayi raasss, Hmmm kawai yace daga haka basu kuma magana ba a haka suka nufi hotel in,inda already Alh kabiru ya sanya an kawo mishi manyan matan yarbawa guda uku,yanda suka raba dare suna aikata sabon Allah, bayan sun gama ya faki idon su ya goga musu kyalle a gaban su bayan sun yi bacci, jaka ya bude tare da sanya wa ciki yana dariyar mugunta,ganin ya fi su wayo,sanin halin mutanan da ke zuwa offa ya sanya karuwan suka daina sanya pant don ibewa suke a bar su da jinya daga baya, SEN kam be wani samu cikakken bacci ba,duk tunanin shi yanda zai samo Jinin new born in jariri yake yi,hakan ma wai Na miji, ga doc Bashir ba wai a gurin yan haihuwa ,balle ya kira shi ya bashi kudi,don ya San shi mayen kudi ne,da haka dai ya samu bacci ya dauke shi ,washegari sassafe suka dauko hanyan Bauchi bayan Alhaji Kabiru ya sallami babies in shi, su kuwa sun ga kudi harda basu no in wayoyin su wai in ya dawo next month ya neme su,karba kawai yayi suna barin gurin ya goge numbers in domin shi fa baya kwantawa da mace sau biyu, daman yana gamawa yake goga wa yarinya kyalle Wanda ke da haihuwa saida ki ji ana yi a makota,suna tafe tana yi wa SEN irin dadin da yaran nan suka jiyar da shi a daran jiya,Dan tsaki SEN yayi toh shi a ina zai ji tunda ba da shi aka ci uwar sabadan ba,don't worry my friend kaima ka kusa barin wannan abunda Odugwu ya sanya ka,a canza maka Na san ka gaji ko,hmmm wlhy ni Kabiru har Na saba, in ban yi ba bana Jin dadi,dariya Kabiru ya kwashe da shi sannan ya nufi kafadun shi yace shege Aboki na kace ka ji dadin abun Amman Na ga randa aka ce ka fara hankalin ka yafi Na kowa tashi, hmm bara ka gane ba nima one the Na zamo addicted,daga haka basu kuma magana ba kowa yayi shiru da abunda yake sakawa a ranshi, ......... 5 Days later Doctor Nameer ya fara aikin shi gadan gadan,babu wata matsalan da yake fuskanta a Asibitin sai Na Doc Bashir da kuma Na Nurse Kareematu domin ba karamin shige masa take yi ba,haka in ta ganshi za tayi ta karkada tana wani farfari da idanu tana lankwashe lankwashen murya,saidai har tayi ga gama be masan tana gurin ba domin yi yake kamar be san da halittan ta ba,Wanda ba karamin haushi take ji ba ganin irin halin ko in kula in da yake nuna mata,sai kuma Doc Bashir da ke yi masa kallon wulakanci domin lokaci daya ya ji ya tsane shi domin ya ga alaman yaron akwai brain kuma yana da hazaka, in ka cire mutane 2 nan to baya fuskantan ko wace matsala aikin shi yake cike da kwanciyan hankali, saidai yana mamakin har yau da be hadu da Nadeeya ba domin haka kawai shi yake son ya ganta, ..........SEN A kwance yake a kan gadon shi ya rasa duk abinda ke masa dadi,yau har kwana biyar sun wuce be samu ya yi aikin da aka bashi ba,shi sam wlhh be san inda zai samu Jinin yaron da ba a fi 30 mints da haihuwar shi ba,karan shigowar wayan shi ne ya katse mishi zurfin tunanin da ya fada, Tsaki ya dan ja tare da janyo wayan domin ganin waye ke son takura shi haka,saidai kafin ya ga me kiran wayan ta tsinke,Kara shigowan kiran ne ya sanya shi Kara Jan tsakin tare da kallon screen in wayan, ganin Alhaji Salis ke kiran shi ya sanya shi gyara zama tare da daukan wayan.......... Asaalamu Alaikum, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi tare da ban hakuri Na rashin jina jiya da kuka yi,hakan ya faru ne sabida dan rashin lfyn da nake fama da shi, ina godia da irin kulawan da kuke nuna mun, Allah ubangiji ya bar kauna, Na so Na ga ya fi haka Amman Allah be yi ba,so bare with this pls,sai kuma Monday in sha Allah, A cigaba da sharing and commenting pls Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEEY BEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Ina maraba da duk me son shiga saidai in har kin san bara ki Na comments ba,toh don Allah kar ki shiga,haka zalika maza kar ku shiga pls wannan group in mata ne zallah akwai kuma matan aure๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ......... Page ten ********** Doctor Nameer Har ya iso masaukin shi yana janjanta wannan alamari Na Nadeeya yar gidan SEN, ikon Allah toh ke nan da gaske dai haukan tayi to me ya hauka ta ,and akan me take yi wa uban ta mahaifi irin wanann zagi haka,dole akwai Abu a kasa,ruwa bata taba tsami banza, Dole akwai boyayyan alamari da ke birne a kasa,haka kawai ya ji yana son sanin miye ke damun yarinyar nan like yana son ya sani miye ya same ta har ta haukatar ta haka,tun yaushe ne ma ta haukacen har da kai ta hospital in mahaukata, And in har da gasken tayi hauka a irin kudi da taimakon SEN ai kasar waje ya kamata ya fidda ta domin nema mata lafiya ba wai a kawo ta asibitin Specialist ba,irin wannan tambayoyin ne ke ta masa yawo a cikin brain in shi, Can kuma wata zuciyar tace da shi kai miye naka Nameer ina ruwan ka da ita ka san ta a ina da har kake Jin wani iri a game da abunda ke samun ta ka bi ka dage hankalin ka,ka San ta ne?? A fili ya amsa aa ni ko ganin ta ma ban taba yi ba sai a video ban San ta ba kuma babu abunda ya hada ni da ita,Allah ya bata lafiya shine abunda ya ce tare da Saurin cire tunanin ta a ranshi ya fito daga cikin motar bayan yayi parking, Key in room in shi ya karba tare da hawa sama ya bude dakin,kai tsaye toilet ya fada ya watsa ruwa sannan ya fito, abinci yayi order domin ba karamin yunwa yake ji ba(ni ko nace kai dai ka ji mutan Bauchi an iya girki ya sanya kake haba haban cin girkin su,lol) Saida ya gama cin abincin sannan ya kira Mama,gaisawa suka yi sannan ya bata labarin yau ya je asibiti yayi reporting an ce gobe ya dawo in sha Allah, Ba karamin dadi ta ji ba,addu'oi tayi ta masa na fatan Alkhairi da kuma tsari,nan suka shiga hira har ta bai wa Haanan tayi ta yi masa gwaranci,yana dariya abun shi,kusan 1 hour sannan yayi mata sallama tare da kashe wayan, yana Jin missing in Maman shi da little angel in shi, Kashe kiran ke da wuya kiran Mujaheed Na shigowa, dauka yayi suka gaisa cike da barkwanci, Mutumina ya hanya hope ka isa lafiya,ya ka ga garin to, Dan murmushi Nameer yayi sannan yace baka da dama Mujaheed duk irin tambayoyin nan ni kadai,wlhy Alhamdulillah Na isa,Bauchi kuma is a very nice city,Na ma yi reporting gobe zan fara aiki In sha Allah, Toh Allah ya kaimu Aboki Na ya sa a fara a saa,ka ga SEN ina kuma hope ka mika sako Na, Goshi ya dafe sannan yace Mujaheed wlhy baka da hankali,ni a ina zan ga SEN Na ma zo barin hospital ne Na ji ihu...anan ya kwashe komai ya sanar da Mujaheed, Idanu Mujaheed ya zaro sannan yace wai you mean Nadeeya Audu Waziri ne ke mental asylum in ku,wlhy nima abun ya bani mamaki sosai Mujaheed kai Na ma ya daure and da alamu ma ta kwana biyu a gurin, Ikon Allah ke nan da gasken dai jifan nata aka yi,Allah sarki baiwar Allah toh Allah bata lfy,ka samu ka ganta ina, Wlhy Mujaheed baka da hankali in ce ma an ce sai gobe a ina zan ganta beside kasan waye mahaifin ta so ba ma tare da sauran majinya ta take ba,a isolated room aka aje ta Wanda ban San a ina yake ba,kar ma ka tambaye ni a ina isolated room in yake , Dan dariya Mujaheed yayi sannan yace wlhy baka da dama Nameer,kai din ne ka cika tambaya ya bashi amsa cike da kosawa,nan suka cigaba da hirar Na su, .........SEN RILWANU Shigowan su part in shi ke nan,inda kallo daya zaka masa ka gano ranshi a matukar bace yake, Jiki a sanyaye Afzaal ya ja legs in shi tare da zama a bakin kujera yana Jin gaba daya jikin shi Na ciwo,more especially fuskan shi,sakamakon dukan da ya sha a hannun Nadeeya, Kallon SEN yake dake zagaye parlor in ya ma kasa zama,cikin muryan shagwaba yace haba daddy marin da ka mun dazu was that necessary?? Juyowa yayi cike da bacin rai yace yes Afzaal Na ga alamun baka cikin hankalin ka ne,that slap nayi maka ne don ka dawo sense in ka,and ko yanzu ka kuma cewa a kashe princess sai ma kuma kwada maka marin da sai ya haukatar da kai, Ban taba sanin baka da hankali ba sai yau in ce nan ni da kai nayi maka bayanin irin mahimmancin da Nadeeya take da shi a cikin rayuwa ta,and ka ce wai a kashe ta,in ka manta in tuna maka in har Nadeeya ta mutu to daga kai har ni Asirin mu tonuwa zai yi,aikin banza ya kare tare da Jan tsaki, Tasowa yayi domin ganin ran daddyn yanda ya baci,a hankali yace am so sorry Dad tashin hakalin ka ne bana so ya sanya nace a kawar da Nadeeya in Na mance Ashe mutuwar nata tonuwar asirin ka ne,ko in ce mu baki daya, Kallon Afzaal in yayi sannan yace is okay Amman kar ka Kara fadin Abu irin haka,baran Kara ba Daddy pls kar ka Kara Mari Na ka ji, ya kare a shagwabe tare da fadawa jikin daddy kamar zai yi kuka, Bata mun rai kayi son Amman kasan ai da baran mare ka ba,ya kamata kana sanin Abu kafin ka fada,baran Kara ba shine abun da Afzaal ya fadi,(ni mamaki nake ganin yanda wannan katon mutumin ke zubawa SEN shagwaba domin a kalla Afzaal zai kai 33 years,yake Abu kamar Dan 6 years old), Ciro shi SEN yayi daga jikin shi sannan yace now wat is the solution son, Hmmm dad ni kai Na gaba daya ya kulle wallahi ban ma San me zan ce ba, Dan shiru SEN yayi sannan yace okay ka kwantar da hankalin ka,i know what to do,Allah ya kaimu gobe dole zan je Kwara state, Baki Afzaal ya zumburo sannan yace amamn tare za mu je ko,face in shi SEN ya shafa sannan yace capital no ni kadai Na zani kwana daya ko biyu zan yi Na dawo so ba sai mun je ba,bari Na shiga Na huta ka ce da Saa'eed yayi shiru sassafe za mu dau hanya domin a mota za mu je,sai ka samu ka shiga ruwan zafi ka gasa jikin ka ko za ka ji dadi,daga fadin haka ya wuce dakin sa, Tun kafin ya rufe kofa ya shiga kiran layin Alhaji Kabiru sai da ya kira sau uku kafin nan ya dauka,murya duk a gajiye kamar Wanda ya gama aikin wahala, Hello Senator ya kake ya fadi da kyar, tsaki SEN tayi sannan yace kana ina ne ina ta kiran ka, Dan dariya ya sanya sannan yace ina ko zan ji kiran ka ina cloud 9 wlhy wasu zafaffan babies Na samu suke jiyar da ni dadi, Tsaki SEN ya ja sannan yace kai dai wlhh Allah ya shirye ka,ya shirye mu tare Kabiru yace tare da tashi yana sanya bathrobe domin rufe tsiraicin sa, Ina Jin ka akwai wani abun ne Na ji muryan ka wani iri, Hmmm wlhy Kabiru ina cikin damuwa da rashin hankali kace da ni ina da mun sanya Nadeeya ta haukace shike nan komai ya zo karshe yau ba ka ga abunda ya same mu ba,nan ya kwashe komai ya sanar da Alhaji Kabiru, ikon Allah toh wannan abun gaskia babban Abu ne ya fara so ya fi karfi Na, Haba Aboki Na ya zan yi ne wlhy kai Na duk ya kulle,ka taimake ni ban son asiri Na ya tonu kuma muddum ta cigaba da fade faden nan za ta iya tona mun asiri, Hmm gashi kai kuma bara ka yarda a kashe ta ba ko,Kabiru ya kare yana dariyan iskanci, Haba kai kuwa sai kace ka manta waye Nadeeya a gurina ai kashe ta ma is not an option, Toh wannan abun kawai ka bar shi sai gobe ma tattauna in mun isa kwaran,tare za mu wuce ne ko in yi tafiya ta, Aa kawai ka je abunka ni da Saa'eed za mu taho in sha Allah,to shike nan babu damuwa sai kun iso in,ka dai kwantar da hankalin ka ka samu ka mori rayuwar ka wannan yawan tsoro da furgicin duk ba naka bane,shine abunda Alhaji Kabiru yace kafin suyi sallama ya kashe wayan shi,shi wlhy har tsoron zuwa kwaran nan yake gobe,bayan tsoro kuma har ya fara tausaya wa kan shi sabida irin nisan tafiyar da za su ci,da haka ya gama duk abunda zai yi da wuri ya kwanta domin ya samu ya tashi da wuri goben, ..........Kwara state Offa village A can cikin wata kauye wai ita Offa da ke karkashin Kwara nake ganin shigewar manya manyan motoci,baka Jin komai sai karan wuce wan su,Wanda yan garin Sam basu da kwanciyar hankali in har wata ta kama,domin shige da fice kam har sai sun gaji, Bin motar da ya zo wuce wa nai,Wanda ke ta tsala gudu,sai kutsawa cikin kauyen yake yi,tafiya ce taki karewa har na ga an fara barin kauyen an sauka a kan titi an fara bullan cikin dajika,Wanda kallon shi kawai abun tsoro ne duba da irin shirun da gurin yayi da kuma yawan bishiyoyi da kuma yawan kukan dabbobi da ake ji, Saida aka yi kusan tafiyar one hour,sannan Na hango wata irin katon building, mamaki ne ya kama ni,domin irin katon duplex building ne me dauke da kalan ja da fari,domin gate in kofar gidan ma Ja ne, Mamaki ne ya kama ni waye zai Gina irin wannan katafaran gidan domin gida ne da mutane dari biyar ma sai suyi rayuwa a cikin ta ba tare da sun takura ba,ko gidan waye wannan oho, Kamar an ce in daga kai Na idona ya sauka akan rubutun da ke manne a cikin mannyeb harufa a saman gate in gidan,BLAZE HOUSE (gidan wuta) Na gani a rubuce tare da alaman wuta a ci a gaban rubutun, Mamaki be karasa kama ni ba saida aka bude gate in,Ashe ban ga komai ba daga waje domin gida ne me girman gaske,tambaya ce fal rai Na ganin different kaloli da designs in motoci Na Alfarma sun kai guda dari biyu a Parke a tsakar gidan, Tsoro ne ya fara kama ni a haka dai Na daure Na kutsa kai Na cikin gidan,Wanda mutane ne birjit a cikin katon Hall in taruwa sanye da jajjaye da bakaken kaya, Mamaki be Ida kashe ni ba sai da Na hango wani tsungune a gaban wata kujera a wani sashi Na gidan a tube haihuwar uwar sa,yana jiran shugaban kungiyar ya bayyana domin ya samu ya isar da kukan shi,kamar an ce da shi ya dago karaf muka hada ido,salati Na sanya tare da wurgi da biron hannu Na sakamakon tozali da nayi da Senator RILWANU AUDU WAZIRI....... Wannan shine ana dara ga dare yayi,mu je zuwa masoya Na yanxu wasan zai fara dadi๐Ÿ’ƒ๐Ÿป, Ina matukar godia da irin kauna da goyan da kuke nuna mun group members ina,ina yi muku son so fisabillilah, Masoya Na Wanda Na sani da Wanda ban son su,ina matukar godia da irin goyan bayan da kuke bani,Allah ubangiji ya bar zumunci, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi, Sai gobe kuma in sha Allah ๐Ÿ™๐Ÿป [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ...... My what's app link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK Ina marhaban da kowa,ammman banda mutuane biyu,mara sa sharhi da kuma maza don ko kun shiga zan cire ku๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ......... Page thirteen *********** Assalamu Alaikum shine abunda SEN ya fadi bayan ya amsa wayan,murya a sake don sun Dan kwana biyu basu gaisa da Abokin Na shi ba, Wa alaika assalam,SEN an wuni lafiya, Alhaji Salis ya fadi murya cike da annashuwa, Wlhy Alhamdulillah yi hakuri fa ina ta so in kira ka zama ne ban samu ba kullum ina gurin yar ka a Asibiti jikin nata sam ya ki dadi wlhy,ya kare murya a raunane, Allah sarki wlhy nima tunda muka je nake son mu koma da kai,zama ne ban samu ba nima,Allah ubangiji ya saka mata sannan ya bata lafiya, Amman cuta kam an cuce mu, Kai dai Bari SEN yace yana girgiza kai,da zan kama Wanda yayi aika aikan nan ai wlhy da hannu Na zan kashe shi,Allah ya sauwaka shine Abunda Alhaji salis yace, SEN ya amsa da Ameen ya Allah, Ni ka ga Na ma kusa manta abunda Na kira don in fada ma,zama SEN ya gyara sannan yace ina Jin ka ina kuma fata dai komai lafiya, Dan dariya Alhani Salis yayi sannan ya ce haba dai lafiya kalau sai Alkhairi wlhy,Albishirin ka, Kana son Kara aure ko,dariya Alhaji salis ya fashe da shi kafin yace wai me yasa babu wata albishir in da zan maka ni da Kabiru sai Na karin aure,shima SEN in dariyar ya sanya sannan yace yo ku din ne wlhy akwai son mata,Na ga kuma duk abun ku matan nan kullum haihuwar su ake kuma yi, Hmmm ni dai babu ni cikin list in nan Na Kabiru ne kawai and bashi Na kira Na fada ma ba,yar ka dai Zahra ta sauka fa, Cike da farinciki SEN yace kai Masha Allah barka Ashe ko dole Na tanadi babban goron albishir in nan,me aka samu aboki ko kishiya, Dariya Alhaji salis yayi sannan yace wlhy kai aka samu Na miji ta haifa tana bude ido ta ganshi tace wannan big daddy ne wai sunan ka take son a Sanya wa yaron, Allahu Akbar Allah sarki my daughter,kai wlhy Salis nayi murna Alhamdulillah SEN duk ya ma rude ya rasa me ma ya kamata yace,shi ko in banda dariya ba abunda Salis ke yi don ya San abokin shi da yaba kyauta ya san ba karamin dadi ya ji ba Jin sunan shi za a maida wa jinjirin da aka haifa,wannan shine jikan shi Na farko, and sam be yi bakin ciki ba da Zahra tace sunan SEN za a sanya wa Dan ta,a cewan ta tana son ya dauko kyawun hali irin Na SEN, Kuna gida ne ko asibiti, Aa wlhy muna Rimi clinic duka duka bata fi 15 mints da sauka ba,don Alhamdulillah normal haihuwa ce babu wata complication, Gani nan zuwa yanzu SEN yace tare da kashe wayan,farinciki lullube a cikin ranshi, Tashi yayi cikin sauri ya canza kaya domin ji yayi gaba daya damuwar da yake ciki ta kau lokaci guda, Yana kokarin fitowa daga dakin ne ko me ya tuna sai yayi saurin komawa tare da daukan wata oil ya mulke hannayen sa da shi,tare da sanya hand gloves a hannun sannan ya fito, Tun a kofar part in shi yake kwala wa Sa'eed kira Wanda a guje ya rugo gudun shan mari, Baka ji ina ta kiran ka shine abunda SEN yace tare da shigewa bayan mota ya zauna, Am sorry sir ina toilet ne,kai ni Rimi clinic shine abunda SEN yace tare da daukan cheque book in shi,5mil ya rubuta tare da yagewa ya sanya a aljihun gaban rigan shi, Ba su dau time ba suka iso Rimi,da sauri SEN ya bude kofar motan,a bakin asibitin suka hadu da Alhaji Salis in da ya masa jagora har dakin me haihuwar, Mutane sun fara cika kasancewar haihuwar fari,daga dangin Salis har Na iyayen mijin Zahra duk sun hallara, Gaisuwa Na mutunci suka yi da Sen ya Na sanar musu shine Wanda aka yi wa me suna,dangin uban jariri suna ta tsokanan sa akan to kuwa dole ya dauke nauyin komai Na sunan takwaran shi,shi dai dariya kawai yake musu domin ya matsu ya ga ya dau babyn a hannun shi, Ko da suka shiga a zaune suka tarar da Zahra da mijin ta yana dauke da babyn a hannun shi an nade shi cikin farin towel Na yara, Dankwalin ta ta gyara fuskan ta cike da faraa tace Big daddy sannu da zuwa ina wuni, Zama SEN yayi sannan ya ce my daughter alhamdulillah Ashe an sauka ubangiji ya raya shi bisa sunnah, a kunyace tayi murmushi tare da amsa ameen a kasan ranta, Gaishe shi AL_ameen mijin Zahra yayi,inda ya amsa cike da sakun fuska tare da yi mishi barka shima, Mika masa takwaran nashi ya gani tun a hanya ya ishe ni baaban naku akwai son yara,Alhaji Salis ya kare yana kallon Mijin, Tasowa yayi tare da nufo SEN da babyn har ya mika mishi,SEN ya mika hannu zai karba sai Alhaji salis yace wait,Aboki Na ya Naga hannun ka da gloves kuma,hope all is well dai, Ohhh God kasan Na manta,ciwo dazu Na ji a hannun shine Na sanya magani,to gudun kar infection ya shiga ne Doc yace Na sanya gloves for at least 20 mints don maganin ya samu ya shiga,shine fa Na manta ban cire ba,ya kare tare da cire gloves in yana mika hannu wa AL_ameen domin karban Dan jinjirin, Yana karban shi,kuwa yaron ya wani Mike kamar Wanda aka jona wa shocking sai kuma ya lafe ya kwanta luf, Kallon shi SEN ke yi cike da kauna da soyayya yaron tabarakallah me kyau da shi fari sol,bakin gashin kanshi har goshin shi, masha Allah shine kalman da ya furta, Murmushi Alhaji Salis yayi yace ka ga yaro sak uban shi ko,aa Aboki Na wannan yaron sak my daughter ne harta hancin nata ya dauko,saidai Allah sa kar ya dauko rashin Jin ta, Baki ta turo sannan tace komai naka zai dauko big daddy saisa ma aka sanya masa sunan ka, Allah miki Albarka ke da yaron ki my daughter Allah ya raya shi ya kare tare da yi wa yaron kiss a goshi yana mika shi wa Maman shi domin shi ba iya daukan yara yayi ba, Cheque in 5 mil in ya mika mata tare da Kara zanga mata Albarka yana kuma bata hakuri kan be sani da wuri ba ya sanya be siyo komai ba tayi hakuri tayi managing wannan har zuwa ran suna,yanzu in ya koma zai aiko Saa'eed da raguna da saniyar sunan yaron,sannan zai dauki nauyin karatun shi tun daga kan nursery har sai in da yaron yace ya gaji da boko,and in suna bukatan wani abu kar suyi hesitating su sanar masa, Godia sosai Zahra da mijin ta suka hau yi wa SEN, da sauri ya Hana su godia yace kar su sake ai duty in shi ne tunda duk su biyun yaran shi ne,Albarka ya sanya musu tare da barin dakin Salis Na bin shi a baya, Har mota ya raka shi suna wa juna tsiya wai yanzu kam tsufa ya kama su sunyi jika,godia sosai Alhaji Salis yayi wa SEN kafin su rabu ya ce da shi don Allah in ya samu Alhaji Kabiru a waya ya sanar masa domin ya kira dazu wayan sa kashe,in sha Allah zan sanar masa granny ni Na wuce sai mun yi waya,da haka Sa'eed ya ja mota wani bari Na zuciyar shi fess yake Jin ta wani barin kuma yana Jin da be aikata abunda ya aikata ba,but bayi da wata option opportunity ne ya samu har gida toh ya zai yi dole yayi using in shi, *************Doctor Nameer Get out of my office pls shine abun da ya ce wa sister Kareematu ko dagowa be yi ya kalle ta ba, Tashi tayi tare da juyi a gaban shi sannan tace haba Doc Nameer wai me na rasa ne don Allah,ka dago ko sau daya ne ka kalle ni,Allah ya hore mun am beautiful sannan ina da welcome ta kare tare da girgiza dukiyar fulanin ta,and I got bye bye ta kare tana shaking bom bom in ta, Ko ya dauko balle ya ga haukan da ta gama,out yace da ita cikin kakkausar murya, Haba Doc Na ji ko bara ka iya soyayya da ni ba wlhy zan yarda Na zamo karuwar ka,zan jiyar da kai dadin da baka San akwai shi ba a duniyar nan just give me chance plsss,ta kare tana hada hannaye, Tassss ta ji saukan mari a fuskan ta,Wanda saida ta dafe kumatun ta,lalle Kareematu Ashe ke karya ce ban sani ba wani irin kula ne bana miki da har sai kin bi wannan sabon yaron da baki ma San shi ba ke wata irin jarababbiya ce eheyee,doctor Bashir ya kare yana Galla mata harara, Kai Nameer ya girgiza tare da barin office in ranshi a bala'in bace wannan wata irin mayyar mata ce sabida Allah tun randa ya fara aiki take masa tayin kan ta suyi iskan ci,kila matar doc bashir ne ya sanya yake Jin haushin shi can musu dai yana kuma yi mata fatan shiriya domin ko da mutuwa zata yi ta dawo duniya don maita,bata ishe shi kallo ba balle har ya yi having affairs da ita don Sam bata da kamun kai, Yana Jin yanda suke musanyar yawu da doc bashir kan akan me xe mare ta shi mijin ta ne,duk matan da yake be an ce masa bata sani ba ne,sai a sannan yake gane Ashe ba mata da miji bane, baya so yayi zargi tunda haramun ne da sai yace suna neman banza ne shine yake nuna kishi a kan ta,tas tayi mishi sannan ta ce da shi kar ya kara kula ta,bata jira cewar sa ba ta fito daga office in har tana bangade doctor Nameer daga gani ranta bace yake, Shi dai Allah ya kyauta ya ce tare da fitowa cikin haraban asibitin,kujera ya samu tare da zama yana kare wa majinya tan kallo yanda suke hauka tuburan abun tausayi, Kamar ance kalli can ya hango ta zaune ta sanya fuskan ta cikin cinyoyin ta gashin kanta duk ya yi buju buju,be san me ya sa ba sai ya ji yana son ganin fuskan wannan baiwar Allahn, and although ya gan ta da uniform in mahaukata sai ya ga she look calm and worried to him,ganin har kusan 3 mints bata dago ba ya sanya shi Mike wa tare da fara nufan inda take zaune, hannun shi da aka kama ne ya tsayar da shi,yana juyowa kuwa ya ga Habeeb ne, Haba Doc Nameer since ka shanya ni ina ta jiran ka,mu je ka ga gidan mana tun dazu mutumin sai kira Na yake yi, Don Allah kayi hakuri Habeeb wlhy mancewa nayi,Amman bani 1 mint pls zan same ka a mota, Wlhy babu mint in da zan ba ka wuce kawai mu tafi,da ka yarda za ka zauna a gida Na ai da shike nan ko,Na ga alama baka gaji da zaman hotel bane, Na gaji man habeeb in da ban gaji ba taya zan ce ka nema mun gida,sabida Allah kuma sai Na bika gidan ka Na tare ai babu tsari, Ko ma miye mu je ya kare yana Jan Nameer Wanda hankalin shi Na aman baiwar Allahn da ta sunkuyar da kai,babu in da be yi da Habeeb ba ya tsaya pls Amman ina saida ya sanya shi a mota hankalin shi ya kwanta, To miye kake ta wani bata rai,don zan maka gata,habeeb ya kare yana kallon doc Nameer, Ni fa ba bata rai nake ba,kace a ina ne aka samu gidan Fadami madan ne ko miye sunan area in, Dariya Habeeb ya kwashe da shi sannan yace Aboki na baka da dama wlhy,yanzu Fadaman madan ne kake kira haka,kai wlhy suna yen unguwan nun kun nan akwai wahala su Bakaro,su Yakubu wanka,Bakin kura ne ko bakin zaki,ga wata ma wai Fadaman mada don Allah ji fa GRA ne kawai me sauki da dadin fada, Dariya Habeeb ya kwashe da shi sannan yace ai in dai sunaye ne kadan ma ka ki,Na Kd in kun ma haka kuke da tarukucan sunayen unguwan ni, Eh koma dai miye,gwara namu sau dubu da Na ku,shi dai Habeeb be ce komai ba domin sam musu da yan Kano da yan Kd akan garin su to ranka ne kawai zai baci, A haka har suka iso fadaman mada layin Maman isa yuguda, nan Nameer ya fara bin unguwar da kallo,but Habeeb are u sure za a samu me yin masa kusa kuwa, Kai dai da wannan masa taka akwai me yi cikin dare ne kawai suke sauke tukunya and masan su akwai dadi yanzu dai mu je ka ga gidan in ya maka to, ***********SEN Around karfe 12 Na dare har ya fara gyangyadawa ya ji zoben hannun shi Na juyawa tare da Kara matse shi sai kuma ta sake shi sai ga wani Jan haske Na fita daga zoben, Wanda ya farkar da Sen tare da mikewa zaune, Dariyan samun Nasara ya saki domin ga dukkan alamu sacrifice in da yayi ya karbu and Odugwu yayi farin ciki da shi,yesssss yace tare da shiga zubowa Odugwu kirari Na kusan 5 mints sannan ya ja barko ya kwanta zuciyar shi fess tunda ya baiwa Odugwu abunda ya ke so to tabbas shima soon zai ga result me kyau, nan take bacci ga dauke shi cike da mafarkin ya zamo gwamman jahar Bauchi....... Ina wa kowa fatan Alkhairi and ina fatan anyi weekend lfy,Allah ya sa hakan ,Ameen. Ina matukar Jin dadin support in da kuke bani,you guys are making me to go further wlhy,thank u so very much Allah kuma ya bar mu tare, Sai kuma gobe in me kowa me komai ya sanya mun kai. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ...... My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba comment bane zai kawo ki to dan Allah kar ki shiga, haka zalika maza kar su shigo don Allah group in mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ........... Page sixteen *********** Doctor Nameer Haka wannan ranar Doc Nameer ya bata shi gurin tunanin ta wani hanya ne zai shiga cikin dakin Nadeeya,haka kawai he is so curious ya san halin da take ciki, And abun haushin shine be san taya zai samu access to her ba,domin shi ba sanin pin code in yayi ba,and the only way da zai yi finding out shine through Bashir or Kareematu,Bashir kuma ya san ko mutuwa zai yi bare fada mishi ba domin bayi da ma gaskia,while Kareematu kuma ba sai na fada muku ba,haushin shi take ji already, Yana kallon yanda suke ta kai kawo a dakin nata,har lokacin tashin shi yayi but sam he is not willing ya tafi gida,ko ba komai yana son Kara ganin ta, A haka har Magriba tayi mishi a cikin hospital in wanda zan iya cewa tun da ya fara aiki be taba kai wa hakan ba,ganin be da wani way out ne ya sanya shi yin give up har ya soma hada kayan shi domin barin hospital in, Yauwa Kawata don Allah taimake ni mana,Kareematu tace da Zaituna da ke kokarin kulle jakar ta, Juyowa tayi ta kalli Kareematun da ta sha kwaliya har da su Jan baki,sai ina kuma shine abunda ta tambaye ta, Ke dai Bari wlhy Alhaji Na ke waje yana jira Na yau ya shigo garin Bauchi da mun yi zan same shi a masaukin sa in Na tashi a gurin aiki,to sabida naci da rashin hakuri irin nashi shine saida ya biyo ni yana waje wai Na fito mu wuce, Ke dai Kareema wlhy baki bin duniya a sannu,wai ke ko tsoron mijin ki ya kama ki ba kya ji, Dan tsaki Kareematu tayi sannan tace ni dadi Na da ke kenan tsoro wlhy kin ga dare ya fara yi,da kike mun maganar mijina me Abdul yake da shi sabida Allah banda rabon yara da ke tsakanin mu,nayi kallan matar shi ne,da ni nace kar ya fita ya nema don sauke mun duk wasu responsibilities ina,tun da shi ya Gaza ai sai a taya shi ta kare tana kanne ido daya, Hmmm Kawata wlhy baki da kyau,ko nayi wanka kuwa ta kare tana dauka jakan ta, Yauwa har zan manta,ki taimake ni don Allah ki mika wa wancan mahaukaciyar abincin ta,tun Rana take hauka sai fashe fashe da Duke Duke take,kar Na tsaya kai mata ta batan lokaci da kwalliya Na, Ah lalle Kareema wato ni ce bana son rai da lafiya ta ko shine za ki tura ni don ban yi kwalliya ba, Dafa ta Kareematu tayi sannan tace common zaituna ta kin San duk hospital in nan banda kawa irin ki and da ke kadai Na yarda, wlhy Bashir sam be bari ana shiga gurin ta ne saisa zan tura ki, Doke hannun ta zaituna tayi sannan tace ji iskanci to ni in ya kama ni fa,haba tawan bara ki iya taimako Na ba pls abinci kawai za ki kai mata,wlhy ni jira Na ake and ina bukatan kudi urgent wlhy,beside taya ma zai sani in ba ke kika sanar masa ba,nan dai ta kanenade ta da dadin baki harda mata Alkwarin bata kyautan 10k gobe da haka ta samu ta yarda za ta kai, Pin cord in ta sanar mata sannan suka yi sallama akan sai sun hadu gobe za ta bata bayani,da haka suka rabu, Abincin Zaituna ta hada akan tray sannan ta fito tana yan wakokin ta Na soyayya har ta iso kofar dakin, A kan idanun Nameer ya ga wulgawan Kareematu Wanda ya tabbatar masa da ficewa za tayi,kamar shima zai fita sai ya hango Zaituna da tray a hannun ta ta nufi isolated room in da Nadeeya take,ganin hakan ya sanya ya bi ta a baya a baya yana me Jin farincikin haka kawai a cikin ranshi, A Dan bayan ta ya labe kamar barawo tare da zuba wa madannin idanu,in da lucky him akan idon shi ta danna pin in,ganin kamar za ta juyo ya sanya shi saurin juyawa yana me Jin tausayin Nadeeyan domin yana iya juyo irin ihun da take yi at the top of her lungs kamar Wanda ake yanka ta sai kuma karan fashe fashe,a haka ya fita tare da fadawa motar shi,I have to see her again shine abunda ya fada wa kanshi tare da Jan motar, Kai tsaye gida ya wuce in da yana isa ana kiran Magriba so tsayawa yayi tare da sauke farali,sannan ya shiga gida, Kai tsaye toilet ya fada wanka yayi sannan ya fito ya hada coffee ya sha,sannan ya shirya in something light, Laptop in shi ya janyo ya shiga yin research just to keep him busy(yo ba budurwa gare ka ba balle ka je hira ko kayi passing time,lonely soul,lol), Around 9:00 ya mike tare da rufe laptop in car key in shi ya dauka tare da wallet in shi,ya fito daga cikin gidan,motar shi ya shiga tare da fitowa daga cikin gidan bayan ya rufe, Kai tsaye Saje restaurant ya nufa Wanda ke opposite da Round about in Nasarawa, Parking yayi tare da shiga,tun Randa Habeeb ya kawo shi gurin shike nan kuma ya haddace yana zuwa,domin ba karya abincin su akwai dadi, Gaisawa suka yi da masu aikin gurin sannan suka taimbaye shi me za a kawo mishi, Ce musu yayi take away yake so Na Sandwich da kuma rubber in ice cream, without waste of time kuwa suka hada mishi duk abunda ya bukata yayi payment sannan ya dauki ledan sai mota, Kai tsaye Specialist ya koma,inda ya sanar wa watch man in mantuwa yayi zai dauki wani file ne,dake suna ganin mutuncin shi ya sanya without thinking twice suka bar shi ya wuce, Saida yayi parking sannan ya fito, da ledan a hannun shi, yana tafe yana sanda kamar wani barawo har ya nufi kofar da Nadeeya ke ciki, Idanu ya lumshe yana kokarin tuno numbers in da Zaituna ta danna dazu,4477 ya dannan ai kuwa sai ga kofa ta bude, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke tare da kutsa kanshi cikin dakin bakin shi dauke da sallama, A can kuryan daki ya hango ta jingine da jikin gado ta kife kanta a cinyan ta, tana ta shesshekan kuka, Hey shine abunda yace da siririyar muryan shi, A zabure ta dago idanun ta sun yi jawur vase in da ke gefen ta ta dauka tare da jefa masa,inda yayi saurin gaucewa saidai ya same shi a hannu,Wanda ya yi nasaran yanka shi har jini Na zuba,saidai yankan is not that deep, Be ko yi gizo ba ya shiga takowa kusa da ita yana mamakin changing behavior nata,ihu take yi tana jefan shi da duk abunda hannun ta ke iya dauko wa Wanda bata samun shi sabida gaucewar da yake yi, Har ya iso inda take tare da durkusa wa,hannun shi ya sanya tare da rufe mata baki domin ihun da take yi gudun kar ta tona musu asiri, Shhhhhhh yace da ita yana me rike hannun nata,a hankali ya shiga hura mata iskan bakin shi yana fadin is okay calm down please, Idanu ta zuba mishi kamar Wanda take gane me yake cewa,murmushi yake mata tare da fadin babu kyau violence and you look good jiya da muka hadu da kike dariya why the sudden change now,ya tambaye ta ba tare da yana expecting amsan ta ba, Saida ya ga ta Dan nutsu sannan ya sake ta tare da kare mata kallo,she looks so pale and tired he is she has been crying tun safe ganin inda idanun ta suka kumbura,a hankali ya ke bin ta da kallo yanda gashin kanta duk ya cukurkude duk ta zama abun tausayi finger nails in ta duk sun fito kamar wata monster, Caraf idanun shi ya sauka akan kafan ta da ke xubda jini,Wanda daga ganin Abu ta taka ya yanka ta,and ba a yi dressing in ciwon ba,tausayin ta ne ya kama shi kila abunda ya sanya take ta kuka da ihu ke nan,toh wai wani irin kula Bashir ke bata da har yake fadin ya fita a hanyan ta,Dan karaman tsaki ya ja tare da nufan inda first aid box yake a dakin ya dauko, gaba daya tayi gaja gaja da dakin don har ta TV in ta fasa shi, A hankali ya tsunguna yana me Adduar Allah ya sa ta yarda ya gyara mata ciwon kar ya zamo miki, Cike da nutsuwa ya kama tsintsiyar kafan nata, Wanda ta yi saurin janye kafan tare da kai mishi naushi inda ta same ki a kafada,ba tare da ya damu ba ya sake mata kafan yana murmushi domin ganin yau mugunta take ji, Ledan da ya shigo da shi ya dauko, sanna ya dawo ya zauna kusa da ita,rubber in ice cream in ya bude tare da sanya spoon ya kai bakin shi,uhmmm dadi ya ce tare da lumshe idanu, Da gefen ido take kallon shi ba tare da ta ce komai ba,ganin haka ya sanya ya mika mata rubber daya inda tayi saurin faucewa ta sanya hannu ta fara lakata tana sha,ganin hakan ne ya sanya shi saurin dawowa gurin kafan nata, Cike da dabara ya shiga goge mata ciwon yana hura mata kafan da iskan bakin shi inda yayi nasaran cire glass in da ta taka, ba karamin tausayi ta bashi ba inda ita ko ko a jikin ta domin ko hawaye bata yi ba ice cream da sandwich in ta kawai take ci tana lashe baki da hannu abun tausayi, daga gani ta wuni da yunwa yau, Saida ya gama sannan ya dawo kusa da ita ya zuba mata ido, inda take cin abincin ba karamin dariya take bashi ba, Hannu ya mika mata wai akan ta samma sa inda ta noke kafada akan bara ta bayar ba,kai kawai ya girgiza sannan yace so you love ice cream, kamar daga sama ya ji ta ce more than anything ma kuwa, Da mamaki ya dago ya kalle ta sai kuma ta kau da kai kamar ba ita tayi maganar ba babu yanda be yi da ita ta fadi me tace ba Amman Sam ta ki,sai ma cigaba da surutan haukan ta da tayi, Haka ya tashi tare da gyara mata dakin tas in da ta fasa glasses in sannan ya zauna yana ta Jan ta da hira,inda ta ringa maintsinin shi tana Jan gashin shi, Shi dai da ido kawai yake bin ta yana jan ta da hira har ta saki jiki da shi ta mika mishi sandwich in guda daya ba musu ya karba tare da gutaira sai ta sanya dariya tana tafa hannu, Rayuwa ke nan,Allah yayi mana jarabawa me sauki a rayuwar nan,don Nadeeya kam haukan ta yayi nisa, Haka Nameer daga cewa file zai zo dauka nan ya lallace a gurin Nadeeya suna ta shirme har kusan 12:30 Na dare sannan ya farga da dare yayi, lokacin ita ma bacci ya dauke ta,so blanket ya rufa mata tare da yi mata Azkar in bacci sannan ya fito,zuciyar shi cike da tausayin Nadeeyan, A haka ya fito tare da creating excuse wa watch man in suka yi sallama ya nufo gida,wannan ranar haka ya kwana yana tunanin Nadeeyan Wanda Allah kadai ya san why ya kasa cire ta a cikin ran shi...... Ramadan is around the corner, so saura mana 2 pages in sha Allah sai kuma bayan sallah, Ubangiji ya sanya mu riski Ramadan lfy Allah kuma ya karba mana ibadun mu,sannan ya sanya ya zama silan dace war mu, Ina godia da kaunar da kuke nuna mun ina wa kowa fatan Alkhairi Sai kuma Monday in sha Allah. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BER) ........ My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin San ba comment bane zai kawo ki to pls ki zauna kar ki shigo domin kar Na fidda ki ranki ya baci,haka ma maza should stay away from my group domin Na mata ne zallah, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ........... Page fourteen ************ Kwana biyu ke nan da tare wan Doc Nameer a gidan da ya kama,gida ne well furnished, me dauke da daku Na biyu,big parlor kitchen toilet da kuma gaban gida me dauke da parking space, Gida ne me kyan gaske domin ba karamin kudi ya kashe ba Amman a ganin shi hakan ya fi masa kwanciyar hankali sabida wannan biyan kudin hotel in caca ya dauke shi, Da Habeeb suka shiga kasuwa suka yo siyayyan kayan cefane domin dole yana bukata sabida Emergency, tsiya sosai Habeeb ke yi masa wai gidan gwauro tunda ya ki aure zaman kadaici ya kama shi,shi dai dariya kawai ya bi Habeeb in da shi kafin ya ce da shi aure ai nufi ne Na Allah, Cike da kwanciyar hankali yake zuwa asibiti yayi aikin shi in an tashi ya dawo Gida abun shi,sometimes ya kan yi take away wani lokacin kuma ya daura abincin da kanshi,tun sanda ya yi wa sister Kareematu tas a office in shi bata kuma kallon in da yake ba,ko sun hadu haka za tayi ta cin chew gum tana wani wani Harare harare, yi yake kamar bata san abunda ta ke yi ba,and ya ga alaman doc Bashir ya dauke shi da gaba domin ko sallaman shi baya amsawa, ************* Zahra Fitowan ta ke nan daga wanka,daure da towel a jikin ta,kallon ta kanwar Maman ta tayi sannan tace Anya Zahra kin gasu kuwa ni irin wannan wanka naku da Baba sam baku Dade wa, Baki Zahra ta turo tana goge hannun ta tace haba ,Anty Haleemah kin san zafin ruwan nan kuwa,haka fa take tsoma towel ta nada da ruwa ta juye mun a jiki Na ko tausayi babu, Yar nema yo ba tausayin ya sanya nake miki haka ba wlhy Na bar ki jikin naki ya rube Ameenun ya karo wata ki shiga uku, Fatan ki ya sauka a kan ki ,Zahra tace tana hararan Baba yalwa, Kin ci gidan ku Zahra ban son iskanci fa,Anty Haleemah tace tana ma Zahra dakuwa,baki kawai ta turo sannan tace to ni me nace kina ji fa fatan kishiya take mun tun ban tsufa ba haka kawai, Dariya Baba yalwa tayi sannan tace oh yaran yau saidai a bar ku wlhy,ni maza zauna in turara ki ga tuwo nan da kunnun Kanwa ki sha, Haba Baba don Allah wlhh duk yanzu an daina irin wannan abun ,turawa nawa ke haihuwa ki gan su garau ba tare da sun sha wannan bakar azaban ba,magani kawai ake basu su sha shike nan sun hade fa,sai mu nan ayi ta dirka mana wahala, Baki bude Baba ke kallon ta,don Allah kar ki kula ta Baba rabu da ita,bara ta san gata ake mata ba,je maza ki dauki babyn tun dazu mustsu mustsu yake kila yunwa yake ji bashi nono ya dan sha kafin ki ci abincin,ta kare tana barin dakin domin Zahra sam bara ta bashi ba in har suna dakin,wai ita kunya, Ba musu Zahran ta nufi gadon da babyn ke kwance cikin shiga Na Alfarma,bashi kam ya sha don tun dazu da nake masa wanka Na ji jikin shi da dumi kamar wani me zazzabi,Allah dai ya sa ba me laulayi aka samo mana ba,Baba yalwa tace tana barin dakin, Zama a bakin gadon Zahra tayi tare da dauko babyn a hankali,ji tayi yayi mata nauyi a hannu kamar duk jikin sa a sake,fuskan shi take kallo,sai ta ga yayi mata wani irin haske yayi fayau da shi,yarinta ya sanya ba ta gano komai ba ta ciro nonon a hankali tare da yin bismillah ta daura mishi a baki,ganin be kama bane ya sanya hankalin ta tashi domin har bude bakin shi tayi ta sanya masa a bakin Amman be ja ba ko alaman tsotsa, A zabure ta mike tana kwala wa Anty Haleemah kira ganin kamar yaron ma be motsi, A rude Anty Haleemah ta shigo tana fadin ke lafiyar ki Zahra kina jego kina irin wannan ihun ,miye?ta tambaya tana kallon zahran da kallo daya za ka mata ka gane a rude take, Hannu take yarfe wa tare da Jan baya,idanun ta har sun kada zuciyar ta Na tsanan ta bugawa,tace Anty Haleemah Anty Haleemah junior ne Na bashi nono be kama ba, Kamar ya be kama ba Anty haleemah tace tana nufan inda babyn ke kwance,Anty haleemah sai Na ga kamar be motsi fa, Haba Zahra daga kin karban nono sai ki ce be motsi kila baya son sha ne baran duba shi,Baba daman tace kamar da zazzabi a jikin shi, Salati ta sanya lokacin da ta dauko yaron domin kallo daya tayi masa ta gano Sam babu rai a jikin yaron, Jin salatin ya sanya a tsorace Zahra tace Anty Haleemah me ya samu baby na bacci yake yi ko,don Allah ki sanar mun me ya samu yaro Na ta kare tana hawaye, Da mugun tausayin ta Anty Haleemah ta bude baki da kyar tace Zahra ke musulma ce dole ki yarda da kaddara me kyau ko mara kyau,saidai muyi hakuri Baby kam ya koma Allahn da ya bamu shi ya karbi abun shi Allah ya sa me ceto ne, Timmmm din da Anty haleemah ta ji ne ya sanya ta juyowa,ganin Zahra zube a kasa Towel in jikin ta har ya bude ya sanya ta aje gawan babyn da mugun sauri ta nufi inda take,tana kiran sunan ta, Ganin babu alaman numfashi a tattare da ita ne ya sanya ta kwalawa Baba yalwa kira,tare da kiran Hajiya Hafsat(mahaifiyar Zahra), Duk an rufu kan ta amman sam numfashin ta ya kasa dawowa,a rude hajiya Hafsa tana kuka ta Kira Alhaji Salis tace ya shigo a kai Zahran Asibiti, Hour guda aka dauka sannan aka samu numfashin Zahra ya dawo daidai Wanda saida aka sanya mata drip sakamakon Jinin ta da ya hau lokaci guda, Ko da ta farfado kuka kawai take yi kallo daya za ka mata ta baka tausayi domin lokaci daya ta koma wani iri,rungume ta gam Alhaji salis yayi yana tofa mata addu'oi domin aljanun ta tashi suka yi,fadi take a kawo mata Dan ta wlhy be mutu ba babu abunda ya samu Dan ta,kuka sosai Hajiya hafsa ke yi domin lokaci daya Zahran komawa tayi kamar Wanda tayi karamin hauka,saida aka mata aluran bacci sannan aka samu suka sauka mata baccin wahala yayi awun gaba da ita, Jiki ba kwari Alhaji salis ya bar hospital in,shi da Alameen Wanda idanun shi sun kada sun yi ja daga ganin alama kukan zuci yake yi,domin miscarriage in Zahran 3 kafin suka samu wannan ya zauna ta haife Dan gashi kwanan shi 3 tal a duniya Allah ya karbi abun shi, Nasiha me shiga jiki da kwantar da hankali Alhaji salis ke yi wa Alameen har suka iso gida,inda suka tarar an gama wanke jariri,an nado shi,ganin rashin kyautuwan a kai dan makwancin shi SEN be sani bane ya sanya shi ja gefe tare da dannawa SEN kira, Yana zaune yana cin breakfast hankali kwance kiran Alhaji salis ya shigo,saisata kanshi yayi tare da danne farincikin da yake ciki,domin ko be dauka ba hakan ya tabbatar mishi an rasa jinjirin da aka haifa, Daukan wayan yayi bayan ya kusa tsinkewa tare da yin sallama kamar kullum, Murya a shake Alhaji salis ya amsa,cike da kulawa SEN yace Aboki na lafiya kuwa Na ji muryan ka haka me ke faruwa ne, Hanci Alhaji Salis ya ja sannan yace wlhy SEN rasuwa aka yi,inalilahi waye ya rasu SEN ya tambaya sounding so very worried, Takwaran ka ne ya koma yau da safen nan yanzu ma ana shirin yi masa sallah shine nace ya ci ace ka sani, Allahu Akbar SEN yace kamar zai yi kuka Allah sarki Ashe yaro ba me zama bane,ikon Allah ba ruwan Allah yanzu kana nufin takwara Na ya koma,ubangiji ya sa me ceto ne gani nan zuwa yanzu,da haka ya kashe wayan bayan ya gama kwararo addu'oi, Cikin sauri ya shirya tare da fitowa,saida suka biya ta gidan Alhaji Kabiru suka dauko shi sannan suka nufi makabar tan domin lokacin har an gama masa sallah, da su aka kai yaro makwancin shi Na gaskia,wanda saidai mu ce Allah ya jikan shi ya sanya me ceton iyayen shi ne, Ganin irin damuwar da Sen ya shiga saida Alhaji salis da Kabiru suka shiga bashi hakuri suna cewa ya dau dangana in be karfafawa Zahra ba ai bare sanya ta kuka ba,da kyar ya nutsu domin ce musu yayi shi wlhy tausayin Zahran yake ji ba kadan ba,haka aka dunga xuwa gaisuwa domin Randa aka yi haihuwar labari ya bazu anyi wa SEN takwara so duk wani mutanan sa saida suka zo taaziya, Kwanan Zahra uku a asbiti kafin jikin nata ya fara sauki aka sallame su suka dawo Gida, Sati guda SEN ya dauka yana zuwa gaisuwa tare da kai goma sha tara Na arziki don daukan nauyin abincin da za a ci Na mutuwar yayi,duk gurin kowa Albarka yake sanya masa ba kamar dangin Alameen da salis domin ba karamin nuna kula da damuwar shi yayi game da mutuwar nan ba,Wanda deep down kuma ba Wanda ya kai shi farinciki, Randa suka hadu da Zahra jikin shi ba karamin sanyi yayi ba domin irin Rama da kukan da take tayi,lallashin ta yayi ta yi,tace da shi in sha Allah ko gobe ta Kara haihuwa sunan shi za ta maida,Allah kuma ya jikan wannan babyn nata da ya mutu, Nasiha sosai yayi mata Wanda Alhamdulillah yayi tasiri akan ta domin har abinci ta ci me yawa wannan ranar, daman tun tana yarinya Allah ya hada Jinin ta da Sen haka kawai take kaunar shi zan iya cewa ma shine role model inta she look up to him,be bar gidan ba saida ya siya mata sabon mota ta mil 30 tare da biya musu ita da mijin ta Makkah da Manchester wai su Dan je hutun ko Na 3 months ne ko za ta manta da damuwar da ke damun ta, Ba karamin dadi da godia Alhaji Salis yayi wa SEN ba yana ta sanya masa Albarka tare da yi mishi fatan gama wa lafiya,haba Aboki Na Zahra ai ya ta ce yau in ka fadi ka mutu ni ne uban ta so wannan ba wani abun godia bane,nayi mata hakan ne ko hankalin ta zai Dan kwanta, domin nasan dole ta ji ciwon abun Amman ya muka iya Allahn da ya bamu shi ya karbi abun shi Allah ya sa me ceto ne,baran wuce Hospital gurin yar ka, Ameen ya Allah mun gode sosai SEN Allah ya bada lada,don Allah ka gaida Nadeeyan in sha Allah nima zan zo duba tan,to ba damuwa da haka suka rabu zuciyar shi cike da farin ciki,gefe daya kuma yana me Jin tausayin Zahra in,but da ya tuna nothing good ke zuwa cikin sauki ya sanya ya watsar da wani tausayin zahran at least ai yayi compensating in ta,ko gurin Allah he is sure be da wani laifi,he did it to protect his dignity, (Ya Allah ka raba mu da son zuciya, Allah ka raba mu da son duniya,sannan ya mana tsari da cin amana ,tabbas mutanan mu sun dauki amana ba a bakin komai ba,kuma wannan a rubuce take duk Wanda ya amince da kai,ka ci amanan sa to tabbas Amana ma za ta ci ka,ina mamakin masu daukan hakki,hakkin ma Na ran Dan Adam ba tare da wata hujja ba suyi tsamanin za su ci bulus,rayuwar mu Na yanzu an maida ran mumuni Na a bakin komai ba,ya Allah,masu hali irin Na SEN Allah ka nisan ta mu da su ka kuma gyara mana halaye da kuma zukatan mu), *************Nadeeya A halin da ake ciki kam yanzu in akwai abun da ke gaba da hauka to Nadeeya tayi shi,sakamakon aluran da doc bashir ke dirka mata,Wanda sabida mugunta irin nashi har shock treatment ya sanya mata Wanda ya dada haukatar da ita,(Marin da SEN ya masa yake ramawa akan Nadeeya,sabida shi mugu ne shine harda sanya mata shocking), Haaaaa Nurse Kareematu tace da Nadeeya da ke irga yatsayun hannayen ta tana dariya, ko kallon Kareematu bata yi ba, Ki bude baki ki sha maganin ki mana, ta fadi cike da kosawa, Harara Nadeeya ta Galla mata tare da cewa ooo,ran Kareematu ne ya soma baci tace zaki bude ko sai Na miki alura, Jin haka ne ya sanya Nadeeya,bude baki da sauri domin ta tsani aluran da suke mata,cokalin maganin ta sanya mata a baki tana ai da baki sha ba da kin ga abunda zan miki, wai ke ga ki yar me kudi, har wani isolating in ki aka yi,banda ina samu a jikin ubanki da wlhy Rama dukan da kike mun zan nayi, Bata kai ga rufe baki ba ta ji Nadeeya ta watso mata maganin bakin nata a fuskan ta,tana me tintairwa da dariya kamar wata karamar yarinya, In ran nurse Kareematu sun kai dubu to duk sun baci yau,a zuciye tayi kan Nadeeya fadi take yar iska ni zaki watsa wa maganin baki, Tashi Nadeeya tayi da gudu suka hau zagaye dakin tana wa Kareematu dariya Wanda sai binta take ita ala dole sai ta buge ta,garin bin ta da gudun ne ta harde kafafun ta sai ga ta a kasa ta fadi akan fuskanta, gwalo Nadeeya tayi mata tare da taka yatsun hannayen ta Wanda saifa ta saki Kara, ganin tana shirin tashi ne ya sanya Nadeeya nufan kofa da gudu tana dariya, Lucky her kofar ba a kulle take ba,ganin tana ja ya bude ya sanya ta sanya ihun murna tare da ficewa da mugun gudu tana waiwayen Nurse Kareematu, Fitowan shi ke nan daga office zai yana sauri zai nufi gidan Habeeb don ya gaiyace shi Lunch yace yayi sauri don harda masa matar shi tayi musu,(oh doc Nameer kai da Masa dai 5&6 ne Na ga alama,lol), Waya ne a kunnan shi yana magana da Mama sai ji yayi kamar daga sama an bangade shi, Wanda saida wayan kunnan nashi ta fadi kasa, Juyowan da zai yi don ganin waye haka ya sanya ta hardewa tayi taga taga za ta fadi da sauri ya riko waist in ta tare da manna ta a kirjin shi yana bin ta da kallon mamaki, domin daga ganin yanda gashin kanta ya rufe mata fuska ya tabbatar mishi da ita ce ya gani wannan ranar a zaune, Jin bata kai kasa bane ya sanya ta sakin dariya cikin siririyar muryan ta tare da sanya hannu ta bude gashin kan nata in da nan take kyakkyawan fuskan ta ya bayyana, Ya salam doc Nameer ya furta yana me zuba mata eyes ko blinking baya yi,ita din ma shi take kallo kafin can kamar Wanda aka tsikara ta fito da tongue in ta tare da lashe mishi kumatu sai kuma ta sanya dariya tare da daka tsalle, Maganar Nurse Kareematu da ya ji a bayan su ne ya sanya shi dawowa daga Dan guntun sumar da yayi because he was totally shocked da abunda Nadeeya tayi mishi, Go get her shine abunda Nurse Kareematu tace in da Sam Nadeeya ta ki sake Nameer daga ganin ta xaka San a tsorace take da Kareematun,domin zan iya ce wa she was so free with Nameer lokaci daya,duk da fitowa take ba,and daga ganin yanayin ta za ka san she is so depressed and scared saidai wannan childish behavior in nata da Nameer zan iya kiran shi watakil wai silan haduwar su, Da kyar da sidin goshi aka ja Nadeeya zuwa dakin ta kuka take tana fadin ita bara ta je ba,ana yi mata injection me zafi bata so,shi dai doc Nameer Na tsaye cak har aka wuce da ita dakin ta tana mika mishi hannu idanun ta cike taf da hawaye.... [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEY BEE) ....... My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba comment bane zai shigo da ke to don Allah kiyi zaman ki,haka zalika maza kar su shigo mun cikin group domin Na mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son tallata musu hajar su contact me via: 08100046388 ........... Page fifteen *********** Da kyar da sidin goshi suka samu suka sanya wa Nadeeya chain a hannun ta domin duka ta shiga kai musu ta ko ta ina, inda ta kai wa sis Kareematu wata hambara saida ta fasa mata baki sai ga jini, haka sauran workers in da suka kawo ta duk saida ta laka da musu duka saida aka mata aluran bacci kafin aka samu hankali ya kwanta, Cike da bacin rai Kareematu ta fito daga dakin,domin kashedi Bashir ya mata kan ko me Nadeeya za ta mata be yarda ta buge ta ba in ba haka ba SEN uban su zai ci daga shi har ita, Nameer Na nan tsaye har kareeamtu ta zo ta wuce shi,kafin ya dawo hayyacin shi,waye wannan yarinyar,me yasa ta rike shi haka,sannan wani irin injection ne suke mata Wanda take kira akwai zafi bata so,duk sune tambayoyin da ke ringing a cikin brain in shi,ganin wuce war Kareematu ne ya sanya ya bi bayan ta,domin babu me amsa mi shi wannan tambayoyin sai ita, Da sallama ya tare ta,ganin shi ne ya sanya ta juyo a wulakance tare da kallon shi tana wani harare harare, Sannu sister shine abunda ya fadi mata ko a jikin shi da irin kallon wulakancin da take bin shi da shi, A yangance kamar wata yarinya karama tace hmmmm Na miji ke nan,in ce ni da kai Na,na biyo ka har office in ka amman kayi mun diban Albarka yanzu miye kake so daga guri na,ta kare tana hararan shi, Dan karamin saki ya ja a ranshi yake fadi ji wannan kamar ce mata aka yi wani abun nake da bukata daga gurin ta, Ka yi shiru ko baka da abun fadi nayi wuce wa ta,ta kare tana adduar Allah sa inviting in ta dakin shi ko in ce gidan sa zai yi, Tambaya daman zan miki game da patient in dazu,wani irin tukukin bakin ciki ne ya tokare ta a kirji,wato shi ta Nadeeya ma yake ba ita ba,to wai ita me ta rasa ne da bare lura da ita ba,kyau ne ko diri bata da shi,in yayi zafi ne fa yace ta Dan fi shi a shekaru and miye a ciki ai age is just a number,ga yanda Bashir ke rawan kafa akan ta tana masa yar hali amman shi a karan banza za ta bashi jikin ta yana mata bura uba, Tsaki ta ja sannan tace da shi ina ruwan ka da ita,ko ina ruwan ka da injection in da ake mata,patient in ka ce for your on information stay away from Nadeeya domin Doc Bashir ke handling case in ta,beside in kana da bukatar tayin da nayi maka har yanzu kofa a bude take za ka iya nema ta,Allah ya mun tsari shine abunda ya ce tare da barin gurin, Kai tsaye motar shi ya nufa,gida direct ya wuce,takalman shi kawai ya iya cire wa tare da fadawa kan gado, Goshin shi ya dafe tare da lumshe idanun shi,fuskan ta ke masa gizo yana kallon dariyar da take mishi,ya salam daman ita ce Nadeeya RILWANU Audu Waziri in,but ta ma fi kyau a fili Ashe akan kallon da ya mata a video in ta da ke treading , Shafo kumatun shi da ta lasa yayi kawai sai ya saki murmushi,lalle hauka bata yi ba,in ba hauka ba ai ko kudi za a bai wa Nadeeya ta yi mishi abunda ta yi masa he is very sure bara ta iya ba,zai iya ce wa this is the first time da wata mace ta taba shi bayan rasuwar Noor in shi,haka kawai ya tsinci kan shi cikin tunanin wani irin Alura ce haka suke mata da take cewa bata so,karan shigowar kira ne ya katse shi daga tunanin da yake yi, Daukan wayan yayi tare da Mike wa don ganin Habeeb ne,nan ko ya hau shi da mitan wai ya shanya shi since an gama abinci,hakuri ya bashi tare da ce da shi gashi nan akan hanyan shi yanzu zai iso, Be dauki tsahon lokaci ba ya isa gidan Habeeb kasan cewar basu da wata nisa, Gaisuwa suka yi da matar shi Muhibbah sannan ta shige ciki don basu guri, Suna cin abinci ne Doc Nameer ke ba wa Doc Habeeb labarin abunda ya faru saidai be sanar da shi kan Nadeeyar ta lashe me kumatu ba, Saida ya kurbi ruwa sannan yace wlhy nayi mamakin da ta fito ma,domin ni tun da aka kawo ta ban taba sanya ta a idona ba,boye ta Bashir yake yi kamar wata Amarya, Wlhy nima abunda Na gani ke nan,and ni wlhh Na kasa nutsuwa sam wai miye ma silan haukan nata ne, Wa ni wlhy Nameer ban sani ba domin ko case file in ta ban taba gani ba,hasali ma da aka kawo ta Bashir cewa yayi shi zai yi handling case in kowa yayi staying away from her,saisa ma ko fitowa shan fresh air ba barin ta yake tana yi ba,beside kai miye Na daga hankalin ka abeg mu ci abinci kar yayi sanyi, Daga haka Nameer be kuma cewa komai ba,Amman deep down ya dauki niyan in sha Allah ya je asibiti gobe zai tuntubi Bashir da maganar,in da zai yarda ma da ya bar mishi case in nata,haka suka gama cin abinci sai yaba girkin matan yake ,a gidan suka wuni har dare suna hira kafin yace zai koma gidan shi,dubu ashirin ya bai wa Muhibba kyauta wai a siya wa baby Fadeel pampers,godia tayi mishi sannan Habeeb ya rako shi har mota ya koma gida, Hira suka sha sosai da Mama,ya so ta bai wa Angel ta ce da shi tayi bacci saidai Amrah, mamaki yayi wai har yanzu ba ta tafi ba,mama za ta bata ya ce aa ta bari zai kira ta da kan shi, da haka ya kwanta bacci abun shi, Washe gari sassafe a asibiti yayi mishi,direct in da ake aje files ya nufa domin shi fa ya kasa yarda Nadeeya hauka tayi, don maganar gaskia yanda ya gan ta babu Wanda zai ce mahaukaciya ce,zai fi ma yarda da maganar jefan da aka ce anyi mata,ya sanya yake son ganin case file in ta domin ya San matakin haukan nata, Saidai kaf ya gama bincike cikin gurin Amman babu case file in Nadeeya,mamaki ne ya kama shi domin a iya sanin shi ba a karban patient ba tare da an rubuta case report in shi ba, ganin dai babu Na tan ya sanya shi fitowa tare da nufan office in doc bashir, Gaishe shi yayi,ya amsa shi a dakile sannan yace da shi lafiya,uhmm daman Na zo ne game da case in number 354, Da sauri Bashir ya mike tare da fadin and what about her,aa actually Nothing kawai dai if you don't mind ina son ganin case file in ta ne,because the why she is isolated haka Na san ita kanta she will be depressed, Rai Bashir ya bata sannan yace ina kace if I will not mind toh I will mind in fact I want to advise you to stay away from her domin ni ke handling in case In ta,and about her isolation mahiafin ta ne ya bukaci hakan so I think we are done babu ruwan ka da ita carry on with your work and stay away daga abunda be shafe ka ba, Ran Nameer ya sosu sosai da abunda Bashir ya fada mishi and right through his eyes ya gano akwai abunda yake boye wa,domin Habeb ya sanar da shi harda pin code aka sanya a kofar shiga inda Nadeeyan take,in har babu abunda yake boye wa miya sa ba a barin ta tana fito wa kamar sauran majinyatan, Saidai ya hadiye bacin ran tare da yin murmushi yace well tunda kace haka daman I was just been concerned ne,and at least hospital daya muke aiki so duty Na ne nayi making sure duk wasu patients Na lafiya, tunda ka ce I should stay away ba damuwa zan yi yanda kake so,Amman kafin nan I want to know wani irin injection kuke mata ne,ko in ce wani irin treatment kuke mata Na ganin recovery in ta don tayi complaining ana yi mata alura me zafi, Tashi Bashir yayi yace yo ga iskanci ganin ido Na,kila Dan sanda ne kai ko kuma lawyer me kariya right halan a court room muke,sabida tsaban ka raina ni,za ka zo har office ina kana mun irin wannan tambayoyin rai nin wayon, Murmushi Nameer yayi sannan yace ko daya kawai dai ina carrying out duty Na ne,rai bace doc bashir yace carrying out duty ko kuma munafurci, daman ni can Na ga take taken ka munafuki ne kai,toh wlhy ba dai wa ni za ka yi wa munafurci ba yo har sai ka kama maganar mahaukaciya , I don't see any reason da zan tsaya explaining kai Na a gurin ka tunda ba uban ta bane kai,one thing da nake so da kai shine ka bar mun office ina right away kafin ka gama bata mun rai, Kai kawai Nameer ya girgiza domin in ya canka daidai doc bashir yana kan Jin haushin shi ne akan abunda ya faru kwanaki, I never thought magana ta za ta bata maka rai I was just being concerned ne but since ran ka ya baci am sorry and as u said babu ruwana so daga yanzu I am stepping back daga abunda be shafe ni ba,daga haka ya fice daga office in ran shi a bace, Da de yafi maka bakin munafuki masu hana ruwa gudu tunda kaine ubana shine za ta zo kai kafi kowa son sauke duty,to Allah ya tsine uban me duty din ma,doc bashir ke ta sababi ko in ce kokarin kare kan shi,shi dai Nameer be kula shi ba office in shi kai tsaye ya wuce ran shi nayi masa zafi domin karara ya ga rashin gaskia a idanun Bashir Amman yayi masa irin wannan diban Albarkan, Saida ya sha ruwan sanyi sannan ya dan ji sassaucin zafin da zuciyar ta shi ke mishi, zama yayi tare da kura wa kofa idanu haka kawai ka bi ka takura kan ka akan Nadeeya ina ruwan ka da ita the best thing is to stay away from her shine abunda zuciyar shi ke fada mishi, Saidai wata zuciyar Na sanar masa kamar yarinya tana cikin wani hali hali Na neman taimako and he will forever hold himself responsible yana da hali be taimaka mata ba, To a taya zai ma taimake ta shi da be ma San takamammiyar abunda ke damun ta ba,ya dauka zai ga case file in ta ne,but daga abunda Bashir ya fada mishi ya gano tabbas akwai abunda suke boyewa shi da Kareematu to miye ne wannan abun,shine abunda yayi ta matsawa ranshi ya sani..... Wlhy Na so ya fi haka saidai ina fama da ciwon hakori, Wanda yayi mun causing in ciwon kai,a sanya ni a addu'a don Allah,sannan ayi mun afuwa don nasan bara a rasa typing error ba wlhy da kyar Na samu nayi page in nan, Ina wa kowa fatan Alkhairi. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ...... My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki to pls kar ki shigo,don ko kin shiga zan yi waje da ke,haka zalika maza should stay far away from my group please๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su kuwa contact me via: 08100046388 ........... Page seventeen ************ Tun daga wannan ranar doc Nameer ya maida isolated room gurin hiran daran shi, domin a kwana ukun nan baya missing kullum sai ya je gurin Nadeeya , Haka zai bari sai kowa ya tafi sannan ya bi dare ya dawo kamar wani barawo, and baya taba zuwa mata hannu haka ice cream dai wajibi ne sai ya kawo mata, sai ya hada mata da wani kayan dadin, Tun tana duka da masa ihu in ya zo har ta gane shi ,tana ganin shi sai ta hau murmushi tana mika mishi hannu ta san ya kawo mata kayan dadi,a haka zai lallace a gurin ta tayi ta masa shirme yana biye ta har sai ya ga bacci ya dauke ta tukuna,ya Na son ya ga an gyara mata gashin ta an yanke mata nails in ta saida baya son yayi mata da kanshi don ba muharramar sa bace be son yana taba ta any how and be San ko tana da aure ko Alkwarin wani akan ta ba tunda ba ganin case file in ta yayi ba,saisa baya son tana shige masa jiki, A matukar rude Kareematu ta shigo office in Bashir inda ta same shi ya tasa wata karamar nurse sai matse ta yake, Tsaki ta ja kamar halcen ta zai tsinke sannan tace kai dai wlhy anyi Dan iska wlhy ka ji kunya wani irin maita ne wannan mutun ace jaraba ta fi karfin shi, Da sauri yarinya ta sauka akan table in office in tare da Saurin ficewa shi ko tashi yayi tare da gyara zaman wandon shi sannan yace Malama uban me ya kawo ki office ina ba tare da neman excuse ba, Yo kace haka ai Dan iska tunda Na kama ka da mace wlhy ka ji kunya in banda iskanci da kana tambaya ta me ya kawo ni office in ka ne,sabida yanzu ka ga karamar yarinya shine duk ka wani bi ka rude ta kare tana Galla masa mugun harara, Look Kareematu daka ta mun and ya zamo karo Na karshe da zaki zage ni,jiki ne Kin ce bara ki sake bani naki ba,toh ai ba ke kadai bace me shi Na ga duk matan duniya da shi aka haife su,don haka ki jiga naki ki shanye sannna ki cire ido akan abunda zan yi domin ba ruwan ki, Ba shakka Bashir ai ka fada mun komai an sha magoro an shanye dadin an yarda ba,toh wlhh baka isa ba, Be ce da ita komai ba ya juya tare da kokarin barin office in Sai kuma ya juyo in kin gama surutan da iska kina iya fitowa ki rufe mun kofa,domin Na ga sabon likitan nan an sha wanka yau kya iya zuwa ya rage miki zafi don Na ga kamar a matse kike, Bura uba Bashir ni kake wa bura uba duk Dan Na kama ka da mace,ka mun laifi sannan ka fi ni baki,Amana ta fa ka ci bura uba shine kake watsa mun magana son ranka,ta kare tana girgiza, shi dai be ce da ita komai ba,yana kokarin fita Ai ka fita Amman ka fin ka bi shegiyar yarinyar ta ka ina so ka biya dakin Nadeeya ka ga halin da take ciki,domin am very sure in har ka ganta sha'awar kan ta sai ta dauke maka domin ka san waye uban ta sarai wlhy ba yarda zai yi ba, Da mugun hanzari ya nufo ta yana fadin Na shiga uku Kareematu me kika yi wa Nadeeyan,hannun shi ta doke sannan tace ka ji mun Dan iska me kuwa zan mata ni ma abunda nake son in tambaye ka ke nan,domin ai kai ka ganta Na karshe jiya har ka jona mata shocking, halin da ake ciki yanzu dai,ai be jira karasa Jin ta ba ya nufi dakin Nadeeya a 360 zuciyar shi Na tsanan ta bugawa,yana adduar Allah sa ba wani abun ya same ta ba,to ko dai mutuwa tayi, Na shiga uku shine abunda ya fadi a fili tare da shiga cikin dakin, A kwance ya same ta idanun ta a bude sai hawaye ke fita,zuwa yayi har gaban ta tare da tsunguna wa yace Nadeeya me ke damun ki,Jin shiru ya sanya shi cewa lfy don't you want to talk, Nan ma shiru,hankalin shi ba karamin kadawa yayi ba ganin ko motsi bata yi,ga magana ma bata yi,ganin haka ne ya sanya ya dauko alura sanin ko ma iskanci take yi in ta ga aluran tana tsorata tayi ta buge buge Amman har ya tsikara mata ko tari bata yi ba, Na shiga uku shine abun da ya fadi a bayyane ganin ko hannun ta bata iya daga wa,nan take cikin shi ya murde sai ya ji wani irin zawo Na kokarin zubo mishi, da sauri ya fada toilet in ta ganin zai iya yi a jikin shi, yana zawo yana hawayen tausayin kanshi domin ya San wlhy SEN ya ji labarin nan sai ya kashe shi, a haka ga fito jiki ba kwari ya bar dakin, Kai tsaye office in shi ya koma tare da kiran Kareematu, da tagumi a fuskan shi ta same shi,dariya ta so yi ganin lokaci daya inda ya ficicike, Hope ka ganta ko Bashir ka ga abunda nake ta fada maka,Na shiga uku Kareematu shine abunda yace kamar zai yi kuka,wai don Allah me kika mata ne, Bura uba na rantse Bashir zan ci uban ka in ka kuma ce wa Na yi wa yarinyar nan wani abu,ni sau nawa ma Na taba mata Alura kai ke da in charge in komai nata,don haka am sure kai ne kayi mata wani abun,ka ga tun wuri baran kira uban ta in sanar masa kafin ka kashe musu yarinya a rufe mu da asibitin mu,Ashe bayan san kudi har kisa za ka iya yi, Zufa ne ya wanke masa fuska cikin muryan tausayi yace Na rantse da Allah Kareematu ban yi wa yarinyar nan komai ba,ni miye hadi Na ko in ce miye riba ta in Na kashe ta ko Na nakasa ta,wlhy babu ruwana da ita,ni ban mata komai ba,don Allah kar ki kira SEN wlhy mutumin nan ba ganewa zai yi ba ki tsaya mu nemi mafita, Mu nema ko ka nema ni miye nawa,and da kake cewa kar mu sanar wa uban ta,to uban wa kake so mu sanar wa,ai dole kuwa ya ji sabida ya san me zai yi,don hka ni yanzun nan zan Kira shi ba sai anjima ba, Na shiga uku kareema in kina wa Allah ki rufa mun asiri sai kace ba masoyiya ta abar kauna ta ba,Kareematu Bashir in ki ne fa, Tsaki ta ja sannan tace kamar ba wa ni ka ga ma yi wa diban Albarka ba sannan yace ka zo kana wani Kareematun ka ce,ai ka je can gidan yari Na San SEN zai sa a kai ka, Cikin shine ya kuma murdewa yace haba tawan kar ki mun haka,zan tura miki dubu dari da hamsi don Allah kiyi shiru kar ki kira shi Na roke ki,ya kare yana hade hannayen shi, Harara ta watsa mishi sannan tace dubu dari uku za ka tura mun kafin nayi shiru harda kudin Mari Na don ba banza ka mara ba, Mamaki yake wai Kareematu ke masa barazana haka ikon Allah, bayi da choice haka a take ya mata transfer in dubu dari ukun, Dariya tayi ta girgiza kai sannan tace Allah ya shirya ka Bashiru Na bari Na je, Allah kawo maka da sauki, Da ido ya bita yana me jin haushin ta saidai bayi da choice da ya wuce ya bi ta a sannu domin ya san kwayancin kareema Sam bata da mutunci bata kuma da tsoro, Kareematu ko tana fita wayan ta ta dauko tare da danna no in SEN, haka kawai ai wlhy Bashir sai Na tona ma asiri, ko ba ni ka mara ba, Har ya gama ringing ba a dauka ba saida tayi kira sau uku sannan aka dauka, Gaishe shi tayi cike da girmamawa sannan tace ita daya daga cikin nurses masu kula da diyar shi Nadeeya,yau tun safe take kuka take kiran sunan ka da alamun son ganin ka take yi,ta kare murya cike da biyayya, Okay I will be on my way shine abunda SEN yace tare da kashe wayan, dan tsallan murna Kareematu tayi kafin ta maida wayan cikin aljuhu tana Jin ranta fesss ko banza ta hadawa Bashir, ...............SEN Cike da mamaki yake bin wayan da kallo, Kabiru ne yace ya ne Aboki Na lafiya, Hmmm kabiru bari kawai wlhy kira ne daga asibitin su Nadeeya wai tun safe take ihun kiran suna Na wai tana son gani na, Ganin ka kuma, wlhy nima abun ya dauran kai Na dau by now bakin ta ya rufu kirif,Amman sai Na ji wani abun daban, kai kan ka fa kasan aikin odugwu kamar yankan wuka ne tunda har ka bada abunda ake so kuma kai kan ka kace mun an karbi sacrifice in ka Odugwu be taba karya alkwari ba,tunda har yace zai yi to wlhy zai yin ne ba fashi ,Amman tashi mu je asibitin Na karasa maganar a hanya, Nan suka nufi mota sai hospital, kai tsaye office in Bashir suka fada wanda suka tarar ya kifa kanshi a jikin table, Doc bashir Alh Kabiru ya kira sunan shi, a razane ya dago ganin SEN a tsaye a Kansa shida Kabiru ya sanya ya ji hanjin cikin shi ya kada,saidai yayi kokarin dannewa tare da mikewa, cikin karfin hali yace SEN sannu da zuwa lafiya Na gan ka ga guri ka zauna, Murmushi SEN yayi sannan yace aa ba sai Na zauna ba Na zo ganin princess ne, Da sauri yace yallabai an ce ma wani abu Na samun ta ne,babu fa abunda ya faru da ita tana nan cikin koshin lafiya, Da ido SEN ya kalle shi sannan yace Bashir ni ka ji Na ce akwai abunda ke damun yarinya ta,ko kuma laifi ne in uba ya zo ganin yar sa, Kai kake masa bayani ma SEN daman ka fada mun yawa magana Bashir ke da shi ,dallah tashi ka kai mu,muna da abun yi, Jiki babu kwari ya mike tare da yin gaba suna bin bayan shi,SEN ke rada wa Kabiru ya yaga Bashir kamar yana cikin damuwa,yoo ni ina nasan wa Dan iska mu dai je mu gan ta first mu san halin da muke ciki, Da sallama Bashir ta shiga dakin zuciyar shi Na bugawa uku uku,ji yake kamar ya rufe su a dakin ya ruga da gudu sabida gudun abunda SEN zai masa,saidai is to late yayi hakan, Shi ko SEN karasa shigowa dakin yayi yana me hango Nadeeya a kwance lah bacci take yi ne ya tambaya yana nufan yanda take, Da sauri Bashir yace eh ta samu bacci ashe mu je kar a tashe ta in ya so sai ku dawo ko jibi ne ku ganta tunda dai ai kun ga tana cikin koshin lfy,normally ba mu cika barin ana yawan ganin majin yatan mu ba, Wani irin harara sen ya jefa masa sannan yace a yaushe kuka fara wannan tsarin iskancin, da rawan baki yace jiya cikin dare,ko kula shi be yi ba ya durgusa a gaban Nadeeya din da ya gani idon ta bude kamar ma hawaye take yi, Kabiru ka ga Ashe ma idon ta biyu tana Jin mu,kanta ya shafa sannan yace hello princess, he was expecting ya ga ta janye hannun nashi kamar yanda ta saba ko ya ji tana jifan shi da mugayen maganganu saidai tsit ya ji ta, Da matukar mamaki ya mike tare da kallon Bashir sannan yace why is she not talking, me ke damun ta kuma, Na ga yau ko ihun da ta saba da fashe fashe bata yi lafiya kuwa, Nan take Bashir ya hau inda inda fadi yake hmmm ammmm ahhhhh daman,tassss SEN ya wanke shi da Mari sannan yace daman in uwar ka ka fada mun uban me kayi wa yarinya ta bata mun magana, Cike da radadi tare da rudewa yace yallabai Na rantse da girman Allah dazun nan Na shigo Na gan ta haka bata magana ko motsi ma bata yi,ya kare yana kare fuskan shi da hannu biyu biyu, Ai Jin haka ya sanya wata irin jiri kwasan senator sai ga shi yuuuuuu yayi baya zai zube a kasa,da sauri suka taro shi Kabiru yana fadin take it easy Aboki na in sha Allah babu abunda zai samu Nadeeyar mu..... Manage this please aiki ya mun yawa wlhy, Bi sa complain in da Na samu Na in Kara 2 more pages kafin Ramadan ya sanya ni yin typing yau, saura yanzu 3 more pages in sha Allah, Bani kuma da bakin gode muku, masoya Na Wanda Na sani da Wanda ban san su ba,saidai nace Allah ya saka da Alkhairi da kaunar da kuke nuna mun,nima ina kaunar ku fisabillah, Ina wa kowa fatan Alkhairi, Sai kina gobe in Allah ya kaimu. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba karanta book ina and comment zai shigo da ke ba,to pls kar ma ki shigo, haka zalika maza should stay far away from my group pls๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu bukatar a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ............ Page eighteen ************ Ruwa Alh Kabiru ya shafa wa SEN a fuskan shi Wanda ya dawo da shi daga duniyar sumar da ya fada,wata irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauke sannan ya bude idanu a hankali, Doc bashir ya gani tsaye a kan shi wanda kallo daya za ka masa ka fahimci yana cikin tsaka me wuya, Ai da sauri ya mike tare da cukumo wuyar rigar Bashir sannan cikin ihu ya hau masa fada,Dan uban ka me kai wa yarinya ta eheyeee bara ka yi magana ba,ya dauke shi da Mari me zafi, Kumatu Bashir ya dafe sannan ya shiga rantse rantse kan cewa wlhy shi ba abunda yayi wa Nadeeya, Wani Marin SEN ya dauke shi da shi a Karo Na uku sannan yace har ni zan yarda da ba abunda kayi mata,nawa suka baka ka maida mun ya haka,toh wai miye ma ka mata ne,wato duk kudin da nake baka be ishe ka ba saida makiya suka Kara maka ka maida mun yarinya haka,haukatar da ita kawai nace kayi wawa ba wai ka nakasa mun rayuwar yarinya ba ya kare ya me tada jijiyoyin wuya, Doc bashir baki ya mutu banda girgiza kai babu abun da yake yi,idanun shi har ya ciko da kwalla ya rasa da wani kalma zai wanke kan shi a gurin SEN, Shigowan sister Kareematu ne ya sanya shi saurin nufan ta,fadi yake yauwa Kareematu Na gode wa Allah da ya kawo ki don Allah sanar da su babu abunda nayi wa Nadeeya, Da kallon wulakanci ta bishi sannan tace ai daman Bashir saida Na fada maka aluran da kake bata sun fara yi mata yawa,Amman kaki ji karshe ka hada harda shock treatment kake mata,taya daman yarinya bara ta zama haka ba, Ai bata hada bakin ta ba ta ji saukan mari me dankaran zafi Wanda saida ya sanya ta zaro idanu, sabida radadi, Na shiga uku miye nayi da za ka mare ni haka ranka ya Dade, Uwar ki kika yi matsiya ciya wato da hadin bakin ki aka kusa kashe mun yarinya, Na rantse da Allah SEN ni babu ruwa Na gashi nan shima saida Na Hana shi yace da ni babu ruwa Na ta kare tana nuna Doc bashir da ya zazzaro ido sabida tsoro, Cukumo shi SEN tayi tare da Kara wanke shi da Mari Wanda saida ya sanya Kara,yanzu Bashir Ashe kai Dan iska ne ban sani ba miye nayi maka da har za ka sanya wa yarinya ta shock treatment, Na rantse da girman Allah ba zan bar ku ba,daga kai har wannan shegiyar ya kare yana nuna Kareematu a gidan yari za ku karasa wahalalliyar rayuwan ku,shegu yan iska marasa mutunci, Kabiru kira mun police su zo suyi gaba da mugayen mutanan nan kafin bakin ciki ya sanya Na kashe su da hannaye Na, Nan take cikin Kareematu ya duuri ruwa ita fa ta zo ne domin ta sanya Bashir a damuwa da matsala sai gashi ta samu rabon Mari harda za a kama su to akan me, Kamar hadin baki sai ga su sun zube a gaban SEN suna hada shi da girman Allah kan yayi hakuri kar a hada su da hukuma,wlhy tallahi babu hannun su a wannan abunda ya farun, Ba karamin kai ruwa Rana aka yi ba kafin aka samu SEN ya ce ya hakura bare kai gurin yan sanda ba Amman fa ya zama dole a dawo mishi da magana da kuma tafiyar yarinyar shi,domin bare yu ya basu yarinya da muryan ta da kafafun ta sannan yanzu a dawo da ita vegetable ba Sam bashi yuwa, Haka dai suka yi ta bashi baki harda Alh Kabiru a masu bada bakin,sannan ya dan sauko daga masifar da yake yi, Haba Alh Kabiru Na basu yarinya da lafiyar ta sannan yanzu ace ta dawo haka wlhy dole suna da masaniya,don haka Na basu Dan kankanin lokaci ko su dawo mun da yarinya ta daidai ko kuma Na kashe su da hannu Na,wuce mu tafi domin Na cigaba da tsayuwa ina iya aikata abunda be dace ba ya kare yana gallawa bashir da Kareematu mugun kallo sannan Alh Kabiru ya biyo bayan shi zuciyar shi cike da mamakin karfin hali irin Na SEN, Suna shiga mota kuwa SEN ya kwashe da wata irin dariyar samun Nasara sannan ya zubo kirari da yar banci wa odugwu sannan ya kalli Alh Kabiru da ya zuba mishi idanu,yace ya aka yi ne mutumina, Hmm Wlhy tallahi RILWANU tsoro ka koma bani,ban taba ganin makirin mutum ne fuska hudu ba irin ka,wlhy ko mace nan ta gan ka ta bar ka gurin tuggu,kwalba uwar sharri,ina tsoron ka wlhy, Dariya SEN yayi sannna yace haba dai Kabiru kai da ka kwanta da Maman matar ka ka baiwa odugwu Jinin ta ban ji tsoron ka ba sai don ni da nayi wannan dan karamin drama in, Tsaki Kabiru yayi sannan yace kai magana bata wuce maka maganar kwanciya da suruka ta nake maka ko ta draman da kai wa Bashir, sanin kan ka ne fa kai ne silan ciwon yarinyar nan Amman ka bude idanu ka nuna Sam baka da masaniya,kamar ma sune suka aikata,duk ka sanya su a guilty conscience,wlhy Sam baka da imani SEN, Har in ana maganar imani za ka sanya baki,ko ka mance yar ka yar 3 years da kai raping ka kashe da hannun ka,sai dan dan wannan abunda nayi kake ce mun banda imani, Don't forget duk abun nan muna yi ne don securing future in mu,and wlhy da asiri Na ya tono Na gwammaci ko ma miye ne nayi,but I have to protect my dignity shine kawai abunda Na sani,and so kake Na nuna nasan komai a gaban doc in look ina cikin mood in farinciki don Allah kar ka bata mun rai,beside Kabiru in mugunta ne har Na isa in kai ka abunda kayi ai ko zan mutu Na dawo ban isa nayi kwatankwacin su ba, Aboki Na ke nan yau kuma tone tonan asiri ne ya tashi ke nan,Dan dariya yayi sannan yace komai kayi ba komai bane in har za ka samu kudi,go chase the bag,kar ka matsa wa kan ka legal or illegal ne in har za ka yi kudin shike nan, Ah toh nima abunda Na gani ke nan,kai ne kake son fito mun da wata tsirfa tun farko da bata san komai ba ai da yanzu muna zaman mu lafiya ko,sannan kasan am damn lucky Nadeeya ta San asiri Na Amman odugwu ya mun Alfarma Na bar ta a raye har yanzu,ka ga ko dole nayi ko me zan yi Na ganin bakin ta yayi tsit gudun tonuwar asiri, Haka ne kam wlhy SEN baka da dama ko kadan,am very sure Bashir be isa bacci ba yau,dariya SEN yayi sannan yace siyasa ke nan mutumi na dole ka koyi dabaru nan ne zaka mori zaman duniyar,mu karasa gida domin a gajiye nake wlhy,Kabiru be sake cewa komai ba har suka iso gidan SEN, inda suka hadu da Alhaji Salis nan aka zauna SEN ke labarta mishi abunda ya faru yana kuka,ba karamin tausayi ya bai wa Alh Salis ba,nan ya shiga zubo tsinuwa da addu'ar samun lfy wa Nadeeyar, ***********Doc Bashir Kadan ya rage be rufe Kareematu da duka ba domin ba karamin haushin ta ya jj ba,banda rawan kai uban me ya kawo ta office in shi har da sanar wa SEN wai yana bata shocking, Kallon ta yayi cike da bakin ciki sannan yace kin kyauta Kareematu Amman ki sani wlhy sai Na rama abunda kika mun tunda ke bakin ki sam be iya yin shiru, banza karuwa kawai, Dariya ta sheke da shi sannan tace karuwai dai yanda nake karuwa haka kake karuwan Na miji,acewar ka banza ka mara ko,toh wlhy ka kiyaye ni, sannan da kake cewa sai ka Rama sharri nayi maka,Na gani duk abunda ke faruwa shine na fada,ni ban ce sai na rama ba akan ka an mare ni sai kai ne me hannun daukan fansa to bismillah,sakarai kawai wlhy in ka kuma kula ni ma sai nayi maka rashin mutunci, da haka ta sanya kai za ta fita,ko me ya tuna sai kuma ya bi bayan ta yana haba my Kareematy ai ba a Jin kan mu tsaya mu sasanta ko kallon yanda yake bata yi ba tayi gaba abun ta, **************Doc Nameer Gama wayan shi ke nan da mama yana sheda mata yayi missing in su yana son shigowa Kd this weekend in sha Allah, agogon hannun shi ya kalla ya ga goma har ya wuce,so yake ya shirya ya tafi gurin Nadeeya Amman sam yau baya Jin karfi a jikin shi,haka kawai kuma wani gefe Na zuciyar shi ke azaxxalar sa akan ya je ya duba ta din kamar tana cikin wani matsala haka yake ji a cikin ranshi ,saidai he is very tired yau be jin xai iya zuwa duba ta, alulan bacci ya dauro sannan ya kwanta bayan yayi adduan bacci tare da yaki ce tunanin Nadeeya a cikin zuciyar shi, Saidai sam baccin ta kasa daukan shi ya kuma kasa daina tunanin Nadeeya, Tsaki ya ja tare da mikewa jallabiya ya zura sannan ya dauko car key in shi tare da fitowa, Saida ya biya Saje ya siyo mata ice cream da Shawarma sannan ya dauko hanyan asibitin,kamar kullum dan cin hanci da ya saba bai wa securities in ta bada tare da shigewa a bun shi, Dakin nata ya nufa kai tsaye,yana adduar Allah sa bata yi bacci ba don kila ta gaji da jiran shi tayi bacci abunta,be taba sanin ya shaku da yarinyar ba sai yau da yace bare zo ganin ta ba har wai ya kasa bacci saida ya fito, Da sallama ya shiga cikin dakin yana me Jin mamakin ganin komai tsaf kamar naughty girl in shi bata wuni a dakin ba yau,shirun da ya ji ya sanya shi tunanin kila baccin tayi, Sleeping beauty har an yi bacci ke nan yace tare da nufo kan gadon nata,kwalbar da kafar shi ba buge ne ya sanya shi tsayawa tsak,tare da tsungunawa don ganin kwalbar miye haka, is not suitable ana barin kwalabe a dakin me jinya jinyan ma Na hauka,in ta ji wa kanta ciwo ba,idanu ya zaro tare da kare wa kwalban kallo,daidai lokacin aka bude dakin tare da shigowa, Idanu Doc bashir ya tsaro cike da mamaki sannan yace kwal uba uban me kake nema ana dakin cikin daran Nan...... Remaining 2 pages in sha Allah sai kuma in Allah ya sa mun kai bayan sallah, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi, Sai kuma gobe in sha Allah [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ......... MY group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki to don Allah kar ki shigo, haka zalika maza should stay far away from this house domin gidan mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ALHAMDULILLAH,A NAN ZA MU DAKATA DA LITTAFIN NAN HAR SAI ME KOWA ME KOMAI YA KAIMU BAYAN SALLAH,INA MIKA GODIA TA GA DUMBIN MASOYA NA WANDA NA SAN SU DA WANDA BAN SAN SU BA,INA GODIA DA IRIN KAUNAR DA KUKE NUNA WA LITTAFINA,UBANGIJI YA SAKA WA KOWA DA ALKHAIRI SANNAN YA SANYA MU FARA RAMADAN A SA'A,ALLAH YA SANYA WANNAN RAMADAN IN YA ZAMO SILAN SHIRYUWAN MU BAKI DAYA,UBANGIJI YA SA MU DACE SANNAN YA SANYA MUNA DAGA CIKIN BAYIN KWARAI DA ZA A YANTA DAGA WUTA ZUWA ALJANNAH, SAI MU KASANCE MASU AIKATA ALKHAIRI DUK KANKANTAN SHI DOMIN DUK ABUNDA KAYI LADA NE A WANNAN WATAN,CIYAR DA MARA SA KARFI BABBAN LADA NE,ALLAH UBANGIJI YA BAMU IKON AIKATA AIKIN ALKHAIRI SANNAN YA RABA MU DA SABA MISHI A WANNAN KWANA 30 DIN, DUK WANDA NAYI WA LAIFI YA YAFE NI SANNAN NA YAFI KOWA,DOMIN YANA DA KYAU KA FARA AZUMI BABU KOWA DA KA RIKE A CIKIN RANKA,UBANGIJI YA MANA ALBARKA BAKI DAYA SANNAN YA AMSHI IBADODIN MU YA KUMA YAFE MANA KURA KURAN MU๐Ÿ™๐Ÿป, ............ Page twenty *********** Da ido Nameer ya bi doc Bashir da kallo,daman yayi expecting ganin shi a daidai wannan lokacin, domin yana iya hango tsantsan tsoro da ya darsa masa a cikin zuciyar shi, Cike da muryan shakiyanci yace ah Doc bashir kai da kan ka ai da aikawa ma kayi Na zo sai na zo ai, Lebe Bashir ya dan ciza sannan ya yayi kwafa a cikin ranshi kafin ya sanya fuskan tausayi yace a a Nameer gwara dai Na zo da kai na din, ya kare yana isowa kusa da shi, Kallon shi kawai Nameer ke yi yanda duk ya bi ya rude kamar ki ce da shi kitt ya ruga da gudu, Haba Nameer a rayuwar nan me na tsare maka da ka tsane ni har haka kake son ganin baya Na, Da mamaki Nameer ke kallon Bashir in kafin yace Allah raba ni da ganin bayan wani bawa naka,doc Bashir hakikanin gaskia ban tsane ka ba hasalima miye hadi Na da kai da zan tsane ka babu abunda kayi mun,banda yau da Na kama ka da rashin gaskia,and sannan kai kanka kasan abunda kake ai be kyautu ba ko tsoro baka ji wannan alurai da kake bawa yarinyar nan ya jefa ta cikin wani hali haba kar mu zama marasa imani mana akan abun duniya da a nan gidan duniyar za mu bar shi, Bashir ji yake kamar ya rufe Nameer da duka domin sam shi wannan waazin da yake masa ba shiga kunnan shi suke ba,amman wai me neman sulhu sai yace, Eh Doc Nameer duk Na ji me kace kuma Na karbi laifi na,nayi kuskure yanzu dai nawa zan baka don ka samu ka sanya wa bakin ka zip,domin maganar nan in har ta fita to wlhy akwai matsala, Wani dariya Nameer ya kwashe da shi sannan yace daman nayi expecting haka,wato dai mara kunya ko a ina yake baya boyuwa,wai ce maka aka yi kowa ne me son zuciya irin ka,kana tunanin akwai kudin da zai siyi lafiyar yarinyar nan,to bari ka ji in baka sani ba Alhamdulillah I lack nothing a rayuwa ta ina da kawaa da zuci abunda ka rasa ni abun wani be taba tsole mun ido ba kan gaskia ta nake kuma aiki Na nake yi, don haka za ka iya barin mun office ka koma naka ka jira zuwan yan sanda, Cikin Bashir ne ya kulle yayi danasani cewa zai bashi cin hanci ai ha ci ya gane ba kowa ke da son zuciya ba gashi garin ya gyara ya bata komai, Amman dake tsohon Dan duniya ne sai cewa yayi,wai Nameer so kake kace da ni baka da son abun duniya,kar ka manta kudi sune maganin zaman duniya,beside miye halakan ka da yarinyar nan ne da ka dage sai ka ga tonuwar asiri Na, Kai Nameer ya girgiza sannan yayi yar murmushi tabbas ina da babban halaka da ita domin yar uwa ta ce a musulince and humanity came first akan komai,da kake maganar son kudi babu Wanda zai ce baya so,saidai da Na ci kudin da zai hana ni kwanciyar kabari gwara Na mutu da talauci wlhy, Ni ga alaman sam baka gane wa don Allah ka fitar mun daga office yanzu ba kuma sai anjima ba zan kira mahaifin yarinyar nan Na sanar da shi komai,bare yu ya baka amanar yar sa ba sannan ka zo kana cin amana, Ganin fa yaron nan ya dage da gaske yake yi in har ya bar shi zai iya tona masa asiri ya sanya shi zuwa tare da zubewa a gaban Nameer in ya kama kafafunshi duk biyu, Na roke ka da girman Allah ka rufa mun asiri kai ba mugu bane haramun ne saka sharri da sharri,kayi hakuri ka taimake ni kar ka sanar wa kowa koami,wlhy nayi kuskusre na kuma amsa laifi na, Da mamaki Nameer ke bin shi da kallo yana kokarin jan kafar shi,doc Nameer in ka fada wa yan sanda wlhy a yari zan kare rayuwa ta shike nan tawa ta kare,ina da mata ina da yara da suka dogara da ni in har bana nan rayuwar su za ta daidaice, Daidaice doc Bashir rayuwar Nadeeya da ka daidaitar fa,wannan hakki har ina za ka kai shi yarinya da hankalin ta ka dage sai ka hauka ta ita kuma fa me za ka ce akan wannan, Cikin kuka Bashir yace wlhh nayi nadama Nameer Na yi danasani Na biye wa son zuciya Na aikata cuta wa baiwar Allahn da bata san komai ba,Amman tona mun asiri won't solve anything, kar ka manta ance duk Wanda ya rufa asirin wani Allah zai rufa nashi, Bashir in har na rufa ma asiri rayuwar Nadeeya fa in bar ka ka cigaba da cutar da ita,kana tunanin Allah zai bar Ni ne ina ganin ana aikata zalunci akan ido na and Na gaza yin komai akai,me zan ce masa, Wlhy in har ka rufa mun asiri nayi maka Alkawari zan zamo mutumin kirki ba zan Kara cutar kowa ba,I will be a change man,and Nadeeya what about her, Nameer I promise you daga yau bazan kara mata injection ba,ka ga ni da kai sai mu hada force gurin neman maganin da xai yi curing in ta,ya kare yana cigaba da bashi hakuri, Shiru Nameer yayi yana tunanin Anya ya yarda da shi kuwa,but why not kowa yana laifi and mutum in da aka fi so shine wanda zai gane laifin shi har ya zo neman afuwa, Allah da kanshi muna masa laifi ya yafe to shi waye da ba zai ba wa doc bashir second chance ba, Cikin sanyin murya yace stop crying and begging me like a little boy,tashi I won't tell anyone anything, Da sauri doc bashir ya dago yace are u serious, yeah I am miye riba Na in Na tona Na asiri,beside ni ba wa ni kai wa laifi ba,ita ya kamata ka nemi gafaran ta tunda har ka gane laifin ka and ka shirya canjawa Allah yafe mu baki daya, But I want u to know one thing in har yaudara ta kake yi wlh bara tayi mana kyau ba daga ni har kai, Da sauri Bashir yace you won't regret this I promise u,Na gode sosai doc Nameer Allah ya yi maka albarka, and am so sorry da irin abubuwan da nayi maka a baya, Murmushi Nameer yayi sannan yace haba babu komai ai ya wuce,yanzu dai mu fuskanci yanda za mu warkar da baiwar Allahn nan, To ba damuwa za muyi magana ai bari Na koma office ina Na gode fa, ya kare kamar zai kwanta wa Nameer a kasa,shi dai da ido yake bin shi yana mamakin yanda zuciyar mutun zai bushe sabida son abun duniya ya iya cutar da Dan uwan shi,no wonder mana ya Hana kowa zuwa kusa da ita,shege Ashe be kulla gaskia ba,dariya ya dan yi sannan yace Allah ka shirya mana zuriaar mu, Doc Bashir kuwa cike da bacin rai da tsantsan tsanar Nameer ya dawo office in shi,Alhamdulillah ya samu yayi wa yaron wayo,Amman ba shakka sai ya muzanta Nameer a cikin asibitin nan yanda ya tozar ta shi sai ya Rama wlhyy, shegen yaro karami da shi sai kwarjinin bala'i,yanzu ya zama dole ya canza takun shi, domin yi wa Nadeeya alurai yanzu ma ya fara, (ni ko nace ba shakka ba ka samu be hada ka da hukuma ba,ai kace komai ma), ************** Haka nan rayuwa ta cigaba da tafiya ba karamin taka tsan doc Bashir ke yi around Nameer ba,domin nuna mishi yayi eh fa da gasken gasken ya shiryu sannan ya canja,domin tun Randa abun ya faru ya bude wa doc Nameer kofa kan ze iya zuwa ganin Nadeeya duk sanda yake so,and ya nuna mishi ya daina bata injections in nan,he is even researching irin treatment in da zai yi curing in ta gaba daya, Randa doc Nameer ya ga condition in Nadeeya sai da ta kusa mata kuka,shi sam ya ras why yake daukan damuwar yarinyar nan too personal ne,he wish da yana daa hali da ya warkar da ita, abun ya mata yawa ga hauka,ga rashin magana da rashin motsa jiki tana nan kwance kamar kayan wanki,sam shi be taba ganin irin case in Nadeeya ba,domin banda ido babu abunda take iya motsawa a jikin ta, Nadeeya Na cikin halin da dole mutum ya tausaya mata,bata hmmm bare uhmm uhmm,saidai tayi ta bin mutum da idanu, at least in haukan ne kawai ai da sauki kana tafiya kana maganar ka,amman a halin da take ciki sai an daga sai an kwantar, banda hawaye ba abunda ke fita a idanun ta kullum kallo daya za ka mata ka gane she is in deep pain, SEN gurin ta yake wuni in be da abun yi yayi ta kuka yana mata addu'ar samun sauki ke nan,in abun nashi kuma ya motsa ya gasa doc Bashir da zagi kan shi ya jefa yar shi cikin halin da take ciki,saida Alhaji Salis ya dage masa da nasihar karban kaddara kafin aka samu salama, ************ Doc bashir Around Magrib yana kokarin hada kan komatsan shi ya je hotel in da suka yi da Kareematu za su hadu ya ji an shigo cikin office in nashi kai tsaye ba tare da neman izini ba,(Allah ka tsare mu da aikata zina domin shi zina kama rai Gare shi daga zaran ka fara to wlhy bari wahala yake maka,duk tsiyan da Kareematu tai wa Bashir ba shi ya Hana shi bin ga ya saukar da kai ba domin he is already addicted to her), Dagowa yayi tare da zuba wa kofar ido domin ganin waye ne haka, cike da takun isa da takagama ya shigo cikin office in, Da kallo doc Bashir ke bin shi yana kokarin so ya tuna a ina ya San face in nan, shade in idanun shi ya zare sannan yace ya aka yi ne Doc found it difficult to recall me, Dan murmushi doc Bashir yayi sannan yace my god am so sorry Afzaal ko, Baki Afzaal ya tabe sannan yace yeah Ashe baka manta Wanda ya taimake ka daga hannun SEN ba, Dariya Bashir yayi tare da shafa kumatun shi don tuno Marin sen sannan yace have a seat mana ina zan na isa manta ka,shine ya dago ka cikin daran nan ai sa ya kira Na zo da kai Na gida, Baki Afzaal ya kuma tabewa sannan yace Mal Bashir ke nan dadi na da kai son duniya, a tunanin ka kudi Daddy ya bani in kawo maka ko, Da sauri Bashir yavr yeah in ba kudi ba miye zai kawo ka office ina cikin daran nan, Zama Afzaal yayi tare da daura daya kan daya sanna yace I come to talk business ko in ce Na zo a Rama wa kura aniyar ta ne, Zama shima Bashir in yayi sannan yace ban fahimci inda maganar taka ta dosa ba gaskia, Dan dariya Afzaal yayi sannan yace bara ka fahimta ba daman ai,like I say business Na zo muyi ni da kai, sannan am willing nayi maka biya me tsoka, from 10 mil har abunda ya kai 50 mil ni me iya biyan ka ne in har za kayi abun da zan sanya ka, Idanu Bashir ya zaro cike da rudewa ya ji kudi yace 50 mil fa,kai Afzaal wani aiki ne zan maka da za ka biya ni huge amount of money haka, Zama Afzaal ya gyara sannan yace relax mana ba wani aiki bane me wahala, in har ka yarda za ka yi yanzun nan zan tura maka 50 mil cikin account in ka, Da sauri Bashir yace fadi koma miye wlhy in har za ka bani wannan kudin ni ko zan iyaiya yi maka koma miye a take ma, Kanshi ya shafa sannan yace well aiki ne me sauki amman zaka iya kallon shi kamar me wuya, Afzaal in dai akan kudi ne nifa koma miye zan iya aikatawa kai dai fada mun kawai don Allah Na matsu Na ji karar credit alert, Tashi Afzal yayi tare da kallon cikin idanun doc Bashir yace so nake a yau ba sai gobe ba ka KASHE MUN MATATA NADEEYA AUDU WAZIRI, wani irin tsoro da jiri ne ya kama doc Bashir Wanda be ma san time in da ya mike ba,cike da rawar baki yace Afzaal kana da hankali kuwa Anya baka yi shaye shaye ba kafin ka shigo office ina, Tsaki Afzaal ya ja sannan yace kana iyawa ko baka iyawa Na nemi wani, Na shiga uku,wai kasan me kake fadi kuwa,kisan kai a hakan ma wai Matar ka Nadeeya audu waziri, wacece ita ma tukun Na, Dariya ya so bai wa Afzaal ganin irin rudewar da yayi, sai ya dake yace yeah ka ji ni sarai Nadeeyar dai da ka sani yar gidan SEN Audu Waziri ita nake nufi, matata ce kuma so nake a yau ka kawo karshen numfashin ta ni kuma Na cika maka banki da kudi, Shiru Bashir yayi yana me nazari shi kam be san a wani irin bala'i ya sanya kanshi ba,wani irin family ne haka me cike da dumbin secrets,for sure yasan Nadeeya matar aure ce Amman be dauka wannan bane mijin nata, shi sam be gane kan wanna family ba,at one hand uban ta mahaifi ke son a hauka Tata,and on the other hand wanna mutum da ke claiming mijin ta ke son a kashe ta,shi kam ya shiga uku, wannan samu baya fatan ya wuce shi, Amman in ya yarda ya ya kashe ta yace da Sen me,mil 50 ba karamin kudi bane shine abunda zuciyar shi ta raya mishi, What do u say are u in or baka so Na nemi wani,goshi Bashir ya dafe yana me nazarin ya zaiyi wannan shine tsaka me wuya, Cikin sanyin murya yace Amman Afzaal why keke so Na kashe ta,and baka tsoron SEN ya sani, Dalili kake so ko kuma mil 50 in ka,beside in har ka yarda za ka yi kar ka damu zan ji da komai, by the way mutuwar be fi mata sauki da irin rayuwar da take leaving yanzu ba ita da vegetable miye maraba, kawai ka kashe ta,ka ga taimakon ta ma za ka yi kayi easing pain inta, Zufa Bashir ya goge yana me Jin tsoro can kasan zuciyar shi while ta saman ran kuma na hango mishi rayuwar dadin da zai yi a kasar waje da yammatan shi turawa, Kayi shiru Bashir bani da time fa,kasan bature yace time is money za kayi ne ko aa, Yawu Bashir ya hadiye sannan yace tura mun kudin yanzu zan yi yaushe kake son a kashe ta, Dan ihun murna Afzal ya sanya sannan yace ko kaifa,gobe nake so a tashi da kukan mutuwar ta,sannan ina so ka sanya mutuwar tayi looking kamar normal mutuwa, kar ka bada kofar zargin mu,and no matter what ko ta fashe kar ka kuskura ka ambaci suna Na,ka dai gane da kai Bashir ya amsa shi deep down yana ji abunda zai yi be dace ba, but yana bukatar kudin nan daga baya ya tuba, A take Afzaal yayi mishi transfer in 55mil harda karin yin shiru in case in ta kwabe musu, tare da jaddada mishi kar ya sake a samu matsala, da haka suka rabu yana bashi tabbacin zai ji da komai a gurin SEN, Har ya zo kofa sannan ya tsaya cak, dan dariya yayi sannan yace ka ji ni da hauka main abunda ya kawo ni ban yi ba,farar takarda ya zaro sannan yace nasan tana ji duk da tana cikin hauka kace da ita ni mijin ta Afzaal Na sake ta saki uku ga takardar ta,in an je lahira a nemi wani mijin domin bara ta mutu mun da jigilar aure Na akan ta ba,da gama fadin haka ya yarda takardar tare da ficewa daga office in yana Jin shi free kamar ya rabu da kaya ne, Inda kasan anyi ruwa an dauke haka brain in docdoc Bashir da gangan jikin shi suka tsaya cak, shi kan shi bare iya misalta halin da yake ciki ba,tsoro ne aa miye ne nan take yaji cikin shi ta murda ya fada toilet in office in sai zawayi, yana yi yana tunanin taya zai fara kashe Nadeeya ta inda bara a gane shi bane, zuciyar shi ce ta raya mishi ya danna mata pillow kawai har sai ta daina numfashi shike nan ya fita y tafi wa ya sani, da wannan tunanin ya fito yana me Jin kwarin gwiwa, sai kace kan shi aka fara kisan kai, beside gaskiar Afzaal ne zai fi mata sauki da ta cigaba da irin rayuwar da take yi,haka ya yanke shawaran kashe wayar sa,don kar a Dame shi, zai jira zuwa cikin dare ya je ya danna mata pillow ya fito ya tafi abun shishi babu Wanda zai sani, A haka ya zauna shi shi kadai kamar maye yana tunano irin pacakar da zai yi da kudin shi, Los Angeles zai fara zuwa ya dan huta kafin ya biya Abu Dhabi shima ya dan wataya, Yana tunanen banzan shi har 12 na dare yayi, shi ba ga magriba ba balle isha, cikin sanda kamar munafuki ya isa dakin Nadeeyar,yana jin babu ko digon tsoro a ranshi, burin shishi ya cika aikin ko ya samu ya ci kudin shi lafiya, A kwance ya tarar da ita Wanda da alamu bacci take yi dariya ya sanya sannan yace Alhamdulillah ke ba magana kike ba balle kiyi ihu asiri na ya tonu Pillow in da take kwance akwai akai ya zare Gare tare da cewa am so sorry fa zan kashe ki ba tare da kin min komai ba tsohon mijin ki ne Afzaal ya sanya yace na ce miki ya sake ki ga ma takardar ki nan kin ga sai ki mutu peacefully ya kare tare da aje mata takardar,sannan ya daura pillow in kan fuskan ta, Forgive me if u can my dear, mil 55 ba karamin kudi bane yana kare hakan ya danna mata pillow in da karfi, inda Nadeeya dake bacci ta ji ta kasa numfashi ta hau mutsu mutsu,idanu ya zaro tare da dan sakin ihu tare da yarda pillow hannun sa sakamakon aluran da ya huda wuyan shi, a take ya zube a kasa sumamme...... A MUN AFUWA NA RASHIN POSTING DA BAN YI DA WURI BA, WWLHY WAYA KE BANI CIWON KAI TUN JIYA, INA MATUKAR GODIA DA KAUNAR DA KUKE YI MUN, ALLAH UBANGIJI YA KARBI IBADUN MU SANNAN YA NUNA MANA BAYAN SALLAH DA RAI DA LAFIYA, INA ME BARAN ADDUA A GUN KU, ALLAH YA BIYA MUN BUKATU NA NA ALKHAIRI SANNAN AKWAI MAHAIFIYAR AMINIYATA DA TA RASU GABANIN AZUMIN NAN KU TAIMAKA KU SANYA TAA CIKIN ADDU'OIN KU, AKWAI MAHAIFIN KAWATA KUMA DAYA DAGA CIKIN GROUP MEMBERS INA RASUWA SHEKARAN JIYA SHIMA KU SANYA SHI A ADDU'A, ALLAH YAYI RAHMA YA KUMA JI KAN DUK WANDA SUKA RIGA MU GIDAN GASKIA,IN NA MU YA ZO YA SANYA MU CIKA DA IMANI, INA YI WA KOWA FATAN ALKHAIRI, ALLAH KUMA YA SA YANDA ZA'A DAUKI AZUMI DA MU MUNA MASU RAI DA LAFIYA YA SANYA A GAMA DA MU HAKA, UBANGIJI YA BIYA WA KOWA BUKATUN SU NA ALKHAIRI, SAI KUMA BAYAN SALLAH IN ME KOWA ME KOMAI YA BAR MU A RAYE, ALLAH YA BAMU IKON AIKATA AIKIN ALKHAIRI A CIKIN WANNAN KWANA 30 IN. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ........ My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh don Allah kiyi zaman ki ba sai kin shigo ba,haka zalika maza should stay away from my group domin Na mata ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ........... Page nineteen *********** A razane doc Nameer ya dago domin sam be yi expecting ganin wani a wannan lokacin ba,caraf suka hada idanu da Doc Bashir, Bura uba kai daman kai ne uban me ka aje a dakin nan da za ka zo dauka cikin daran Nan,ya kare yana nufo in da Nameer in ke tsaye, Shiru doc Nameer yayi ba tare da ya kula shi ba domin gaba daya tunanin shi ya tsaya ne da kwalban dake rike a hannun shi, Kwalan rigan shi Bashir ya cukumo,cike da bacin rai ya hau sababi,wato kai sam baka Jin magana ko,sau dubu nawa zan fada maka kayi staying away from Nadeeya ni ke handling case inta,Amman sam kunnan ka Na kashi ne,sabida ka maida mutane yan iska shine kake biyo wa dare kake shigowa dakin ta uban me kake mata,mara da'a mara tarbiya shege Wanda be da tausayi a cikin ranshi, Irin kune mugayen doctors da ke taking advantage in patient kuke lalata da su a cikin dare in kowa ya tafi to Allah yau ya toni asiri ka Dan uban ka,kila kai ka jefa ta cikin wannan halin da take ciki aka zo za. a daura komai a kaina, ya kare har bakin shi Na kumfa, Tasss Doc Nameer ya dauke doc bashir da mari, da mugun mamaki doc bashir ya dago ya kasa yarda wannan yaron ne ya mare shi, Bakin shi har rawa yake gurin fadin kai ni ka mara,cike da tsantsan bacin rai doc Nameer yace an mare ka ko za ka Rama ne bismillah, Tsoro ne ya kama doc bashir ganin inda idanun doc Nameer suka kada suka yi ja daga ganin kasan ran shi a matukar bace yake, Cikin zafin rai yace sake mun Riga ko na yanke maka hannu yanzun nan wlhy kuma Na yanka banza babu abunda aka isa a mun, Cikin sauri doc bashir ya cika mishi kwalan rigan domin sam be ga alamun wasa a tattare da doc Nameer in ba,daga haka Nameer be kuma cewa komai ba ya sanya kai tare da ficewa daga cikin dakin zuciyar shi Na tafarfasa bisa irin mugayen kalaman da Bashir ya jefe shi da su, Shi ko Bashir mamaki ne ya kama shi da kuma Jin haushin kan shi,akan wani dalili zai sake shi ya tafi,be san ya aka yi ba sai ya ga yaron yayi mashi wani irin kwarjini,toh uban me ya zo nema a dakin Nadeeyan a taya ma ya san pin code in shiga dakin,Kareematu shine abun da zuciyar shi ta sanar masa, shegiya kila ita ta sanar mishi tunda ita ke ta rawan kafa a kan shi, ai ko daga shi har ita sai ya ci uban su gobe, Tsaki ya ja tare da shafa kumatun shi,ji yake kamar ya danna wa Nadeeya pillow bare daga ba har sai ta daina numfashi ko ya samu ya huta daga azabar Marukan da yake karba,ace da girman shi da matsayin shi ana dauke shi da maruka haka bini bini, and daga shigowar wannan shegiyar rayuwar shi ne fuskan shi ya zamo available haka kowani Dan iska mara yake,ace wai har Nameer nawa yake da zai kwashe shi da Mari,toh in har dai a cikin asibitin nan yake aiki da yardar Allah sai ya hada mishi abunda zaman garin Bauchi ma sai ta gagare shi,tsaki yayi tare da Galla wa Nadeeya da ke kwance harara sannan ya fice daga dakin yana auna musu zagi a cikin ranshi, *************Doc Nameer Isowan shi gida ke nan ko parking me kyau be tsaya yi ba,ya fice daga motar tare da fadawa cikin daki, Jallabiyar jikin shi kawai ya tube tare da shige wa cikin bandagi,domin yanda yake Jin zuciyar shi Na tafasa hakan nan in ba ruwan sanyi ya watsa a jikin nashi ba bare samu sauki ba, Ya dauki Dan tsahon lokaci yana sheka wa kan shi ruwan sanyi wai ko zuciyar shi za ta Dan yi sanyi,Nameer mutum ne me saukin kai da sanyin hali Amman sam baya daukan wulakanci da kuma kazafi, Saida ya dan ji dama dama sannan ya fito daga bandakin waist in shi daure da towel,kan gado ya fada tare da lumshe idanun shi maganganun Bashir Na dawo mishi cikin ka, Daga jin tausayi ko in ce daga taimako shine zai na jefan shi da irin wannan mugayen kalaman,Allah Na tuba ni har akwai macen da za ta burge ni nayi taking advantage in ta ne,beside in da iskanci yake so ga mata nan birjit a gari,a cikin asibitin ma matan da ke kawo musu kan su sun fi guda nawa,ya Na ki,sai ace ya rasa Wanda zai lalata sai Nadeeya Wanda ke kwance bata ma san inda kanta yake ba, A rayuwa babu abun da ya tsana kuma yake tsoran sa kamar zina,domin ya san bashi ce,in har ya bata yar wani to dole a bata mishi angel in shi tunda ai ya haifa,bare sanya kanshi cikin layin maza da basu da bukatan mace a tare da su ba ya sanya tun rasuwar Raa'isah ya lazumci yin azumin nafila da sallan dare domin kare kanshi daga fadawa halaka, Hakika nin gaskia ba karamin sosuwa ranshi yayi ba yau,and yayi Alkwari daga Rana me kamar ta yau babu shi babu Nadeeya,ba zai Kara zuwa inda take ba balle har wani banza can ya kuma zagin uban shi da ya Dade da kwanta dama, Nameer irin mutanan nan ne masu takatsan tsan da gudun shiga damuwa,saisa abu kadan in har ya same shi to sai ya zamo ya dame shi kuma,wannan daran gaba daya cikin bacin rai yayi shi,yayi danasanin zuwa ganin ta ma in the first place da be je ba ai da duk hakan be faru ba,ganin bacci yana kokarin gagaran shi ne ya sanya shi mikewa tare da dauro alola ya shiga yin sallah,ba shi ya samu ya rintsa ba saida ya gabatar da sallan asuba bayan ya gama Azkar in shi nan kan sallayan bacci ya dauke shi, Karar alarm in shi ne ya farkar da shi,in da ya mike ya shiga wanka,cike da nutsuwa ya shirya cikin blue trouser and black t shirt Wanda ba karamin amsan shi yayi ba, Combing in gashin shi yayi tare da feshe jikin shi da turaruka masu sanyin kamshi sannan ya fito, coffee ya hada tare da warming in sandwich in da ya aje a cikin fridge shi ya ci as breakfast in shi sannan ya hada all necessary abubuwan da yake bukata tare da fitowa don tafiya asibiti, Saida ya zo bakin motar sannan ya tuna Ashe a cikin aljihun wandon shi Na jiya ya bar car key in,dan goshin shi ya dafe sannan ya koma cikin gidan, wandon ya dauka tare da sa hannu a cikin aljihun har ya dauko key in Sai kuma ya ji kwalban da ya sanya jiya,dauka yayi tare da aje wandon ya fito ya shige motar shi,shi ba ya manta ma da kwalban ba,wani Abu ke ce masa ya yarda shi ina ruwan shi tunda yace yanzu kam babu shi babu Nadeeya so ba bukatar ya je yana confronting in doc Bashir, saidai wani zuciyar ta shi ta ki yarda da ya yarda in,a haka ya sanya cikin aljihun shi tare da nufar asibitin yana Jin he is ready koma miye Bashir zai yi masa, Cikin sanyin jiki ya ke gudanar da aikin shi,haka kawai sai yake ji kamar in ya ce ya rabu da ita be yi mata adalci ba sabida babu abunda tayi mishi ai,beside he is curious ya san me ke damun ta ya ji Bashir yana cewa wai shi ya jefa ta cikin halin da take ciki,shi dai ya san lafiya lau suka rabu da ita shekaran jiya,ji yake kamar ya je dakin nata ya duba halin da take ciki Amman kuma sai ya Hana kanshi,dole ya yakice tunanin yarinyar,to akan me ma zai na sanya ta a ranshi, a ina ya santa da har yake jin anya matakin da ya dauka Na nisan ta kanshi da ita shine daidai, Wata nurse ce ta shigo office in nashi tare da sanar da shi ya je doc Bashir Na son ganin shi, Dan guntun tsaki ya ja sannan ya mike daman ya san za a yi haka,shi dai he is not ready for all this dramas in,but be da zabi da ya wuce ya je gurin Bashir in suyi ta ta kare, Cike da takun shi na nutsuwa ya nufi office in doc Bashir in,saida yayi knocking yace ya shigo sannan ya shiga bakin shi dauke da sallama,a zaune ya tarar da doctor Bashir ya daura daya kan daya fuskan shi sanya da wata bakar glass kamar wani boss irin baya cike da nonsense in nan lol, A nutse Nameer ya ja kujera tare da zama yana wasa da ring in finger in shi, Cike da kallon tsana ya dago ya kare wa Nameer kallo yana ji kamar ya shake shi ,amman ba daman yin hakan, Cike da isa da izza yace waye ya baka izinin zama,dagowa Nameer yayi tare da nuna kanshi cike da izgilan ci yace wai ni ya kare yana nuna kanshi, Ran Bashir ne ya baci ganin wani rainin wayo da Nameer ke shirin masa,aa da aljanin ka nake yi, Dan dariya Nameer yayi sannan yace doc Bashir ke nan,wai duk tsannan nan Na miye ne,and da kake maganar kujera in ba mu zauna a kai ba su za su zauna akan kan su ne, Mike wa Bashir yayi cike da bacin rai ya cire glass in sannan yace wlhy ban taba ganin Dan rainin wayo irin ka ba,ko ban fada maka ba kasan kai me laifi ne,maimakon ka bani hakuri Na rufa maka asiri shine kake mun iskanci son ranka, Tashi Nameer yayi shima cike da bacin rai yace kai Bashir daka ta mun ba wai don fa ka gani a hospital in ku muna aiki guri daya kayi kokarin ci mun fuska ba,baka San ni waye ba wlhy da ko kudi aka baka ka tsaya a gaba Na kayi mun ihu bara ka samo ba balle harda zagi Na, Sannan kasan in har nace zan kai ka court akan furucin da ka mun jiya sai an daure ka sabida kayi mun kazafi, kace ina neman Nadeeya da lalata tunda muke ka taba kama mu,beside jiya da ka shigo ko finger in ta ka ga Na rike ne, Katse shi Bashir yayi da cewa duk wannan abun da kake yi borin kunya ne wlhy ga ka dai a fuska kamar mutumin kirki,Amman Ashe ba haka bane, in har ba lalata kake yi da ita ba miye zai shigo da ita dakin ta karfe 11 Na dare me kake nema,ban sanar da kai kayi staying away from her ba,amman kaki,sabida akwai boyayyan nufi a ranka to wlhy ni babu ruwana zan Kira hukuma yanzu Na shigar da karar ka gudun abunda zai je ya zo ah toh babu ruwan uban yarinyar ba yarda zai yi ba muddum wani abu ya same ta, Dariya Nameer ya sanya tare da tafa hannuwa sannan yace Wow Bashir just wow don Allah ka kira su yanzu ma nima zan fi son ka kira su din ka ga Na sanar da su miye empty kwalban CHLORPHENIRAMINE ke yi a dakin Nadeeya, Idanu Bashir ya zaro tare da goge zuban da ke goshin shi,call them mana Na ga ni da kai case in waye xa a fara shigar wa Na ga ko uban yarinyar da ni da kai wa zai fi Jin haushi, Ni da kai dukkan mu doctors ne and am very sure ka San aluran miye kwalban shi ke dakin Nadeeya, Yawu Bashir ya hadiye sannan yace a yaushe ne ka ga kwalban, and da kake cewa haka kana da sheda ne, Dariya Nameer ya kuma sannan ya fiddo da kwalban daga aljihun shi Ni bana nufin kowa da sharri sannan bana magana ba tare da hujja ba,kasan in har nayi presenting wannan kwalban to taka ta kare,domin am very sure a prison za ka kare rayuwar ka,and am very sure sai an kwace lasisin ka in ba a yi wasa ba harta asibitin nan sai an kulle, Don nasan ko ban fada ma ba aluran CHLORPHENIRAMINE bashi ya dace ana yi wa mara lafiya irin Nadeeya ba,shi alura ne da ake wa lafiyayyar mutum in ana son ya kamu da deep depression Wanda zai yi leading to haukan shi, In har na can ka daidai aluran da kuke yi wa Nadeeya ke nan Wanda take complain yana mata zafi Na sanar maka kace I should stay away from her kai ke handling case inta, Baiwar Allah Ashe lafiyar ta lau kai ne mugu Wanda wasu mugayen suka hada baki da shi ake son cutar da ita wlhy ka ji kunya Bashir, a hakan in an taba ka kace malamin jinya me kula da marasa lafiya kai, Ka fada mun in har da irin ku taya daman duniyar mu za ta cigaba, akan kudin da be taka Kara ya karya ba kake neman salwantar da Rayuwar yarinya in har yar ka aka yi wa haka fa,sam zuciyar ka ba imani, don baka da kunya har ka tsare ni kana fada mun maganganun banza,toh wlhy baran fada maka this should be the first and last time da za ka shiga harka ta if not I will fuck you up wlhy,sai na kashe ka Na cinye namanka tas ba tare da uban kowa ya sani ba,sannan ni baran iya zama in zuba ido ana zaluntar baiwar Allah ba,ya zama dole Na shigar da Kara ko Na nemi mahaifin ta in sanar da shi komai da ke faruwa,am done talking to u am taking my leave, ya kare tare da barin office in yana Jin sanyi cikin ranshi, daman aka ce in har kasan Na fada toh baka san Na mayar wa ba, Na shiga uku na lalace shine abunda Doc bashir yace tare da safe kai, garin Yaya yaron nan ya gano aluran da yake bai wa Nadeeya, abunda ya sanya ya hana kowa zuwa kusa da ita ke nan,shi da ya shirya sirfa mishi buhun wulakanci in ta kama ya masa dukan tsiya shine rashe ta juya da mujiya, in har ya kai maganar nan gaba ya shiga uku,domin babu Wanda zai yarda SEN ne ya sanya shi ya haukatar da yar cikin shi,babu Wanda zai ma yarda da maganar don hankali ma ba dauka zai yi ba,wat if yaron nan ya fada wa yan sanda da gaske a prison zan kare rayuwa ta,nan take ya ji wata irin zazzabi ya sauko masa,abunda fa ya shigar da shi dakin Nadeeyar ke nan fa jiya don ganin ya mance kwalbar aluran haduwar shi da Nameer shi ya mantar da shi abunda ya shigo yi,ashe shegen yaro dauka yayi, yayi danasanin tsanan yaron da yayi tun farko ma, Zaga office in shi ya hau yi yana Jin zuciyar shi kamar zai fito tsaban tsoro, kalman Na shiga uku kawai yake maimaitawa,ganin tsayuwa ba inda za ta kai shi ne ya sanya shi fitowa daga office in shi ya nufo office in Nameer in har yana kusan faduwa tsaban sauri, A zaune ya tarar da au shi da doc Habeeb suna ta dariya da alamun hira suke yi, ganin yanda ya fada musu a fujajan ne ya sanya su mikewa suna tambayan doc Bashir lafiya?? Haushi ne ya kama Bashir in ganin harda Nameer yake tambayan wai yana lafiya, ji wani tambayan rainin hankali, Amman sai ya matse tare da gyara tsayuwar shi yace lafiya klau doc Nameer na dan gan ka mana don Allah, jin hakan ne ya sanya doc Habeeb excusing kan shi tare da ficewa ya bar musu office in..... Yooooo Saura 1 page to go in sha Allah Ina godia da kaunar ku a Gare ni ubangiji ya bar zumunci, Sai kuma gobe in sha Allah Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin San ba sharhi bane zai Shigo dake to don Allah na hutar ki Kar kiyi joining,haka zalika Maza stay far away from my group domin na Mata ne xallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 .......... Page twenty-two *********** Saida ya fito harabar gidan ne Jin an ki tsayawa da bugun kofar ya Sanya gaban Shi faduwa,Kar dai an gano Shi ya dauko Nadeeya,ji yake kamar Kar ya ma Bude kofar coz Allah ya gani be shirya wani drama da safiyar Allahn nan ba, Aro jarumta yayi tare da nufan gate in yace Waye,Jin muryan Habeeb ne ya amsa da cewa Bude Mr handsome ni ne,ya Sanya shi sakin ajiyar zuciya,tare da Bude kofar, Da kallo Habeeb ya bishi sannan yace dan wulakanci sai yanzu Ka ga daman Bude mun ke nan tun dazu nake tsaye, Tsaki Nameer ya ja sannan yace bara Ka gane ba wlhy bacci ne ya dauke me,ko wanka fa ban yi ba, Kallon Shi Habeeb yayi cike da kulawa sannan yace are u sure lfy kake kuwa doc, Murmushi Nameer yayi sannan yace yeah gajiya ce kawai,by the way lafiya na gan Ka da sassafiyar nan, Wlhy mafarkin Ka nayi wai wani mummunan Abu ya faru da kai har ta Kai Ka ga jinya ya sanya hankali na ya kasa kwanciya,ina yin sadaka nace sai dai na zo na ga lafiyar Ka, Murmushi Nameer yayi yace Kai Habeeb shine Ka fito sassafen nan,AI mafarki ba gaskia bane Banda abunka, Wlhy Nameer I was so scared ne na kasa samun peace of mind Saida na zo na gan Ka you are safe and sound Alhamdulilah toh,matsa mun na shiga na sha ruwa na Jira kayi wankan mu wuce hospital, Har Nameer na kokarin matsawa sai ya tuno akwai Nadeeya a cikin gidan fa,da sauri yace AI kayi tafiyar Ka kawai babu ruwa a gidan nan, Da kallon tuhuma Habeeb ke bin Shi da Shi sannan yace wani irin ba ruwa,yau lafiyar Ka kuwa to matsa na fasa shan ruwan mu shiga Ka samu Ka shirya mu wuce Kar muyi late, Kai doctor Nameer ya sosa sannan yace kawai Ka je abun Ka zan biyo bayan Ka akwai abunda nake son na gama tukun na, Mamaki ne ya kama doc Habeeb da Jin abunda abokin nashi yace,ganin Nameer in na kokarin komawa cikin ne ya sanya Shi ce what are you hiding ne, Me,me zan boye kawai dai I don't want to waste your time ne just go I will soon meet you a asibitin,thank you so much for the concern bye bye,da haka ya rufe kofar abun Shi,tare da sauke ajiyar zuciya ya koma cikin gidan, Da Ido Bude Habeeb ke bin kofar gate in,anya lafiyar Nameer kuwa,kafadu ya dage tare da shige wa motar Shi tare da fadin koma miye ne in tayi tsami za mu ji, Toilet Kai tsaye ya fada a gurguje yayi wanka tare da shiryawa cikin kananun Kaya Wanda suka amshi jikin Shi,Saida ya gyara gashin kanshi ya feshe jikin Shi da designers in turaruka masu dadin kamshi, sannan ya fito ya shiga Kitchen,da sauri ya hada tea tare da saisatawa inda bare Kona wa mutum Baki ba,sannan ya fito da ya koma dakin da Nadeeya ke kwance, Hamdala yayi ganin idanun ta a Bude suke,alamun ta tashi daga baccin ke nan, Murmushi ya Mata sannan yace morning my naughty naughty girl,an tashi ke nan oya time for breakfast,ya kare tare da Aje tray in da cup in ke Kai a bedside table in dakin,har ya zauna ya mike Dan dariya yayi sannan yace sorry my bad Ashe ba ayi brush ba Zan Baki abinci,daga haka ya shige toilet in Shi,Sabon toothbrush ya dauko tare da matsa toothpaste a jiki sannan ya dauko bowl da soft towel ya fito, Cike da tausayin ta ya dago ta Saidai sam jikin nata is not responding kamar wata vegetable,a haka dai da dabara da komai ya samu ya dan jingina ta a jikin Shi tare da support in jikin Shi da na pillow in da ya jingina Mata ya Fara wanke Mata baki a nutse a kuma hankali yanda bare ji Mata ciwo ba, Towel in ya manna Mata a wuya sabida inda ruwan ke zuba daga bakin nata,while yayi using dayan gurin tsomawa a ruwa ya goge Mata ciki da wajen bakin,tunda ba iya zubo da ruwan za ta yi ba, A haka dai ya samu suka Gama brush in sannan ya maida ta kwance ya mike tare da xubda ruwan,ya kuma Ibo sabo, A nan kwance ya samu ya daura Mata alula,duk da ya san ba iya sallahn za tayi ba,sanna ya zauna ya shiga bata tea in a hankali da karamin spoon,inda ta shiga sha Sosai hakan ya tabbatar mishi da yunwa a jikin ta, Saida ya ga ta koshi sannan ya goge Mata baki tare da maida ta kwance, Sannan ya shiga tattare wajen,Yana tunanin ya zai yi ba zai yu ya Kula da Nadeeya ita kadai ba, domin ba muharammar sa bace,dole tana bukatan wanka in tayi fitsari a gyara ta Wanda Shi kuma ba zai iya Mata ba,ya Zama dole ya samu Wanda za ta taya Shi Kula da ita Amman kafin nan Bari ya samu ya tafi hospital don yau kam ya Gama yin latti,da haka yayi Maza Maza ya gama shiryawa tare da Kara duba Nadeeyar Yana Jin kamar Kar ya tafi ya bar,ta Kar ta bukaci wani abun ba kowa Kusan ta, duk sai ya ji wani iri, **********Doc Bashir Kanshi ya rike da yake ji Yana barazanar fice masa sakamakon farkawar firgicin da yayi,a hankali ya shiga Bude idanun Shi da suke masa dishi dishi,da kyar ya Bude su tare da rike kanshi da hannu biyu Yana kokarin tuna me ya faru da Shi, In har zai tuna dai ya Shigo cikin dakin nan domin kashe Nadeeya don har pillow ya dauka ya daura a fuskan ta Saidai daga time in be tuna komai ba ya dai ji sharp pain a wuyan Shi Wanda ya Sanya Shi sakin pillow in, Idanu ya zaro sosai tare da saurin mikewa tsaye Nadeeya shine kalman da ya Fadi a tsorace kafin ya shiga bin dakin da kallo, Tsoro ne ya kama Shi ganin babu Nadeeya babu alamun ta,Na shiga uku ni Basheer Nadeeya ya kwala mata Kira Yana sa ran Jin ta amsa๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚, Tsoro be Gama kama Shi ba Saida ya leka ko ina ya ga dai babu ita babu alamun ta,AI wani irin jiri ne ya dibe Shi a take ya zube a kasa don Ji yake kafafuwan Shi sam sun gaza daukan Shi, Da hannu biyu ya kama Kai tare da kwala wani irin Ihu Fadi yake na shiga uku na lalace shike nan yau karshe na ya zo ina kike Nadeeya kuka yake hawaye biyu biyu Yana sumbatu, Jin ihun Shi ne ya sanya sauran staff's in saurin shigowa,ganin Shi a durkushe ya Sanya doctor Jameel nufan Shi tare da dafa Shi Yana tambayan lafiya doctor, Da sauri ya dago idanun Shi jige da hawaye hanci duk majina,ya samu ya mike da kyar Yana Jin jiri,Amman gwamma jirin nan da abunda zai fuskanta a gurin Sen, Cikin muryan kuka yace Jameel Waye ya Shigo dakin nan ya dauki Nadeeya, Cike da mamaki suke kallon sa,kamar ya waya Shigo ya dauki Nadeeya Waye ma Nadeeya doc Haneefa tace tana hararan Shi, Yarinyar Sen Rilwanu da na killace a cikin dakin nan babu ita Waye ya dauke ta cikin Ku, Tsaki Haneefar tayi sannan tace Ka ji mun maganar banza Kai ma kace Wanda Ka killece ni tunda nake ban taba ganin fuskan yarinyar ba Ka nanike ta a daki kullum ko waje bata fitowa Shan iska,beside duk asibitin nan daga Kai dai Kareematu na ga ke shiga cikin gurin ta,domin na ga harda pin in munafurci a kofar dakin nata,toh idan ma dauke ta aka yi saidai in ko Kai ko Kareematu ya Ku yaku kuka yi abun Ku za ka zo kana wani ihu da kuka kana neman daga mana hankali,ta kare tana hararan sa, Ke kika tsaya Kula Shi Haneefa,Shi daman haka yake Baya son Zaman lafiya da uban wa yace Ka boye ta daki Ka Hana kowa ganin ta,tunda Ka ga uban ta na da zagi da maiko nan kace da mu kowa yayi staying away from her Kai za Ka yi handling case in ta so yanzu am very sure wannan in ma you can handle it,Mr handler ,doc jabir ya kare yana Dariyan shakiyan ci, Haba Ku kuwa Ku Bari mana,abun nan fa duk ya shafe mu kun Riga kun San Waye uban ta wlhy batan yarinyar nan baraxana ne ga mu gaba daya, Allah sauwaka Jameel wa dai Shi wlhy be shafe ni ba,tunda tunda aka kawo ta daga Shi sai Kareematu ke shiga gurin ta bara a daura mun gawan da ba ni na kashe ba,in za su bazama neman ta ma gwara sun fara,kafin uban ta ya samu labari,in kana iya taya Shi toh Allah ya bada lada,ni dai Ka ga fita na ina da abun yi AI daman Kuda gurin kwadayi yake mutuwa,daga haka ta Sanya Kai za ta fice Jira ni Haneefa mu hada hanya domin ban ga amfanin Zama na a nan ba, A nan kasa Bashir ya kwanta Yana kuka kamar karamin yaro,sai yanzu ya ga wautan Shi da be barin kowa ya rabi Nadeeya daga Shi sai Kareematu gashi yanzu babu Wanda ya Isa yayi blaming,wa ma ya Isa ya daura wa laifi bayan duk haushin shi suke ji gani suke ya kannenade komai ya Hana kowa dangwalan arziki a jikin Sen, Ka kwantar da hankalin Ka Bashir in sha Allah za a same ta mu samu mu je gurin securities ko sun ga wani Abu, Cikin shesheka yace haba Jameel a taya kake tunanin hankali na zai kwanta wlhy yanzu haka ban jin zan iya mike wa don Allah taimake ni Ka daura mun drip ko zan dan samu sauki, Ba musu kuwa Jameel in ya ja Shi zuwa gadon Nadeeyan ya kwantar da Shi tare da daura masa ruwan, Idanu ya lumshe zuciyar Shi na tsanan ta bugawa domin ya san tabbas Sen ya ji maganar nan ya mutu ya lalace,wata zuciyar ce ta rayo masa what of Afzaal in ya ji Nadeeya ta bata bayan Ka karbi makudan kudadan Shi don kashe ta me zaka ce masa, AI sai ya fashe da kuka me karfi,na shiga uku na lalace wayyo ni,ya Fadi Yana daura hannu a Kai, Haba Bashir miye haka sai kace yaro karami behave yourself mana,wlhy Jameel bara Ka taba gane halin da nake ciki ba don Allah cire drip in nan Ka rike ni mu je gurin securities in nan yarinyar nan ta bata wlhy asiri na ya tonu,ya kare Yana kokarin mikewa, AA Ka dai yi hakuri ruwan ya Gama shiga jikin Ka tukun na,zai taimaka maka sosai, Jameel Ka cire mun ko ni na cire Shi da kai na,amfanin me zai mun bayan na San ni mutuwa ta ta Kusa,ya kare Yana hawaye ba karya ya san tabbas in ba a ga yarinyar nan ba toh Sen sai ya kashe Shi, Ba musu kuwa Jameel ya cire masa drip in,inda ya bashi daman tashi Yana Jin jiri da komai Amman haka ya daure suka fitowa,kallo daya za Ka masa Ka gane Yana cikin tashin hankali domin lokaci daya har ya fada, Gurin securities in suka je tambayan duniya ya musu Amman sun ce sam su Basu ga wani bakon mota ya fita da kowa ba,ba yanda Bashir be yi ba Amman be samu komai ba karshe kuka ya Sanya tare da rufe su da duka Yana zagin su wai Basu iya aiki ba,da kyar Jameel ya ja Shi suka koma cikin asibitin, Haka dai kafin kace me labari ya karade cikin asibiti an nemi yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri an Rasa ta,duban duniya sun yi cikin clinic in ga Amman sama da kasa an rasa Nadeeya,Banda kuka babu abunda Doc Bashir ke yi,sam ya Rasa gane garin yaya yarinyar nan ta bata,ita da ba tashi take ba balle ace guduwa tayi,dole shigowa aka yi aka dauke ta to Waye,a iya sannin Shi dai daga Shi sai Kareematu ne suka san pin in shiga dakin nata,toh Waye haka yake neman jawo mishi mutuwa, Ana haka doctor Nameer ya iso asibitin,ganin inda duk aka yi carko carko ya Sanya Shi tambayan Habeeb lafiya kuwa, Wlhy Nameer Bari kawai yarinyar isolated room in nan ne aka neme ta aka Rasa, subhanallahi Kar dai Nadeeya yar gidan Sen, Wlhy Nameer ita fa,an wayi gari an rasa ta, subhanallahi toh tana ina, Waya sani dazu dai da na Shigo na ji Bashir na cewa wai an Rasa ta ,toh kasan ance fadan da babu ruwan Ka dadin kallo gare shi daman can ya Hana kowa zuwa gurin ta to Ka ga Wanda ya Ibo da zafi bakin Shi sai yayi aikin neman ta,kowa madallah yake masa, Ikon Allah toh wai taya za a ce babu ita ta bata,kuma har securities an tamabya ,wlhy dazu ma da zagi suka rabu da su wai su Basu ga komai ba, Murmushi Nameer yayi sannan yace Abu Sam be yi dadi ba gaskia toh ubangiji ya bayyana ta Bari na je gurin Bashir in, Ameen fa AI da kyar Ka gane Kan Shi domin sai Suma yake Yana farfadowa tun dazu,shege Ashe dai mara kunyar karya ne Yana tsoron zuwa prison,dariya Nameer yayi sannan yace Kai dai Baka da dama wlhy ni dai Bari na je in na dawo zan same Ka a office in Ka,da haka ya wuce office in Doc Bashir zuciyar Shi fes babu Wanda ya ganshi yana fita da ita jiya Ashe..... Ayi mun afuwa na jina shiru jiya hakan ya faru ne sabida dalili๐Ÿ™๐Ÿป, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi na gode sosai da kulawan Ku gare ni. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANE KO KISHIYA TA๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ย  ย  ย  ย  Assalam ย  ย  ย  ย  ย ย  Masoyan ย  ย  ย  ย  ย  ย  ย ย  Asaliโค๐Ÿ’– Before i begin to say anything, before wani ya riga ni, i want to be d first to wish beautiful pure souls like all of u guys, Ina so in fara da gode wa Ubangijin mu, mahallicin mu da ya bamu aran tsahon rai da lafiya har muka shiga wannan wata me tarin dumbin falala lfy, cikin aminci da yardar sa lfy, kuma ya nuna mana fitan sa lfy, wannan ba karamin arziki bane, duk da cewa Azumin Ramadanan bana ya zo ta daban kasancewar tsadar rayuwa da zafin da aka yi ta fama da Shi, amman duk da haka Alhamdulilah za muce, da har Allah ya nuna mana ranar Karamar Sallah, What a happy year har yanzu muna rayeย  Alhamdulilah, Allah muna kara mika godia a gare ka da ka kara ba mu aron rai har muka yi Azumin watan Ramadanan muna masu koshin lfy, kuma muka ga fitan ta lfy, ya Allah ba dan mu ba muna rokon ka ka karbi ibadun mu na gari, ka yafe mana kurakuran mu, ka sanya muna daga cikin yantatatatun bayi da aka yanta cikin watan, Gaskia I have to admit it that I have missed u guys a lot, in nace a lot i really mean irin sosai in nan fah, kamar yanda nima nasan kun yi missing ina together with Nameer &Nadeeyah ๐Ÿ˜‹ right, but maganar gaskia wa kuka fi missing Ni ce koh Su Nameer amman gaskia ya kama ta ya zama ni(lol) Kar na cika ku da surutu, ya kuke masoyana, ya ibada, ya aiyuka, ya rayuwa kwana da yawa, one whole month ba mu ji juna ba, Allah i missed u fah ji nai kamar nai kuka ๐Ÿ˜ฅ๐Ÿ˜ฅ๐Ÿ˜ฅ, But Alhamdulilah i am back, and ina fatan duk kuna cikin koshin lfy, Happy Eid Al Fitir, To All my lovelies i love u guys, ubangiji ya sa mun yi karbabbiya sannan ya Kara mana lafiya da nisan kwana,Wanda suka Riga mu gidan gaskia ya gafarta musu,ya Sanya sun huta in namu ya zo ya kyautata karshen mu, Thanks a lot for ur support guys, i really do appriete it, and I love each one of u with pure one heart, โคโคโค๐Ÿ’–๐Ÿ’– ....... https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba comment bane zai Shigo da ke to don Allah Kar ma ki Shigo na gode,haka zalika Maza should stay away from my group don ki sun shiga Zan cire mutun, group in Mata ne xallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su contact me via: 08100046388 ............ Page twenty-one *********** Faduwar da doctor Bashir yayi ne ya bayyana Nameer dake tsaye a bayan Shi da sirinjin alura a hannun Shi, Wani irin kallo me cike da tsana yake bin doc Bashir da Shi,ya kasa yarda wai Shi Bashir ya so fooling,so all those tears da rokon duk pretence ne, wow Dan Adam me wuyan gane hali,Banda son zuciya har akwai amount in da za a biya Ka Ka dauki ran dan Adam da shi ko kunya babu a cikin idanun sa,yo in ya kashe Nadeeya ya je gaban Allah aka taimabe Shi me tayi mishi ya dau ranta miye ne amsan da zai bada,tunda a iya sannin Shi bata taba cutar sa ba,ko ta taba ba Shi ya bashi daman daukan ran ta ba, Har yanzu he is still shocked da maganganun da ya ji a suka yi dazu a office in Shi,kallon Nadeeyah yayi da ke kwance,wani irin tausayin ta ne ya kama Shi Wanda be san time in da tears suka zubo mishi ba, Wato daxu Allah ne ya aiko Shi office in Doc Bashir ya je domin yi mishi magana game da case in Nadeeya,kamar zai shiga sai ya ji magana abunda be taba ba evesdrop ya tsinci Kan Shi da labewa ya ji me suke Fadi,ashe taimako ke Kiran Shi, In sha Allah yau ce ranar karshen wahalar ki zan taimake ki daga hannun wayan nan mugayen Wanda babu Allah ko kadan a cikin ran su, Tsalleke Doc Bashir yayi da yake yashe magashiyan a kasa,Wanda garin haka har yatsun Shi ya murje,saidai sabida aluran baccin da yayi mishi ya Sanya be ji zafin ba, Gaban gadon ya je tare da tsungunawa ya zuba Mata idanu, bacci take hankalin ta kwance,sai ya ji ta kuma bashi tausayi, Cikin soft voice yace I don't know if wat am about to do is the right thing ko aa,I just don't know what to think or who to trust kuma,how on earth your own husband is willing to pay huge amount of money don kawai a kashe ki, You got an innocent face dake nuna bara ki iya hurting ko da ant ba balle Dan mutun,saidai I don't know why ake neman rayuwar ki, I don't know why Nadeeyah ji nake kawai ya zame mun dole na taimake ki, although ban san komai game da ke ba,but ba zan iya barin a cutar da ke ba,ya kare yana girgiza Kai, tare da mikewa, Astaghafurillah yayi a cikin ranshi domin he is about to carry her,he got no option Banda ya dauke ta daga wannan asibitin kafin mugayen nan su kashe ta, Daukan ta yayi cak kamar baby bayan ya cire Mata chains in hannun ta,farin takartar sakin ta ya dauka tare da sanyawa a aljihun Shi sannan suka fito daga cikin dakin Yana me jin kamar ya rufe doc Bashir da mugun duka, Allah ya rufa mishi asiri dare ne so ba mutane a haraban asibitin,addua yayi ta yi har ya Isa motar da,a bayan mota ya shimfida ta sannan ya shiga ya ja sai gida, ********Sister Kareematu Tsaki kam ta ja Shi ya Kai cikin kwando ta cika tayi tsam kamar ta fashe tsaban bakin ciki,ji take kamar ta kashe doc Bashir dan wahala tun dazu take ta Kiran Shi yaki dauka,ya Sanya ta ta shiryo ta zo hostel Amman yaki zuwa, Kusan hours in ta biyu,wayar ma tun tana Kira tana samu har ya daina shiga, Tsaki ta kuma ja a bayyane sannan tace wannan akwai dan iska daman ya san be zuwa ya Sanya ni Shaye shayen magun gunan Mata to wai nayi yaya, Mikewa tayi tana me hararan kofar dakin duk mostin da ta ji dauka take Shi be,wlhy Bashir ya cika Dan rainin wayo,don ya ga ma ina Kula Shi ne ya sanya yake mun Bura uban da ya ga dama, Tsaki ta kuma ja tare da daukan jakan ta domin babu amfanin ta cigaba da Zama a cikin dakin ita kadai, Fitowa tayi tana tafe tana kare wa Bashir zagi tare da alkwarin sai ta ci uban Shi muddum yayi Mata magana gobe, Key in ta watsa musu suna tambayan madam lafiya,ko kallon su bata yi ba ta fito burin ta kawai ta nemi Wanda zai dan rage Mata zafi muddum ta kwana haka toh za a samu matsala,toh wa ma za ta samu,duk abokan shashancin nata ta sanar musu yau tana gida throughout Kar wanda ya Kira ta,domin haka Bashir ya sanya ta cewa yayi yau akwai till down Shi da ita(wa'iyazubillah) Tafiya take tana hade hanya a harabar hotel in Allah Allah take ta Isa motar ta,bata da option da ya wuce ta koma gida gurin Abdul,buguwar da tayi ne ya sanya ta yin Baya zata fadi da sauri Alhaji Muhammad Jidda ya taro ta, Jin ta a kirjin mutun ya Sanya ta Bude Ido cike da tsiwa,saidai arba da tayi da fari kal in mutun tsaye a kanta ya sanya ta shan Jinin jikin ta,wato ba karamin kwarjini yayi Mata ba wanda ya sanya ta saurin zare idanu daga kallon Shi, Na gode ta samu ta Fadi da kyar domin daga kallo daya wannan magidan cin ya saye zuciyar ya kuma tafi da imanin ta, Dariya ya Dan yi Wanda ya bayyana farar hakorin makkan da ke manne a bakin Shi,sannan yace haba babu komai ai yarinya me kyau, Jin abunda ya Fadi ne ya sanya ta Kara wani gyara tsayuwa tare da murmusawa tace Allah Alhaji Shima dariyar yayi tare da shafa tumbin Shi Wanda ke nuna kudi sun zauna sannan yace kwarai kuwa ya aka yi ne Yan mata muna shigowa kina fita, Da sauri tace AA daman mantuwa nayi zani daukowa a mota ba tafiya xan yi ba, Dadi ya ji a ranshi ganin cikin sauki ya samu kan yar banza,toh ya za mu je ne ki taya ni hiran dare ya kare yana kashe Mata Ido daya, Da sauri tace ai girman ka ne Alhaji mu je kawai na ma fasa dauko abun,tayi gaba tana me juya zaunannan mazaunan ta,murna fal cikin ta wannan Shi Ake Kira farin dare,daga ganin kyakkyawan alhajin nan me kama da larabawa (dake shuwa ne),naira gare Shi,irin su kuma ba sanin zafin kudin suka yi ba,da haka suka shige ya karbi makullin daki ta bi bayan Shi zuciyar ta fal za ta cafki Yan kudade ta mance da Amanar auran da ke Kan ta Wanda za ta ci ta mance uwa ce ita akwai Amanar Yara Akan ta,ta mance kimar ta na ya mace idanun ta sun rufe,bata son mutun ba bata san daga ina yake ba miye intentions in shi ta mika kai buri ya hau, (Ubangiji Ka tsare mana Imani mutunci da lafiyar mu,Allah Ka Raba mu da son abun duniya ya Allah Ka kare mu daga San zuciya,masu hali irin na Kareematu Allah ubangiji ya shirya Ku in masu shiryuwa ne Ku), **********Doc Nameer A hankali ya dauko ta bayan yayi parking har lokacin bacci take yi,Kai tsaye dakin baccin sa ya wuce da ita tare da shimfide ta akan gado, Zama yayi tare da zuba Mata idanu,Yana me tunanin da be je ya ji me su Bashir ke shirya wa ba fa,kila da iyanzu wani zancen Ake daban, Tabbas be taba ganin mugun mutun me son abun duniya irin Bashir ba,kana likita a hada Baki da Kai a yi kokarin kisan Kai, Shi kuma Afzaal sam brain in Shi ya kasa yarda wai Shi mijin Nadeeya ne,wai daman tana da aure,toh me tayi mishi da zafi da zai biya don a kashe ta, Wai shin ma ina Mahaifiyar ta take,and a yanda ya ji mahaifin ta na kaunan ta Yana ina har sirikin Shi ke son kashe mishi yarinya, Kwata kwata brain in Shi ya kulle ya kasa sanin amsoshin tambayoyin da yake da su game da ita, Ganin tunanin be da amfani ya Sanya Shi Mike wa,sai kuma zuciyar Shi ta tambaye Shi,wait Nameer da Ka dauko ta Ka kawo ta gidan ka wat about her family, Numfashi ya sauke,maganar gaskia Shi be san wanda zai yarda da Shi kuma,haka kawai ya ke Jin yarinyar tana cikin danger,and haka kawai yake jin bazai iya yarda da kowa ba kuma, Wat of her Father zuciyar Shi ta kuma tambayan Shi, actually har Shi ban yarda da shi ba for Allah knows why,domin ya Dade Yana tunanan nan akan Shi,why be tsaya kai da fata gurin samun lafiyar Nadeeyar ba,beside tun Randa ya ga injections in da Bashir ke Dura wa Nadeeya jikin Shi yayi sanyi game da lamuran Sen,toh daman can da lafiyar ta ya Sanya aka kawo ta gidan mahaukata,ko kuwa ta Dan yi haukan kadan shine Bashir ke dada birkita Mata brain, wannan duk tambayoyin ke ringing a head in Shi, Tsaki ya ja tare da dafe goshi,har ga Allah be san ko daidai yayi ko laifi ba da ya dauke ta daga hospital in nan,shi dai kawai ya bi shawarar zuciyar Shi ne,domin tunda ya ji su Bashir na Shirin kashe ta ya kasa zaune balle tsaye,karshe ya yanke shawarar yi wa Bashir aluran bacci ya dauke ita Nadeeyar, Wat if wani ya gan ka shine wani tambayan da zuciyar ta Shi ta masa,Nameer kasan aka gane kama Ka za ayi da laifin kidnapping,tunda daukan ta kayi ba tare da yardar ta ba, Mikewa yayi tare da sauke ajiyar zuciya ya san tabbas haka ne toh Amman Shi a ganin Shi taimakon ta yayi,ganin in ya zauna tunani ne kawai zai cika masa kai ya Sanya Shi juyawa don shiga toilet ya watsa ruwa ko ya ji sanyi a jikin Shi da zuciyar sa, Jallabiya ya dauka tare da quranin Shi da laptop in Shi ya ja Mata bargo bayan ya rage Mata sanyin AC in dakin sannan ya fito tare da rufe kofar,a palor ya Aje kayan tare da fadawa dayan dakin nan yayi wanka ya shirya sannan ya zo ya tada nafila,ya Dade Yana adduo'i ,kafin ya shafa ya shiga karatun Alqurani me girma,Saida ya ji ya fara jin bacci sannan ya aje ya kwana,a nan Kan kujera, Bacci yayi hankalin sa kwance babu wani tsoro ko fargaba a ranshi,ji yake Yana daidai da kowa a cikin asibitin like he is ready wa koma miye zai faru,abunda ya sani dai shine be bayar da Nadeeya har sai Allah yayi ta warke, Ba Shi ya farka ba sai asuba,Saida ya leka ya ga tana lafiya sannan yayi alola ya tada sallah,a nan kan sallayan ya maida bacci kafin alarm in Shi ta tada Shi, Around 7:00 ya ji ana buga masa kofa Wanda karar bugun ne ya farkar da Shi da sallati a bakin Shi,ya mike yana me karanto adduar tashi daga bacci,wayar Shi ya dauka tare da ganin time, Ya salam Ashe bacci Nayi sosai,time ya tafi,be ma yi wanka ba break balle Shirin zuwa aiki,Jin ana cigaba da buga gate in ne ya sanya Shi mikewa Yana me mamakin Waye haka zai zo mishi gida da sassafiyar Allah..... Ayi mun afuwa na so ya fi haka wlhy Allah be yi ba๐Ÿฅน, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi da kuma fatan ayi shagalin sallah lafiya. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ........ My group link https://chat.whatsapp.com/JYJvskgTzZICC4ksRfiMlK In har kin san ba sharhi da karanta book ina ne zai Shigo da ke ba toh don Allah yi Zaman ki ba sai kin yi joining ba,haka zalika Maza stay away from my group domin wannan group na Mata ne xallah ko Ka shiga Zan hidda ka๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 .......... Page twenty- three ************ A kwance ya samu doc Bashir ana yi mashi Karin ruwa kallo daya zaka masa ya Baka tausayi,inda ya kuma duhu har Ramar dole yayi na lokaci daya,doc Jameel ke gefan Shi Yana me bashi Baki Kan ya dau komai a sannu za a gan ta in sha Allah domin daga fargawar Shi zuwa yanzu ya Suma ya Kai sau 8๐Ÿคฃ๐ŸคฃNi ko nace madallah AI daman kwadayi aka ce mabudin wahala, Da sallama doc Nameer ya Shigo inda doc Jameel ya amsa sallaman tare da Mika mishi hannu Yana fadin doc sai yanzu, Hannun shima ya Mika suka yi musabaha sannan yace wlhy fa doc yau makara nayi,Ayya ai daman jiki da jini dole wataran a gaji, hope kana lfy, Kujera ya ja ya zauna sannan yace Alhamdulilah wlhy ya aikin, Alhamdulilah fa,toh madallah, Da kallon tsana ya bi doc Bashir ganin yanda ya ficiccike daga jiya da dare zuwa yau sai abun ya so bashi dariya,Amman sai ya daure yace, Doc Bashir Ashe abunda ya faru ke nan,wlhy yanzu shigowa ta nake Jin wannan munannan labarin garin yaya haka ta faru, Da kyar ya iya Bude idanu ya kalli Nameer in sai ya yi shaar da Shi,nan take tausayin kanshi ya kama Shi sai kwalla ya kuma kallan doc Jameel ya ga sai danna waya yake abun Shi,kuka ce ta kwufce masa,yayi danasanin Sanya kanshi a matsala kila da be bi son zuciya ba da shima Yana rayuwar Shi cikin Jin dadi da annashuwa,yanzu da wani yare zai sanar da Sen Kan cewa an sace yarinyar sa,ai ba ma zai kama zancan ba, Doc kayi shiru yana maka magana,Jameel yace Yana mikewa, Ajiyar zuciya me nauyi ya sauke sannan yace wlhy Nameer ni Kai na ban san garin ya haka ta faru ba,abunda Zan iya tunawa dai na shiga in duba ta ci abinci ko as da daddare sannan na bata maganin dare ganin Kareematu bata nan,shine wani makiyin Annabin Wanda babu Allah a zuciyar Shi ya soka mun alura suka dauke ta, Subhanallahi toh garin ya su Waye su Ka san su ko Ka ga yawan su,a garin ya ma suka shiga dakin na ga da pin a jiki, Wani zufa ne ya kuma karyo mashi domin tabbas babu Wanda zai yarda ba Shi ya sace Nadeeya ba tunda duk asibitin babu Wanda ya san pin in sai Shi kadai da Kareematu,ita kuma throughout jiya bata nan,ya Zama dole Shi za a tuhuma,na shiga uku shine abunda yace tare da matso kwalla, Nameer dariya ce fal cikin Shi, farinciki kamar ya mutu,ba karamin dadin ganin Bashir a cikin tashin hankali yayi ba,AI daman duk wanda ya hau motar kwadayi tashan wulakanci yake sauka, Cikin sanyin murya yace wlhy Doc Bani na sace yarinyar nan ba, Goshi Nameer ya shafa sannan yace in har mu mun yarda da Kai doctor mahaifin ta da sauran alumma fa,kasan ko kwana dubu za Ka yi kana fada wa duniya Baka da hannu batan yarinyar nan babu me yarda domin wannan magana ce ma da hankali ba zai dauka ba,yarinyar nan hannun Ka take hasalima babu Wanda kake Bari ya zo ko kusa da ita,daga Kai sai Kareematu ke Kula da ita,to kuwa Ka ga duk wani alamomin zargi suna Kan Ka ne da ita,don haka Ka kara tunani da kyau, Kuka Bashir yake yi hawaye biyu biyu Yana matukar tausayin kanshi,wallahi tallahi doc Ku yarda da ni na rantse ban san komai game da batan yarinyar nan ba,na san ni kadai da Kareematu muka san pin in shiga dakin ta Amman wlhy ni babu inda na dauke ta na Kai ta,kila aljanu ne suka sace ta tunda yarinyar ma ba iya motsi take da jikin ta ba,tunda na ji an ce aljanu na iya dauke mutane๐Ÿ˜‚๐Ÿ˜‚, Dariya ne ya so kama doc Nameer Jin furucin Bashir,tabbas ya yarda doc Bashir na da matukar tsoro,Amman madallahn sa ai tunda junin Shi son zuciya da duniya ne, Hmmm ni duk ba ma haka na,Ka dai san bare yu yarinyar Sen ta bata baida masaniya ko,ko Ka sanar masa ne, Da sauri Bashir ya mike cike da kidima yace don girman Allah na roge Ka Nameer Kar Wanda ya sanar da mahaifin yarinyar nan,na rantse da girman Allah wlhy kashe ni zai yi har lahira, AA Doc wannan Sam ba shawara me kyau bane,ya za a yi yar sa a nema a rasa bayan ya damka Amanar ta a hannun Ka sannan ace Kar a Bari ya sani,AI hakan be yi ba ko da dabbar gidan Shi kake kiwo ya bace dole ya sani balle Dan mutun,don haka Ka kwantar da hankalin ka a sanar masa kila ya san inda take tunda yana da connection,don haka ina so Ka Bani no sa in Kira in sanar masa halin da Ake ciki, Aa Nameer Ka duba girman Allah da soyayyar da kake wa mahaifan Ka,Kar ka Kira Sen wlhy baka san Waye shi na rantse da Allah ba karamin so yake wa Nadeeya ba,in har ya ji babu ita toh wlhy rayuwa ta ta zo karshe, Dariya Nameer yayi sanann yace Ka san da haka kake kokarin kashe ta a cikin ranshi while a fili kuma cewa yayi duk dai boye boyen nan babu inda zai Kai ka,abune ya riga da ya faru ba za mu iya canzawa ba,sannan Shirun amfanin me zai yi ba gwara a sanar masa ba let him do his worst in har za a same ta,AI lafiyar ta da halin da take ciki yanzu ne abun dubawa,so be a man babu abunda ya Isa ya maka abunda Allah be ma ba,so Ka kwantar da hankalin ka ka bani no in sa, Aa Nameer don girman Allah Ka bari mu gani zuwa gobe in ba a ganta ba a sanar mashi wlhy tallahi Baka san Sen ba na rantse da Allah bare taba raga mun ba ya kare yana kuka, Doc ke nan kana ganin za a same ta ne,Nadeeya fa bata cikin asibitin nan don da tana nan da an ganta tun tun,Ka dai Bari a sanar in, Na roke ka Nameer Ka rufa mun asiri don kaunar Ka da Manzon Allah,zan shiga in fita in sha Allah za a samo ta,akwai wani malami da ke kan tudu naji Yana bada taimako Zan je ya bincika mun inda yarinyar nan take, Nameer can't hold it Saida yayi dariya,kafin ya rike bakin Shi,sannan ya mike yace toh shike nan as you wish baran sanar masa ba Allah ya Baka lafiya, ubangiji kuma ya sa a ganta din,da ameen Doc Bashir ya amsa Shi tare da cewa Jameel ya cire masa drip in nan don Allah ya samu ya mike ya tafi gurin malamin, *************Sen Rilwanu Kwance yake kan tafkeken gadon Shi yana baccin Rana,domin ba karamin gajiya ce a jikin Shi kasancewar jiya ya dawo daga kasar waje, Knocking in da Ake tayi ne ya sanya Shi jan tsaki tare da mikewa ran Shi bacci wani dan iskan ke son katse mishi baccin ranar sa, Rai a bace ya Bude kofar Saa'eed ya gani fuskan Shi cike da tashin hankali, Kai Dan uban Ka ban ce da Kai Kar uban da ya tashe ni ba,ina son yin bacci ya kare tare da wanke fuskan Shi da Mari, Kumatu ya dafe sannan ya zube a kasa tare da cewa ranka ya Dade kayi hakuri hankali na ne a tashe ya sanya na kasa hakuri Saida na tashe Ka, Harara ya maka masa sannan yace uban miye ya daga maka hankali beside ina ruwana da tashin hankalin naka,don Rashin kunya za Ka daga ni bacci wai kana cikin tashin hankali tashin hankali uwar me ya kare cike da Ihu, Kayi hakuri yallabe, yanzu ne na ga wani posting Yana ta yawo wai an nemi karamar hajiya an Rasa, Da mamaki Sen ke kallon Sa"eed kafin yace kamar ya wacece wata karamar hajiya (domin sam hankalin Shi be bashi wai akan Nadeeya Ake magana ba), Shiru Sa"eed yayi Yana me jin tsoron sanar mishi ganin be gane me yake nufi ba, Ba magana nake maka ba Dan uban Ka kayi mun shiru ya kare a harzuke kamar zai rufe Shi da duka, Cikin sanyin murya yace Sen daman yanzu na gani Yana ta yawo wai an nemi Princess Nadeeya Sama da kasa an Rasa a cikin asibitin mahaukata,AI da Jin wannan zance wani irin jiri ne ya Debi Sen yayi baya yuuuuu,a tsorace Saa"eed ya mike yana yallabe kafin ya Kai ga taro Shi ina har ya kai kasa sai karan faduwar wa Tiiim kake ji........ Kuyi hakuri da ji na shiru jiya wlhy mara lafiya gare ni ina jinya,Ku Sanya ta cikin adduo'in Ku don Allah, Na san na yau babu yawa ayi mun uzuri in sha Allah na samu dama Zan Kara page daya zuwa dare in kuma ban samu ba a yi mun afuwa sai zuwa Monday in sha Allah, Na gode sosai da kulawa da kaunar Ku gare ni Allah saka wa kowa da khairan, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜” UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ..... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh Don Allah kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba,Maza should stay away from my group domin wannan group in Mata ne zallah ๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ............ Page twenty- four ************ A matukar rude Saa'eed yayi Kan Sen Yana kuka yana yallabai Ka tashi don Allah domin Shi dauka ma yayi zuciyar sa ce ta buga ya mutu, Daman ya sani muddum Sen ya samu labarin nan toh zuciyar Shi bara ta iya dauka ba ya Sanya yake ta Jin tsoron sanar masa tun daga lokacin da ya ga abun na trending a social media(kun Riga kun san zamanin da muke ciki yanzu kafin ki Isa gidan ki ma in kika yi wanni abun sai ki ga ya watsu duniya,wani kamar jiran Ka ake wannin baka ma sanin an dauka Yana da kyau mu kasance masu aikata alkhairi sannan masu guje wa riya.da kuma sabon Allah domin wannan social media in saidai godiar Allah kawai,Allah yafe mana sannan ya cigaba da rufa mana asiri duniya da lahira), Ganin Sen Baya mosti ne ya sanya Shi a tsorace ya dauko waya Yana kuka ya shiga kiran layin Alh Kabeeru, Kira biyu kuwa ya dauka,cikin rudewa Saa"eed yace yallabai akwai matsala,Sen ne tun dazu ya Fadi na yayyafa mishi ruwa har yanzu be motsa ba ina tsoron ko dai mutuwa yayi, A zabure Kabiru ya mike tare da fadin what Saa"eed Ka ko san me kake Fadi kuwa miya samu Sen in,ko da yake ba lokacin bayani bane yanzu gani tahowa daga haka ya kashe wayan, A hanzarce ya mike tare da zira babbar rigan shi sannan ya dauko makullin motar Shi,tsaban rudewa mancewa yayi ma wai Yana da wani driver, Kai tsaye gidan family doctor in Shi ya nufa lucky him ya same Shi Yana nan a gida so da sauri ya ce da Shi ya fito su tafi,grabbing kayan aikin Shi yayi a box sannan ya fito ba bata time suka nufo gidan Sen, A daki suka same Shi kwance be numfashi Saa"eed da sauran workers in gidan na tsaye bisa kanshi sai kuka suke suna ya tashi, Tsawa Kabiru ya daka musu sannan yace kowa ya fice daga dakin ya koma bakin aikin Shi while Saa"eed ya Jira Shi a parlor,sim sim haka kowa ya fice, Doc bismillah check on him ko Yana Raye, Da haka Doc ya shiga baiwa Sen taimakon gaggawa inda ya tabbatar wa Kabiru da Yana raye dogon Suma ce kawai yayi sabida wata yar firgici da ya samu,kuma muddum hakan ta cigaba da faruwa watarana kumbura zuciyar Shi za ta yi ta fashe Allah ya kyauta,Saida ya ga Doc ya dawo da daidaituwar numfashin Aminin nashi sannan ya fito domin ganawa da Saa"eed ya ji menene ya razana Shi har ta Kai Shi ga suma, A tsaye ya tarar da Saa"eed yayi tagumi daga gani Yana cikin damuwa, Kujera ya nema ya zauna sannan yace ya Ka Saa"eed da sauri ya nufe Shi tare da zubewa a kasa nan gurin kafafun Shi,domin ya san halin Alh Kabiru Sarai da saurin fushi da kuma saurin hannu, Miye ke faruwa da Amini na har ya haifar mishi da firgici har ta Kai Shi ga suma, Cikin sanyin murya yace yallabai daman yau ne a Facebook na ga news in nan na ta trending wai an nemi Princess Nadeeya Sama da kasa an Rasa, What Kabiru ya ce tare da mike wa,kamar yaya wai an neme ta an Rasa toh tana ina,ina ma securities in hospital in suke,waye ma yake da gut in shiga cikin clinic in ya sace yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri ya kare cike da Ihu da fada,Shi dai Saa"eed kasa yayi da kanshi be ce da Shi komai ba don be ma san me zai ce in ba, **********Doc Bashir A razane ya dago idanun Shi da suke masa nauyi tsaban kuka ya zuba su a kan Doc Jameel, Cikin sanyin murya yace don girman Allah kace da ni karya kake,hmm wlhy Doc Bashir ba karya nake ma ka ba duk wani kafofin sadarwa da Ka sani labarin da ke ta trending ke nan na bace war yar gidan Sen da ke cikin asibitin mu, Wani irin jiri ne ya kuma kama doc Bashir Yana nan a kwance,Shi tsaf ya ma mance wlhy a modern world muke yanzu duk abun da ke faruwa mutum ko a Ina yake Yana iya sani,thanks to social networking,ya tara mutane yayi musu kashedin Kar Wanda ya fitar da zancen nan shine aka samu wani mugun mara tsoron Allahn ya yada a yanar gizo,Shi be taba sanin haka yayi bakin Jini cikin hospital in ga ba sai yau,ban da Jameel babu Wanda ya zo kanshi duba halin da yake ciki,thank god ma Allah ya taimake Shi suna yi da Jameel in domin duk asibitin babu wanda yake daga wa kafa ko ya Bari Ka ci albarkacin Shi bayan Kareematu da Yan matan da yake latsewa,Sam sam bashi da good muamalat da mutanan asibitin(Tabbas iya Zama da mutane ma rahma ne,duk rintsi yar uwa ki zama me good muamalat da mutanan da kike zaune da su,domin shedar duniya Shi ke bin mutum har kiyama,mutumin da ya iya Zama da mutane,sai Ka ga ko gurin Allah yana saukaka mishi alamuran Shi ga kyakkyawan sheda daga bakin alummah,saisa duk wuya duk rintsi yi kokari ki zauna da kowa zuciya daya da ki cuta gwara a cutar da ke, Allah Ka zaunar da mu da jama'ar Ka lafiya,ya kuma tsare mu daga cutar da ko da dabba ne balle Dan Adam), Shiru yayi kawai Yana me tausaya wa kan Shi yau tunda garin Allah ya Waye ya Bude idanun Shi yake haduwa da masifu, Suma da zawayi be san sau nawa yayi su ba,lokaci daya ya koma mara lafiyan karfi da yaji, yanzu haka ma cikin nashi ta murda zawayin yake kuma ji, Jameel kama ni mana ka raka ni toilet cikin ya kuma lalace mun, Tsaki Jameel ya ja cikin ranshi don ba karya Shi kam ya Fara gajiya da dawainiya da Bashir da yake yi,kafin ya zo ya kama Shi din ya raka Shi toilet in Yana me Galla masa harara, Fitowan Shi yayi daidai da shigowan Nameer,gaisawa suka yi sannan yayi wa Bashir ya jiki,amsawa yayi da kyar sannan Nameer in ya zauna Doc ka ko san an samu wani dan iskan da ya yada batan yarinyar nan a social media, Ya salam a garin ya Doc Jameel ai daman ilar wannan media in ke nan yanzu yanzu za a yi Abu sai Ka ga ya yadu,Allah dai ya sa mahaifin ta kar ya gani, Wani gani ai wlhy Nameer ina maka tabbacin Sen zai ga abun nan ko da shi be gani da kanshi ba dole wanda suke tare da Shi in har suka gani za su sanar masa, Wayyo ni Kan na shiga uku na lalace na mutu na lalace shike nan karshen rayuwa ta ya zo,wlhy Sen tsaf kashe ni zai yi tunowa da yayi da irin mugun warning in da suka mishi Randa za a bashi Nadeeya,Saida suka tabbatar mishi da ya Kula musu da yarinya Kar a ji Kar a gani,muddum wani Abu ya same ta toh wlhy bare ga da kyau ba, Sabida zalama da zarmewar zuciya irin nashi ba tare da dogon tunani ba ya ce ya yarda harda dauka musu alkawarin Kan Kar su ji komai zai bata cikkakcen kulan da take bukata,inda hakan ya zame masa opportunity hanyan samun kudin Shi,ya ringa tatsan kudade a gurin Sen kamar Wanda Allah ya aiko Shi,sannan Rana tsaka ace an wayi gari yarinya ta bata,ai wlhy Sen bare yarda da wannan labarin ba, Cikin muryan kuka yace na san any moment from now Sen is on his way ya zo hospital in nan,don Allah Ku taimake ni ku kama ni Ku kaini Airport na samu na gudu na bar kasan nan ni ko Burkina Faso ne na samu na fada kafin in kuran nan ta lafa na dawo, Haba me Doc Jameel da Nameer za suyi in Banda dariya,Saida suka Dara sannan Nameer yace haba dai Doc AI wlhy ko Ghana bara ka iya tafiya ana tsaka da tashin hankalin nan ba in Ka gudu ya ma nuna kan cewa kana da masaniya a batan nata ke nan,just be a man stay back strongly and face your fear,sai Ka ga komai ya zo maka cikin sauki amman tunanin guduwa duk be taso ba, Fada mishi dai Doc Nima tun safe abunda nake fada mishi ke nan mutum be Isa maka abunda Allahn Ka be maka ba,stop acting like a girl be a man dallah Ka kwantar da hankalin ka since sai Suma yake Yana farfado wa fa sai kace Wanda aka ce da Shi mala'ikan daukan ran sa ke tafe,beside Sen is not a bad person abun dai zai masa xafi coz zai ga kamar rashin Kula ne amamn bare yi komai ba am sure of that, Hmmm wlhy su bara su taba gane waye Sen Rilwanu Audu Waziri bane,Akan wannan yarinya tashi babu abunda ba zai iya aikata wa ba,a Karin banza ma ya dauke Shi da Mari balle ace masa ta bata,a wlhy yau kashin Shi ya bushe, Ganin duk sunyi shiru ne ya sanya Nameer mikewa tare da cewa am damn hungry thank god it's break time lemme go and grab something ko karyawa ban yi ba na fito,wanna go along ya tambayi Jameel, Aa doc just carry on kasan ni ke Kula da matsoracin nan,so I have to stay back ko Dan shi just enjoy yourself,da haka Nameer ya bar dakin zuciyar Shi fes domin babu wani break in da zai je Nadeeya yake son zuwa ya ga ya take ciki, Saida ya biya ta Saje ya Mata ice cream,sannan ya dauko hanyan gida Yana tunanin ta,tabbas wannan shayi da ice cream ba kosar da ita zai na yi ba,and a condition in da take ciki yanzu bara ta iya cin heavy food ba ba ma za ta iya tauna ba daga ganin alama,dole ya san abun yi,ya kama ta ma ya samo wacce za ta taya Shi kula da ita domin is not safe Yana barin ta ita kadai a gida Yana zuwa hospital,dole za ta bukaci taimako,da haka ya samu ya Isa gidan, **********Sen Rilwanu Audu Waziri Farfadowar Shi ke nan yayi daidai da karewar drip in da aka daura masa,cire masa doc in yayi tare da tambayan Shi hope babu abunda yake hi,kai ya daga mishi toh Masha Allah yallabai kana kokarin controlling temper naka domin gudun fadawa babban matsala,be ce da Shi komai ba sai kokarin mikewa da yake yi domin bayi da burin da ya wuce ya gan shi a specialist yanzu yanzu, Haba Kai kuwa Sen ya daga cire maka drip sai kokarin mikewa take it essay pls Kabiru yace da shigowar Shi ke nan, Essay I should take it essay fa kace Kabiru shin Ka san me ke ma faruwa kuwa,Nadeeya fa wai an neme ta an rasa Saa"eed ke sanar mun, Bari na sallami doc na zo muyi magana Kar a bar Shi a tsaye,mu je Doc AI ba wani damuwar ko, Eh komai lafiya Alhamdulilah na fada mishi Yana kokarin controlling temper in Shi sannan ya na Shan ruwa akai akai komai zai tafi daidai,toh mun gode I will transfer your money through your bank account,godiya yayi sannan ya fice daga gidan, Kamo hannun Shi Kabiru yayi tare da zaunar da Shi sannan yace aboki na pls try to relax lafiyar Ka na gaba da komai, Haba Kabiru wai wani relaxing kake son nayi Kai fa kasan wacece Nadeeya a guri na ba sai na sanar maka ba,and don iskanci da rainin wayo wai ace an neme ta an rasa yar tsana ce da za a ce ba a gan ta ba, Wlhy Nima tunda Saa"eed ya fada mun nake ta nanata maganar a Raina,kwata kwata na kasa yarda,toh ba a gan ta ba ta je ina, Shine Nima Kabiru yarinyar da tana kwance ko finger na ta bata iya lifting ina ta samu kafar da za ta gudu,toh ta gudu ta je ma ina, Babu guduwar da tayi yarinyar da hauka take ko Ka mance, Ban mance ba Kabiru ina sane na rantse da Allah yanzu ba sai anjima ba zani asibitin nan sai na tabbatar da na ci durun uwar Bashir da ni yake wasan,Kila saken da nake mishi ne ya sanya Shi zai mun Wasan banza,toh wlhy Zan iya daukan komai Amman Banda Nadeeya,muddum na je asibitin nan na samu babu yarinya ta toh wlhy Ka zamo sheda sai na kashe Dan iskan yaron nan da hannaye na,tashi mu tafi in kana zuwa domin sam ban ga amfanin Zama na a nan ba.... Don Allah ayi mun afuwa na jina shiru jiya wlhy sau biyu ina typing Yana goge wa๐Ÿ˜ญ,wannan ma da kyar na samu nayi, Sannan Bana dan jin dadi Ku Sanya ni cikin adduo'in Ku pls, Na gode sosai da kaunar Ku gare ni, ubangiji ya biya wa kowa bukatun su na Alkhairi, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi sai zuwa gobe in me kowa me komai ya Sanya mun Kai. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA Don Allah in har kin san ba reading and commenting in book ina bane zai kawo ki toh kiyi wa Allah Kar ki yi joining in group ina,haka zalika Maza pls should stay far away from my group domin na Mata ne zallah ko Ka shiga zan hiddo ka๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 .......... Page twenty- seven ********* Jin kalman tayi kamar saukar aradu a ka,hakan ya Sanya ta ja ta kame da matukar mamaki take juyowa,ganin rundunan Yan sanda tsaye kanta da uniforms fuska daure bakake munana da su babu alamun sassauci ko rahma a tare da su ya Sanya ta shan Jinin jikin ta,duk iskancin Kareematu akwai ta da tsoron hukuma, A hankali ta shiga waige waige wai so take ta ga da wa suke domin a iya sanin ta babu Wanda ta samu matsala da,lafiya Lau suka rabu da Alh Jidda babu abunda ta daukar masa balle ace ya zo karba, Haka zalika a hanyar ta bata samu rikici ko matsala da kowa ba in ba Abdul da suka Dan yi kace nace ba Shi kuma be Isa dauko mata yan sanda ba, Ganin ta tsaya Baki Bude ya sanya daya daga cikin su yace officer arrest her mana, A zabure ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada,bakin ta na rawa gurin fadin Arrest me ta kare tana nuna kanta,for what crime me nayi, Be kuma kallan ta ba yace in mun je can station kya ma ji koma miye kika yi, Mamaki ya Hana ta tabuka komai tana ji tana gani aka Sanya mata handcuffs tare da tusa keyan ta zuwa jerin motocin Yan sanda Wanda suka Ibo da yawa kamar Wanda aka zo kama Dan kinmashin๐Ÿคฃ, Tafiyar yan mintoci ne ya iso da su Yan doka road dake babu wani tazara daga asibiti zuwa gurin,kasancewar a nan babbar head quarters na Yan sandan duk Bauchi yake, Haka aka wangale katon gate in police command suka shige da motocin su sai kara yake,ita dai Kareematu kanta a matukar kulle yake domin sam bata gane komai ba,rabo aka ce da ita ana yi ta zo da sauri ta karbi share in ta daga ina duk wannan tashin hankalin ke fitowa,ita ce a cikin police command a hakan ma wai crime in da bata ma san da Shi ba, Jin tsayuwar motar ne ya bata daman gaining courage domin har ga Allah duk da ba Law tayi ba ta San right inta,domin ko banza tayi civic education a junior secondary school Inta, ba zai yu haka kawai ayi arresting inta without sanin me tayi ba, Bude ta ke da wuya ta ga an hangado keyar doc Bashir,wani irin yankewa gaban ta yayi take zuciyar ta ta bada rassss,bata san sanda kalman na shiga uku ya kwace daga bakin ta ba, Tsawa Dan sandan ya daga mata tare da cewa fito bakar munafuka AI you don't enter 3 sai bayan mun Gama azabtar da ke ma, Jiki a sukwane ta fito domin ta fara gano kwanan zancan duk tsiya ta san Bashir ne kila yayi wata Bura uban ta shi aka kama Shi yayi involving inta a ciki,AI ko bata ga abunda zai hana ta ci wa Bashir uwa ba idan ya Bari ta fito, Nan kasa aka yarda su domin Sen ya ja wa officer incharge in gurin Kan Kar ya kuskura ya raga wa doc Bashir ko Kareematu har sai sun fito mishi da yarinya,in ta kama yayi using ko wani irin azaba ne in har gaskia za ta fito daga bakin su,he don't bloody care ko da dayan su ko duka za su Rasa rayukan su,zai ji da wannan abunda ya sani kawai a fito mishi da Nadeeyar sa, Zaman mayafin ta gyara sannan ta juyo tare da watsa wa Bashir wani irin kallon tsana me cike da sakon Ka kyauta Bashir ni za Ka Sanya a matsala, Kasa yayi da idanun Shi domin sam bare iya juran kallon nan nata ba, Bashir ubaidullah shine cikakken sunan Ka ko,eh sir Doc Bashir ubaidullah haka sunan yake, Take polices in gurin suka sheke da dariya sanann daya yace ko ba Doc ba kai kana cikin wannan halin ai ko sunan uban naka kawai aka Kira amsawa zaka yi kayi godia ba wai Ka tsaya wa mutane iyayi ba, Ya Isa Dauda Kai dadi na da Kai yawan magana,sorry sir shine abunda yayi saurin cewa, Zama ogan Nasu me suna Jabiru ya gyara sannan yace are u ready to talk I mean kun shirya Ku sanar da ni gaskiar me ke faruwa cikin ruwan sanyi ko sai na fiddo gaskia ta karfin tsiya daga bakin Ku,ku kalle ni da kyau,wlhy Bani da mutunci I hate crime and criminals in har na ga me laifi toh hankali na be taba kwanciya har sai na san yanda aka yi nayi punishing in Shi,in such a way gobe ko kudin duniya za a bashi bare Kara aikata makamanciyar laifin ba ma, Hantar cikin Kareematu ne ya kada domin kallon fuskan Jabiru ma kawai abun tsoro ne balle yanda yake magana cike da iza Isa da kuma Ihu,ga uwa uba ita har yanzu ba sanin laifin da ta aika tayi ba, Cikin sanyin murya doc Bashir yace yallabai wlhy iya Kar gaskia ta na fada maka ni wlhy Bani na dauke ta ba, Na shiga uku Bashir wa aka dauke Ake zargin Kaine Ka dauke ta yaushe Ka fara dauke mutane ban sani ba, Kareematu ta kare a matukar rude domin case irin wannan da kyar mutum ke fita in ba Allah ya taimake Ka ba sai Ka gan Ka har court daga nan a zarce da Kai gidan gyaran Hali, Ke dallah ki rabu da ni in ji da daya ni a yaushe na sace Nadeeya through out jiya an neme ki an rasa kuma daga ni sai ke muke shiga gurin ta,yau kuma an wayi gari babu ita babu labarin ta toh ya Zama dole kina da masaniya Akan batan Nadeeya, A Kareematu bata san sanda ta mike tayi wata tsallan albarka tare da direwa kan Bashir, Kukan Kura ta Saka tare da danko wuyan rigan Shi,Bura uba Bashir ni Kareematu za Ka yi WA sharri na shiga uku na lalace yau ni na ga boni a yaushe na sace yarinya, Jijiga Shi take tana fadin haba ai daman buri yayi kama da mutu,Banda hauka irin ta wa ko yaushe Ka taba Sona da harkan karuwa harda Ibo jiki na zo, Ashe tsiya da sharri kake nema ta da Shi, Ubangiji ya Saka mun wlhy ban yafe ba,ke dallah cika ni AI maganar gaskia nake yi ko karya nayi Baki zuwa dakin nata,ko ba daga ni sai ke muke shiga ba, Ganin suna neman maida guri filin dambe domin yanda zuciyar Kareematu ke Saman nan anjima kadan za su iya kicimewa da dambe ya Sanya oga Jabiru daka musu wata tsawa, Nan kowa ya shiga hayyacin sa,Ku watsa mun su a cell sannan a kira me bada horo ya zo mun yi Baki,domin na ga alama suna da taurin Kai sai sunyi laushi tukun na,Yana gama fadin haka ya mike abun Shi, Hawaye ne tab idanun Kareematu Banda zagi babu abunda take aunawa Bashir domin sai yanzu take gane komai,wato Nadeeya aka Rasa shine yake kokarin maida komai kanta,abunda tayi ta gudu ke nan,tana ji tana gani aka cire su dan kunne zobe abun hannu hatta Dan kwalin ta da takalmi ba a bar ta da su ba sannan aka tasa keyar ta zuwa cell da tunda uwar ta ta haife ta bata taba shiga ba sai yau a sanadin Doc Bashir,Shi din ma cell in aka cilla sa sannan aka tafi kirawo me bada horo domin ya zo ya isar da umarnin oga, *********Sen Rilwanu Iya kan tashin hankali yau Sen Yana cikin shi,domin sam be dauka wai zai bar cikin hospital in nan ba tare da an gano in da yarinyar Shi take ba, Abun Ku da abun social media tuni labari ya watsu Kan an nemi Princess Nadeeya yar gidan Sen Sama da kasa an rasa,a take abokai da mutanan arziki suka shiga Kiran layin Sen da na Aminin Shi Kabiru domin Jin shin gaskia ne wannan labarin ko karya,ganin mutane na neman addaban rayuwar Shi da waya ya Sanya Shi kashe wayar tashi Baki daya,zai yi cifa da ita Kabiru ya amsa, Da kyar ya samu ya Sanya Shi cikin mota suka dawo gida domin lokaci daya ya ga wata zazzabi ne from no where ta kama Sen, A hanya ya Kira doc Akan ya dawo jikin ya motsa inda suka dawo suka samu ya Riga su isowa, Da taimakon Saa"eed aka riko Sen tare da Shigo da Shi part in Shi nan kan kujera a parlor aka kwantar Shi,alura doc yayi mishi sannan ya shiga Sanya masa drip da kyar ya Bari ma aka Gama Sanya masa din he was insisting a bar Shi shi fa lafiyar shi kalau,sabida tashin hankalin da ke kan Shi ya ci ace ya dan samu bacci domin harda aluran bacci aka mishi Amman sam ya Bude idanu tangararas, Da haka suka samu drip in ya kare Yana ta uban Mita,doc ya cire tare da mishi adduar samun sauki sannan ya yi ficewar Shi, Cikin hanzari Sen ya mike sannan yace Kabiru na shiga uku wasa wasa batan yarinyar nan Yana son Zama serious fa,wai ina Nadeeya ta ne ya kare kamar zararre, Sen don Allah Ka kwantar da hankalin Ka za a same ta ba dai an danka komai gurin Jabiru ba just trust him yaron yasan akin Shi, Are you talking about trust I should trust who Wanda Ka kawo, don't forget Kabiru kai Ka kawo mun Bashir kace I should trust him with my daughter na yarda nayi trusting and now kana ganin abunda ke faruwa, Can you stop blaming me for crying out loud na gani ba dole nayi maka ba akan sai kayi trusting Bashir kawo Shi nayi kace yayi maka kaima so ni miye nawa laifin a ciki,Yana kokarin bada amsa suka ji sallaman Alh Salis, Saida suka gaisa sannan ya shiga jajantawa Sen wai garin yaya ma haka ta faru daman babu tsaro ne a cikin asibitin, Sai da Sen ya sauke numfashi sannan ya shiga baiwa Abokin na Shi labarin da Doc Bashir in ya bashi sannan ya kare da sanar masa ya Sanya anyi arresting in su, Goshi Alh Salis ya dafe sannan yace oh Allah mun gode maka masifu dai haka nan daga wannan sai wannan,ko ina ma yarinyar take yanzu oho,ko tana cikin wani hali sai Allah ubangiji ya sa tana hannu na gari, Ka Bari dai Salis wlhy me hanani cin mutuncin likitocin nan sai Allah na rantse da girman Allah ko a dawo mun da yarinya ta ko kuma a ga babu dadi a cikin garin Bauchi nan, Da sauri Alh Kabiru ya tsayar da Shi domin ya San halin Aminin nashi muddum ran Shi ya Baci toh Baya iya sanin abunda yake fada ma,kafin ya je ya saki ba yayi Barin zance, Cikin kwantar masa da hankali yace duk komai zai wuce za a ganta Ka yarda da ni,Bari na Kira Shi na ji ya Ake ciki yanzu,da haka ya sanya waya tare da dannawa Jabiru Kira, Ringing biyu ya dauka,cike da ladabi ya gaida Shi sannan ya ke sanar masa tun dazu yake ta Kiran layin Sen Baya shiga,dan tsaki Kabiru ya ja sannan yace ya Ake ciki an ganta kuwa, Goshi Jabiru ya dafe sannan yace gaskia ranka ya Dade wannan suna da mugun taurin Kai har yanzu Basu ce komai ba na sanya a shiga a ladabtar da su dole sun suyi magana I promise you bara a kai zuwa gobe ba sai sun fada mana inda suka kai Nadeeya,ace wa Sen ya kwantar da hankalin Shi yar Shi kamar ta ma dawo gida ne,toh shike nan Ka turo mun da account details in Ka kar Ka mance da haka suka yi ending call in, A can cell kuwa kafin zuwa yamma kamannin Kareematu da Bashir ya soma canza wa sabida irin bugun da suke ci,domin Jabiru cewa yayi sam kar a nuna musu sassauci a yi musu dukan da har sai ta Sanya su sun Fadi gaskia, Kareematu tai kuka kamar ranta zai fita ta tsinewa Bashir ya fi kwando dubu,domin babu Abu mafi ciwo kamar a tuhume Ka da abunda Baka ma da masaniya a kanta,tayi nadaman zuwan ta, da ta sani for the first time in her life da ta ji maganar Abdul da Khairat inta kila da yanzu tana gida ta baje ta Sanya su yi Mata fifita,Amman sabida son zuciya Akan kudin da be taka kara ya karya ba ta jefa kanta a matsala,ita ba yi suke da makota ba balle tace za ta neme su su bada sheda Akan ta,Abdoul kuma bata ma San taya za ta soma sanar masa ba,domin tambayan shine tun farko miye hadin ta da Bashir tana matar aure upon all mutanan asibitin ya zabe ta tana karamar nurse wannan magana ko mara kai ya ji dole sense in Shi ya hasko masa wani Abu na daban...... Asaalamu alaikum Ina fatan mun wayi gari Lafiya ubangiji ya sa haka ameen, Ina matukar godia da sakon nin ku masu Kira duba ya jiki na masu mani addua ubangiji ya amsa ya kuma Saka da Alkhairi,Allah kuma ya bar zumunci, Alhamdulilah jiki na Fara Jin sauki duk da har yanzu ina kwance,ina cigaba da baran adduo'in ku๐Ÿ˜”๐Ÿ™๐Ÿป,ina kuma me Baku hakurin jina shiru da kuka yi komai yar lafiya ne, ubangiji ya kara mana lafiya da Nisan kwana me amfani, Banyi alkwarin typing kullum ba domin ko nace Zan yi wahalar da kai na da Ku kawai Zan yi don ba fahimtar komai za kiyi ba Amman in sha Allah in har na warware za Ku ji ni,na gode sosai da kaunar Ku gare ni, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi๐Ÿ™๐Ÿป [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ......... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai Shigo da ke,toh na hutar da ke ba sai kin Shigo ba, haka Maza don Allah stay away from my group domin na Mata ne xallah ๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ........... Page twenty-five ********* Aboki na don Allah Ka zauna Ka san dai yanke hukunci cikin fushi regret kawai yake jawowa ko,so pls Ka zauna ran Ka ya sauka tukun na koma miye ma je, Da wani irin kallo Sen ke bin Alh Kabiru da Shi sannan yace wai wani Zama ne kake son nayi ne,for crying loud wai Baka Jin me nake fada maka ne,Nadeeya ta fa aka nema aka Rasa and you are telling me to relax,are you for real,ya kare yana karkada kafa kamar me Shirin dambe, Hey common na sani ni Kai na hankali na a tashe yake but fighting won't solve anything,you have to stay calm ko don health in Ka wat if muka je a halin yanzu ranka na Sama Ka je Ka kashe shin kamar yanda Ka ce kayi ruining image and reputation in Ka ne fa,and for your own information you are going to end your life in prison which mean Kai da mulkan jahar bauchi har abada, Da sauri yace I reject it you better stop saying that kafin Yan Ameen su amsa,Odugwu yace in har na ga ban hau kujeran gwammna ba toh mutuwa nayi,ko ni na koma nace Bana so,and ya ce da ni I should rest ba Zan mutu ba har sai nayi 8 years a Kan mulki so you better stop saying such things,ya kare yana Sanya babban riga, Murmushi Kabiru yayi sannan yace Nima Kai na ai zan so Ka hau wanga kujera domin muddum Ka hau toh Kaka ta ta yanke Saka,ni dai try to control your anger that all am saying, Dariyar takaici Sen yayi sannan yace see who is talking about controlling temper,any way I won't blame you,Kai source in samun kudin Ka na tare da Kai sai sa kake mun duk wannan surutun,are u going ko in yi tafiya ta domin ban ga abunda zai Hana ni zuwa dubo where about in yarinya ta ba, Sanin halin Aminin nashi ya Sanya Alh Kabiru saurin mikewa tare da cewa mu je AI abunda ya shafe Ka ni ya shafa, let's get going da haka suka fito tare da shigewa cikin mota, ************Doc Nameer Saida ya tabbatar da Nadeeya ta koshi ya goge Mata baki sannan ya fito daga dakin,in har ya canka daidai kamar tayi fitsara and dole tana bukatan a canja Mata Kaya,Wanda Shi bare iya yi ba,Shi sam be san me ya shige Shi da ya dauko ta ya kawo ta gidan Shi ba tare da tunanin abubuwa da yawa ba, Shi ba auran ta yayi ba a taya zai na bata cikakken kulawan da take bukata,sanann Shi ba Mata gare Shi ba balle ace ya Sanya ran za ta Kula da ita,and a halin da Ake ciki be Isa ya dauke ta ya Kai ta Kaduna ba ana tsakiyar gurmin nan,don ya san can ne kawai za ta samu Kula a gurin Mamah, Shi yanzu yaya zai yi,ya Zama dole ne ya samo yar aiki Wanda za ta taimaka masa ta gyara masa Nadeeya ko yayi wa daya daga cikin nurses in magana,abun haushin shine ba kowa ya sani a garin Bauchi ba Banda Habeeb,Shi kuma Habeeb bakin Shi ya fi karfin Shi he is not that sure his secret is safe with him,da wannan nazarin ya fito daga gidan har ya iso hospital in Yana me tunanin mafita because is not good ya na barin ta haka,dole ya Nemo Wanda zata taya Shi Kula da ita, *********Sen Rilwanu Ko parking be bari an gama yi ba ya balle murfin Motan cikin sauri ya sauko Yana gyara babban rigan Shi da ke neman tatile shi, Tafiya yake cike da sauri domin bayi da burin da wuce ya gan shi a office in Doc Bashir,ya ji daga bakin Shi ina diyar Shi, Da sauri Alh Kabiru ya fito tare da mara mishi Baya yana kara kwantar mishi da hankali Kan in sha Allahu za a ganta, Be tsaya amsa gaisuwa da maulan mutane ba domin ba Shi ne a gaban Shi ba,yau yar fake concern and attention da yake baiwa talakawan Shi,Wanda su kuma suka yi masa uzuri kasancewar yawanci labari ya bazu,ba laifin Shi bane duk Wanda ke matsayin Shi fiye da haka ma sai yayi, Da karfi ya bugo kofar office in Doc Bashir ko tsaya wa sauraran abunda Doc Hanifa be yi ba,sai Alh Kabiru ne ya tsaya tayi mishi bayanin Kan Bashir fa yana isolated room, Bashir shine abunda Sen yayi shouting at the top of his lungs,where the hell are u hiding you low life of a person,Jin shiru ya Sanya shi shiga dube dube, Baya nan shine abunda Alh Kabiru ya fada yana me karasa shigowa office in, Yana ina kasan be nan in Ka sanya ni bata lokaci na,ya kare kamar zai buge shi, A ina Ka tsaya balle har nayi maka bayani in,nima isowar mun wata Doc ke sanar mun wai tun safe Yana isolated room be fita ko ina ba, that's good shine abunda Sen yace sanann ya juya cikin sauri yace let's go get him, Cike da tafiyar sauri suka iso dakin inda suka tarar da Doc Bashir kwance magashiyan a Kan gado sai numfarfashi yake saukewa kamar wani me Shirin haiwuwa๐Ÿคฃ, Bashir shine abunda Sen ya fara fadi yana me zaro idanu,so you are here relaxing and having a fun time of your life bayan yarinya ta is lost ya kare yana bin Maltina da madaran ruwa da ya ga anyi mixing a cikin cup, A zabure Doc Bashir ya mike yana furta na shiga uku na lalace Jameel don Allah ce da ni mafarki nake kamar muryan Sen nake ji,ya kare yana zazzaro idanu a kan Sen don son ya gaskata shin da gaske Sen in ne ko kuwa mafarkin da ya wuni yake yi yake kuma yi, Karasowa Sen yayi tare da daga hannu ba tare da wata wata ba ya dauke shi da Mari me dankaran zafi sanann yace Dan uban ka ni ne nan,shege matsiyaci Wanda be gaji arziki ba yau sai na ci uwar Ka na ga gatan Ka a cikin garin Bauchi,har ni ce zan baka Amana Ka zo mun da maganar banza wai an ce ta,uwar Ka ce ta sace ta ko gidan uban Ka aka kaita,shege Wanda be iya cin arziki ba, AI da sauri Jameel ya mike tare da barin dakin domin be dauka abunda Bashir ke ta tsoro ba ke nan,Ashe this man is very dangerous har haka a fuska sim sim kamar bare iya cize yatsa ba,Ashe shima ya iya hayaniya,gudun Kar a hada dashi shida babu abunda ya sani taimako ne kawai yayi wa Bashir ya sanya Shi ficewa daga dakin don har ga Allah wannan Mari ya tsorata Shi, Kabiru ne yayi saurin riko Sen Yana cewa haba don Allah Ka bar Marin nan haka let's talk this is the 5th time da ka mare Shi ba, Fincike jikin Shi Sen yayi sannan yace let go of me Kabiru,Dan Bura uban yaron nan a kwance na same Shi fa yana shan Maltina wato Shi har Yana da peace in da zai sha Maltina da madara while ba a san wani hali yarinya ta ke ciki ba, Cike da galabaita Bashir ya dago tare da cewa na rantse da Allah Alh Kabiru ba wai fun time of my life nake having ba tun da garin Allah ya Waye na bude Ido na ga babu Nadeeya hankali na be kuma kwanciya ba,I tried all my very best na gano inda take but ban samu ba, I have been fainting and using the toilet tun safe na sha drip ya Kai Leda nawa duk akan wanna yarinya amman sabida rashin godia da tunanin wannan mutumin zai zo ya hau Mari da duka na,haba is this fair am tired wlhy am not a piece of doll to u da zaka na duka na duk sanda Ka so am a fucking qualified doctor for crying out loud with a good qualification for your own information,ya kare Yana goge Jinin hancin Shi, Baki Bude daga Sen har Kabiru ke kallon doc Bashir,Kabiru kana ko Jin me shegen yaron nan ke fada mun kuwa,bura uba ai wlhy duk lalacewar goma ta fi biyar, Miye Doc dan ubanka who do u think are you da zan tsaya ina fada kana maida mun,ya kare tare da cikumo wuyan Bashir Yana kara dauke Shi da Mari,so mun Zama playing mate right,ka sace mun yarinya sanann Ka zo kana musanyan yawu da ni sabida wuyan Ka ya Isa yanka, Wai miye riba na in na sace maka yarinya meye zanyi da ita,na ga duk wani kudi kana biya na don Kula da ita,why will I take a vegetable na Kai ta ina,Akan wani dalili ma,beside ai farinciki ya kamata kayi na ga daman neman Kai kake da diyar ta ka,so godia ya kamata kayi wa duk Wanda ya dauke ta,Shi aka Bari da dawainiya, AI wani kukan kura Sen yayi tare da danko wuyan Bashir yace Kai dan iska karamin shege wlhy kayi kadan Ka yaba mun magana son ranka,ba a haifi Wanda zai ja da ni ba wlhy,Dan uwar Ka ni kake cewa neman Kai nake da Diya ta ya kare Yana Kara dauke Shi da Mari, Na rantse da Allah Sen in Ka kuma taba ni sai na tabbatar da na Tona maka asiri duk duniya su san Kai ne Ka Sanya na haukatar maka da yarinyar Ka akan wani son zuciya taka,haba na gaji na gaji ni ba jaki bane kayi ta duka na kamar uban da ya kawo ni duniya Doc Bashir ya kare da dan Ihu...... Ayi mun afuwa wlhy har yanzu ba wani sauki na samu ba wannan ma da kyar na samu nayi Shi,๐Ÿ˜ญ๐Ÿ™๐Ÿป, Ina cigaba da baran adduo'in ku don Allah,am kind of sick๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜ญ, Ina godia da kaunar Ku gare ni, ubangiji ya biya wa kowa bukatun Shi na Alkhairi, In sha Allah in dai na ji Dana dama za Ku ji ni zuwa gobe, Ina wa kowa fatan Alkhairi๐Ÿฅฐโค๏ธ [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin san ba karanta book ina da comment bane zai Shigo da ke toh don Allah yi Zaman ki na gode ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza Don Allah Kar kuyi joining group Ina domin na matan aure ne zallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ........... Page twenty- six ********** Wata irin shegiyar dariya Sen ya sake har yana dafe ciki,Alh Kabiru na taya Shi,Wanda ya sanya doc Bashir wangale Baki yana ganin ikon Allah, A tunanin Shi abunda ya fada zai Sanya hantan cikin Sen kadawa har ya firgita Shi ya haifar masa da tsoro Wanda zai Sanya Shi bashi hakuri Kan ya rufa mishi asiri,gudun Kar siyasar sa ta lalace,a karshe yayi amfani da daman Shi ya karbi makudan kudade a gurin shi,na rufin baki,amman sai ya ga sabanin haka, actually shi be ga abun dariya a maganar Shi ba da ya sanya wannan bayin Allahn ke dariya har haka, Kujera Sen ya ja tare da Zama ya daura daya kan daya sannan ya tsagaita dariyar, Alh Kabiru ni har yau mamakin talaka nake wlhy wato shi fa talaka bashi da abokin gaba da ya wuci me arziki, Sam mutanan duniya saidai a bar su,Ka ga daga ka kawo Shi ya zo shima ya ci arziki, shine wai ni Rilwanu Audu Waziri yake wa empty threat, Dan dariya ya kuma saki kafin yace wonder shall never end,me ma kake cewa, Yauwa za Ka yi exposing na kan ni na sanya Ka haukatar da diya tah,yeah ni nace Ka hauka ta din amman dole nayi maka?? Kudi na maka offering Wanda son duniya irin naka Ka mance da matsayin so called qualification in naka,Ka karba ko dole nayi ma, Aje ma wannan maganar in ana magana muna yi da evidence don ko karshen court in duniya muka je tambayan farko shine kana da evidence in Baka da shi ya zamo deformation of character kawai kake son mun don Ka batan siyasata,poor me karshe har tara za a Sanya Ka bani am I right Alh Kabiru ya kare Yana smiling, Kyalle Dan iska Sen ko Shi a gidan uban Waye aka ce masa ana sa'insa da masu kudi,AI duk abunda me kudi yayi daidai ne a gurin talaka irin Shi, Haba dai ai na ga yayi baki ne,toh Allah na tuba don Allah Waye Bashir da har empty threat in sa zai tsorata ni,nayi dealing da wanda suka ci uwar Ka in sanar maka, Na rantse da girman Allah in ban ce raping yarinya ta kayi,Ka kashe ta har lahira sannan Ka binne ta cikin hospital in nan,in kuma siye gaba daya staff's in hospital in nan su bata sheda a court room,a yanke maka hukuncin kisa da na rape Ka ga shike nan na rufe shafin rayuwar Ka har abada me kama da Kai ma babu, Haba Sen a dan wannan karamin alhakin har sai mun wahala shigar da Kara court kawai mu kwantar Shi muyi masa yankan rago mu Kai wa police dogs in gidan Ka su cinye Naman Dan iska, daman sun Dade ba su ci naman mutum ba,Ka ga shike nan in ya shiga cikin kare ya cigaba da rashin kunyar tashi a can, Hantar cikin Bashir ne ya kada nan take ya ji kamar zawayi za ta zubo mishi,cike da mamaki yake kallon su Sen, Go on Doc ko has cat got your tongue ne,Sen yace cike da shakiyanci, A mutunci irin nawa Zan Baka zabi na Kira police da media team yanzu na sanar da su kayi raping yarinya ta Ka kashe ta ko kuma mu bi shawarar Aminina mu kashe Ka kawai a baiwa dogs Naman ka,shike nan kowa sai ya huta in Ka je lahiran Ka cigaba da likitancin naka,ya kare tare da sakin dariya, A sukwane bashir ya iso gaba Sen idanu cike da hawaye yace na roke ka kar Ka mun komai,wlhy Bana son ko daya, AA qualified Doc dole muyi daya cikin biyun nan,tunda na ga ai kasan right in Ka,in ka je court sai Ka sanar wa judge ko ba haka ba Kabiru, Haka ne Sen AI wlhy ni Bashir ni Ka baiwa kunya in hada Ka da Aminina don Ka ci arziki shine za Ka sace masa yarinya Ka bishi da rashin kunya har kana za Ka tona masa asiri,kila ma Ka riga da Ka tona since, Kyalle Shi wlhy ko ya fadi babu uban da zai yarda da Shi,coz ina da good reputation a garin nan fiye da tunanin me tunani in ya ga dama,ya bi gida gida Yana sanar musu Shi za ayi wa kallon mahaukaci,daman an cappa likitan mahauka karshe shima haukan yake if care not taken, Na rantse da girman Allah babu Wanda na sanar wa kai Ka Sanya ni haukatar da Nadeeya ba Wanda ya sani,daga ni sai Allah na, Ni fa duk ba wannan ya dame ni ba qualified Doc ina yarinyar da Ka je har gida Ka dauko ta, Gumin goshin Shi ya goge sannan yace na rantse da Allah Sen Ka yarda da ni ban san inda Nadeeya take ba, Wannan ce abunda hankalina Sam bare taba dauka ba,in Baka yar cikin girma da arziki na cika maka account da kudi Kan zaka Kula mun da ita,na kawo ta da bakin ta da kafafun ta Ka maida ta babu Baki babu kafa,duk na dauka na jure yanzu a wayi gari Ka ce da ni babu ita AI kasan ko kwana zamu yi kana nanata mun zancen ga baza ta taba kama Kai na ba, Bashir ina Nadeeya ta shine abunda Sen ya ce a tsawace Yana me mikewa tsaye, Cike da rudewa shima Bashir in ya mike ya shiga zare ido yana yar fa yatsu kafin ki ce me mutane sun cika a dakin,su doc Haneefa and co makiyan doc Bashir abun ya Kai musu Banda dariya da Allah Kara babu abunda suke yi, Cike da rudewa ya shiga be wa Sen labarin iya abunda ya sani Kan ya Shigo duba Nadeeya around 12 kafin ya tafi gida shine ya ji an caka masa alura be kuma sanin inda kanshi yake ba,Saida safe ya farka ya ga babu ita ba alamun ta, Kai Doc Bashir Ka ji tsoron Allah wlhy duk fadin asibitin nan babu Wanda yake Bari ya je Kusa da dakin ma daga Shi sai Kareematu ne suka iya Bude pin in dakin, Sen Ka rike su wlhy tsakanin Shi da Kareematu ne dayan su ne ya dauke ta mugun mutum ne daman Shi,Doc Haneefa ta kare tana hararan Bashir in, Ji yayi kamar ya shake yar iska ana babu guri tana ta kwanta, cikin raunin murya yace na rantse ni dai ban dauki Nadeeya ba ni in dauke ta in yi me da ita, Waya sani maka duniyar yanzu AI ba gaskia aka fiya ba kaidai kawai Ka ga mutun inda Ka gashi,wani Doc ya fada, Nan fa aka hau ce ce kuce tsakanin Bashir da doctors suna cewa sam Shi ya sace Nadeeya while Shi kuma ya kafe be san komai ba game da bacewar Nadeeyan,Shi yayi danasanin sanin Alh Kabiru da ya hada shi da Sen har ya shiga wannan halin(ni ko na ce son zuciyar Ka ta janyo maka), Kuyi wa mutane shiru dallah,da me ze ji da batan yar sa ce ko kuma da wannan hayaniyar ta ku da ke neman cika mana kunne, Sen I think the best option here is to call the police tunda mun bishi ta lallami yaki sanar mana inda Nadeeya take kila in ya sha matsa a gurin Yan sanda zai yi bayani,Bari na Kira su Auwal su zo su tafi da shi, Maza Kira su Kabiru saidai ba Shi kadai za a kama ba,duk wasu maaikatan cikin hospital in nan duk a kame su don Basu da gaskiya kace da su su zo da mota da yawa, Yallabe a duba mu wlhy mu ba mu san ko mai ba,ni ko kallan fuskanta ban taba, gani ba Ni wlhy ko kalan dakin ban ma San ya yake ba, tunda aka kawo ta bashir ya kange komai ya Hana kowa zuwa Kusan ta,daga Shi sai Kareematu kawai ke shiga duba ta, Kareematu wacece ita shine abunda Alh Kabiru ya tambaya, Nurse ce kuma tare suke komai da doc Bashir Baya boye Mata komai kila ita tasan yanda ya boye ta, Tana ina shine abunda Sen ya tambaya, through jiya da yau bata zo asibiti ba Bashir ya amsa da kyar, Wonderful sai Ka Kira ta yanzu kace ta zo,in Ka ga dama Ka bari ta gane kana cikin wani hali taki zuwa Kai kadai za Ka kwana ciki, Jiki a mace ya dauki waya tare da dannawa Kareematu Kira, Shigowan ta gida ke nan duk jiki a gajiya domin tun haduwar su da Dan shuwa bata dawo ba sai yau da yace da ita zai tafi Sudan ya mata sallama mafi tsoka domin 5 mil ya bata tare da bata complimentary card in Shi,ba yanda ba tayi da Shi kan tana son bin Shi ba Amman yaki,yace ta Bari zai dawo zai neme ta,a haka suka rabu tayi masa kukan shagwaba wai bata son rabuwa da Shi,za ta yi missing in Shi,(ni ko nace ko a ina ta san Shi oho har tana ikirarin bin shi ko mijin ta da yaran ta tayi yaya da su sai Allah), Da Abdul ta ci Karo a bakin kofar dakin ta,sai lokacin take tunawa Ashe fa tana da aure ta bar gida kan asibiti za ta bata dawo ba sai yau and bata Kira ta sanar da Shi ga dalili ba, Da kallon mamaki da takaici yake binta kafin da kyar tace da Shi sannu da gida baban khairat, Hmmm yanzu Kareematu kin kyauta abunda kike yi kina tunanin hakan ya dace,tsakani da Allah ace ki bar gida sai yau kike dawowa da sunan aiki wani irin aiki ne haka,Anya kina son gamawa da duniya lafiya kuwa, Baki ta cuno sannan tace toh yanzu don girman Allah me nayi,Kai zuciyar Ka ta mutu ba fita nemowa kake yi ba,in ban Nemo ba uban me kake son mu CI ni da yarana,mu zauna yunwa ta kashe mu ko miye,Sam ba zai yu wa ba wlhy dole na fita na nema ko Dan rufa wa Kai na asiri,Kai kanka kasan akwai ni da son dadi, don haka Bana son dogon surutu a gajiye nake, In da sabo ya Saba da wannan mugun halin matar tashi domin sam ita bata laifi a rayuwa Baka isa sanar Mata tayi ba daidai ba,Kai kawai ya girgiza sannan yace Allah ya shirya, Ameen ya shirya harda Wanda yayi aure Baya iya yin cefane me kyau a gidan Shi,ta ja tsaki aikin banza mutun be da Sisi sai iskanci ai sai kayi, (Maza a ji tsoron Allah Ku sani aure bautan ubangiji ne Ka dauko yarinya Ka kawo ta gida,toh Ka sani nauyin ta na kanka,a ringa kokari ana ciyar da iyali daidai gwargwado Kar Ka zamo mugu,kana da Shi Baka yi,and Kar Ka zamo me mutuwar zuciya da karfin Ka don Ka Rasa aikin gwamnati shike nan bara Ka tashi Ka nema na,toh wlhy Ku ji tsoron Allah Shi dai hakkin ciyarwa tana Kan wuyan Ka ne,sannan Lada gare ta ci da iyali,and Yana tsare mutunci da gudun raini,muddum Ka kasance Baka ciyar da iyalan Ka sai sun tashi sun nema sun Baka toh wlhy Ka siyawa Kan Ka raini da wulakanci da kudin Ka,Mata kuma Ku ji tsoron Allah duk abunda me gida ya kawo komin kankantan Shi learn how to appreciate sai ki ga ya samu karfin nemowa gobe,rainako ko hangen na gaba da ke sam ba naki bane,my sisters duk halin kuncin da kuke ciki wlhy kin fi wasu,in kika ga wasu sai kin daga hannu kin ce Alhamdulilah, ubangiji ya ba mu ikon gyarawa,), A Kan kujera ta yarda jakar hannun ta tare da fiddo wayan ta dake ringing, Ko uban wake Kira na oho ni wanka nake son yi na hutawa raina,mitar da take ke nan tare da kallon screen in wayan ganin Bashir ke Kira ya Sanya ta lailayo ashar tare da kunduma mishi, Lalle bashir Ka cika Dan rainin wayo to me kuma Ka Kira kace mun shine abunda ta Fadi bayan ta dauki wayan, Yi hakuri Kareematu nasan haushi na kike ji Amman, Amman me ruwan masifan da ke cin ta ya Sanya ta kasa gano tashin hankalin da ke dauke a muryan Shi, AI wlhy babu abunda za Ka ce da ni, Bashir ni kareema Ka wulakanta,sabida Rashin mutunci Ka Sanya ni na je guri Ka ki zuwa,toh wlhy Kar Ka kuma Kira na in ba haka ba sai na yi maka abunda baza Ka mance ba ta kare tana jan tsaki tare da kashe Kiran, Kuma Kira yayi taki dauka Kara Kira yayi sai a na uku ta dauka,cikin bacin Rai tace wai miye haka Ka bi Ka takurawa rayuwa ta fa, Don Allah Kareematu kiyi hakuri nasan ban kyauta Miki ba Amman wani urgent Abu ne ya taso,ni da ke AI kin San bata Baci yanzu haka ma wlhy Sen mahaifin Nadeeya ne ya zo Yana ta barin kudi a staff's shine nace baran bari a barki a Baya ba kiyi sauri ki zo ki karbi rabon ki Kar ya tafi, Nan take ta washe Baki ayya dan bashiru na,Ashe da arziki kake Kirana nake ma Bura uba ta saki dariya saisa nake kaunar Ka nawa,Sam in har Kan samu ne Baka mance ni,gani nan tahowa yanzu wankan ma na fasa Shi, Toh Maza hanzarta ina jiran ki da haka ya kashe Kiran,haba mikewa tayi tare da karkabe dankwalin ta tare da kafa dauri, Sannan ta dauko turaruka ta fesa tana Yan wakokin ta na haka za Ka ganni ayye,haka za Ka bar ni,tana daga murya don Abdul in ya ji, Jakar ta ta dauka tare da mayafi,Bari na hanzar ta domin manyan nan Basu son Jira yau Allah so na yake da arziki,kila na je ma nayi mishi yayi inviting na guest house in Shi, dariya tayi tare da karkada kirji da kuwa Kaka ta ta yanke saka,da haka ta Sanya takalmi ta fito, Khairat ce ta tare ta da Mommy mommy ina zaki ,kallon yarinyar tayi Sama da kasa kafin tace gidan da ubanki ya aike ni,Ka ji mun shegiyar yarinya dallah Ka ki Bani guri, Da haka ta wuce yarinyar a kofar gida ta tarar da Abdoul zaune abun duniya duk ya dame Shi, Yauwa Baban Khairat anyo Kirana na emergency a asibiti ni Zan wuce sai Allah ya juyo da ni,ga wannan ta Mika mishi 2k Ka baiwa Khairat tayo muku cefane don nasan ba abunda kuka CI tun safe,Kar a dafa da ni Zan ci abinci a hanya ta ta dawowa bye,ta kare tare da wucewar ta ba tare da jiran Jin amsan Shi ba, Adaidai ta ta tare da sauri tace ya Kai ta TH dake a unguwar Railway suke so akwai Dan tafiya kafin a Kai specialist hakan ya Sanya doc Bashir Kiran ta, Yi hakuri ga mu nan mun wuce Wunti yanzu za mu iso,okay kiyi sauri shine abunda yace tare da kashe waya, Ita kadai sai sakin murmushi take gani take yau Allah ya Gama Mata komai,har Allah Allah take su Isa, A haka suka iso asibitin cikin sauri ta sallami me adaidai tan,tare da cefa chewing gum a bakin ta tana tauna tare da taku irin na isasun Mata ta iso bakin clinic in Nasu, YOU ARE UNDER ARREST shine kalman da ta ji daga bayan ta....... Asaalamu alaikum Ina fatan duk kuna lafiya Allah ya sa haka ya kuma Kara mana lafiya da Nisan kwana me amfani, Na ga sakonin Ku ina godia ubangiji ya amsa ya kuma bar zumunci na gode sosai, Ayi hakuri tun dazu na so posting yanayi na jikin ne be bar ni ba, A cigaba da Sanya ni a addua don Allah ๐Ÿ˜ญ๐Ÿคฒ๐Ÿป, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi, Sai kuma zuwa Monday in me kowa me komai ya Sanya mun Kai. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜” UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ......... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA Don girman Allah in har kin san ba reading novel ina and commenting bane zai Sanya ki joining to kiyi Zaman ki na gode ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah ๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 .......... Page twenty- nine *********** Da matukar mamaki Afzaal ke kallon Sen toh ko dai dimaucewa yayi ne ya san dole ya ji a jikin Shi daman in Nadeeyar ta mutu Amman ya zai yi toh,aikin Gama ya riga ya Gama, Domin Shi har ga Allah duk tunanin Shi na bashi Nadeeya dai babu ita a wannan duniyar,doc Bashir ya cika aikin da ya bashi,abunda ya Sanya Shi kirkiran tafiyar karya ke nan ya kashe wayoyin Shi Baki daya akan sai an yi kamar kwana uku da mutuwar sai ya dawo ya zamo comfort zone wa Daddy ya san in no time xai mance da mutuwar although ya san zai iya affecting in Shi both mentally and physically but with time zai mance, Ba magana nake maka,kana jina Ka share ni wani Dan iskan ne ya sanar da Kai Diya ta babu ita ta mutu,Sen ya kare Yana tsare Shi da idanu, Kan Afzaal ne ya daure domin Shi fa a tunanin Shi ta mutun,toh yanzu kuma da ya ji bata mutu ba dole Sen ya tambaye Shi a gidan uban wa ya ji Nadeeya ta mutu,ko Karan hauka ce ta cije Shi bare ce Shi yace a kashe ta ba, Suna cikin haka sai ga shigowar Alh Kabiru,kafadun Afzaal ya dafe sannan yace na san dole Ka shiga rudu but matar ka ba mutuwa tayi ba my son sace ta aka yi an neme ta Sama da kasa an Rasa cikin hospital in, Idanu ya zaro tare da cewa Whattt impossible,a garin yaya aka sace ta,tana ina kuma yanzu, Calm down case in na hannun Jabiru yace mana mu kwantar da hankalin mu Nadeeya za ta fito,ya kare tare da neman gurin zama, Aboki na,Kai dai har yanzu bara Ka bar zafin nan naka ba,zo Ka zauna na zo da labari me dadi, Tsaki Sen ya ja sannan ya zaunan Yana me fadin yaron nan kayan cika ciki gare Shi, banda iskanci ya zo mun da zancen wai Nadeeya ta mutu,ana ba guri Dan uban Shi Yana ya kwanta, Kabiru dai Kai ya girgiza Yana jinjina ashar da wulakanci irin na Sen,yanzu Kai a haka za Ka Zama governor in a gayyace Ka taro gurin speech kana auna wa bayin Allah ashariyar Ka ta fama,kamar Dan maguzawa, Ba sai na zagi uban da zai hana ni Zama governor in ba,yi sauri Ka Fadi mun abunda kace za Ka fada, Zama Alh Kabiru ya gyara sannan yace yanzu Jabiru ya Kira ni wai sun kamo wata Nurse me suna Zaituna yanzu haka tana gurin su,Kareematu tace rannan ta ce ta shiga dakin Nadeeya Kai Mata abinci so ta shiga layin Yan zargi, Tsaki Sen ya ja sannan yace wannan Bashir wannan Bashir akwai Dan iska wlhy,ni su Gama duk haukar su,su fito mun da yarinya shine kawai bukata na, Afzaal da ke labe Yana Jin su a daki,wani tukukin bakin ciki ne ya tokari kirjin Shi,wato shi Bashir zai yaudara ya karbe masa Yan kudade har million 55 dan uban Shi kuma a banza,bata yu wa dole ya san abun yi bare yu ya ci masa kudi a banza ba,ya kare Yana huci kamar wani Wanda yayi race, ********Police command Har cikin hospital oga Jabiru ya tura yaran Shi suka kado mishi keyar Zaituna tana tsaka da aiki,ba karamin tsorata tayi ba,ba ita kadai ba hatta sauran workers in sun tsorata ganin yanda Ake musu daukan dai dai, Ko da aka kawo ta sai da ya tambayi Kareematu ita ce wannan,cikin sauri ta amsa da ita, Ba karamin kuka da tsinewa Kareematu Zaituna tayi ba Jin sharrin da take neman daura Mata, Fadi take Amman wlhy ke dai Kareematu akwai yar iska ki Rasa Wanda zaki wa sharri sai ni,me na Miki yallabai wlhy sau daya na taba shiga cikin dakin kuma itace ta Fadi mun pin in shiga abinci kawai na Kai Mata,Amman da ke butulu ce ita ka ji abunda take Fadi,Allah dai ya wadaran ki Kareematu, Ke dallah rufe wa mutane Baki sai dai ke Allah ya wadaran ki ba ni ba,sharri nayi Miki AI kin shiga dake da wannan shegen kune last in shiga gurin ta, Tsawa Jabiru ya daka musu sannan yace a zo a maida su cell har yanzu Basu Gama cin uban su na more especially Zaituna a tabbtar an lallasa ta in tayi laushi za tayi bayani,tana kuka tana Ihu haka aka kwabe ta ko Dan kwali babu aka watsa ta cell aka hau kirba kamar an samu sakwara, Kwanan ta uku a hannun su,Banda uban bugu babu abunda suke ci,kuka kam sun yi Shi har Basu son adadin Shi ba,doc Bashir abun ba karamin mamaki ya bashi ba sai yanzu ya tabbatar da iyalan Shi Basu damu da Shi ba kamar yanda shima ya ke watsar da lamuran su,domin tun sanda aka daure Shi ko kafar makocin Shi be gani ba balle na Yara ko matan Shi,tabbas yasan duk rintsi za su samu labari domin duniyar yanzu kana kwance gadon baccin Ka labari ke iso Ka,be taba sanin mugun Zaman na su ya Kai haka ba sai yanzu wato Basu damu ba ko a raye ko a mace yake,ikon Allah abunda ya fi masa ciwo ke nan duk rintsi dai a Kan idanun Shi mijin Kareematu da yaran ta ke ta sunturin zuwa ganin ta suna me kwantar Mata da hankalin in sha Allah za ta fito haka ma Zaituna Amman Shi kam wai ko aboki be zo masa ba, *******Doc Bashir Ubaidullah Shine cikakkiyar sunan dan asalin garin Bauchi ne a karamin hukumar Burkacuwa,mutum ne Shi me tsananin son Mata da kuma abun duniya, Like Akan mace toh ranshi ma zai iya bada WA,matar Shi ta farko auran Hadi aka yi musu Wanda sam be kaunar ta amman aka dage da auran a haka ya aure ta ubangiji ya azurta su da Yara 4,sannan ya Karo ta biyu Wanda yake Kira zabin nashi, In takai ce muku zance dai Bashir Mayen Mata ne Wanda ya sanya Shi aure da sake,domin ya auri Mata sun Kai 10 a rayuwar Shi,likita ne kwararai na kwakwalwa,wanda kila abunda ya dan taba Shi ke nan kun san in karatu tayi yawa sai a hankali lol, A irin son matan Shi ne ya sanya Shi Fara bin staff's in Shi,watsatsu irin Shi su bada Kai wasu su ki,kamar na Doc Haneefa babu yanda be yi Kan ya tatile ta ba sam taki ya Sanya sam tashi da ita Basu zo daya ba ya tsane ta haka ita ma ta tsane Shi, Kareematu tafiyar su ta zo daya ne ta hanya mugun son kudin ta Shi kuma irin macen da yake so ke nan ya Sanya ya maida ta kamar matar Shi kullum tana cikin cewa ta tafi night duty hospital alhalin suna can guest house in Doc Bashir suna tsabon Allah in da yake Mata barin kudi domin babu karya Yana samun satisfaction iya makura a gurin Kareematu, Mind you ko don an canfa ne daman an ce liktoci akwai son Mata sannan akwai su da mako Basu rike iyalan su at all(am sorry ba wai na Fadi don cin fuskan doctors bane base on abunda nake ji kuma nake gani ne,so ayi mun afuwa pls,ba cin mutuncin doctors nake ba ko wani aiki akwai na kwarai akwai bata gari๐Ÿ™๐Ÿป), Yaran Shi sun Kai 10 gaba daya in Ka gansu bara Ka dau uban su Yana aiki Yana daukan albashi na,ya sakar wa matan ragamar gidan domin kwakwaran cefane wannan ba yi yake ba balle aje ga biyan sch fees da kuma sauran abubuwan bukata na rayuwa, Ko wace uwa ita ke fafutuka Akan yaran ta don ta samu ta rufa musu asiri, Gidan da suke ciki wannan bara Ka dauka nashi bane,in kana son ganin bacin ranshi to Yana cikin iyalan Shi ko kuma sun yi demanding in abun kudi toh nan zai ta hada fuska Yana masifa,karatu kuwa be damu suyi ko Kar suyi ba,in uwar yaro tana da shawar boko sai ta Sanya Dan ta Amman Shi babu ruwan Shi, Kudin Shi wa kanshi ne da kuma Matan banza,in one word doc Bashir dai MUGUN MIJI ne mara tausayi mara adalci sannan mara mutunci me tauye hakkin family in Shi,ya Sanya gaba daya ya fice musu a rai daga yaran gidan har matan gidan babu Wanda ke Jin dadin Zama da Shi gaba daya ya fice musu a rai,wannan ke nan, Roka yayi Allah Annabi a Bude Shi ya je office in oga Jabiru akwai bayanin da zai mishi,domin bayan dogon nazari da yayi,gaskia Baya ji zai iya kara kwana daya a cell in nan ya gaji matuka gayya,burin Shi ya gan Shi ya zama free man shima,in har ya tuno kudadan da ke shake a cikin account in Shi sai ya ji Rabin azaban duk ya bar jikin Shi,Dan uban iyalan Shi Yana fitowa yau ko gobe in ya je asibiti ya dan karbi treatment sai airport bare zarce ko ina ba sai Los Angeles dole ya je ya samu kamar Sati biyu Yana hutawa a jikin fararan fata, Da kyar da sidin goshi wani dan sandan ya Bude Shi bayan yayi mishi alkwari zai bashi kyautan 10k in ya fito, Jiki a mace Yana jan kafafu ya nufi office in Jabiru,da sallama ya shiga, In da ya tadda Jabiru zaune Yana Shan Maltina me sanyi ga namar suya a gefe Yana afawa, Da tsawa ya ce kai uban me ya fito da kai,Saida Doc Bashir ya hadiye yawun kwadayi sanann yace yallabai na zo magana da Kai ne don Allah in bara Ka damu ba, Be Jira amsan Shi ba ya cigaba da fadin yallabai jiya da na kwanta bacci nayi wani dogon tunani da nazari,tunda duk cikin mu ukun nan babu Wanda ya aika laifin nan toh tabbas na san shine zai aika ta domin tun zuwan Shi na ga alaman Yana yawan shige shige Yana son sanin komai ya kare Yana lashe Baki domin babu karya yawun Shi ya biya , Can in Jabiru ya aje tare da mikewa tsaye sanan yace Waye and for all this while Ka san Wanda ya aika laifin nan kake ta wahala mu har muna Shirin cike muku file mu aika Ku court ranar Monday, Idanu Bashir ya zaro sannan yace yallabai na tabbatar ko da ba Shi ya sace ta ba toh dole ya san wani abu akai, Waye Shi fada mun sunan Shi da hanzari kuma a ina yake, Saida Doc Bashir ya nemi gurun zama sanan yace yallabai sunan Shi Doc Nameer ,duk tare muke aiki haka kawai zuciya ta bata yarda da Shi ba,kuma ina ji a jiki na kamar Shi ya dauke ta, Da Ka san da haka Ka tsaya bata mana lokaci a ina za mu same Shi, Yallabai ina na samu fuska gurin Ka kullum duka fa kake Sanya ayi mana,da Shi na ke breakfast nayi lunch harda dinner fa,Haba don Allah ba dole tunani na ya dauke ba, Tsawa Jabiru ya daka mishi domin ganin ya Fara wuce Gona da iri,sallamar Shi yayi kan ya koma cell in Shi,za su koma asibitin yanzu domin bincike,da haka kuwa ya fice daga office in Yana me tsine wa oga Jabiru a ranshi na ranshin bashi suya da yayi,(ni ko nace kila Kai Ka Siya masa ai), Nan ya tara yaran Shi babu bata lokaci be Jira ya sanar wa Sen ba ma domin Shi kanshi case in nan ya Fara fita masa a Kai,be taba Kai wa iyanzu Yana solving case babu solution ba sai this time around Yana adduar Allah ya sa zargin Bashir in ya zamo gaskia a rufe case kowa ya huta, Ko da suka isa Kai tsaye office in Nameer suka nufa lucky them be Riga ya tafi gida ba, Sama da kasa Jabiru ke kare masa kallon wulanci kafin cikin Isa da izza yace da Shi you are under arrest, A nutse doc Nameer ya dago tare da kare wa Jabiru kallo sannan yace da Shi wa alaika assalam, Kallon kallo Jabiru ke yi da yaran Shi kafin ya sheke da dariya sannan yace da kyau ustaz mike a Sanya maka ankwa mu wuce da Kai gidan Ka sauri muke, Mike wa Nameer yayi tare da cewa wannan kuma shine impossible Kai look at me very well I know my right KO su Bashir da Kareematu da kuka kame su suka so suka kuma bar Ku,Amman ni kam na rantse da girman Allah Baku Isa kama ni ba domin babu abunda nayi,ya kare tare da koma wa ya zauna, Kai Jabiru ke jijigawa domin ganin irin wannan confidence na yaron nan,Shi sai ma ya Fara bashi tsoro,irin wannan Ka tabo mutum ne Baka san Waye Shi ba,Amman sai ya daure yace, Ka tashi mu tafi gidan Ka na karbo search warrant domin Bashir ya sanar mana Yana zargin Kai Ka sace Nadeeya, Dariya Nameer yayi har hakwaran Shi suka fito kafin yace a taya zan sace Nadeeya miye Hadi na da ita,hasali ma ni ko haduwa da ita ban tunanin mun taba yi,kawai dai yayi cooking up stories ne koh mun je gidan nawa am very sure babu abunda za Ku samu so a shawarce Ku koma abun Ku domin Bashir ba isashen hankali yake da ba,don anjima ma zai iya cewa Shi Sen da kanshi ya sace diyar ta Shi,ya kare tare da sipping in bottle water, Duk bayanin nan be gamsar da oga Jabiru ba Saida suka sako Nameer a gaba Wanda sam be yarda sun ci mutuncin Shi domin idanu ya Bude musu,a motar Shi suka bi bayan Shi har suka iso unguwar nashi, Gate in ya Bude sannan suka Shigo cikin gidan,zuciyar Shi sake sam babu tsoro ko wani alamu da zai nuna bayi da gaskia, Kofar palor ya Bude sannan yace da Jabiru mu kalli search warrant in da aka bada,nan ya mika mishi Saida ya karance tsaf ya ga ba cooking up stories suka yi ba sannan ya matsa yace su shiga,su bincike ko ina,Amman da sharadi ko tsinke nashi ya Rasa ko aka lalata mishi wanni abun in the process in neman ta wlhy tallahi sai yayi Karan su court,da haka suka wuce, oga Jabiru yace wlhy kowa yayi taka tsan tsan in mutum ya fasa Abu ko ya lalata uban Shi zai ci, Guri Nameer ya nema ya zauna tare da daura daya kan daya ko a jikin Shi, Nan ko suka shiga dube dube da ke ya musu warning ya Sanya Basu masa binciken hauka ba a sannu suke komai ko ina sun duba saidai Sama ko kasa sun Rasa,babu ma wani alamun da zai nuna Nadeeya ta taba rayuwa a gidan, Bincike sukai sosai Amman duk a banza domin Basu Sami komai ba,a haka suka fito, Ina take kila kun same ta Nameer ya tambaya cike da shakiyanci, Kwafa Jabiru yayi sannan yace Allah ya taimake Ka ba mu sami komai ba da Ka yaba wa Aya zakin ta,domin yanda kake da yawan maganan cikin minti daya Zan Sanya Ka shiru na watanni guda, Kai kawai Nameer ya girgiza sannan yace officers ga can kofar fita tunda har kun Gama abun da ya kawo Ku you guys should get going daman na fada muku indai zancen Bashir za Ka dauka toh gantali yanzu ya kama Ka,daga haka yayi shigewar Shi cikin daki,ba karamin ciwo Jabiru ya ji ba saidai babu yanda ya iya haka ya tasa Kan yaran nashi suka fice daga gidan tare da daukan alkwarin sai ya ci uban Bashir ya in suka koma police command. A cigaba da hakuri da ni komai yar lafiya ce, Ina godia da dumbin kaunar Ku da kuma fatan Alkhairi da kuke a gare ni ubangiji ya Saka da alkhairi ๐Ÿ™๐Ÿปโค๏ธ, Sai gobe in me kowa me komai ya so, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA Don Allah in har kin San ba karatun book ina da commenting bane zai kawo ki toh Kar kiyi joining,haka zalika Maza Don Allah stay away from my group domin na Mata ne xallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ......... Page twenty- eight *********** Doc Nameer****** A gajiye Nameer ke driver domin drama in da Sen yayi creating tun safe ma ya Isa gajiyar da su,Habeeb da ke xaune gefan Shi ke ta zuba mishi hira Wanda da eh ko aa kawai yake amsa Shi domin Rabin hankalin Shi na gurin Nadeeya, Shoulder in Shi Habeeb ya taba Wanda ya sanya Shi saurin juyowa tare da cewa Nadeeya, Da kallon mamaki Habeeb ke bin Shi da Shi,goshi ya dafe tare da yin parking sannan yace ya aka yi ne Habeeb, Nameer wat the hell is wrong with u ne,I have been talking since Ka share ni and yanzu Ka Kira ni da Nadeeya, Dan kallon Shi yayi sannan yace a yaushe Kai dai kawai sabida an wuni maganar ta ne ya sanya kake ji kamar na Kira sunan ta, Hmm wlhy ko kaffara bazan yi ba Doc Handsome akwai abunda kake boye wa,and am very sure Nadeeya na ji Ka Kira ba wani kunne na bane, Shi dai Nameer be kuma Kula Shi ba mota ya ja tare da nufan gidan Habeeb in,Saida suka iso sannan yace da Shi Bari ya koma, Nan ko Habeeb yace be san zance ba ya Shigo Muhibba ta gama abinci su ci sai ya wuce,ganin yanda ya matsa ne ya sanya Shi bin Shi cikin gidan, A nan parlor inta suka yada zango,nan ta fito da warmers a hannun ta sanye da fararan kayan nursing,alamu daga aiki ta dawo ko kayan bata Kai ga cire wa ba, Har kun Shigo shine tace tana smiling tare da nufan dining area in su,aa my love kawo mana nan kawai wlhy gajiya ce jikin mu sosai, Bata ce komai ba ta dawo nan gaban Nasu ta Aje sannan ta gaida doc cike da sakon fuska ya amsa Mata,tare da tambayan ina baby,Yana bacci shine abunda ta amsa masa tare da mikewa, Ke dai Hibbaty har yanzu ba a cire uniform ba,wlhy Ka Bari kawai yau din nan Nima a gajiye na dawo yanzu nake son yin wanka na canza kayan,daga haka ta shige kitchen tare da karasa Ibo musu abubuwan da za su bukata na cin abincin sannan tayi shigewar ta daki, Nan ko Habeeb ya ware hannu ya shiga cin tuwon semo da miyar vegetables da ya ji Nama da kifi ga cup cike da zobo me sanyi a gefe, Doc Nameer dai ya kasa Kai ko Loma daya,Shi be ga wautar Shi ba sam Saida ya dauko ta,toh ba tsayawa yayi dogon nazari ba kawai ya biye wa abunda zuciyar Shi ta Raya mishi ne,gashi yanzu duk ya gagara sukuni, Ganin har yayi Rabin plate Nameer ko loma daya beyi bane ya Sanya Shi tsame hannun shi,sanann ya ce doc Nameer don Allah tashi kayi tafiyar Ka tunda har ni Baka dauke ni da mutunci kamar yanda na dauke Ka ba, Da mamaki Nameer yace haba dai ban gane me kake Fadi ba kamar ya, Eh kamar yanda Ka ji ace tun yau da safe ne nake bi dakai Ka sanar da ni damuwar Ka for Allah sake ko ban zamo silan daukewar sa AI na taya Ka roko gurin Allah amman sam kaki,is like you don't trust me or ko kana ganin ban Kai in san damuwar Ka ba,Wanda hakan ba karamin batan Rai yake ba,yanda na dauke Ka bazan so ganin Ka cikin matsala ba,domin ni a dan uwan Jini na dauke ba not just a friend,but is like ni ba haka nake gurin Ka ba, whatsoever ke damun Ka I promise not to ask again ubangiji ya yaye maka damuwar Ka ya kare tare da mike wa,domin har ga Allah abun ya bata mishi Rai,bubu dadi kana tare da mutun kuma kana ganin Sarai Yana cikin damuwa Amman ya boye maka,sai Ka ga kamar be yarda da Kai bane, Hannun shi ya riko sanann yace haba Kai kuwa Habeeb toh miye abun fushin, Yaya baran yi fushi ba Nameer a problem share is a problem solve Kai kan,Ka san two heads are better than one,ni sakar ni in Ka ga dama Ka ci abinci Ka yi tafiyar Ka ni na tafi dakin Mata na, Dan murmushi Doc Nameer yayi sanann yace in Ka tafin toh Waye zai yi solving problems in nawa come back and seat down let us talk man to man, Habeeb be ce komai ba face dawowa da yayi ya zauna Kusa da Nameer in sannan yace ina Jin ka, Actually ban san taya zan Fara maka bayani ba,I don't even know how to explain myself,and I don't know da wani Ido ko fassara za Ka yi mun but trust me wlhy nayi ne with pure intentions, Da Ido Habeeb ke bin Shi kafin ni fa Ka Sanya ni cikin duhu go straight to the point, Numfashi Nameer ya ja sannan yace Habeeb I do trust you saisa Zan sanar da Kai damuwa ta don Allah don't let me down,da Kai ya amsa Shi domin har ga Allah Shi ya ma Fara Jin tsoro toh me Nameer in yayi haka, A hankali ya ce Habeeb Ni ne na dauki Nadeeya,a zabure Habeeb yace Whatttt, Nameer Ka kuwa san abunda kake Fadi kuwa are u mad or something taya za Ka ce Nadeeya is with you ,how comes a ma tayaya a yaushe Akan me yasa,shine duk abubuwan da Habeeb ke Fadi, Mikewa shima Nameer in yayi tare da dafe shoulders in sa sannan yace I can explain but seat down first, Nan take ya kwashe tun farkon haduwar Shi da Nadeeya har zuwa jiya da ya dauke ta daga hospital tare da tsitatar da ita daga mutuwar dole da Afzaal ya Sanya Bashir yayi mata, Baki Bude Habeeb ke kallon Shi kafin ya ja ajiyar zuciya sannan yace lalle wannan doc Bashir in Ashe Dan iska ne, Tambaya ta a nan shine why Baka sanar da mahaifin ta ba and akan wani dalili zai Sanya miji ya so ganin bayan matar Shi me tayi masa, That wat I want to know Habeeb haka kawai nake Jin rayuwar yarinyar nan Yana cikin hadari,and maganar gaskia at this point ban san who to trust ba,haka kawai nake Jin a jiki na kamar Shi uban nata shima son cutar da ita yake yi,kawai I don't know why nake Jin bazan iya trusting kowa da ita ba, Shiru duk suka yi kafin Habeeb yayi breaking Shirin da cewa Nameer kana son Nadeeya ne?? Da sauri ya dago tare da nuna kanshi kafin yace haba haba nooo ba wannan maganar kawai dai ji nake kamar ya za me mun dole na taimake ta and I don't know why Is just like kamar ina da strong connection with her or something,ya kare yana shafa Kan Shi, Dan murmushi Doc Habeeb yayi sannan yace ban taba ganin actor irin Ka ba,Ka dauke yarinya ka Sanya dan iskan can a wani hali,na san Yana can hannun su Jabiru wlhy uban Shi za su ci,ya Kare Yana dariya tare da haskako fuskan Bashir in, Kai kawai Nameer ya girgiza domin Habeeb ba dai mugunta ba,kafin yace can you help me pls, Say it out Allah ya sa Zan iya, Madam za ka bani Aron ta,pls ta samu ta je ta yi wa Nadeeya wanka a samu a canja Mata Kaya tun jiya suke jikin ta,na san by now sun dame ta, Sure Bari na Kira ta,AI dole su dame ta ina za Ka bar ta ita kadai,ya kare tare da shige wa dakin Hibban,ba dadewa suka fito da dan first aid kit in ta,tare da babyn su a hannun Habeeb in,mamaki ful ranta a yaushe Nameer in yayi aure ba ta sani ba,da haka suka shige mota har ya tada motar tace ya tsaya tai mantuwa,da sauri ta koma ciki tare da dauko simple brown gown me hade da cap in Shi sabo gal sai kamshi yake zubawa sannan ta dawo suka taho, 3 Days Later******* Kwanakin ukun nan ba karamin azaba Ake ganawa su Bashir da Kareematu ba,oga Jabiru ya dage by fire by force sai ya samu information out of them, Kareematu ba karamin kuka tayi ba barin ranar da Abdoul ya zo domin ya samu labarin abunda ya faru a asibitin su,babu yanda be yi ba Akan a bada bail In ta Amman sam Jabiru yace bare yu ba,karshe ma rashin mutunci ya karta wa Abdoul Wanda Saida ya sanya Shi kwalla da haka ya bar police command in tana kuka tana rokan Shi Kar ya tafi,Shi ya Rasa gane wannan rashin ji irin na Kareematu da ta daura wa kanta tun tana budurwa Allah yayi ta mace me shegen kadadi rawan Kai da shegen son abun duniya,abun haushin kuwa ubangiji yayi ta ba yar gidan uban kowa ba,sai shegen fadin Kai da hangen nesa, Zai iya cewa kaddara da blind love da kuma rabon su Khairat ne ya hada auran su,domin rawar Kai kam ko kadangare nan ya ga Kareematu ya bar ta, Aure na soyayya suka yi domin ya kasance Dan unguwar su ne wanda zai iya kiran sunan kaunar da yake Mata akan jarabawa, Yayi matukar mamaki da ta saurare Shi tun ranar farko,wai gamon Jini daga Allah soyayya suka yi me tsafta domin Abdoul irin social uztaz in nan ne,sannan kuma malamin makaranta ne, Haka ko da suka yi aure duk da rashin kunya da rawar kanta suna Zama lafiya har ta kammala karatun ta na Nursing wanda Shi ya tsaya Mata kai da fata domin har rancan kudin banki ya karbo duk don Faranta Mata, Daga sanda ta samu aiki toh wannan lokacin suka yi sallama da farinciki don tunda ta Fara haduwa da doc Bashir ya Fara bude Mata idanu da fari ta ki yarda Amman ganin irin barin kudin da yake Mata,Wanda a lokacin samun Abdoul yayi Baya domin gidan da suke ciki ma Saida Shi yayi ya biya bashin bankij da Ake bin shi suka koma na haya, Da haka Bashir ya siye zuciyar ta shike nan suka dinke ko bata da duty sai ta je hotel sun sheke Aya ita da doc Bashir,a sunan ta ta fi Night duty,Wanda Abdoul Sam be da masaniya kan irin wannan mugun dabia da Kareematu ke aikatawa,tun tana yi da Bashir har idanun ta suka kuma budewa ta Fara bin wasu Maza Jen can daban in har zaka bata kudi toh tabbas za ta Bude maka kafa,idanun ta gaba daya sun rufe neman duniya kawai ta Sanya a gaba, Tsawa me razanar wa Oga Jabiru ya daka musu tare da fadin Ku wai ga Ku yan iska masu taurin Kai ko,bara Ku sanar mun yanda kuka kai yarinyar mutane ba, Cike da kuka jiki duk tsami Baki duk ya kumbura,Kareematu tace yallabai wlhy tallahi iyakan gaskiar ke nan ni dai ina shiga duba ta time to time bisa umurnin doc Bashir amman ba ni na dauke ta ba, Kin taba ganin criminal yayi confessing laifin Shi daman,har yanzu Baku bugu bane kila sai na sanya a tsinke muku gashin jikin ku ko an sanya muku shocking zaku samu Ku Fadi gaskia, Cikin kuka doc Bashir yace yallabai kayi wa girman Allah Ka bar ni haka wlhy ko zama Bani iya wa sai kwanciya, Dariya Jabiru ya sheke dashi kafin yace AI kadan Ka gani in har junin Ku taurin kai ne gaba kwanciyar ma kasa ta za kayi, Sabida zarmewar zuciya ina Ku ina Satan yarinyar dan takaran gwammna,uban me za kuyi da ita,a taya ma zaku ba Ku bane dole a cikin Ku akwai mugun da ya dauke ta, domin duk asibitin sun Fadi daga Kai sai ita wannan munafukar ke shiga gurin ta,ko bayan Ku akwai Wanda ya San pin in shiga dakin, Cikin zabura Kareematu tace yallabai wlhy na tuna akwai wata kawata a asibitin Nurse Zaituna rannan ita na baiwa abincin Nadeeya ta kai Mata bayan kwana biyu kuma shine aka neme ta aka Rasa, yarinya ta babu lafiya ya Sanya through out ban zo aiki ba, Mikewa Jabiru yayi tare da kwada wa Kareematu mari me zafi da kara sanann yace shegiya dan uban ki duk kin san da haka kika tsaya bata mana lokaci a ina zan samo Zaituna ko miye sunan ta, Idanu cike da kwalla tace tana cikin asibiti ita ma maaikaciya ce a can, Daga haka be kuma ce musu komai ba ya Sanya Kai tare da bada umarnin a maida su cell,tare da daukan wayar Shi ya shiga Kiran layin Alh Kabiru, **********Sen Rilwanu Zaune yake a parlor ya zuba uban tagumi,kayan cima ta alfarma ce a gaban Shi Amaman sam ya kasa cin ko Abu daya,past days in nan Yana nan kawai ya Rasa me ke masa dadi a duniya,ya Sanya ya Hana kowa zuwa ganin Shi Banda Alh Kabiru sai Salis kawai yake iya gani, Tunani yake toh wai shin Ina Nadeeya take ne ya shiga uku yarinyar nan in har bakin ta ya Bude Yana wani hali shike nan tashi ta kare muddum asirin Shi ya tonu Zaman garin Bauchi sai ta gagare Shi,wata yawu me daci ya hadiye da kyar tare da lumshe idanu,abun haushin wannan masifa ta Fado mishi ba time in haduwar kungiyar su ba,he is very sure da zai ga Odugwu da matsalan Shi ta kare domin sam babu wani effort da su Jabirun nan ke making,abun haushin kuwa shine ba a ganin Odugwu in ba ranar haduwa ba gashi shi sam Allah be bashi juriya ba yana shiga cikin matsala take nuna masa, Fadowar da ya ji anyi a jikin Shi ana kuka ne ya sanya Shi zabura daga tunanin da ya fada tare da bin Afzaal dake kuka hawaye biyu biyu Akan kirjin Shi, Da sauri ya Ciro Shi sanann ya bi Shi da kallon mamaki Yana Kai Afzaal uban me ya same Ka zaka zo kana irin wannan kukan, Cikin kuka sosai har da shesheka yace Daddy Ashe Ashe,Ashe me Sen ya Fadi xuciyar Shi na bugawa, Cikin kuka yace daddy Ashe Nadeeya ta ta mutu shine aka boye mun ba a a fada mun ba,Banda yau da jiki na ya Bani ba lafiya ba nace gwara na dawo na gani, Be Kai ga karasawa ba Sen ya dauke Shi da Mari Tasssss kake ji,da sauri ya dafe kumatun Shi tare da mikewa, Shima mikewar Sen yayi sannan yace Dan uban Ka ina Ka ji labarin Nadeeya ta mutu,shege me bakin Yan wuta......... Assalamu alaikum๐Ÿฅฐ๐Ÿ‘๐Ÿป Ina fatan mun wuni lafiya ubangiji ya sa haka, Alhamdulilah jiki Yana ta sauki na gode sosai da adduo'in Ku masu Kira masu turo mun sakon ni ubangiji ya Saka da alkhairi,Allah kuma ya bar kauna, Ina me Baku hakurin jina shiru da kukai kwana biyu,Amman yanxu Alhamdulilah da sauki za kuna ji na akai akai in sha Allah, Ina yi wa kowa fatan Alkhairiโค๏ธ Sai zuwa gobe in me kowa me komai ya Sanya mun Kai. [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ....... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA Don Allah in har kin San ba karanta book ina da commenting bane zai kawo ki toh yi Zaman ki ba sai kin yi joining ba,haka zalika maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 .......... Page thirty ********* Doc Nameer***** Habeeb wai ina Ka Sanya wayan Ka ne tun dazu I have been calling u Baka dauka, Yi hakuri doc Handsome na shiga wanka ne,me ke faruwa ko Ka Kira Ka ji lafiyar Ajiyar Ka ne, Murmushi Nameer yayi kafin yace I trust you gee na san tana nan lafiya,kasan me ya faru, AA sai Ka fada Habeeb yace Yana goge ruwan jikin Shi da towel tare da Zama a kujeran gaban mirror, As expected kasan yanzu Yan sanda suka bar gida na, Idanu Habeeb ya zaro tare da fadin Yan sanda kuma na me toh, Wlhy ina asibiti suka daga ni wai suna son su yi searching in gida na,wai Bashir ya sanar da su Yana zargin ni na sace ta,Saida sun yi late daman jiki na ya Bani za a yi haka Wanda ya tsane Ka toh zai iya yin komai don ya ga bayan Ka, gudun haka ya sanya nace da Kai Zan maida ta gidan Ka don nasan Bashir ba Bari na zai yi na huta ba, Dariya Habeeb ya Sanya tare da fadin gaskia I salute you my friend kana da brain ni ban taba tunanin abunda ya Sanya ka dawo da ita nan ba,na dau kana gudun zama daga Kai sai ita ne gudun samun matsala,ya kare Yana dariya, Zan zage Ka Habeeb dan iskanci ko ni na kawo jaraba duniya AI na tausaya mata balle kai kan ka shaida ne ni bana bin Mata, Jiki da Jini aboki na an Dade ba a Hadu ba,ya kare Yana dariyar tsokana,tsaki Nameer ya ja sannan yace Ka ji da Shi dallah ni lemme shower in zo mu karasa magana domin yanda aka Fara zargi na din nan gwara as soon as possible in dauke ta mu bar garin nan gudun fada wa matsala,thank god yau Allah ya taimake ni,toh shike nan sai Ka iso Nima lemme pray da haka ya kashe wayar tashi, Kai Nameer ya girgiza da ya shiga dakin nashi ya ga komai Yana nan fes kamar ba bincike aka Shigo aka yi ba,Yan iska ashe mara sa kunyar karya ne, da haka ya kwabe ya shige wanka Yana mamakin me yayi wa Bashir ne da ya tsane Shi har haka, *********Police command Rai a matukar bace oga Jabiru ya Shigo cikin police command in,Kai tsaye office in Shi ya wuce tare da bada umurnin a Shigo mishi da doc Bashir, Jiki na rawa Bashir ya Shigo office in ganin yanda fuskan Jabiru ke a turbune nan take jikin Shi ya bashi ba a dace ba,cikin dauriya yace ranka ya Dade kun same ta, Mikewa Jabiru yayi sanann yace a gidan uwar Ka muka same ta,ni zaka bata wa lokaci Kai ya kare cike da tsawa, Nan take ya rude cike da rawar murya yace sorry yallabai kuskure aka samu,ba gidan doc Nameer nake son cewa ba, Da kallon mamaki yake bin Bashir in kafin yace toh gidan wa kake son cewa, Yauwa yallabai bayan dogon nazari da na kuma yi na gano Shi Sen da kanshi ya sace ta Dan kawai ya Sanya mu a damuwa ya kuma bata maka lokaci ya Sanya shi cewa mu ne muka dauke ta,Amman am very sure da za Ku je gidan Shi za Ku ganta,that man is very evil aswear to almighty God Yana samun pleasure a yayin da yake azabtar da wasu Kai ne Baka san Shi ba, Be Kai ga hade lips in Shi ba ya ji saukan Mari tassss,tsaban bacin Rai har idanun Jabiru yayi jawur, Cikin Ihu yace out of my office nonsense,na ga alama Kai ma brain in Ka ya Fara tabuwa daman an fada mun zaka ce Shi ne ya sace yar sa,Banda hauka taya babban mutum kamar Sen zai sace yar Shi ya daura muku Akan me me zai yi gaining in yayi haka, stupid an Jima ma cewa za Ka yi ita ce ta boye Kan ta ko kuma ni ne nan na sace ta na boye,and I promise you yau sai Ka sha bugun da tunda uwar Ka ta yafe Ka ba a taba maka irin Shi tunda Ka bata mun lokaci sai na fanshe a jikin Ka fice mun a office Wawa kawai ya kare har Yana kumfan Baki, Sim sim doc Bashir ya ja kafar Shi tare da barin office in Shi wlhy ya gaji ya gaji sosai da irin wannan bakar hukuban da suke ci a hannun wannan mugun Dan sandan da be son darajar bayin Allah ba(ni ko nace Kai kan Ka ba sanin darajar Kan Ka kayi ba,domin duk wanda zai je ya kwanta da matar wani ko yayi kokarin daukan ran wanni ko ya hofantar da lamuran iyalan Shi toh tabbas be san darajar Kan Shi ba balle har wani ya San darajar Shi), *******Doc Nameer Saida ya Bari Rana tayi sanyi sanna ya shirya cikin kananun Kaya tare da nufan gidan Habeeb bayan ya hado su tarkacen kayan Wasa da madaran Yara,sai ya siyo ice cream don ya san Nadeeya na so saidai be San ko za ta iya sha ba domin har yanzu jikin nata dai babu wani ci gaba,ko ruwa in Baka yi da gaske ba dawo maka da Shi take in Ka bata,tana nan kwance sai an daga sai an kwantar da tube Ake samun abinci yake shiga jikin ta,Shi ya Rasa wannan mutuwar jiki da ta samu na ba gyara babu dalili,duk wani necessary gwaje gwaje yayi ya gano babu wani matsala tattare da kashin ta ko jijiyan ta Banda brain in ta da ya tabu sakamakon aluran da aka yi ta Dura Mata,to sam ya kasa gane miye ke damun ta da ya haddasa Mata halin da take jiki, A nutse yake driving Yana sauraran wakar Bunna boy ft Ed Sheeran (for my hands),Yana bin wakan a hankali a haka har ya iso gidan Habeeb in yayi horn aka Bude masa gate ya shiga da motar Shi, A tsakar gida ya tarar da Habeeb suna Wasa da dan babyn Shi da ba wai ya gama koyan tafiya bane,sai abun ya bashi shaawa nan take ya ji Yana missing little Hanan in Shi,wannan matsalan Nadeeyar ne duk ta dauke mishi hankali kwana biyu be Kira ya ji lafiyar ta ba, Parking yayi tare da fitowa,gaisawa suka yi da Habeeb in sanann yace da gate man in Shi ya fito da kayan da ke cikin motar Nameer in ya Shigo da su parlor, Karban babyn yayi sannan suka shigo,na san ko na ce Ka zauna Ka sha ruwa ba yarda za Ka yi ba in ba Ka ga Nadeeya ba mu je suna jiki da Muhibba, Murmushi kawai Nameer yayi sanan suka nufi dakin tarar wa suka yi Muhibba na fesa wa Nadeeya turare alamu sun gwada wanka ta Gama Mata, Da kallo kawai Nameer yake bin ta ganin yanda take kwance tana bacci hankali kwance sai tayi masa kyau domin har simple kwalliya Muhibba ke Mata time to time a cewar ta mace ce AI don jinya ta Gama ta bara a Kula da ita ba, Babu abunda zai ce da Muhibba ko Habeeb saidai fatan Allah ya Sanya su Gama da duniya lafiya domin tabbas Yan uwan rufin asiri ne su, Tun Ranar da ya sanar musu Nadeeya na gurin Shi Muhibba ta dauke ta kamar yar uwa komai bata kyashin yi Mata,saisa at times Akan ce dadin Zama sai bare domin yanda take kula da ita ko uwar ta sai haka,bayi da bakin gode musu wlhy, Lah ya Nameer Ka zo ne ta Fadi tana murmushi, Shi din ma murmushin yayi sannan yace eh wlhy mommyn Fadeel ya dawainiya kuma,na gode sosai ubangiji ya Miki Albarka sanann ya biya ki da Aljannah, Murmushi tayi domin a rayuwa tana Jin dadin adduo'in nan da Nameer ke Mata kullum,tana matukar respecting in Shi don duk friends in Habeeb zata iya ce wa babu Wanda Jinin su ya zo daya kamar Nameer in kallon babban yaya take mishi,and ba kowa ne za Ka yi mishi abu yayi appreciating har ya San kayi masa ba,akwai dadi duk kankantar abunda mutun xai yi maka Ka gode Ka kuma nuna Jin dadin Ka,shima dai gaba ya samu karfin gwiwa, Ameen ya rabil Alameen Ka Shigo mutuniyar tayi bacci, Eh wlhy haka nake gani, ubangiji dai ya Baku ladan jinya,ita kuma Allah ya bata lafiya,Ameen duk suka amsa,sannan suka fito daga dakin, Nan parlor suka baje ta kawo musu abinci suka shiga ci suna hira irin nasu na abokai a nan ne yake sanar wa Habeeb Yana so in sha Allah tunda gobe Saturday babu aiki Yana ga gwara ya dauki Nadeeya ya tafi da ita Kaduna daman tunda ya zo be je ba, Nan take kuwa ran Habeeb ya Baci Akan meyasa zai ce haka,gani yake Yana takura su ko kuma su din sun gaza bara su iya Kula da ita ba, AA wlhy ko daya Ka fahimce ni ba daidai ba,gani nayi yanda aka Fara binciken nan toh ban san iya yanda zai tsaya ba gwara in dauke ta tayi nisa da garin nan gudun Kar in Sanya Ku a wata matsalar, Da kyar ya samu Habeeb in ya fahimce Shi be bar gidan ba sai dare bayan yace da Muhibba ta shirya ta da wuri don Allah don asubanci yake so suyi, Da haka ya koma gida,Saida ya kuma wanka sabida Yana yi na zafi kafin ya gabatar da sallahn Isha sannan ya dauki waya ya Kira Mama, Idar wan ta ke nan itama tana lazumi kiran nashi ya Shigo,ajiyar zuciya me karfi ta sauke domin yau Kusan kwana uku ba suyi magana ba duk hankalin ta ya tashi addua kawai take Allah ya Sanya Yana lafiya domin ko sun Kira basa samun Shi, Da sauri ta dauka tare da sallama,amsawa yayi sannan yace ina wuni Mama, Baba na ba zan amsa ba Ka ga yanda Ka daga mana hankali kuwa ina Ka shiga ne haba baba na,AI ko sako Ka turo in ma busy kake in dai san kana cikin koshi lafiya,ta kare kamar za ta sa kuka, Numfashi ya sauke sannan yace kiyi hakuri hajiya mama wlhy ana ta dan rikici ne a gurin aikin na mu, Subhanallahi ina fatan dai ba da Kai Ake rikicin ba dai ko, Dan dariya yayi sanna yace haba mama ni kan AI bana rikici da kowa ba da ni bane, Toh Alhamdulilah ina fatan kana lafiya sanan kuma kana cin abinci,ni wlhy duk hankali na ba a kwance yake da garin da Baka san kowa nan ba,ta kare tana jimami, Dan murmushi yayi sanann yace hajiya mama ke nan toh ki kwantar da hankalin ki in sha Allah gobe a Kaduna Zan kwana asubanci ma Zan yi da yardar Allah kafin 10 ina gida, breakfast in ki ma Zan ci, Cike da murna domin ita kanta tayi missing Dan nata tace da gaske kake Babana,Bani son zolaya fa, Shima dariyar yayi sanann yace da gaske nake mama gobe Zan zo ba ma ni kadai zan zo ba, Kai dawa ye ta tambaya,mama labarin da tsaho ki Bari sai na iso Zan Miki bayani za ki fi gane wa, Toh shike nan ubangiji ya kawo Ku lafiya Allah ya tsare hanya, Ameen thuma ameen Mama tah ina angel take, Ka ganta can ta gama fitina ta na dake ta na hurga ta gado tayi bacci, Haba mama nawa angel take da za a Mata dukan da har sai tai bacci ya kare kamar zai yi kuka, Gidan Ku Baba na yarinya tayi mun bar na bazan buge ta ba,Ka fita a idona da wannan kwalafucin da kake Akan yarinyar nan fa, Baki ya turo kamar karamin yaro sanan yace shike nan kiyi hakuri sai da safe, Dariya ta Sanya sannan tace au don nayi fada shine zaka kashe wayar taka ko, AA mama ba don haka bane fa,Allah ya shirye Ka Baba na da haka suka shiga hira irin ta " da uwa Wanda daga gani za Ka gane akwai tsantsan shakuwa da soyayya me karfi a tsakanin su,Saida suka yi Kusan 1 kafin suka yi sallama ya ya kwanta Yana Jin kamar ya janyo gobe tayi ya ganshi a gida,saidai wani gefen zuciyar Shi na tambayan Shi me zai ce da mama in ta ganshi da Nadeeya, inda ya samu kwanciyar hankali ya San Mahaifiyar tashi akwai saukin Hali da fahimta he is sure za ta fahimce Shi,da haka ya kwanta bacci me dadi ya dauke Shi, Ko da ya tashi sallan asuba be koma bacci ba,kayan Shi ya hada Wanda ya san zai bukata Saida ya Gama sannan ya fada wanka,bayan ya fito ne ya shiga Kitchen cikin sauri yayi frying egg da plantain sannan ya hada tea ya fito,a nutse yake cin abinci don in yace zai Bari sai ya Isa ya ci abinci zai jigata,domin daga Bauchi zuwa Kaduna ba karamin tafiya bane, Around 6:30 ya gama hada koman Shi ya zuba a mota,Saida ya rufe ko ina na gidan sannan ya fito ya shiga motar nashi, Saida ya biya inda yake Siyan masa ya siyo don yayi alkwarin Kai wa mama,sannan ya biya Jifatu siyayya yayi musu sosai wa mama Nadeeya da kuma angel inshi sannan ya dau hanyar gidan Habeeb, Da isar Shi kuwa ya tarar da Muhibba ta gama shirya Nadeeya cikin dogon Riga,dauko ta yayi zai shimfida Leda tace da Shi AI ta Sanya Mata pampers Kar ya damu har su Isa bara ta yi komai ba don ba wani ruwa sosai ta bata ba, Godia sosai yayi musu inda a karshe ya dauki kyautar 100k ya baiwa Muhibba sam taki karba Akan ita fa ya wuci haka don Allah ta kula da Nadeeya,da kyar ta karba bayan yace da ita AI ance gaida me gaida Ka ko bare amsa ba,godia tayi mishi sosai don har da kwallan ta,sabida ba karya ta Fara shakuwa da Nadeeyar duk da ba magana take ba, Sallama suka yi da Habeeb bayan ya sanar da Shi in sha Allah bare wuce week in nan ba zai dawo gudun Kar a zarge Shi,shima ya kuma mishi godia sannan ya shige motar sa,adduar Allah ya kiyaye hanya suka yi mishi tare da daga mishi hannu har ya fice daga gidan, Cikin kwanciyar hankali ya dauki hanya Saisa ya zabi tafiyar samako domin gujewa idon sani KO kuma road safety suke ne ko yan sanda ๐Ÿคฃ,da haka ya dauki hanya Yana tafe Yana duba halin da yar mutane ke ciki,sai muce Doc Nameer Allah ya kiyaye hanya, *********Sen Rilwanu Bugun kofar dakin Shi ne ya farkar da Shi daga baccin safen da yake yi,da kyar ya samu ya tashi ya nufi kofar domin ya sha maganin bacci jiya kafin ya kwantan, Bude kofar ya ga Falmata ce durgusawa tai tare da gaishe shi,da hannu ya amsa ta,a ladabce tace da Shi ranka ya Dade kayi bakuwa, Bakuwa ya maimata da mamaki,eh Waye shine abunda ya tambaye ta, Yallabai Hajiya ce,idanu ya zaro yace hajiya fa kika ce eh tace da Shi a nutse,be koma cewa komai ba ya fada daki cikin sauri ya wanke Baki tare da wanke fuska ya xura milk jallabiya tare da feshe turaruka ya dauko carbi yana dan ja a nutse ya fito da murmushi Kan fuskar Shi, A zaune ya tarar da yar dattijiwar matar da ke tsananin kama da Shi,sanye da hijabin ta har kasa tana jan nata carbin, A gaban ta ya zube tare da fadin sannu da zuwa Hajiya Ashe kina tafe, Kallon Shi tayi tsaf daga Sama har kasa saidai sam yaki barin su hada idanu da ita, Kai ta girgiza sannan tace Abul bait wai me ke damun Ka ne, Cikin saukar da murya yace hajiya magauta sun sako ni gaba na rasa yanda zanyi, Anya kuwa Abul bait Anya,sai kuma ta girgiza Kai,tare da gyara zama, Mikewa yayi tare da fadin Bari na sanya a kawo Miki abinci na san Baki karya ba kika taho, Dawo Ka zauan ba abinci ne gaba na ba,magana nake son muyi ta fahimtar juna, Ba musu kuwa ya dawo tare da zaunawa Kusa da ita,duk iskancin Sen Yana mugun shakka da tsoron Mahaifiyar shi (Hajiya Rakiba), Abul bait,naaam hajiya ya amsa ta,na tambaye Ka miye damuwar Ka Amman kace Dani magauta sun Saka Ka gaba,na Rasa gane wani irin abu ke bibiyar Ka Ka duba fa ace tun mutuwar Mahaifiyar Nadeeya ace har yau shekaru Kusan 25 baka kuma aure ba, In anyi magana kace mun komai yar lokaci ne,sannan ace yarinyar nan jarabawa ta fada Mata ni Banda nasani ya and kace da ni babu abunda kake boye mun, Ina yawan mugayen mafarkai da Kai Wanda na Rasa gane dalilin haka,Ka ji tsoron Allah Ka fada mun in har akwai abunda kake boye wa duk duniyar nan Baka da kamata ni ce uwar Ka ni ce uban Ka,don haka Ka sanar da ni miye kake boye mun, Kan Shi ya kwantar a cinyar ta sai ya Sanya kuka,hajiya mutane sun Saka ni gaba kaina aka Fara siyasa an samu wasu mugayen da suka jefi yarinyar nan hauka tuburan tayi hajiya bata komai sai auna mun zagi, Kallon Shi kawai Hajiya ke yi kafin tace Ka tabbatar babu abunda kayi wa yarinyar nan Baka zalunce ta ta ko ina ba, Dagowa yayi sanann yace haba hajiya ke fa kin fi kowa sanin halina, Yo wani sanin Hali Dan mutun da Ka Haifa ne Baka Haifi halin Shi ba,AI kana iya canzawa a KO wani lokaci amamn da mamamki ace Nadeeya ke maka irin wannan diban albarkan da na gani a video, Wlhy hajiya sa hannun magauta ne, Kayi mun shiru in sanya hannu ne Miya Sanya Baka kawo ta gurina ba sanin Kan Ka ne Ubana babban malami ne kafin ya mutu duk garin Azare har nan cikin garin Bauchi babu Wanda be san da Zaman Shi ba, Kawunan Ka wani irin ayoyi da adduo'in karya sanmu ne Basu San Shi ba Amman Ka dauke ta Ka Mika ta asibiti,tunda ga rannan nasan tabbas akwai wani Abu a kasa KO ba haka bane,ta kare tana tsare Shi da idanu don son karantar Shi, Idanu yayi saurin saukewa domin wani yarrr yake ji a duk lokacin da ta tsare Shi da idanu har rawa jikin Shi ke yi at times, Cikin kwantar da Kai yace wlhy hajiya Bani son daga Miki hankali ne na ga ba isashen lafiya gare ki ba,and Kabiru ne ya bada shawaran a Kai ta asibitin domin likita yace kwakwalwan ta ya dan tabu dole akwai bukatan ayi na asibitin kafin a yi na gidan,Jira nake in an Gama daman sai na kawo ta gurin ki,sai kuma aka yi rashin dace an bita can asibitin an sace ta yanzu haka case in na gurin Yan sanda suna bincike akai, A Ka sace ta salati hajiya ta Sanya tare da tafa hannuwa wanann masifa har ina,Anya Abul bait ba wani Sabon Allah kake yi ba shine ya tashi kama Ka ta wanann hanyan, Cikin sauri yace wlhy hajiya Bana aika ta komai ina sallah ina azumi ina zakka ina sadaka ina kyauta,ina sauke farali sannan Ina kyautata muamala ta da mutane da makota na uwa uba kuma ina Miki biyayya ke dai kawai in jarabawa ta samu mutum, Dan shiru hajiya tayi sannan tace ina fatan dai kana gujewa haramun domin cin haram kadai Kan iya wargaxa ma lamuran rayuwar Ka, Da sauri yace Allah ya mana tsari da haram hajiya Bana cin ta Bana kusantar ta kuma Bana kaunar me taammali da haramun, Shiru suka Dan yi Basu ce komai ba sannan can tace ko dai za Ka hakura da neman wannan takaran ne haka kawai Bani da good feelings Akan takaran nan naka Abul bait,Ka dube Ka duk Ka Rasa nutsuwa yarinyar nan ba ma mu san halin da take ciki ba duk Akan neman duniya wani irin arziki da dadi ne Allah be azurta Ka da Shi ba, Kirjin Shi ne ya buga,a taya zai ma Fara Aje takaran nan bayan abubuwa da yawa da ya Rasa sabida Shi,AI ina bare ma taba yuwa ba, Kayi shiru ina yi maka magana, Zama ya gyara sanann yace hajiya Nima da zan so ajewar tunda hankalin ki be kwanta da Shi ba,Amman kuma mutane zaki duba gabada hopes in su na ga Allah na gare ni don alummah ta nake son yi,domin kawo cigaba Amman in Baki so zan hakura, Dan tsaki tayi sanann tace ubangiji ya shige mana gaba Ka dai dage da azkar yanda kace an sako Ka gaban nan Nima Zan na taya Ka,sannan Ka ji tsoron Allah a duk yanda kake in kayi Abu kana tunanin bazan sani ba Allah zai sani kuma Yana gani domin Shi ya yayi mu duka,Allah ya gani na Baka tarbiya da ilimi daidai iyawa ta, Haka ne hajiya ina Kan ji wlhy ayi ta taya mu da addua in sha Allah komai zai zo ya wuce,maganar Nadeeya kuma yau Zan Kara Sanya yan sanda suna checking duk wani shige da ficen motoci sannan Zan Sanya ayi sanarwa duk Wanda ya same ta Zan bashi kyautan makudan kudade,da yardar Odugwu nan take zaki ga an same ta, Idanu ta watsa mishi tare da fadan Waye wani Odugwu,Abul bait da hankalin Ka kuwa,wani irin sakarci ne hka, Da sauri yace hajiya Odugwu Yana nufin shugaba ne ina nufin Allah ke nan, Bana son iskanci fa wani hauka ke nan Allah za Ka wani kira Shi Odugwu wlhy ka na kiyaye halcen Ka Kar Ka je fa kanka a wuta da kanka,ta kare cike da fada,hakuri ya bata sannan ta mike tace ni kam Zan koma ubangiji ya shige mana gaba, Haba hajiya ko ruwa fa Baki sha ba,ina azumi Abul bait daman Jin Shirun ne ya sanya ni cewa Zan zo tunda Kai ka gagara zuwa, Nan ma hakuri ya bata sannan yace da ita Yana zuwa,daki ya nufa kudi ya Ibo masu yawa sannan ya fito yayi daidai da fitowan Afzaal da gajeran wando, Kai ko ba Afzaal ba,eh hajiya ni din ne Ina kwana ya kare Yana Sosa keya, Abul bait uban me yaron nan ke yi cikin gidan nan na gani Yana da gida KO ba haka bane, Eh hajiya daman sabida laluran da ta sami Nadeeya ne ya sanya Shi dawowa nan domin Zama Shi kadai in babu daadi, Harara hajiya ta jefa mishi sannan tace yaron goye ne Shi,yanzu hka ya dace inda yake yawo daga Shi sai guntun wando,wannan AI iskanci ne,nan ko ta hau Sababi, Shi dai Sen hakuri ya yi ta bata da kyar ya samu ya lalabata tayi shiru suka fito tana kuma mishi nisiha Kan ya ji tsoron Allah a duk abunda ya Sanya gaba,sannan in ya samu lokaci ya ci ya zo ya gaida kawunnan Shi tunda Shi komai sai an fada ma ka, Hakuri ya kuma bata tare da Mika Mata kudadan hajiya gashi ayi tsaraba tunda kin ki kwana, Mota ta shige sannan tace rike kudin ma Abul bait Wanda Ka aiko wancan satin ma ko ficika ban taba ba,ni dai ina kuma maka nasiha da Ka ji tsoron Allah a duk inda kake,murtala ja Mota mu tafi,a haka suka fice daga gidan aka bar Sen tsaye da kudi a hannu duk jiki a sanyaye,toh ko dai hajiya ta san abunda yake aikata wa ne,in ko haka ne da ya shiga uku,wani zuciyar ce tace da ta sani hajiya bara ta iya shiru ba sai ta tare Ka da maganar,sai dai in ta Fara zargi na,AI ko ya Zama dole ya canza taku domin ko giyar wake yake sha bare so hajiya ko wani ya San asirin Shi ba,ajiyar zuciya ya sauke tare da komawa cikin gidan. Asaalamu alaikum Ina fatan anyi jumma lfy ubangiji ya kara mana lafiya da Zaman Lafiya Allah kuma ya amsa mana ibadun mu da adduo'in mu๐Ÿ™๐Ÿป [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜” UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ........ My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin San ba karanta book ina da commenting bane zai kawo ki toh kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba, haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah ๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ......... Page twenty-two ********* Doc Nameer******* Tsaye yake a bakin kofar dakin Mama, Yana me jiran umarnin shigowar Shi, Shigo Babana mun Gama wankan tace da Shi,da dan karfi yanda zai ji abunda tace, Cikin sallama ya Shigo cikin dakin,a kwance ya tarar da Nadeeya sanye cikin sky blue dogon Riga ban da kamshi babu abunda take yi,idanu ya lumshe yana me kara gode wa Allah da ya bashi Mama a matsayin Mahaifiyar shi, A kujeran dakin ya ja ya zauan sannan ya ce sannan da kokari Mama ta ubangiji ya Saka miki da gidan Aljannah, Murmushi tayi sanann tace Ameen Baba na Bana fatan yanda kake kyautata mun kake tattalin rayuwa ta da farinciki na,a ce ka nuna abunda kake so na Gaza yi maka,ko na Gaza Kula maka da shi,ta kare tana murmushi, Shima murmushin yayi domin sam be gane inda zancen nata ya nufa ba, Zama ta gyara sanann tace ni kam Babana jikin yarinyar nan Anya kuwa ma tsaya na asibiti kawai, Shi din ma Zama ya gyara sanann yace wlhy mama Nima abun yana Bani mamaki,yanda kika ce tana yawan firgici cikin dare kamar me yin miyakun mafarkai, Haka kawai fa Mama na gan ta ranar tsaka ta Zama haka,ko yatsa bata iya moving,ya kare cike da jimami, Numfashi mama ta sauke sannan tace wannan lamari nata da daure Kai Babana babu komai Amman muyi ta fada wa Allah in sha Allah zai amsa ya bata lafiya, Ameen ya rabil Alameen mama tah Bari na je 44 gurin Mujaheed tun shekaran jiya yake ta Kira nasan ya na can yana Mita na dawo ban neme Shi ba,kuna bukatar wani Abu ne, Murmushi tayi tana me matsa kafan Nadeeya da ke bacci tace ubangiji ya kiyaye ya tsare Babana Bama bukatar komai,saidai in kana dawowa Ka biya ta Islamic chemist Ka karbo mana pure honey da man Habbatus Sauda,na gurina ya kare, In sha Allah zan taho da su iya kan Shi kuke bukata?? Eh iya kan Shi ne Shi din ma ita nake baiwa tunda Manzon Allah da kanshi yace kuna shan Habbatus Sauda da Zuma domin yana magance ko wace irin cuta da ke jikin Ku banda mutuwa, Haka ne kam Mama ubangiji ya Kara mana lafiya da nisan kwana me amfani Bari na je sai na dawo, Toh ubangiji ya tsare,da haka ya samu ya fito daga dakin da kyar ya samu Zaliha ta Raba Shi da Hanan domin rikici ta Sanya Kan sai ta bishi, Kai tsaye 44 ya nufa inda Saida ya tsaya aka gaggaisa da mutanan arziki sanann ya nufi office in Mujaheed, A Bude ya samu kofar so shiga yayi Kai tsaye tare da sallama inda ya samu babu kowa a office in,guri ya samu ya zauna Yana me kare wa office in kallo, Rayuwa ke nan kamar be yi rayuwa a hospital in nan ba,shigowar Mujaheed ne ya katse mishi tunanin da ya dan fada, Mikewa yayi fuskan Shi cike da annuri Ashe dai nayi missing in Ka my gee ya kare Yana Mika mishi hannu, Harara Mujaheed ya watsa mishi kamar wani mace kafin yace dallah Malam zo Ka fice mun a office, AI wlhy Nameer Ka gwada mun matsayi na ace sabida Allah yau kusan week da zuwan Ka Amman sai yau muke haduwa,haba daga zuwa Bauchi shine har Ka Hadu da abokan da suka Fini ko??toh wlhy Ka sani Shi dai tuwo sunan Shi tuwo ba a canza masa suna ni din nan dai nine Aminin Ka na tun yarinta duk Wanda za kayi Baya na suke eheee, Nameer kasa rike dariyar da yayi ganin inda Majaheed ya rufe Ido yake surfa mishi masifa, Nan ko Mujaheed ya kuma kulewa,harara ya kuma buga mishi sannan ya juya,ni baran bar maka office in bare yu Ka Sanya ni gaba kana mun dariya ba instead Ka Bani hakuri kayi mun laifi,amman Ka zauna kana mun dariya kamar Ka samu mahaukaci, Kasa kasa Nameer yace miye maraba Likitan mahaukata kam AI shima ya zautun, Dadin abun kaima zautatcen ne Ashe ya kare tare da bugun kafadun Shi,nan duk suka kwashe da dariya, Zama suka yi bayan sun yi musabaha sannan aka shiga gaisawa, Mutumina gaskia Bauchi ta karbe Ka fa,Ka ga yanda kayi fresh Ka Kara kyau kuwa har Dan kiba fa na ga Ka Kara mun, Kallon kanshi Nameer yayi sanann yace a hakan wai,domin Shi a tunanin Shi ma Rama yayi ko don pressure irin ta Sen da ya sanya musu, Eh wlhy Masha Allah kayi kyan gani kamar wani Sabon ango ko dai ko dai,kayi gamo da kyakkyawar Diya a garin Bauchi dake Kula mana da Kai ne,daman matan Bauchi an canfa kyawawa ne akwai su kuwa da iya tatali da iya Kula da saurayi ko miji, Dariya Nameer ya Sanya sannan yace AI ko sanin Hali ya Sanya na taho maka da number in wata me kawo mana tallan masa a hospital,ganin yanda kake ta son karawa Maman Afreen kanwa, Allah ya sauwaka wlhh Ka ma cuce ni AI ko class ina ya zuba duk aji na na kare da me kawo tallan masa ya kare Yana checking Kan Shi in, Dariya Nameer ya sanya sanna yace yanzu fa Ka Gama cewa matan Bauchi akwai iya Kula da rike Maza,Kai ina ruwan Ka da kyan ta in da za ta Kula da Kai AI lafiya Lau, Be Kai ga bashi Amsa ba wayan Nameer tayi Kara,ganin Habeeb ke Kira Saida kunya ya kama Shi don zai iya cewa tunda ya dawo be Kira Shi ko sau daya ba sai Shi Habeeb in ke ta Kira, Dauka yayi tare da sallama,amsawa Habeeb in yayi sanan yace wlhy Doc Handsome zumuncin Ka kadan ne,AI ko ba dan komai ba mana magana akai akai mu samu mu ji ya jikin Nadeeya domin Muhibba sam bata da kwanciyar hankali kullum tambayar ta ya me jiki, Murmushi Nameer yayi sannan yace don Allah kayi hakuri ban kyauta ba Kan wlhy abubuwa ne suka hade mun Amman a baiwa sister na hakuri a kuma ce da ita jiki Yana ta kyau Alhamdulilah, Toh Masha Allah ya mutan gidan duka su mama hope dai duk kuna lafiya ko, Wlhh lafiya kalau Alhamdulilah ya baby boy,da kuma aiki, Dan dariya ya Sanya sannan yace ba Ka gudu Ka bar Baya da Kura ba,Kai Ka ga yanda garin Bauchi ya burkice da jamian tsaro ,ko wani lugun da sako suna gurin bincike Ake na inalilahi, Dan dariya Nameer ya sanya sanan yace su yi ta yi,kashe kudi ne wlhy be ishe su ba kila da kudin ma aje Shi yayi campaign in Shi da Shi,domin wanann Jabiru kana ganin Shi idon Shi idon kudi,karba zai yi ta yi gurin Sen, Kai dai Bari AI yanzu kam abun ma ya bar hannun Shi sun shiga court na ji tun last Monday yanzu haka an dage shariar suna gidan yari an bada tsaron su sai nan da 2 weeks za a koma a cigaba da case,Zan so mu samu mu je mu ga idanun mutanan Ka ya kare da dariyar mugunta, Allah ya shirya ka Habeeb wlhy,yanzu kama sun ne abun dariya ko me, AI dole nayi Dariya Nameer duk Wanda ya sai kwando daman ya san za ta zubda mishi ruwa,ba dai su son abun duniya da kwandayi ba wlhy kadan ma suka gani,ni AI Zan so a yanke wa ko wannan su hukuncin ko da 3 years in prison ne with hard labour kila su shige hankalin su in sun fito, Dariya Nameer ya sanya sannan yace amman wlhy Kai kam akwai mugu , Ba wani mugunta abunda Ka shuka Shi zaka girba in ji bahaushe,yanzu dai yaushe za Ka dawo in ban da abun court in nan Bashir is busy AI da yanzu ayoyin zargi sun dawo kanka, Hmmm haka ne kam yanzu dai ina gurin Mujaheed ne Bari na koma gida I will call u, Okay Ka gaida Mujaheed in da haka suka yi sallama ya kashe wayar Shi,abun har yanzu dariya yake bashi,irin wannan Ka amshi laifin da ba Ka ma san a yaushe Ka aikata Shi ba,Amman kana paying price haka, (One thing in life shine Ka ji tsoron Allah Ka ji tsoron shiga ko daukan hakkin bayin Allah, mugunta kyeta son zuciya ubangiji Ka Raba mu da Shi,zalunci babbar musiba ce,Ka zalunci Dan uwan ka ya daga hannu yace be yafe ba Allah ya Isa and Ka dauki hakan ba a bakin komai ba,Kai kasan isan Allah kuwa,Ka kuwa san ta inda wanann Allah ya isan zai fada maka kuwa??kila Kan dukiyar Ka kila lafiyar Ka,kila kan ranka babu ta inda bata faduwa, saisa no matter how try your possible best Ka ga Ka zauna Ka kuma rabu da kowa lafiya,Manzon Allah SAW yace Ka zo da ko wani irin laifi ranar kiyama yayi alkwarin tsaya maka Amman Banda shirka,Sata,da kuma laifi tsakanin bawa da bawa,domin wannan tsakanin Ka da Dan uwan ka ne in ya ji ya yafe fine and good, ubangiji Ka Raba mu da zulantar Kan mu da Yan uwan mu,ya kuma Sanya mu fi karfin zukatan mu domin da Ka cutar gwara Kai an cutar da Kai,Allah kayi mana me kyau duniya da kiyama๐Ÿคฒ๐Ÿป) Kashe wayar Shi ke nan ya mike tare da zuba su a aljuhu ganin fuskan Aminin nashi cike yake da tambayoyi Wanda he is not ready ya amsa su, Amman Sarai kasan dai ina son muyi magana Ka wani mike, Agogon hannun Shi ya kalla sannan yace sorry friend I have to go mama ta aike ni but don't worry zuwa gobe in sha Allah zan dawo mayi duk maganar da kake son yi,bye bye a gaida Afreen da haka ya fice daga office in ya bar Mujaheed Baki Bude brain in Shi cike fal da tambayoyi Wanda babu me bashi amsoshin su sai Nameer in, Nameer ko,be tsaya ko ina ba sai Islamic chemist in Zuma da Habbatus Sauda in ya siyo da yawa ya biya aka bashi sanann ya biya ya siyo musu ice cream kafin ya dawo gida, Mama ya tarar ta Sanya Khadija a gaba tana yi Mata fada Wanda harda zagi,abunda zai ce rabon da ya ji har ya mance, Da sallama ya Shigo dakin tare da neman guri Kusa da ita ya zauna tare da riko hannayen ta Mama me ya faru waya bata Miki Rai har haka, Cike da fushi take fadin haba Babana yanzu ace kamar khadija ce za ta zamo me bakin Hali ta fita zakka cikin yara na,tun ranar da Ka kawo yarinyar nan cikin gidan nan Naga alaman ran ta be so ba,sai wasu irin halaye take yi ta matsa mun lalle sai na Fadi Mata daga ina take,ba dama in ce ta taya ni Kula da yarinyar nan sai tayi Mata yar ko oho ko kuma ta hau Mita, Yanzu Dan ubanta ita ta fi karfin Allah ya Mata irin wannan jarabawar ce ko ma fiye da haka,and ya Zama dole sai Ka san mutum a rayuwa kafin Ka ji tausayin Shi ko Ka taimaka mishi, Gida dai nawa ne and Babana Dana ne na ciki na KO Kuda KO kuliya kana da right in kawowa Ka aje cikin gidan nan tunda na mahaifin Ka ne,Akan me za ta Saka yarinya a gaba toh an ki sanar da ke daga ina take akwai abunda zai Kara Miki ne in kin sani?? Ya Isa Mama don Allah kiyi hakuri dole ta so sani Kin san duniyar yanzu ba tsaro,na san tana yin hakan ne for our well being, Wani well being Kai mance mugun hali irin na khadija kake wlhh, toh ni dai ka fada Mata babu ruwan ta,in har bara ta iya taya ni Kula da Amanar da Ka Bani ba toh let her stay away Kar na kuma Jin tayi wasu kananun maganganu in ba haka ba ranta zai yi munanniyar Baci,ta kare tana mikewa, Numfashi Nameer ya sauke domin Sarai ya san halin kanwar tashi za ta aikata fiye da hakan ma in dai Khadija ce, Nan ya shiga yi Mata nasiha tare da Mata bayanin taimakon Nadeeya yayi,ta dai ji amamn ita har yanzu so take ta san miye dalilin da zai Sanya Shi dauko ta all the way from wani gari zuwa Kd, 2 weeks later******* Yau ta kama Monday ko wani maaikaci haba haba yake ya samu ya Isa gurin aikin Shi da wuri, Nameer ya dawo bakin aikin Shi tun bayan kwana uku da suka yi waya da Habeeb inda ya bar Nadeeya can Kd karkashin kulawar Mama, khadija ma ta koma gidan ta domin Allah yayi ta da wata irin zuciyar banza Sam bara Ka ce yarinyar mama bace,gidan ya rage daga mama sai Zaliha sai little,Saida ya bar musu duk wani abunda za su bukata kafin ya taho ya cigaba da aikin Shi cike da kwanciyar hankali like babu abunda ya sani, Babu yanda Habeeb be yi ba Kan su shirya su tafi court ganin yanda za a karasa wai ance zuwa da Kai ya fi sako amman sam Doc Nameer yace Yana da abun yi da ya fi wannan mahimmanci Shi dai ya je in ya dawo ya bashi labari, Da haka ko Doc Habeeb ya shirya ya tafi high court, Kasancewar rashin zuwan alkali da wuri Shi ya dan yi delaying in su domin har an taho da su doc Bashir,an Shigo da su cikin court room, Dariya ce ta kusa subucewa Doc Habeeb yayin da yayi arba da doc Bashir da Kareematu,yanda kasan an babbaka gallon a fuskan su,wani irin Baki muni da kwanjamewar da suka yi,Kar Zaituna ta samu labari daman can ba auki gare ta ba, Shigowar alkali ne ya daidai ta surutu da hayaniyar da ke cikin court in duk aka Mike domin nuna girma wa alkali inda saida ya zauna sanann kowa ya nemi gurun Zaman Shi,nan ko aka shiga karanto cases har aka zo Kan su doc Bashir, Nan aka Kara fiddo su inda aka nemi lawyern me Kara da Wanda Ake Kara su fito, Ba sai na ja Ku da dogon surutu ba nan dai aka shiga gabatar da shariar su inda sam su doc Bashir sun ki karba laifin su acewar su babu Abunda suka yi, Asaalamu alaikum Ina fatan kuna lafiya Ayi mun afuwa 2 days in nan ayuka ne suka Dan mun yawa,GA ciwon Kai da ya sako ni gaba ๐Ÿ™๐Ÿป, Na so in yi ya fi haka amman Allah be so ba,so bare with me pls In sha Allah sai zuwa gobe in me kowa me komai ya so, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi ๐Ÿ™๐Ÿป [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ...... My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin San ba karanta book ina da comment bane zai kawo ki toh yi Zaman ki don Allah ba sai kinyi joining ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah ๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 Alhamdulilah ya rabil Alameen ๐Ÿคฒ๐Ÿปโค๏ธAllah na gode da Ka nuna mun zagayo war haihuwa ta ina me Rai da lafiya, Happy birthday to my humble self ubangiji Ka mun albarka ni da zuriah tah,Allah Ka kare ni daga dukkan sharri, sannan ya Karo mun shekaru masu Albarka ๐Ÿคฒ๐Ÿป,I am a year older today ,y"all should say a prayer for me da bakunan Ku masu Albarka ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ ......... Page thirty_one ********** Tafiyar hours ne suka iso da doc Nameer cikin garin Kaduna,a matukar gajiye ya dauki hanyar gidan hajiya, Numfashi ya Shaka sai ya ji wani irin sanyi a ranshi komai dadin wani gari garin Ku ya fi,ji yake kamar be da wani sauran damuwa cikin duniyar nan,a nutse yake driving bayi da burin da ya wuce ya ganshi rungume da little in Shi, Da haka ya karaso gidan yayi horn aka Bude mishi gate,Wanda be sanar da hajiya ya iso ba,ganin motar kanwar Shi Khadija ne ya bashi mamaki toh yaushe ta zo jiya suka yi waya da hajiya har ya kashe bata yi Mai tadin khadija ta zo ba,Baki ya tabe sannan yayi parking tare da fitowa, Sai a lokacin ya ji zuciyar Shi ta Fara bugawa be gane yayi hauka ba sai yanzu,toh me zai Fara ce da Mama game da Nadeeya Akan miya sa ma ya dauko ta ba tare da yayi shawara da uwar Shi ba abunda tun Yana karami be taba yi ba shine yanke hukunci ba tare da ya sanar da mama ba,duk abunda zai yi sai ta sani ta bashi kuma go ahead,toh ko ya fice ya kaita hotel ne wani xuciyar ta Fadi mishi, Da sauri ya girgiza Kai tare da aro jarumta kawai ya fito tare da rufe motar ya nufi cikin gidan,fuskar Shi dauke da murmushi, Bakin Shi dauke da sallama ya shiga parlor in hajiyar, Da gudu Hanaan ta yo inda yake tana dariya tare da Bude hannaye tana Fadi tana tashi duk a zumman oyayo, Fuskar Shi dauke da murmushi domin ganin ta kawai ya Sanya Shi farin ciki,be dauka hka yayi missing in tilon diyar ta Shi ba sai da ya rungume ta a kirjin Shi, Cikin gwarance tace papa,tana dariya tare da tsalle a jikin shi, Kanta da ya sha kitso ya shafo tare da amsa ta da ya aka yi my angel,kallon Shi take kamar tana fahimtar abunda yake Fadi, Ah Babana har Ka iso,mama tace tana murmushi,har ga Allah tana tsananin Jin kaunar Dan nata Nameer a ranta,yaron akwai Shiga Rai and tana matukar tausayin Shi,ko don Rashin matar Shi da yayi, Aje Hanan yayi Wanda take kokarin Sanya mishi kuka, Ka ji yar nema da can da be nan ya kike yi don neman ta yau shine za ki mana kuka,Maza yi mun shiru, Kai kawai ya girgiza don in yace zai yi magana mama haushin Shi za ta ji,an wuni lafiya mama ta, Lafiya kalau Babana Ka iso lafiya,ya hanya,ya kuma aiki, Wlhy Alhamdulilah mama na same Ku lafiya,wlhy duk Alhamdulilah tashi mu shiga Khadija ma na ciki dazu da safe suka zo, Mikewa yayi tare da riko yar hannun angel suka karasa shiga cikin parlor, Kujera ya samu ya zauna tare da sauke ajiyar zuciya wato ba karamin gajiya ya kwaso ba, Daddyn Hanaan Ashe da rabon mu Hadu,khadija ta Fadi tare da fitowa daga dakin hajiya, Juyowa yayi fuskan Shi da murmushi yace ah mutanan Abuja yaushe a gari,wlhy yaya dazu muka zo ya aje ni ya koma,ina ta missing in Ku ne nace Bari dai na leko, Murmushi yayi sannan yace toh sannnu da zuwa ina baby,bacci tace da Shi daga haka be kuma ce Mata komai ba,ita din ma haka ta juya tare da shigewa daki, Ruwa da lemo yar aiki mama ta Sanya ta kawo mishi, sanna ta kawo mishi tuwon shinkafa miyar taushe ta sha Naman rago kifi da kayan Hadi, Murmushi yayi Yana Kara Jin dadin samun mahaifiya irin maman Shi, Fitowa tayi ta ga ko warmers in be Bude ba,kallon Shi tayi da mamaki bayan ta zauna sannan tace Baba na lafiya kuwa, A hankali ya dago tare da cewa me kika gani mama,yo gani nai AI Baka taba komai ba,Kai da Ka Ibo gajiya AI Ka samu Ka ci Ka koshi,ko dai sai Ka watsa ruwa ne gajiyar ta fi sakin Ka, Ni ban ma ga bakon da kace da ni za Ku zo tare ba,ko dai ya fasa biyo Ka ne,domin har na sanya an gyara mishi dakin Baki, Sai a lokacin ya tuna da ya rufe yar mutane a mota ita kadai,da hanzari ya mike tare da kokarin yin waje, Hannun Shi mama ta riko sannan ta janyo Shi ya koma ya zauna,idanu ta tsare Shi da su,Kai Baba na lafiya kake kuwa?? Shiru yayi domin har ga Allah be ma san ta inda zai Fara yi Mata bayani ba,be san ta ya za ta dauki maganar ba, Kayi shiru ina maka magana,da alamu dai akwai abunda kake son fada Amman Ka kasa,yaushe muka Fara boye boye tsakanin mu Baba na wani abun ne ya faru na kalli gaba daya Baka da kuzari, Jarumta ya aro tare da riko hannaye ta cikin taushin murya yace hajiya mama nayi Miki laifi ki ya yafe ni sabida Allah, Kallon Shi ta dan yi na mintuna kafin ta nisa tace me kuma Ka aikata mun da har kake neman yafiya ta, Mikewa yayi tare da saukowa ya zauna Kusa da kafafun ta kamar wani yaro karami tare da kama hannun ta, Cikin sanyi murya yace mama ban ma san ta ina zan Fara Miki Baya ni ba,saidai ya Zama dole in sanar da ke domin Bani da Wanda ya wuce mun ke,you are the only one da nake da,and I don't know taya za ki dauki maganar I don't even know ko abunda nayi daidai ne ya dace ko be dace ba,but trust me mama ta wlhy I did it with pure intentions babu komai a Raina sai tausayi da kika koyar mun tun ina yaro, Ita dai mama kallon Shi kawai take Kan ta duk ya kulle,don har ga Allah bata gane inda kalaman nashi ke nufa, Cikin sanyin murya ya kwashe labarin Shi da Nadeeya from A to Z be rage komai ba sai inda ta lashe mishi kumatu๐Ÿ˜‚ ya sanar wa mama,Yana Jin zuciyar Shi na bugawa domin a rayuwa babu abunda ya tsana kamar bacin ran Mahaifiyar shi(Yan uwa mu ji tsoron Allah mu kyautata wa iyayen mu iya iya war mu,domin suna silan duk abunda muka Zama a rayuwar mu iyaye ba abun Wasa bane,mu guji Saba musu ko Sanya su a kunci,domin Allah da kanshi yace yardar Shi na tare da yardar iyaye hka zalika fushin Shi na tare da fushin iyaye,duk wacce ta, ta taso ta samu iyayen ta biyu a raye to wlhy key in shiga Aljannah Inta na gurin su haka ma na wutar ta in tai musu biyayya musamman ma uwa toh ta samu rabo ta shige ta in ta Saba musu ubangiji ya kyauta wutar ta na nan in har bata tuba ba, ubangiji ya kare mu,ya kuma ba mu iko da juriyar kyautata wa iyayen mu har karshen rayuwar mu,Wanda iyayen su suka Riga mu gidan gaskia ubangiji ya Sanya sun tafi a saa,Wanda kuma Nasu babu lafiya ubangiji ya Basu lafiya ya kuma Yaye wahala,mu da namu suke a raye Allah ya Kara mana hakuri da juriyar kyautata musu๐Ÿคฒ๐Ÿป), Mikewar da hajiya tayi bata ce komai bane ya Sanya duk jikin doc Nameer yin sanyi,daman ya san za a yi haka,bayi da choice in da ya wuce ya maida ta Bauchi gidan mahaifin ta,in ya so ya bi ta da addua, Babana yaushe Ka zamo mara tausayi ban sani ba, idanu ya zaro tare da mikewa Yana hajiya nayi wani abun ne, Haba Kai kuwa ace tun shigowar Ka yarinyar nan ke cikin mota a rufe AI zafi ya kashe ta Allah ya kyauta, Khadija Maza fito ki zo ki taya ni Shigo da bakuwa,idanu Nameer ya zaro cike da mamaki yace hajiya are you for real, Murmushi tayi sannan tace Babana ke nan har akwai abunda za Ka kawo na kyamace Shi ko na ki babu wannan abun mu je Maza Ka Bude mota a fito da ita kafin Ka kashe musu yarinya, Yanda kuka san Nameer ya zuba ruwa a kasa ya sha KO kuma ya taka rawa haka yake ji, Allah ke nan ance daman Allah maji rokon bayin sa,addua yayi ta yi Akan hanyar Shi Kan ubangiji ya Sanya Mahaifiyar shi ta fahimce Shi ba tare da an samu wata matsala ba sai gashi Allah ya amsa(Yan uwa mu yawaita rokon Allah a yayin da muke Kan abun hawa Akan hanyar mu ta tafiya domin duk wata addua da matafiyi zai yi to karbabbiya ce bata dawo wa,haka zalika me azumi, ubangiji ya ji Kan mu ya kuma cigaba da amsa mana adduo'in mu Allah sa mu dace๐Ÿคฒ๐Ÿป), Kira ta kuma kwala wa khadija,Wanda ta amsa da dan karfi don ta san ta ji kiran da tai Mata din,tare da fito wa,mama gani,tace tana gyara Zaman dankwalin ta, Kira Zaliha mu je Ku taya ni Shigo da bakuwa,mamaki ne kwance fuskan khadija wace irin bakuwa ce har sai an yi gayya kafin a Shigo da ita,amman babu halin tambaya domin har su mama sun fice abun su,dakin zalihan ta je tare da Kiran ta kan su je mama na haraban gida, A kofar motar suka tarar da mama ta zuba wa Nadeeya Ido dake bacci Wanda za mu iya Kiran Shi na gajiya ko wahala, Da kanta ta shiga motar cike da nutsuwa ta dago Nadeeyar tare da manna ta a jikin ta,tana yaba kyawu da hasken fata irin ta Nadeeya, Kama mun ita mu fito da ita Khadija kun tsaya kuna kallo na, Idanu ta zaro sannan tace Hajiya wace ce wanann in da za a kamo ta ina kuma za a shigar ta, Ni fa Bani son surutun banza da hofin kin nan Khadija Baki gani tare suka zo da Babana in kina kama mun ki kmaa mun ita in Baki yi ki matsa Zaliha ta rike mun ita tunda aikin kudin ta take na San baza ta ki ba, Baki khadijan ta turo tare da kamo Nadeeyar nan dai suka samu suka fito da ita da kyar suka dauke ta suka shigar da ita parlor Kai tsaye mama tace a wuce da ita dakin ta,mamaki ne kwance fuskan khadija yo to a ina mama ta san wannan farar yarinyar me Sufan mayu,da har za a kule da ita uwar daka,mamaki be Gama kashe ta ba Saida ta ji mama na ce wa Zaliha ta shiga toilet ta hado Mata ruwa me dumi a bucket sannan ta dauko new towel a cikin drower tare da toothpaste da auduga ta kawo Mata,ba musu kuwa ta je ta hado duk abubuwan da Ake bukata,inda ta kawo ta Aje gaban mama,ce da su tayi su fita tana son ta gasa Mata jiki ko gajiyar tafiyar zai warware a jikin ta,duk yanda Khadija ta so suyi magaana mama nuna wa tai kamar bata gane me take nufi ba,ala dole ta fice daga dakin,zuciyar ta cike da tunanin wacece wannan haka, ********Police command Sen Rilwanu tun safe yake police command in an buga yin duniya kan su Bashir su fito mishi da diyar Shi amman dai amsan ke nan guda daya Basu San yanda take ba, Duka kam har na Bura uba sun sha ta a hannun oga Jabiru domin jika Shi da kudi Sen yake yi Wanda ke bashi daman yin Shaye shayen Shi yayi tatil ya zo ya sauke komai Kan su Bashir domin bugu kam sun sha Shi har na Allah ya Isa, Matakan tsoron da aka zuba kuwa ba a cewa komai Ka dauka mulkin sojoji Ake yi,ko in ce Yan sanda domin duk wani gurare an zuba police masu duba shige da ficen mutane,bincike sosai Ake yi amamn har yanzu shiru don babu motar da zai Shigo ko zai fita da ba a bincika ba, A kwanakin da suka yi hannun Yan sanda ba karamin wahala da azabtuwa suka yi ba,sun yi kuka in akwai na Jini bayan hawaye to Shi suka yi,Kareematu ta tsinewa Bashir ya Kai kwando dubu,haka zalika Zaituna ma ta tsine Mata ya fi abunda ya fi, Ganin bata musu lokaci kawai suke yi ya Sanya aka cike musu FIR in da za a tangade keyar su sai court,domin Sen cewa yayi sam be san zancen ya yarda da su ba, Kareematu tayi kuka kamar ta Rasa ranta tunda take a rayuwa ko Kusa da police station bata taba zuwa ba sai gashi karewar ta yau wai court za a wuce da su, Suna ji suna gani haka aka kade kansu ranar Monday aka watsa su court, A Zaman farko aka karanto case in su inda Ake zargin su da laifin hadin Baki su uku suka sace yar gidan Sen Rilwanu Audu Waziri (wato ana charging su da offence Conspiracy and abduction in Nadeeya), Bugun farko alkali yace ko akwai Lawyer in me Kara,da Wanda Ake Kara,nan Barrister Hassan buba ya mike ya gabatar da kanshi GA court in tare da fadin shine lawyer in me kara, Bayan ya Gama ne alkali ya kuma tambayan ko akwai Lawyer Wanda Ake Kara zuru suka yi da idanu kafin suka ce babu, Nan alkali ya tambaye su wani yare suke ganewa kuma za su iya magana da duk turanci suka ce da Shi,nan ko ya tambaye su one by one do you plead guilty or not,gaba dayan su suka ce they are not guilty, A karshe dai daga case in aka yi zuwa nan da 2 weeks masu zuwa kafin nan su tabbatar sun samu Lawyer saidai alkali ya bada umarni a wuce da su gidan gyaran Hali a Aje su har sai ranar da za a dawo Zaman court da haka aka tashi alkali ya mike ya wuce abun Shi, Kareematu Ihu ta Sanya tana zagi Bashir tana kuka inda Zaituna a nan ta yanki jiki ta Fadi ta Suma,Bashir ko wani irin gumi ne ya karyo masa da ya san haka zai faru tun farko da be hada Kai da Sen ba,yau gashi ya Kai Shi ya baro Shi, Haka nan aka watsa wa Zaituna ruwa aka tasa keyar su aka wuce da su suna kuka suna Ihu amman duk a banza,(ni ko nace Allah ya kara kadan ma Ku Ka gani indai son zuciya ce), Asaalamu alaikum Da fatan duk kuna lafiya,Allah ya sa hka,ya kuma ruwa ubangiji ya bamu damuna me albarka ๐Ÿคฒ๐Ÿป Ayi mun afuwa hidimar biki ce ta boye ni Amman in sha Allah gobe za mu kammala zan cigaba da typing kamar yanda na Saba kullum, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi๐Ÿ™๐Ÿป, [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜”UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ........ NA DAINA AJE GROUP LINK INA DOMIN ANA SAMUN MAZA MARA SA TSORON ALLAH NA JOINING SUNA BIN MATAN AURE DA BADALA,DUK ME BUKATAR SHIGA GROUP INA SHOULD TALK TO ME IN TABBATAR MACE CE SAI NAYI ADDING IN MUTUM DA KAI NA,BUT PLS IN HAR KIN SAN BA KARANTA BOOK INA ZAI KAWO KI BA TOH KI YI ZAMAN KI BA SAI KIN YI JOINING BA, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 ........... Page thirty _four ******** Da kyar ya iya bude Baki yace Afzaal me ya kawo Ka gurina kuma??? Da karfi Afzaal ya sake kofar dakin inda Saida yayi making loud noise,sanna ya Shigo cikin dakin cike da takun Isa da kasaita,idanun sa suna Kan doc Bashir Yana jefan Shi da kallon me cike da tsana, Afzaal am talking to u kana kin responding and kana Kan Shigo mun daki,for crying out loud wat are you looking for,let me be Bana son wani damuwa ko tashin hankali, Da karfi Afzaal ya janyo kujeran da ke dakin tare da Zama,idanun Shi har yanzu suna Kan doc Bashir kafa daya ya daura Kan daya,tare da shiga girgiza kafan, Afzaal this is the last time da Zan tambaye Ka what brought you here,me kake nema,just let me be pls Bana son damuwa, Damuwa damuwa fa kace Kai karamin Dan iska ne Ashe,Afzaal ya fada a harzuke, Da Ka kara hakuri ma ni da kaina Zan maka bayanin me ya kawo ni gurin duk da already it's all writing over your face Ka san me ya kawo ni,so nake na Gama kallon fuskan munafuki kuma maciyi Amana irin Ka, Mikewa Afzaal in yayi tare da cukumo kwalan rigar Bashir ba tare da damuwa da kwance yake gadon marasa lafiya Yana Shan Karin ruwa ba, Cikin Ihu yace how dare you little Bastard har Ka Kai ni Afzaal za Ka yi playing ,shiru yayi tare da jijiga Bashir in sannan yace ya muka yi da Kai,Dan Bura uba ni za Ka Raina wa wayo sabida Kai Ka fi uban kowa son kudi,Ka karbi makudan kudade na sanan kayi thinking you are free Ka CI su without yin abun da nake so??? Ina bazai yu ba a sau nawa na maimaita maka make sure Kar a samu wani matsala Ka Bani false hope Kan komai zai tafi yanda nace and yanzu yarinya na can a raye ba a ma San inda take ba sabida zalama da son abun duniya AI Ka neme ni kace toh Afzaal aikin fa be yi ba in dawo maka da kudin Ka ne KO ya???Amman sabida zarme war zuciya Baka yi ba,tunani kake za Ka CI banza ko toh Ka sani wlhy ko cikin rami Ka shige sai ka fito Ka Bani kudi na mutumin banza kawai, Jin haka ne ya harzuka doc Bashir cikin sauri ya pincike drip in hannun nashi,tare da bige hannun Afzaal mikewa yayi tsam Kan kafufuwan Shi,idanun Shi jajur tsaban bacin Rai, Sama da kasa yake kallon Afzaal sai haki yake sauke wa kamar Wanda yayi race, Bani kudi na tsohon mara mutunci Afzaal yace Yana hararan Bashir, An ki a bada kudin naka,doc Bashir ya ce without any fear, Idanu Afzaal ya zaro like wat, Yes Ka ji ni Sarai Nace baza a bada kudadan naka ba and so fucking wat,kudi ne dai sun Shigo Basu kuma fita Ka ji Ka sani, Kana maganar Imani ko son zuciya akwai Dan iska irin Ka me son zuciyar tsiya AI ni daga Sen da aminin Shi ban taba ganin mugu irin Ka ba, Sabida Baka da kunya matar Ka diyar Sen kake son kashe wa,Abu be yi ba wai har zuwa kake karban kudadan Ka,ko uban wahalan da nasha kuma WA zai biya ni oho, Ah lalle bakin Ka ya Bude to hell with the wahala da Ka sha waya dama all I know is that 55 mil ina in gansu gaba na, Dariya Yan iska doc Bashir yayi sanna ya ja kafa a sannnu ya koma bakin gadon Shi ya zauna, Ni fa daman na san za ayi haka,tun Randa na baiwa Ahmed ATM ina ya Ciro mun kudi aka ce anyi freezing account ina nace aikin Ka ne,daman I have been waiting for you tun Randa na fito daga prison, Akan Ka Afzaal har prison na je wani irin bakar wahala ce ban sha ba,da na so Zan iya Kiran sunan Ka in ma nuna evidence Kan cewa Kai da bakin Ka kace a kashe Nadeeya but ban yi ba, because ina da Amana and Ka yarda da ni ne ya sa haka,haka nayi taking blame in a ciki harda wasu nurses ina da ba su ji Basu gani ba,irin azaban da aka gana mana na Wasa ne??? Kasan kwana nawa nayi ban yi wanka ba??babu wanka babu wanki sai wanke idanu,abinci me dandano rabon da na CI tun yaushe???an katse mun rayuwa ta as a qualified Doc iri na wai na kare gidan yari duk sabida Kai and sabida Baka da kunya me makon Ka zo kayi mun godia sai Ka zo kana Bina da maganganun banza da iskanci, Toh wlhy ni ba sa'an Ka bane,Baka san Waye Bashir ubaidullah ba Akan kudi babu abunda bazan iya aikata wa ba,don haka tun muna sheda juna Ka koma kayi unfreezing account ina KO kuma wlhy In Kai wa Sen evidence in da nake da Shi Akan Ka,ya kare Yana hararan Shi, Da kallon mamaki Afzaal ke bin Bashir daman Yana da Baki haka,da kyar ya daure yace and wani evidence ne gare Ka da za Ka kaiwa daddy??? A cewar Ka am so stupid ne right gani kake Kai kadai ne me wayo,kamar na san wannan ranar za ta zo duk maganar da muka yi da Kai a office ina wancan ranar anyi recording in Shi,Ka ga in na kaiwa Sen shike nan wlhy har kyautan kudin da ya fi tsiyar da Ka Bani zai yi,Ka ga yanzu Kai za Ka koma abun zargi ba zai taba yarda yarsa bata gurin Ka ba, Tsaki Afzaal ya ja tare da naushin iska,sannan ya daure yace okay fine Bashir let's do it this way Ka Bani 20 mil Ka rike 25 mil Ka ga shike nan AI ko mun Raba asara??? Dariya Bashir ya kwashe da Shi sannan yace Sisi Afzaal baran Baka ba domin na Riga nayi planning in kudadan nan,don haka ga kofa yanda Ka zo Ka bi Ka fita and make sure to unfreeze my account yau yau din nan domin ina da tafiya jibi if not wlhy tallahi sai dai Ka amsa Kiran Sen, Idanu jawur Afzaal ke kallon Bashir haka kace ina,Kai Bashir ya daga mishi, murmushi yayi Wanda Ake kira tafi kuka ciwo sannan ya gyada kanshi then we shall see Bashir Ka Kira war wa kanka,In dai ni ne I will make sure to show u shege,da haka ya ja kafa ya fice ranshi a matukar bace tare da bugo kafar da karfi, Hhhhhhhhhhhhh,in Ka so Ka karya musu kofan shegen yaro mara mutunci ni zaka koya wa bariki abunda a cikin ta na taso,kudi ne kuma na rantse da Allah ban bayar wa ko iyalai na ba kamshin su za su ji ba balle Kai banzan bazara acewar Ka Kai kadai Ka iya Bura uba,ya kare tare da komawa ya kwanta ya dauki wayar Shi Yana latsawa,ni ina Ahmad ne ya zo mu karasa maganar samun Viza ta domin wannan kywawan Yan matan da nake gani masu fararan jiki kamar madara in samu in je in rungume ko uku ne,in ji Suma fararan nan ya taste in su yake, **************BLAZE๐Ÿ”ฅ HOUSE Kamar yanda suka Saba haduwa don gudanar da meeting in su duk ending of the month,this time around ma haka ne, Yan kauyen Offa Basu da kwanciyar hankali in har aka ce end of month ya zo,Karan shige da ficen motoci Kam kamar a cikin gidajen su Ake yi,sai Sanya duk ranar da meeting in ke holding kowa ke rufe gida Jen Shi Ka ji kauyen tsit kamar ba kowa, Babban hall in da aka Saba taruwa don ganawa da Odugwu cike yake da mutane bila a dadin kowannan su sanye da Jajaye da bakaken Kaya mazan su da matan su, while wainda ke son ganawa da Odugwu don biyan bukatun son ransu ke zaune tsirara haihuwar iyayen su,domin doka ce ba a ganawa da Odugwu da Kaya, Duhu hall in yayi guri yayi tsit sai wasu sautuka Mara dadin sauraro ke tashi a cikin hall in for about 5 mints sannan haske ya bayyana sai ga Odugwu xaune bisa kujeran tsafin iskancin Shi, Da rawar jiki kowa ya mike tare da Fadi kamar yanda suka Saba suka zube suna me yi mishi kirari suna daukan hakkin Allah tare da bashi a karshe suka yi mashi sujada(wa iyazu billah,ya Rahman duk tsanani duk wuya Kar Ka bar mu muyi barin imanin mu,Ka Kara mana tsoron Ka da ikon bauta maka๐Ÿ˜ญ๐Ÿ™๐Ÿป), Idanu ya zuba musu Yana me jin Isa da mulki Ace duk fadin hall in ga duk gurin Shi aka zo neman biyan bukuta,sai ya saki dariya me ban tsoro Wanda ya so razanar da new members in da suka yi joining recently while Wanda suka Saba da Jin Shi kuwa sun San yau Odugwu na cike da farin ciki, Umarni yayi musu da su Mike ba tare da bata time ba kuwa kowa ya mike tare da Zama Kan kujeran shi, Nan yayi umarni da Wanda aka baiwa task KO masu kawo abun sacrifice su Fara kowa wa, Nan aka hau layi kowa na Mika abunda aka umarce Shi da ya kawo,masu pant ne,used pads be,bra in Mata, masu kawo sassan jikin Dan Adam,zuciya aa koda idanu,rukakkun cikin su kuma irin su Kabiru this time around jinjirai suka kawo, Ba karamin dadi masu bada sacrifice in suka ji ba domin ganin yanda Odugwu yayi appreciating,Yana ta dariya tabbas sun San Jinin da suka bada ya karbu kuma yayi farinciki da su,hakan na nuna za su samu biyan bukatun son ransu ke nan, Sam Odugwu yaki karban sacrifice in Sen kallo wanna ya ki duban Shi balle ya Sanya ran yin magana da Shi,hakan ba karamin kashe mishi jiki yayi ba,daman abunda yake ta Jin tsoro ke nan,saisa yace da Kabiru ma kamar ba zai zo ba don ya san tabbas Odugwu zai yi mugun fushi da Shi,Saida yayi ta kwantar mishi da hankali sannan ya lallaba Shi suka taho,tunda kuwa ya ga Odugwu ya ki karban abun hannun Shi ya San Shi kam yau ya shiga uku,(ni ko nace Baka shiga ba ai duk Wanda ya sake Allah ya kama wani Shi toh Shi da bakin ciki da damuwa sun kulla ke nan), Bayan an Gama ne masu bukatu suka shiga iso gare Shi kawukan su kasa suna zuba mishi kirari kamar Wanda aka ce Shi ke rike da rayukan su ko numfashin su, Cike da Isa da izza ya Fadi wa kowa abunda yake son yi in ko kayi Shi babu kuskure toh bukatar Ka tabbas za ta biya, Bayan ya Gama ganawa da su ne ya mike tare da bin wata kofa Yana me nuni da Sen Kan ya biyo Shi Yana son ganin Shi, Hantar cikin Sen ne ya kada,har ga Allah be taba Jin tsoron Odugwu irin na yau ba don ko Randa Kabiru ya kawo Shi be tsorata irin na yau ba, Jiki ba kwari ya mike ya bi bayan Shi Saida ya kwabe tas tukun na ya shiga cikin dakin, Baki Kirin ko palm in Ka Baka iya gani,AI sai Sen ya zube a nan kasa,cikin kaskantar da Kai,ya shiga rokon Odugwu Fadi yake na tuba na bika kayi mun aikin gafara,in Baka soni Ka tausaya mun ba rayuwa ta za ta tagayyara Kaine gata na, Odugwu Kaine gaba na da Baya na,Kai ne silan samun daukaka ta,na Roke Ka kayi hakuri fushin Ka azaba ce a gare ni ya kare kamar zai yi kuka, Cikin tsawa me tazanar wa Odugwu yace Kaiiiii Rilwanu, Jin yanda ya Kira Shi ne ya kuma tabbatar mishi da tabbas Odugwu Yana cikin tsananin fushi da Shi, Cikin kuka yace na roke ka Odugwu the greatest of all Kar Ka bar ni Kar fushin Ka ya shafe ni,fushin Ka azaba ce gare ni Ka yafe ni na san na kasance me Saba maka, Tokaran da aka mishi ne Wanda Saida ya Sanya Shi kwanciya flat da bayan Shi ya katse mishi rokon Shi,nan take kuwa huta ya bayana, Fuskan Odugwu ne ya ga yayi Baki Kirin ya koma sak na katuwar macijiya idanun Shi sunyi kore sharr,sai fiddo da halce yake ta faman yi, Ba karamin tsorata Sen yayi ba tabbas duk abunda zai Sanya Odugwu rikida har ya canza sufa toh ba karamin Abu bane, Cikin fushi ya daga hannun Shi tare da matsewa sai GA Sen ya mike Sama Yana kakari sakamakon shake mishi wuya da Odugwu yayi, Nan ya shiga jujuya Kai Yana tare kamar Wanda Ake zare wa Rai sam numfashin Shi ya kasa fito,Banda hawayen azaba babu abunda ke fitowa daga idanun Shi,a haka ya samu ya hade hanayen Shi guri Daya alaman dai roko yake har iyanzu, Saida Odugwu ya ga Sen Yana neman mutuwa tukun na ya sake Shi tare da watsa Shi kasa ji kake Tim a take goshin Shi ya fashe, Tare Sen ya shiga yi kamar ranshi zai fita idanun Shi sun firfito lokaci daya har ya canza kamanni, Kafin ya Kai ga dawowa setin Shi sai Jin manyan kafan Odugwu Akan cinyar Shi ya take Shi, Wata irin radadin zafi da azaba ya ziyarce Shi Amman sam babu daman Ihu hawaye kawai ke fitowa me dumi daga cikin idanun Shi, Rilwanu Odugwu ya Kira cikin daga murya Saida dakin gaba daya ya amsa, Naam Odugwu na ka yafe ni my lord, Rilwanu you are playing with fire, Kai Kan Ka kasan Waye ni,tun zuwan Ka brotherhood in nan nake kaunar Ka kasancewar kana baiwa kungiya abunda take bukata a duk sanda ta nema,ya Sanya wasu cikin mu ke Jin haushin Ka suna ganin kamar na fi kaunar Ka ne, Na daka maka kafa da dama a rayuwar nan na Baka abubuwa da yawa har da ma Wanda baka roka ba,na cika maka dreams in Ka da dama kuma ina Kan cika maka ma Zan ce,na maida duk wani impossibles in Ka sun koma possible,na Baka fame money ,da duk wani abunda kake takama da Shi,ita Kan ta Yarinyar da kake masifan kauna da ban so ba do you think za ta zo duniya ne??ya kare Yana tofa wa Sen yawu a fuska na tsaban masifa, Zuciyar Sen Banda zafi da kuna babu abunda take yi,idanu kawai ya rintse Yana me sauraran maganganun Odugwu, You have gain a lot tun sanda Ka shigo cikin mu from nobody na maida ka me fada a ji a duk fadin garin Ku, duk cikin harshen turanci Odugwu ke bayanin nan, Amman na ga alaman gani kake kamar bazan iya punishing in Ka ba,mancewa kake da ni da ya sanya Ka crossing limits inka, Tun haihuwar yarinyar nan nace da ita namu ce Ka Bani Jinin ta kaki yarda,Ka Bani soul in ta kaki,Ka Bani brain inta Ka ki, da kyar na samu Ka bamu WOMB in ta,why on earth Ka Bari tayi nisa da Kai??? Cikin kuka Sen yace na roke ka kayi hakuri Odugwu the greatest ni kaina neman ta nake babu dare babu Rana, Ka kuwa san me hakan ke nufi??bacewar yarinyar nan tonuwar asirin Ka ne kuma tonuwar asirin Ka na mu ne Baki daya kamar yanda kullum nake fada, Rilwanu Baka ji,tun haihuwar ta da Ka Bani ita da duk haka be faru ba, Na sani Odugwu na sani kayi hakuri a Nemo mun ita Ka taimake ni Kai kadai za Ka iya mun wanna aikin, Dariya Odugwu yayi me abun tsoro sannan yace kana da son Kan Ka Rilwanu,tabbas zan gano inda take amman kafin nan dole Sai an yi maka punishment in da Ake wa duk Wanda ya karya mana doka, Hannu ya tafa AI kuwa sai GA wasu majiya karfi su hudu sun Shigo da bulalai masu kauri da girma a hannayen su fuskan su babu alaman Imani ko tausayi, Sen be farga da abunda zai faru ba sai ji yayi an daga Shi an wulla Shi Sama tare da cabewa nan ko suka mike Shi, Beat the hell out of him shine abunda Sen ya ji Odugwu yace,nan ko kamar Wanda Allah ya aiko su suka shiga tsula wa Sen bulalun nan a jikin sa,Ihu yake Yana kuka da hawayen Shi bazai iya tuna when last aka buge Shi ba, Baka Jin komai sai Karan saukan bulalai da ihun kukan Sen Fadi yake Odugwu am sorry pls forgive me,tun Yana iya magana Har ya koma numfashi kawai yake iya saukewa,sai hawaye, Basu suka dakata ba Saida suka ga Jini na zuba daga bayan Shi,sanann Odugwu yace da su aikin su yayi kyau su tafi, Nan suka yarda Sen jiki ba dadi suka yi gaba abun su, Yatsa wanann Sen ya kasa dagawa ba tare da Odugwu ya kalli KO inda yake ba ya sa Kai ya fice abun Shi, Kabiru ne da ke bakin kofa yayi saurin shigowa cikin dakin tare da nufan inda Sen yake cikin sauri ya dago Shi ina babu numfashi jikin Shi, Da gudu ya Ibo ruwa a toilet tare da watsa mishi wata irin wawan ajiyar zuciyar Sen ya ja sannan ya Bude idanun Shi, Suna hada ido da Kabiru kuwa ya fashe da wani irin kuka Wanda Zan iya Kiran Shi da na takaici ne ko bakin ciki, Sannu Aboki na yau kam tabbas ran Odugwu ya Baci da Kai, Cikin kuka Sen yace Kabiru na gaji na gaji,shekaru nawa ina bautan Odugwu ina kyautata mashi ina bin umarni Shi amman Ka duba Ka ga diban Albarkan da ya sanya aka mun,ya kare Yana kuka,na gaji Kabiru Bana Jin Zan iya cigaba da Zaman kungiyar nan,I have sacrificed enough,abubuwa nayi losing daga Randa na shiga kawo yau, And abubuwa nawa kayi gaining where u like this before???shine tambayar da Kabiru yayi mishi, Maganar fita ma fa bata taso ba,abubuwa nawa Odugwu ya Baka,in ce na hadu da Kai kana fama da muguwar Talauci duk wani kayan wanka da Gaye na samari Baka da Shi, Odugwu miye be Baka ba ya Baka gida mota,kudi har mulki aboki na Kar Ka zamo butulu mana, Butulu fa kace Kabiru duk abun nan da ya Bani are they for free??in ce Saida yayi demanding something in return miye ban yi ba abunda in duniya suka ji wasu daga cikin mugayen abubuwan da na aika ta sai sunyi mun tofin Allah tsine I don't think I can continue with this thing gaskia Sen ya Fadi da iyakan gaskiar da, Dariyar you most be joking Kabiru ya yi WA Sen sanna yace Ka ma isa,as I told u in an shiga babu fita Ka kuma yarda Ka shiga you have to bare da duk abunda Ka gani,Ka ma gode wa Allah Odugwu na kaunar Ka ya Sanya aka yi maka punishment me sauki,Ka tashi Maza Ka maida kayan Ka mu je Ka Kara rokon Shi yafiya ya samu ya sanar da Kai in da yarinyar nan take lokaci na korewa kasan in aka Riga aka yi serving abinci toh ya Gama Jin complains kuma Sai dai next meeting..... Assalamu alaikum Ayi mun hakuri 2 days busy na shiga wlhy ziyara na je kuma inda na je ba a cika samun wuta ba ya Sanya kuka jini shiru, Sai zuwa Monday kuma in sha Allah, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi . [6/21, 8:37 PM] My Best Best โค๏ธ: ๐Ÿ˜ญ๐Ÿ˜” UBANA NE KO KISHIYA TA ๐Ÿ’”๐Ÿ’” WRITTEN AND STORY BY NERNAH MARYAM (MARTEYBEE) ........ My what's app group link https://chat.whatsapp.com/FKZuWu1yj7VJ9L6izLqLhA In har kin san ba karanta book ina and commenting bane zai kawo ki toh Don Allah kiyi Zaman ki ba sai kin Shigo ba,haka zalika Maza should stay away from my group domin na Mata ne xallah ko Ka shiga Zan cire ka๐Ÿ™๐Ÿป, Ga masu son a tallata musu hajojin su should contact me via: 08100046388 Ayi mun afuwa nai mistake a last page in da nai yi madadin in Sanya 32 sai na sa 22 typing error ne๐Ÿ™๐Ÿป, .......... Page Thirty_three ********** Sen Rilwanu****** Zaune yake Shi da Alh Kabiru a gurin hutawar Shi,lemu Ka da kayan dadi ne cike a gaban su saidai daga kallon fuskan Sen za Ka fahimce bayi da kwanciyar hankali ko walwalan da zai iya Kai ko da ruwa ne bakin Shi balle har ya Kula tarkacan kayan dadin, Sen ina so Ka saurare ni da kyau da kuma kunann basira because I got point a abunda nake fada, Point fa kace Kabiru a taya kake expecting na janye karar nan bayan Nisan da aka yi a shariar nan AI kawai mu zuba wa hukuma Ido su fito mun da yarinya ta, Dan murmushi Kabiru yayi sannan yace dadi na da Kai wlhh ga Abu a bayyane Amman sam sai kana yi kamar Baka gane ba, Na sani Ka sani Nadeeya bata hannun su doc Bashir domin da tana nan wlhy a sanin da nayi wa Bashir tun sanda su Jabiru suka kama Shi Zai yi bayani,mutum ne mu Dan banzan son kudi saidai akwai Shi da tsoro ba na kadan ba,and in har Ka kalli abun nan from my own view wani hujja Bashir ke da Shi na sace Nadeeya a sani na da doc Bashir Yana da rikon Amana tunda har kuka Kula deal da Shi toh babu wani Dan iskan da ya Isa biyan Shi ya sace ta,so pls enough of all this mun azabtar da su yayi yawa,abun haushin ma duk a banza domin mun bar asalin me laifi Yana can,su kuwa bayin Allah are paying the price of abunda ba su San komai a Kai ba,ya kare a sanyaye, Tsaki me sauti Sen ya ja sannan yace Kabiru in muka sake su toh princess ita fa??a taya zan gan ta, Common sai kace yau Ka Fara zuwa blaze house ko dai Ka Fara kokonto Akan Odugwu ne??ko Ka mance ya Kan maida impossible ya zamo possible,zuwan mu da za muyi cikin week in nan Ka sanar da Shi am very sure kafin mu bar gurin zai sanar mana da inda take wa kuma ya dauke ta,AI tunda kana da Odugwu toh komai me sauki ne,ya kare Yana kurban lemo a glass cup, Dan shiru Sen yayi Yana tunano irin abubuwan da Odugwu ya malaka mishi , Odugwu shine silan samun komai nashi a duniyar nan,ya maida Shi from poor to the most richest man in the north,ya maida mishi so many impossibles in Shi to possible, Yana da faith Akan Shi sosai wannan karamin Abu ne kamar yanda Kabiru yace zai masa finding solution kamar yanda ya Saba Odugwu the greatest babu abunda ya gagare Shi ya Fadi a bayyane, Toh Ka gani so just chill kasa a ranka kamar an ga Nadeeya yanzu Ka Kira court Ka ce da su Ka janye karar ta Ka ayi freeing Nasu Kar Ka mance mulki kake nema voice in su kadai ya Isa bata maka siyasa,Shi kuma Bashir Ka bar ni da Shi in ma har yanzu zuciyar Ka be kwanta Akan bashi ya sace ta ba Zan yi handling komai, Babu musu Sen ya dauki waya abunku da me Fadi aji,one phone call yace ya janye Kara ayi freeing in su a yau yau in nan, *********Court Ko da alkali ya ji haka shima farinciki yayi domin wanann case Nasu akwai daure Kai,an sauwakar da Shi, without waste of time kuwa ya sanar da su an janye karar sanan yayi freeing in su za su iya tafiya, Kamar Wanda aka yi ruwa aka dauke cak haka suka ji saukan maganar nashi,ta Malam bahaushe wai yace kamar saukar aradu da Ka, Tabbas sun ji ance za su iya tafiya saidai gani suke kamar mafarkin da suka Saba yi ne,Khairat da Abdoul Banda hawayen farinciki babu abunda suke yi, Haka ma Yan uwan Zaituna da suka halaci Zaman court in,a ta bangaran doc Bashir kuwa ko mutum daya daga cikin family members insa Basu samu zuwa ba ko Ince sun ki zuwa, A sukwane suka fito daga cikin Accused box in, kafafuwan ko wannan su rawa kawai yake yi,da sauri mamar Zaituna ta je ta taro Zaituna da ke kokarin faduwa hawaye take na farin ciki Fadi take Alhamdulilah tsarki da godia sun tabbata ga Allah daman ance Ramin karya kurarre ne yau gashi gaskia tayi halin ta barka Zaituna yau sai kwanan gida ta kare tana kuka, Abdoul ma nufan Kareematu suka yi shida yaran ta tare da rike ta,haki take tana fadin Abdoul take me to hospital pls wlhy tallahi kafafu na rawa suke babu Jini a jiki na ruwan jiki na ya kare,Abdoul kafafu na bayana ciki na Zan mutu, Rungume ta yayi ba tare da damuwa da tulun datti da warin da take yi ba,domin Rabon ta da wanka har ta mance, Yi shiru Kareematu na in sha Allah babu abunda zai same ki Alhamdulilah tunda har an sake Ku yanzu za mu tafi gida kiyi wanka sai mu wuce asibitin ko, Cikin kuka tace Abdoul bazan iya wankan nan ba ji nake kamar Zan mutu sai luuuu tayi Baya ta zube a kasa babu numfashi, Su Khairat da Kannan ta ne suka yo kanta suna Kiran ummah ummah don Allah ki tashi,ganin bata motsi ya Sanya Abdoul saurin taran abun hawa da taimakon wasu Mata suka sanya ta a ciki ya nufi Specialist da ita, Doc Bashir ko da dafe bango ya samu ya fito daga cikin court in be taba danasanin rashin nuna kulawan Shi ga family in Shi ba sai yau kowa dai sai nan nan yake da zuriar Shi amman Shi kam ko fly be zo daga family in Shi ba,haka a sannu Yana Jin jiri Yana komai ya fito daga cikin court room in Yan gulma da suka zo ganin case sai barka Ake yi mishi, Ba karamin bakin ciki ya ji na rashin zuwan family members in Shi ba saidai wani side in heart in Shi in ya tuno makudan kudadan da ke shake cikin account in Shi sai ya ji duk damuwar ma ta kau,asibiti yanzu zai samu ya je a masa treatment Yana warkewa Los Angeles zai wuce ko bashi suka nuna wa rashin kauna ba toh wlhy sai ya nuna musu shima Dan iska ne,sai yayi good 3 months bayi gida sai sun Raina kansu is a promise ko kwayar shinkafa bare Aje wa ko wace shegiya ba,sai sun San shi suka wulakanta suka nuna mishi be Isa b bayi da gata,sai ya CI uban su gaba daya,gashi zai musu a sannu inda sai sun Kira suna kuka begging in Shi ya dawo,tsaki ya ja tare da yin kwafa sannan ya tare me adedaita sahu da kyar ya iya daga kafafun Shi da suka mishi nauyi ya shiga tare da cewa a Kai Shi RIMI CLINIC,ciniki suka yi ya shiga Akan sai sun Isa zai shiga ya karbi mishi kudin domin sisi wanann babu a jikin Shi, *********Doc Nameer Kasan Allah Nameer ko kadan ban so aka Kori karar nan ba,Dan uban su da an yake musu hukunci duk an tura su gidan yari, Murmushi Nameer yayi tare da daukan tissue a nutse ya goge gefen bakin Shi sannan ya goge hannayen Shi ,kafin ya dago idanun Shi ya zuba su Kan Habeeb, Ni wlhy ban San me bayin Allahn nan suka maka ba Ka bi Ka tsane su,ya kare kamar ba Shi yayi maganar ba idanun Shi na Kan Habeeb in da is busy enjoying his slice of pizza, Saida ya hadiye sannan yace wlhh Kai dadi na da Kai Baka da kirki,Ka ji iskanci kamar ba don Kai nake hakan ba,sabida tsanan da yayi maka fa nake taya Ka tsanar Shi, Nameer can't help it Saida ya saki dariya wani abun ma dai saidai a bar Habeeb in yayi Abu kamar wani karamin yaro in Banda Habeeb wai kishi yake taya Shi can you imagine, Ka cigaba da dariya ba dai ni Ka mayar Dan iska ba,ya kare a kufule, Kafadun Shi Nameer ya Dan daka sannan yace dallah Malam tashi mu tafi na biye Ka sai Ka ci box takwa a rasa kudin Siya wa my boy madara, Dariya Habeeb ya Sanya sannan ya mike shima Yana fadin dadin abun in ni na Rasa akwai Kai zaka siya mashi,mu je muyi clearing bills in mu mu samu mu koma asibiti Kar a neme mu, Phones in su suka tattare tare da car key sannan suka nufo gurin biyan kudi,total aka musu Nameer ya bada ATM in Shi aka cire kudin sannan suka fito, Habeeb jakan can ya mun kyau,ya kare Yana pointing wata mini bag daga cikin glass, Hmm AI Beenazeer na kawo bags and shoes masu mugun kyau harda veils laces and Atampa,Saje is one of the best places da ke Saida Kaya na gani na fada,kayan ta duk masu quality ne saisa at times mutane ke complaining ta cika tsada,saisa ko taste in abincin ta daban ne da na sauran restaurant dake garin nan,ko za mu shiga Ka duba wa mutuniyar ne?? Wuce mu tafi Bani son gulma daga cewa jaka ya mun kyau,na san dai kan Nadeeya kake batun nan toh Banda abunka na Siya ma AI ba iya Sanya wa za tai ba, Banda abunka kamar gobe ne za ta warke sumul in sha Allah mu zo mu sha biki tunda kace jikin nata da sauki sosai AI ko, Kai Nameer ya girgiza sannan yace ni nace da Kai auran ta Zan yi,ko kun yi da ita za ta aure ni?? Ah Malam ni dai bazan ce komai ba time will speak wuce mu tafi,Beenazeer dai an Miki bakin ciki,ya ce bare Siya jakar ki ba, Nameer be ce da Shi komai ba domin ya ga alaman neman maganar sa kawai yake yi,a haka suka shige mota sai hospital, Duk inda Ka wuce babu chaptan da ake kasawa sai na su doc Bashir wasu suna musu barka an sake su while wasu kuwa ran su be so ba,suna bakin cikin doc bashir zai dawo hospital ya cigaba da zuba mulkin sa, ********Doc Bashir Kwanan Shi biyu a kwance a hospital in da ya dace da wani abokin Shi doc ne a gurin so Shi ke Kula da Shi, Ya sha drip sosai tare da magunguna harda Karin Jini Saida aka yi mishi,wanka yayi sosai tare da cude jikin Shi ya tsine wa Sen ya fi cikin kwando Dari,kwanan Shi nawa babu wanka babu wanki,ji yake kamar ya sauya skin in Shi,Shi kanshi kyankyamin kanshi yake yi, Abokin Shi me suna Doc Ahmed Shi ya kawo mishi Kaya abinci da duk wasu abun bukatu har waya da wallet in Shi ya dauko mishi,ko da ya tambaye Shi ina matayen nashi tsaki Bashir ya ja tare da cewa rabu da Yan iska watan Kada su gida Yana gab da kamawa, Shi dai Ahmed hakuri ya bashi tare da fada mishi hidimar Mata sai a hankali sai ana yi ana musu uzuri,hmm kawai Bashir yace tare da gyara kwanciya, Ganin Baya son maganan ne ya sanya Ahmed mikewa yace Bari na dubo wata mara lafiya Zan dawo anjima,sai Ka dawo Bashir yace da Shi tare da komawa ya kwanta tare da lumshe idanu Yana Jin yanda ruwan drip in hannun Shi ke shiga cikin jikin Shi, Karar Bude kofar da aka yi da mugun karfi ne ya sanya zuciyar Shi bugawa tare da saurin Bude idanu,domin har ga Allah a mugun tsorace yake gani yake kamar mistake kadan xai yi za a maida Shi hannun su Jabiru, Idanu ya Bude da kyau domin so yake ya tabbatar zargi yake ko hakan ne,a taya ma wa ma ya sanar da Shi inda yake me ya kawo Shi gurin Shi,shine tambayoyin da yake ta running a kanshi, Da kyar ya Bude Baki yace AFZAAL me ya kawo Ka guri na kuma??? Ayi mun afuwa Charge ne Bani da Shi ,na so ya fi haka yawa, Yawan comments in Ku yawan typing da update in da za Ku samu,in kuka nade kuka yi shiru ghost readers toh Nima nadewa zan yi in sha Hutu na, Sai zuwa gobe In me kowa me komai ya yarda, Ina yi wa kowa fatan Alkhairi๐Ÿ™๐Ÿป An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels