*HAUWA KULU WOMEN LEADER* Oum yasmeen Da sunan Allah me Rahman mejinkai Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfanar da al'umma *Perfectly pens* *King and queen writing chamber* Wannan littafin sadaukarwa ne ga yan amanah kaf duniyar marubuta bani da kamar su *Queen kaina Nainarh kd's* Ahayye sama ruwa kasa ruwa sama....ai bata ƙarasa ba taja burki tace "Kut melesi......tab yau ana yin'ta yasin in na yarda inya yawo ba kafa a garin nan...., Tsit gidan yayi yawa ba magana take ba ƙara daga murya tayi tace "Gwaggo gwaggo wallahi ki fito ki zame min sheda dan yasin in murɗe kan dabba in hullar ba wani aiki ne a guna ba...., da sauri lami ta fito tana gyara daurin zanin ta abin da ta raya shi ya faru jidda ta zubawa tattabarun ta gyada uwar garken'ta ta zo tana ci dafe kirji tayi tasan halin jidda sarai ba kirkine da ita ba wannan abin da ta fada ƙaramin aiki ne a gun'ta ƙasa tayi da murya tace "Yar gidan gwaggo kiyi hakuri ban san taxo ci ba gaba in xaki basu abinci ki dinga barin su a cikin wajan su ko dan sharar gidan nan ......, Hamgame baki tayi ta saki kwafa tace "Iyee baba lami kin ga kun kwana na yanzu ni kike fadawa wannan magana...? Wato daman yi dani kuke in bana nan to wallahi in kara fito da su wannan shegiyar figaggiyar tinkiyar nan taki tazo taci ki ga yarda ake banƙare tinkiya Duka ta kaiwa tinkiyar ciki wanii kuka tasa ki.... Jikake ɓeeeyyy ɓeyyy da saurin takama tinkiyar baba lami tayi ta jata har zuwa turƙen ta ta daure tinkiyar tata tasan halinta sarai yan zu labari zai sha banban sai ta yanka ta bawa kartin banza suci ba gaira ba dalili kai mata cibi ya zama ƙari in Allah ya hadaka da mutumin banza sai addu'a Tsaki taja ta buɗe duroɗin ruwa ta ɗiba tana wanke ƙafar'ta yawa ba siyan ruwan ake ba sai wanke kafa take da sauri hansai ta fito tana cewa wanne dan durin uwar....ai kafin ta ƙarasa ta ci karo da uwar yan ɓarna jiddodo arnan daji haɗiye sauran zancan tayi tace "a'a yar gwaggo kin dawo kenan....., banza tayi mata ta daki jikin diroɗin da kafa daman ruwan kaɗan ya rage aikuwa ya waɗi ruwan ya zube Ɗaki ta shiga duk abin nan da ake gwaggo na kan wata yaloluwar katifa tana taunar goro ta turo dauri gaba kama kugu jiddah tayi tace "Gwaggo yanzu duk kiran nan da nake kina jin kikai min banza...., gyara zama tayi tace "Kululu kwantar da hankalin ki yau ba yan tujararne akai na ba ƙarar su nakai gun Allah...., hmmm kawai tace ta zauna kallon katifar da gwaggo take zaune tayi tace "Gwaggo wallahi ni'ma harkar siyasar nan zan fara jibi fa baraka kawata yadda take shanawa...., Wallahi duk lokacin da kika sake na ganki a gun yan siyasa sai na ɓalla kafar ki ban da daukar maganar da kike jamana a gari har sai kin tafi yawon siyasa cewar wani matashi daya ɗaga labulan ɗaƙin gwaggo cikin faɗa gwaggo tace "Wallahi Allah hamisu in baka dena abin da ake ba Allah sai yayi maka babbakar tsiri shifa maraya ba'a taɓa shi a zauna lafiya......wato baƙin ciki kake mata kai kana yi ita kar tayi hice ko kai ba yaron ASHARAF bane.....waya san irin arzikin da kake samu.., tana magana jiddah na gyada kai ran hamisune ya ɓaci inde gwaggo tana gidan nan to fa baza ta bari ayiwa jidda fada ba kwata kwata shekarunta nawa dan dai tana da girman jiki amma ko sha shidda bata ƙarasa ba kasa magana yayi ya juya....... Buda ta saki tace "Allah ya barmin ke gwaggo wato in har kina garin nan bani ba kuka....., dariya ta saki tace "Kululu kenan ai ni ba jahila bace irin su waya ce musu ana taɓa maraya tab ai ban shirya mutuwa ba ..... tashi tayi tsaye ba zaka kirata da kajeriya ba haka ba zaka kirata me tsayi ba wani irin sanyin kyau ne da ita zaka dade kana kallon'ta bare da ka kosa ba duk da kananun shekarun'ta amma kirjin'ta cike yake dam ga hibs kasancewar t-shirt ce a jikin'ta da jeans me irin matsai jikin nan hular kanta ta ture gashin kan'ta baƙi siɗik kitsone guda biyu wato (two step) akan'ta Fatar ta ita ba fara ba ba kuma za a kira'ta baƙa ba wata irin fatace irin chocolate colour ɗin'nan kalar yan Ethiopia baby face din Ka dauke take da idanuwa dara dara ga beautiful point ɗin ta ko magana tayi sai ya loɓa kallon sama da kasa gwaggo ke mata tace "Ke kululu bana son rashin arziki..., da sauri ta kalli gwaggo tace "Gwaggo me nayi.....?, taunar goron'ta ta ciga ba dayi bata son kayan arnan da take sawa zama tayi tace "Hmm gwaggo nace ko zaki ban kuɗi wallahi bakina ba dadi yau balango nake sha'awar ci naga kamar yau su baba lami basu yi girki ba...., ke kawo ƙunanki kiji matsowa tayi..raɗa tayi mata a kunnan ta wata dariya ta kwashe da ita tace yau za muci dabgeee saurin rufe mata baki tayi tace "Ni dadi na dake akwai shashanci maza tashi ungu wazobiya ki ziyo mana attaruhu na duka..., amsa tayi ta tashi neman mayafi take da sauri gwaggo tace "Da kata kinsan fa ni bana son dabi'ar arnan nan sa hijabi ko ki canza kaya, zumɓuro baki tayi tace "Wallahi gwaggo ni ina so..., to amma ai kululu kalle ki fa jibi cinyoyin ki yawa na bijimin sa kina tafiya mazaunan ki na rawa yawa ana buga ganga ki daure ki canza tun da nasan bakya shiri da hijabi tom shikkenan an gama uwar daki ta shiga ta cire kayan ta sa wani lace duguwar riga ta sa dauko mayafi ta yafa ko gwaggo batayi wa sallama ba ta fita a soro ta ci karo da lantana fakar numfashin ta tayi ta rufe'ta da duka sai da tayi mata lilis sannan ta tashi ta riƙe kugu tace "Wallahi lantana kadan kika gani inhar bazaki dena shiga sabgata ba....., kuka tasa tace "Wallahi Allah ya isa...ta ruga gida a guje tsaki jidda tayi ta fita tafiya take cikin nutsuwa ......✍️ *Daga alkalamin oum Yasmeen* *(Fatahiyyah Muhammad yakasai)* *HAUWA KULU WOMAN LEADER* *Perfectly pen's* *King and queen writing chamber* Story and writing *Oum yasmeen* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Domin samun cigaba kuyi following din channel dina Book 1 page 1 🔞 Ji tayi an buge'ta da sauri ta dago zata zuba uwar tijara sai kuma taga baraka tace "Baraka ina zuwa haka...da tsakar ranar nan..?, ke kai zan tambaya ina zaki ai ni kinsan inda nake zuwa Haɗa rai tayi tace "Baraka kin san halina sarai bana son rashin arziƙi ina tambayar ki kina tambaya ta..., dariya tasa tace "Maida hukar gidan gwamnati zani...., washe baki hauwa tayi tace "Dan Allah aikuwa nima gobe in zaki zani.., Tsalle baraka ta daka tace "Dan Allah gwaggo ta barki...?, guntun tsaki taja tace "Ai ita gwaggo bata da matsala inhar ina so to itama tana so kahu hamisu ne matsalata amma shima a sannu zan maganin sa.., kai baraka ta jinjina tace "Wallahi hauwa in kika shiga gidan gwamnati zaki iya da ko wanne shege barin shegun woman leader ɗin nan da basu da mutunci.... turo daurin ta gaba tayi tace "Ke nima ai woman leader zan zama..., dafa kafaɗar mara tayi tace "Uhmmm kin san kuwa zaki iya..., dariya ta sheƙe da ita baka ganin dariyar hauwa in ba mugun'ta ba zata yi ba tace "Dan Allah ai kuwa kaf garin geza sai an san da zamana ke har fadar shugaban kasa sai naje...... siyasa sanadi.., Jinjina kai Baraka tayi tace "Allah ya nufa kin ga tafiya ta..., To sai kin dawo ai zanzo kai kurun baraka ta gyada mata tayi gaba itama ta ci gaba da tafiya har ta isa gun me kayan miya washe baƙi yayi yace "A'a rabebe arnan daji kece yau a gun nawa..., haɗa rai tayi ta miƙo mai hamsin tace "Bani attaruhu......na hamsin.., da rawar jiki ya amsa saurin ja da baya tayi ta ya mutsa fuska tace "haba jolu ka dinga tsabta gaka warin da kake kaga bani kuɗina in kara gaba in siya..., ransane ya ɓaci yace "To yar hau in baki ba ai ace bake bace shegiyar jikar masifaffiyar tsohuwa.......ai kafin ya ƙarasa ta daddage ta zabga mai kasa baki diɓar attaruhun'ta tayi ta fita a guje kasa haɗe baƙin sa yayi ya shiga tofar da yahu haɗe da kasa ya bita a guje da gudu ta shiga cikin gidan su ta rufo kofar langa langa dafe gwuiwoyin'ta tayi tana mai da numfashi tasan tun da tazo gida ta tsira zuwa gobe kuma zata ƙara shammatar sa ta rama zagin da ya yiwa gwaggon'ta yar aljanna tana jin irin zagin da yake yi nan zuciyarta ta har zuƙa ta shiga gida ajiye attarun da ta siyo tayi yafi na dari...... ta shiga ɗakin da mage yake ajiye karan..... farautar mage ta kunto da yake sun saba da karan in ya kace yabi mutum binsa yake duk inda ya shiga sai ya bi wan da kanuna mai buɗe kofar tayi ai jolo yana ganin karan a guje ya fita bama takai da sakin sa ba dariya ta sheƙe da ita ta kamosa mai dashi ma'ajiyar'sa tayi gurin kahu musa ta nufa buɗe wajan da yake kiwon zaɓin'sa tayi ta kamu uwar garken'sa ta mai da ta kulle jikake tana kuyat kuyat kuyat Da saurin kama baƙin zabuwar nan tayi ta salallaɓa ta fito sai ta kanta tayi a rariya zata ta yanka saita kan tayi ta yanka ta murɗe kanta a fuka fuki ta ƙari burburwar'ta Wanke hukar tayi ta wanke gun daman kafin ta dawo gwaggo ta dora ruwa fige'ta tayi tsab ta sa gashin a baƙar leda duk bidirin nan da take ba wanda ya sani a gidan hakan kuwa baƙaramin dadi yayi mata ba dan haka ta cikin sauri take komai gwaggo tane gefe tana jajjage tace "Amma wannan attaruhu yayi araha..., ta gefen ido ta kalli gwaggo tace "In ana cin ɓaure ba'a tone tone...kawai ki ci gaba da daka, banza tayi mata har ta gama ta kwashe ta koma ɗaki tafasa zabuwar nan tayi sannan soya zabuwar nan tayi sannan ta soya attaruhun nan tayi tare albasa yaji kayan kamshi saka ta tayi a cikin soyayyan attaruhun nan ta juja'ta nan fa kamshi ya baza ko ina gafaran ku dai masu gida gaban jidda ne ya waɗi sai ta dake ta washe baki tace "Kahu musa barka da dawo wa.., mamaki ne ya kama shi to jidda hankali tayi ne ......har tana mai barka da zuwa in kana da rai zaka sha kallo ya raya a zuciyarsa yace "yauwa kululu me kike dafawa haka...kamshi ya ƙaraɗe ko ina..na garin ɗurma.., Sosa keya tayi tace "yauwa kahu zo kai ma ka kwashi rabon ka biyan bashi akai min da kaza shine nace mun dade bamu motsa baki ba bara nayi mana dabgee muciiii...yau kowa ya mai da mugun yahu...., tattare malin malin ɗin'sa yayi zuciyarsa tayi fari kal yau zai washe baki....da jajjaja..an dade ba ahaɗuba ƙaraso kujera ya samu ya zauna dariya ce ta kusab kubbucewa jidda gashi dai yana giwo amma ba wanda ya isa yaci shima ba ci yake ba sai dai su mutu ba wanda ya isa yaci aikuwa yau tasan ladan kowa na gidan nan domin sai sun tauna kashin uwar garken kahu musa tace "Kahu lafiya naga kayi hurjajan da kai kaga fuskar ka kuwa...? yawa kwan lantarki duk ta motsi..., haɗa rai yayi kome ta tuna sai kuma ya saki yace "Am kululu bara in samo kwano ki zuba min nawa naga kamar ya dahu..., Da sauri gwaggo ta fito tace "Wallahi baka isa ba ko ni ban ciba sai kai daga zuwan ka da kafa yawa katafila kana cewa a zuba maka da sai miƙe huya kake yawa murriƙen lema...anya kuwa musa kana so kaga annabi...?, me jidda zata yi inba dariya ba haɗa rai yayi ya kasa magana saukewa tayi ta zubawa gwaggo nata sannan ta zuba nata ta miƙowa haku tukunya da huya da kafafuwa zaman dirshan yayi yana ci yace "Amma kululu wallahi baki da kirki jibi wanda kika bani me maƙon ki raba dai-dai ni da gwaggo ki dau karami shine kika nuna wariyar launin fata ko....?, Kut gwaggo ta haɗe naman bakin ta taci "Kululu dauko min tukunyar nan tun da bashi da godiyar Allah....duk wanda be godewa Allah ba zai godewa azabarsa.., saurin jan tukunyar yayi ya zuge huya yace "Haba gwaggo agaban yarinyar nan kike min haka.., gyara zama tayi tace "Wato jidda anya akwai tsuntsuwar da takai zabo dadi...?, kasa haɗiye yar tsokar da ya cira yayi besan lokacin da ya zunduma ihu ba yace "Wayyo Allah na shiga uku gwaggo me kike faɗa.., saurin tashi kululu tayi ta sheƙe da dariya tana kallon kahun nata sai zare ido yake yawa wanda ya yiwa sarki karya ga dalalal da yahu da yake ya kasa haɗiyewa tace "Wayyo Allah gwaggo kahu musa bashi da lafiya abin mahaukata yake....mu gudu...kar ya murɗe mana huya kamar yarda ya murɗewa zabuwar....sa, Baba lami ce ta fito tana lasati tace "Malam ban ga uwar garken ka ba...kuma kamar kwai zata fara Allah isa ɓarayi ne suka shigo ba..., da hannun'sa ya shiga nuna su kululu yama rasa bakin magana Karab jidda tayi tace "Kar ka doramin jakar tsaba kaji su dinga bina biyan bashi akai min na zabuwa..., malin malin ɗinsa ya cire yayo kan jidda a zafafe gwaggo ta jawo shi tace "Wallahi ka taɓa ta zan ɓatar maka jidda ce tace tana son cin dabgee shine ni kuma bani da kuɗi nace ta zaɓo mana me tsoka da maiƙo a cikin zabin ka muci tun da nasan kai in na tambaye ka ba bani zakai ba shi kuma maraya ba a hanashi a bu..., wani irin tukuƙi zuciyar kahu musa take kai ya gyaɗa yawa kadangare ya dauki malin malin ɗinsa bal yayi da tukunyar cikin daga murya gwaggo tace "Kayi ball da ɗuwawun Rabi'u..., tsalle jidda tayi ta dinga dariya ran baba lamine ya ɓaci ta bar gurin ..... fakar idon gwaggo yayi ya dauki kwanon jidda ya tafi ihu jidda tayi tana ta zauna a kasa tana rusar kuka kai kace mahafin'ta da ya rage mata shine ya mutu tsaki gwaggo tayi tace "Na dawo gareki shine kika zuba naki yafi nawa Allah shiƙara da ya dauke miki.., dakata wa tayi da kukan ta zaro manya manyan idanuwanta....., ******** Cikin sauri ta ballo magani ta watsa a bakin ta ta dauki glass cup ɗin dake kan table ta sha daga shi sai trouser milk colour sai singlet ya shigo saurin boye raguwar maganin tayi da sauri ya ƙarasa cikin haɗa rai yace "Bani abin da kike sha..., gaban tane ya waɗi kut ta haɗiye wani yahu duk rashin kunyar'ta tana tsoron mijin'ta saidai komai zai yi yayi bazata iya daukar ciki ba a wannan shekarun nata da yarinyar ta ta tsofa ya ga wata ya auro mata jikinta a sanyaye ta miƙo masa kara family planning da sauri ya dago fuskarsa har ja take saboda ɓacin rai yace "Nadeeya daman ke kike hana kanki haihuwa me isa zaki min haka kinsan kuwa yarda nake son yara....?, tashi tayi ta tushe kunnu wanta tace "Please ash ka saurare ni ban yi haka ba sai dai da na tsaya nayi tunani a gaskiya bazan iya haihuwa ba sa da kananun shekaruna zan tsofa da huri ne bazan iya rainon yara ba a inzo cikin dare in kula da kai ga aikina bani da lokacin kai na balle naka sai in kara shigo da yara cikin lissafin mu...., ai ba ta ƙarasa ba ya wanke ta da mari dafa kuncin ta tayi tace "Asharaf yau nika mara...?, A fusace yace "Nadeeya ban san baki da tunani sai yau ashe daman ke kike hanani samin muradina...wallahi zan dau kwakkwaran mataki a kan ki.., cikin kuka tace "Wallahi yau a gidan mu zan kwana hulakancin naka har ya kai haka..., Ransa in ya kai dubu ya ɓaci fita yayi cikin sassarfa yake tafiya har ya isa part ɗinsa murɗa handle ɗin yayi ya buda kofar kan royal sofa ya hau ya dafe kan'sa dake tsakanin sara mai Allah ya jarab beshi da wata irin mata fadeela auran soyayya sukai amma a komai nuna mai gazawar ta take musamman ɓangaran auratayyah bata iya jure buƙatunsa a kullum cikin korafi take Allah yayi mai son yaya dole ta dau kwakkwaran mataki a kan'ta bashi da burin auran mata biyu da a yau ba sai gobe ma ya daura aure wayar sa ce tayi ruri be kula da ita ba har ta kusan katsaiwa sannan ya daga haɗe da yin sallama cikin dadtako mutumin ya amsa sallamar yace "Asharaf gobe ka biyo geza akwai Magana da zamu yi...., Cikin ladabi yace "Barka da dare to insha Allah zanzo..., yauwa Ashraf ya harkar siyasar zaɓe na ƙaratowa..ko Asharaf yace "Eh wallahi abba..., to Allah ya bada narasa da sa'a Amin ya amsa Abban nasa yace "Ya iyalin naka..., Ajiyar zuciya ya saki me nauyi har mahaifin nasa yana iya jiyowa shi mutum ne da ba'a gane inda ya dosa ga zurfin ciki yace "Tana lafiya..., sallama yayi mai ya kashe wayar tashi yayi yana zirga-zirga ya kai ya komo dole fa in har yana son farin cikin sa ta dore sai Nadeeya ta gyara halin'ta inba ta gyara fa shashin zuciyarsa ya cillo mai wannan tambayar limshe idanuwansa yayi hakan na nufin zai dawwama ba farin ciki kenan ya cillowa kan'sa wannan tambayar cije lips ɗinsa yayi ya sami gu ya zauna system ɗin'sa ya dauko aiki ya fara saurin kallon tamfatsaitsan agogon dake manne abango karfe 10:00 cikin takaici ya girgiza kai Yanzu Nadeela bazata gyara halinta ba yau shekarar su tara da aure amma bata sati biyar batare da tayi yaji ba akan ɗan karamin dalili wannan wacce irin mata ce bata san ta rufe sirrin ta ba sai daita bankada shi kasa aikin yayi ya rufe system ɗin yayi ya tashi tunani yayiwa ƙwaƙwalwarsa yawa ga na yan uwansa tabbas dole ya nemo mafita inhar fadeela ba zata gyara halinta ba bata son shiga dangin'sa ko wanne taro in za'ai ba ruwan'ta ga ƙazan'ta kwanon da taci abinci anan zata barshi saidai yan aiki su ɗauke shi mutum ne babba be daci a gan'sa a restaurant ba dole saidai kullum yana aikin order musamman ma yanzu da yake neman takarar shugaban ƙasar GEZA wayar sa ce tayi ruru sai da takusan kasaiwa sannan ya dauka yace "Innalillahi an kona ofishin jam'iya.., kashe wayar yayi batare da ya tsaya jin me za'a ci gaba da ce mai zaman dirshan yayi daman haka siyasa take ko kuma shi kade akewa haka ba me bashi amsar nan lulawa duniyar tunani yayi...... ***** Yi min shiru shasha sha wallahi ki guji ranar da asharaf zai gaji da halin ki wannan wanne irin sakarci ne Nadeela...asharaf ya manyan'ta dole yanzu yana bukatar ya'ya da kwanciyar hankali amma kin gaza samar mai ya fita waje a cazo mai kai ke kixo ki chazamai kai dame zai ji... wallahi tun huri ki dena biyewa shawarar ummi... Fab ta buge baƙin'ta to ta uwar...ubanki zata ji... wallahi mubeena ki fita a idona nawa fadeela take da har zata iya wata haihuwa girgiza kai tayi ta fita tana kukan baƙin ciki bawai dukan bakin ta da tayi bane ya ɓata mata rai aa saidan ta'kaicin halin mahaifiyar tasu duk abin da nadeela tayi to wallahi ummi ce tasa'ta ga bin masu tsubbu ko ina in taji taje Kwantar da hankalinki yar lele yanzu na fadawa hajiya saratu zata nemo mana mafita yaron ne a kwai taurin kai da yaya aka samu ya aure ki Tagumi ta zare tace "Wallahi ummi kullum har wasiwasi nake anya kuwa malaman nan suna yin aiki kuwa karkarin sa kwana uku daga nan zan rasa control ɗin ASH zai ƙara juyemin bai bai, dafata tayi tace "Kar ki damu zamuje gun malam me kankat aikin sa yawa yankan huka...., Tsalle ta duka tace "Saini uwar gida kuma amarya a gidan Asharaf imam geza A.I.G , tashi ummi tayi ta sa dariya tace "Faɗi dawai ki ƙara da ihu inde ina raye ke kaɗece matar Asharaf..., 🤔 🤔 Wani irin juyi tayi gami da rausaya tace "Shiyasa nake son ki ummi na.., dariya ta sheƙe da'ta......✍️ *HAUWA KULU WOMAN LEADER* 🤣🤣🤣🤣 Yawan sharing din Ku yawan read more # *HAUWA KULU WOMEN LEADER* 🔞 Book 1 https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Gashshan malango ta gutsura yana tururi tace "Gaskiya iliya ka iya gashi..., Washe baki yayi ya gyara hutar tsiransa yace "Allah ko jidda...., sakamakon tana tauna gyaɗamai kai kawai tayi komawa gefe yayi ya sarke hannuwansa yace "Wallahi jidda duk randa na same ki nayi babbar sa'a..., kut ta haɗeye naman kallon sama da kasa tayi mai tace "ILIYA ILIYA......taja karshan sunan tace Wallahi ka gyara kalaman ka nan da ka ganni wallahi bazan aure ba sai na zama woman leader bara in maka da manyan baki gobe insha Allah gidan gwamnati za ni nida baraka Shiru yayi ya shiga tunani can kuma yace "Jidda bakya gudun abin da mutan garin nan zasu faɗa....kinsan fa ita kanta baraka kallon karuwa ake mata sannan kina ji kina gani zaki tsoma kanki kar fa ki zo ki gujeni...., Wani dogon tsaki ta ja ta tashi ta tufar da yahu tace "Wallahi iliya baka taɓa batan rai irin yau ba har kasa naman nan da nake ci yayi min ɗaci sanin kan kane ni abin kunya baya na bashi wallahi , Ƙasa yayi da murya yace "Dan girman Allah ki yi hakuri..., gyara mayafin'ta tayi ta sashi a kafaɗa tasa hannu ta dauki takardar balangon'ta tace "Okay ni na tafi daman ai yan gidan ku kallon mara mutunci suke min ga saƙo ka faɗawa zulai na rantsai da Allah in har na ganta sai nasa su jagwal sun yanke ta a fuska daman chajimoshin na saba zuwan'ta dan nasan karshen ta a kai ni can ko huni bazan ba zan fito....., Da sauri ya kalle'ta cikin sarkewar harshe yace "Jidda kiyiwa Allah da manzon'sa ki dena abin da kike wallahi ina gudun randa yan gidan mu za suce bazan aure ki ba me zulai tayi miki...., Hannu ta tafa tace "Good question kamata yayi tun farko tambayar da zakai min kenan amma ka tsaya dogon jawabi yanxu wanne zan amsa maka a ciki kafin in tafi...., "Duka.., Zaro kyawawan idanuwan'ta tayi tace "Zan amsa maka daya amma yanxu time ya kure.., Tazarcan rigarsa ya karkaɗi yace "To sai yau she yanzu...?, Far tayi da idanuwan'ta tace "Sai nan da jibi.., Allah ya kai mu amin tace ta fara tafiya wani uban warin ganye taji tsaki taja ta laɓe a jikin wata ƙatuwar bishiya kasancewar darene ba me ganin'ta dan haka ta daddage ta maƙe murya tace "Wayyo inna ya takan Kashim kaina.., da sauri goje ya ja rigar umaruju yace "Da kata kaji kamar magana naji anayi sama sama karab a kunnan jidda ƙara maimaita tayi aikuwa tuni suka bar bushe bushen da suke duk kuwa da sunyi mankas Waige-waige suka fara ƙara ɗaga murya tayi ta maƙe'ta tace "Wayyo inna wannan mataƙi zan dauka a kan su kinga waccan me farar jamfar ya dodana min taba a kwakwalwa..., Gaban umaruje ne ya waɗi ba shiri ya zura tabar a baki ya taune ta duk kuwa da irin zafin da yake ji zare ido yayi yace "Mun shiga uku munyi gamo Allah ka zama gatana...., Jabiru da yazo yana tangaɗi ya zaune yace "Gayu ya akai naga kunyi likimo bame kwakkwaran motsi a cikin ku....ko kun luluƙa hazo da yawa ne.....?, Kuka goje yasa fyace majina yayi da hannun rigar'sa yace "Jabiru yau mun shiga komar aljanu har umaruju ya ɗoɗana mata taba a kashin kwakwalwar'ta...., Wani uban ihusa yace "Goje zance kut....ubanka kaga dan bantan uba...me kai yawa lauje ni zaka kawo wa zancan banza wanne irin aljani..buga ƙafafuwan'sa yayi wani irin ihu irin na yan tsaki jadda tayi jikake "Tsiyau tsiyau inna ga wani can ya take min ƙashin kuguna....., Zaro ido umaruju yayi yace "Shikkenan jabiru ka cuce mu yanzu Allah ne kaɗe yasan abin da zata yi mana wallahi daga yau na dena daba da shayeshaye...tashin hankali ba'a samai rana kamar daga sama su kaji tace "To inna ɗaya in shanye mai kafa ɗaya allon kafaɗa shi wancan wanda ya zo daga baya in kwashe mai ya'yan hanji...., Hannu jabiru ya ɗora akai ya saki ihu ga futsari da ya saki wani irin gumi ke karyo mai ba rayuwa ba kenan in ta kwashe mai ya'yan hanji cikin kuka yace "Goje Umaru je baku zakuyi kuka ba....nizan yi dan girman Allah ke temake ni nasan kina jina bansan kin kwan'ta ba nazo da wallahi na sani ba dalilin da zai sa in taka ƙashin ki me daraja....., Wata dariya ta bushe da ita abin ka da kauye gidaje ba a haɗe suke ba tuni ta shiga amsa kuwa curewa gu ɗaya sukai tace "Wato ku bil'adama Allah yayi muku kunnan ƙashi......kuna jina ina ihu sakamakon ballamin kashin ƙwaƙwalwa da kukai amma ko a jikin ku tun dazu kun hanani sakat na gayyato kawayena domin party cikar shekara'ta dari takwas da haihuwa kun dame su da warin wiiiiiwiii to yau zaku ci kaniyar ku bara ɗan tsitaka yazo ya kaddamar muku........., Dan girman Allah da manzonsa ki hakuri haka suka haɗa baki suka ce ɗib suka ji ba sai can suka ji tace "To inna ta ban hakuri amma zan kafa muku doka ko wannan ku ya tafi gida da rarrafe sannan kar wanda ya sake ya ƙara yin dare a waje haɗa baki suka ce to suka fara jan kafa sai da'taga sun yi nisa tafito tana kyalkyala dariya yau zuciyar'ta kyal tayi maganin shegu kofar gidan su taja ta tsaya sakamakon ganin malam yana zaune da radiyo a gaban'sa cije lips ɗin'ta tayi ta fara sanda domin bacci yace har takai kofar gida taji yace "Ja'ira zo.....nan ke nake jira juyowa tayi ta ɗurkuwa ƙasa tace "Malam gani..., Tashi zaune yayi ya kalle'ta ya girgiza kan'sa yace "Hauwa'u Hauwa'u Hauwa'u rashin ji wallahi ba inda zai kaiki ki mace ce ba namiji ba namji ma inyayi ba riba yake ci ba balle ke kina mace ki tausaya wa maraicinki ki gyara halinki Hauwa'u mahaifiyar ki mutuniyar kirkice wallahi dube ni duk narame kullum cikin jawo min magana kike ɗazu haka musa yayi min tass duk keki ka jawo min kina biyewa gwaggo Allah ya shirye-ki ya gyara min ke ni bazan miki baki ba , Tashi tayi ta karkaɗe jikin'ta tace "Amin malam amma wallahi duk wanda kaga nayi wa yimin yayi kahu musa kuwa gwaggo ce tasani nayi ta yammun..., Shiru yayi mata ya kashe radio ya nannaɗe tabarmar ya bi bayan ta ɓagaran'sa ya shiga ita kuma ta shiga bayan gida jabiru ne ya shigo dai-dai fitowar ta cikin daga murya tace "Innalillahi inna baba lami iya hansai babar su hamza kahu hamisu kahu musa malam......gwaggo ku fito yau jabiru yasha wacce tafi ƙarfin'sa yayi tumu tumu a ƙasa rarrafe yake ma...., Kowa fitowa yayi wani kukan takaici jabiru ya fashe dashi yau yana ganin darasi cin naka ne kunama ce be sani ba shine yaji an zabga mai wani uban cizo a gwuiwa ba abin ya tashi ya duba ba aljani ɗan tsitaka ya kwashe mai ya'yan hanji tambayar'sa aka shi ga yi kallon su kawai yake yana girgiza kai yana kuka kahu hamisu ne yazo zai ɗaga shi da sauri yace "Dan girman Allah ku barni kar ta kwashe min ya'yan hanji tsaki jidda ta saki ta ajiye bota tace "Kuma ku barsa yasha wacce tafi karfin kansa ne cikin saui gwaggo tace "Aikuwa dan daga gani daga kun yan iskan yaran nan yake kai dai Allah ya shirye ka jikalle zo mu shiga inda ta ajiye naman'ta taje ta dauka suka shiga ɗaki ta baje musu suka fara ci gwaggo tace "Allah yayi miki albarka in kika auri iliya kululu mun gama hutawa wallahi ke fadaman ta gaban mota ce wallahi..., ɓata rai tayi tace "Gwaggo in aure iliya kuma tab.....ai wallahi sai na zama woman leader ke fa makkan nan wallahi sai kikaga na kai ki..., Washe baki tayi tace "Dan Allah..., Gyara zama tayi tace "Wallahi...., To bayan sun gama ci ta wanko bakin'ta lokacin ba kowa a tsakar gidan sun watsai ana jiran gobe tayi a kira me ruƙiya ta kwanta Asuba ta gari ******* Karfe 2:30 na dare GEZA Government house Sa'eed mai garo ne zaune yana girgiza kafa ɗaya abin duniya ya ishe shi sai da yaja fasali sannan yace "Kwana arba'in ya rage ayi zaɓe abubuwa matsowa suke bana so in rasa kujerar shugaban ƙasa alamun da nagani al'umma sun fi son Asharaf imam geza amma zan maganin shi...., Dariya ɗaga daga ciki yayi yace "Allah ya jada ran ka ai wannan abin kabar min shi ahannu na sufa talakawa da han watsa musu tsaba shikkenan za su ta caccaka kaga mun kauda musu da hankali mu ci gaba da kwasar dukiya....., 🤔 🤔 Yusuf jirga yace "His excellency ai wannan abin ba abin da muwa bane saboda mu muke da yan jagaliya muke da yan daba ga woman leaders muna da su ban da shugaban nin local government kana ganin shi kansa matawalle zai barsa ne ya zama shugaban ƙasa bayan ba biyayya zai masa ba shi talakawa ne a ransa a tsarin ƙasar nan duk me tausayin takala bazai mulki ba wallahi......, Dariya suka sheƙe da ita Mustapha Umar jiran lokaci yace "Zan sa sojojin baka su ruɗashi da yan media sai ya gagari bacci sannan za muje gub boka ya hana shi sakat har sai ya janye....., Yusuf jirga yace "A'a ai bama so ya janye kawai ya waɗi zaɓe shikkenan ..., daga nan taro ya watsai his excellency ya shigo cikin gida da sauri Hajiya adabiya ta ƙaraso tace "Your welcome his excellency daga gun daga mata hannu yayi yace "Hajiya adabiya na gaji inna huta kyamin bayani....., Kai ta gyaɗa tace "Ka huta lafiya...., ta huce ta bar part ɗin nasa.... floor ta ta koma ta zauna najuwa ce zaune tana daddana waya zama tayi a kujerar da take kusa da ita tace "Najuwa yau shene komawar ki Jerusalem.....?, Ajiye wayar hannun ta tayi tace "End of this month.., Tunani Hajiya adabiya tayi kana tace "Yauwa sai ki tafi da yasir da basma saboda gab zaɓen mahaifin ku ba zaku zauna anan ba nika daga baya zan biyo ku sai mu huce America ke kuma ki zauna a can...., Tashi tayi tace "Okay ta shiga bedroom ɗin'ta key tasa ta kulle akan luxury bed ɗin'ta wayar ta ce tayi ruri da sauri ta daga ganin me kiran tace "Hello annuwar ka samo number tasa....?, ɗan jim yayi yace "Najuwa wallahi ban samu ba duk yadda kike tunanin mutumin nan ya huce haka nayi bincike akan sa amma abin da nasamo bazai miki dad'i ba shine abokin karawar his excellency sannan kuma yana da mata nadeeya....., Bata san lokacin da tayi jifa da pillow ba hakan kenan yana nufin bazata sami burin'ta ba komai saita nutsuwar'ta tayi tace "Hakan ba damuwata bace wallahi tun da na ɗora ido akansa naji ina ba'in son sa abu ɗaya ne matsala'ta matar'sa., Matar'sa ba ita bace matsalal his excellency shine matsal kinsan kuwa ba wanda his excellency ya tsana sama da kowa a duniyar nan face Ansh Imam geza shine mutum na farko da yake kokarin dakyile tauraruwa his excellency shine mutum na farko da yake wayarwa da al'umma kai game da mulkin damakwaraɗiya har suke ƙoƙarin fito na fito da his excellency Najuwa daman zaki hakuri ko da daddy ki yayarda tofa shi bazai yarda ba duba da irin haɗuwar da kukai mutum ne me addini dan boko kinsan wane mahaifinsa kuwa a GEZA babban malamin nan kuma alkali a kotun musulunci IMAM NASIR Muhammad geza kinsan kuwa zuri'ar gidan tarbiyya ruƙo da addini ga son juna akwai yar tsama tsakanin mahaifinki da ya Sheikh dan haka ina me baki shawara tun huri ki janye batun nan a ranki.... # *OUMYASMEEN.........✍️* *Kar ki bari ayi tafiyar book 2 bake only 🔞 please* *HAUWA KULU WOMEN LEADER* 🔞 *Gargaɗi banyarda wani ko wata su maida min littafina document ba ko audio kunyi yarda kuka gadama a destiny love Wallahi wannan karon bazan yarda ba* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Book 1 Tashi tsaye tayi ta kalli dressing mirro tace "Wallahi in har kaga ban aure shi ba to ba na doron ƙasa ......ban taɓa neman abu narasa ba.., Annuwar yace "To shikkenan Allah ya bada sa'a, Amin tace ta kashe wayar kwanciya tayi rub da ciki yayi da wanda yafi kowa sata ya lallabo yayi a wan gaba da ita ******** Da asubar fari ta sheƙa wanka wani material tasa blue da adon fari yayi mutuƙar amsar jikin'ta daurin nan tayi ture kaga tsiya ta rayata mayafi ta nemi guri ta zauna jira take gari yayi haske ta fita gidan su Baraka ... Kallon tsanaki gwaggo take nata zama tayi ta ajiye kofin kokon da ta shigo da shi ta ci gaba da taunar goron ta yar karamar wayar tace tayi ƙara da sauri ta buɗe jaka ta dauko washe baki tayi ta daga tace "Baraka gani ai tun safe na shirya ashe tafiyar ma ta asuba ce..., Ehwllh ki sauri da sauri tatashi tace "Gwaggo ai min addu'a na tafi Allah isa in shiga harkar nan asa'a..., amin kululu ki fita tayi kamar daga sama taji ance "Dan uwar....ki ina zaki, Bata juyo ba tace "Gidan tsohuwa me sai da yaɗiya nan zani..., Tana faɗa haka tasa kai ta fita da sauri ya bi bayan'ta da katawa yayi sakamaƙon ganin ɗan isiya dan daba da baraka baraka CE ta fara hawa gaba sannan sai jidda cizon yatsa sameer yayi ya juya a guje ɗan isiya ya fisge mashin ɗin Sun yi tafiya me nesa tukunna suka iso *GEZA Government House* Suna zuwa ka buɗe musu gate ɗin farko sauka sukai dan isiya ya juya wara ido jidda tayi sosai tayi tana kallon kwawacaccan gidan me kyau da tsari gaban hani hol suka tsaya cike yake damƙam da mutane maza da mata da sauri ta dubi baraka tace "Baraka badai mun makara ba...?, Samin guri tayi ta zauna tace "Ga shi kuwa kina gani in bada Allah ya hadani da dan isiya da sai an gama zamu zo.., wata tsohuwa ce ta fito taci man kwallin ga bulal hanci ta ƙwama wani tabkeken glasses a fuskar'ta cikin fara'a tace "Kawata sannun ki...., da sauri ta daga tace "Yauwa aunty Barka da safiya..., Yauwa baraka yau wallahi akwai tashin hankali a gidan nan Joseph ne ya cinye mana kuɗin da jiya muka fita wallahi yau sai dai a yi waje da ni amma sai na ci ubansa Ai bake kaɗe ba hajja ta madina billahillazi mu mun fi sheɗan iya iskanci taɓa ta shaƙa ta fesar taci gaba da cewa in banda hulakanci har mu kwana mu tashi ba muga kuɗin mu ba mu mun mai kama da wayan da zai cinyewa kuɗi yau sai naci bura......ubansa yau sai yafi fulawa laushi wankin babban bargo za muyi mai Sakar baki hauwa tayi tana kallon su inda ranka zaka sha kallo su wayan nan su waye wa kuma zasu jibga Baraka tace "Ai gwara da ya taɓo ku mu ba ya raina mu ba wallahi ku yi mai rashin arziki shege arnan banza..., Baraka wace wannan kallon jidda tayi tace "Hauwa kulu arabebe arnan daji itama harkar nan zata fara...., Sheƙewa sukai har da tafi suka ce "Muna yi miki barka da zuwa gidan shege da shegiya dan banza da na kirki duk wanda kika gani buƙatar kansa ce ta kawo shi..., Zaro ido tayi tace "Ai kuwa ya sami dai-dai da shi ni warki ce dai-dai ƙugun ko wanne ɗan iska sai na gyarawa ko wanne shege zama...ni hauwa kulu woman leader GEZA ban fito sai da na shirya...., Hannu suka bata suka tafa luba tace "Zaki iya ai daga ganin idon ki zaki aikata wannan fagen yafi son mara kunya...., Dariya tasa tace "Tun da Allah ya haɗani da ku nasami dai-dai da ajina...., Hajja ta madina tace "Bara in gabatar dake gun barɗe ka shuka tsiya ka gama lafiya....., Zaro ido tayi tace "Badai shugaban yan bakan Radio ba...., Luba taja taba tafesar tace "Shifa zo muje kafin muci bura...ubansa la'ada waje..., Bin su tayi suka bar baraka ta shige cikin hol ɗin Gaban wani kwatatcan lambu suka tsaya waya luba ta fito da ita tayi dan danne danne ta kara a kunne tace "Shegen gari kana ina ne....?, Daga can ɓangaran yace "Ina cikin lambu..., Tsai wayar tayi tace "Zo mu shiga to tace ta bisu samun sa sukai a zaune ya ɗora kafa daya kan ɗaya yana busa yahaƙi jan kujera sukai suka zauna nima ganin tsayuwa ba zata kai ni ba na zauna cikin sanyin murya nace "Ina kwana...., Cire glasses ɗin'sa yayi yace "Lafiya qalau luba yar jila ina kika samu wannan....?, Far tayi da idanuwan'ta tace "Sabuwar yar gwagwarmayar siyasa muka samu me jini a jika...., Dariya ya sheƙe da ita yace "Daman honourable Mustapha Umar jiran lokaci ya sani in samo sojojin baka wayan da zasu yaƙi waccan gurgun magen to zaki iya....., Dan jim tayi tace "Yi min bayani yadda abin yake...., ajiye tabar hannun'sa yayi yace "Bani abu bane me huya zaki shiga gidan Radio GEZA zan rubuta miki komai zaki karanta tare ma zamu yau za ayi hirar Insha Allahu muka ga aikin ki yayi kyau tofa zamu yi tafiyar nan dake..., Jikin'ta a sannayaye tace "To..., Tashi sukai suka bar luba yar shila a gun suka ci gaba da busa taba yawa ba gobe # *oum Yasmeen* *HAUWA KULU WOMEN LEADER* *Ban yarda wani ko wata su mai damin da littafina Document ba ko audio wallahi kun yi min yarda kuka ga dama a DESTINY LOVE wannan karon bazan yarda ba kar wanda ya samin shi a website ba tare da sani ba* *Masu yimim fantan alkairi ina godiya my lovely fan's my real fan's masu yimin aka sin haka ma ina godiya daman shi ɗan adam ba'a iya mai 🤗😏* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Book 1 🔞 Lumahe idanuwan'sa yayi kansa ke masa wani irin ciwo abubuwa sun mai yawa wayar'sa ce tayi ƙara share'ta yayi ganin me kiran yana ƙara nema ya tunzura ciwon kan'sa ya ɗaga cikin muryar shagwaɓa tace "Honey kazo gida in anjima mu tafi.... wallahi nayi kewar ka.., Wani takaici ne ya tukare mai huya yace "Bada sa hannuna ba kika tafi dan haka kar ki ƙara kirana akan wannan maganar wallahi nadeeya in har bazaki sauya ra'ayi ba tofa kina gab da rasani ta har a bada sanin kankine bana son yin mata biyu amma kiyi ƙoƙarin kaini bango me al'umma zasu ɗauke ni nakasa riƙe gidana ina neman ƙarin nauyin al'umma da dama..., cikin ɗaga murya tace "Sai me Asharaf kafito fili kace min aure kake nema kadeba kwana kwana wallahi in har ina numfashi asharaf bakai ba wata mace wacce mace zata zauna dakai bayan nima zaman hakuri nake dakai...., Be jira me zaka ƙara cemai ba ya kashe wayar dole zai tauna aya ɗan tsakuwa taji tsoro amma wazai aura wace zata iya riƙe mai sirrin sa wacce mace ce zata yi dai-dai da ra'ayin'sa turo kofa akai aka shigo da sauri ya dawo hayyacin'sa yace "Wa'alaikas salam jafar..., Zama yayi yace "Abokina lafiya ka lula duniyar tunani ko dai har nauyin ƙasa ya fara hawa kan ka...?, ɗan murmushi yayi jafar baya rabo da abin dariya yace "Ina file ɗin....?, Miƙo mai yayi buɗewa yayi yace "Wayan nan sunayan mene amfanin su....?, Shugaban jam'iya ne ya bani yace sunan wayan da zaka bawa kwangilane in Allah ya bamu nasara sun yi hidima da jam'iya...., Tsaki yayi ya ajiye yace "Wacce hidima ba cancanta za a duba ba ina cewa Sani me dala shi ne wanda efcc ta kama tana zarginsa da amsar kuɗade batare da yayi aikin da aka sa shi ba tsohon shugaban jam'iyyar adawa ta NBB ne ya dawo tafiyar nan saboda sun ƙi bashi wasu kuɗaɗe...., dafa kai jafar yayi yace "Wannan haka yake wai me isa a yan kwanakin nan bara gurbi suke yawan shigowa jam'iyyar nan anya ba kura bace da fatar akuya..... Wata kila kasan haka suke in suka ga mulki yana yane neman ƙarewa sai su koma jam'iyya me ci nidai wallahi cancanta zanbi duk wanda na bincika ya taɓa sama da dukiyar al'umma bazan yi tafiyar nan da shi ba saidai suyi abin da za suyi ace duk azzalumai suka taro suke mulki ba me son al'umma ..., Hakane Allah ya datar da mu yanzu kenan bazaka sa hannu ba ..? dafa kansa yayi yace "Jafar kamar bada hausa nayi maka wannan bayanin ba kace mai na ajiye zan duba shi...., To yace mai ya tashi ya fita ɗaukan mukullin motar'sa yayi tare da brief case ɗinsa ya fito cikin nutsuwa yake takawa wanda be sani ba zato zaiyi ɗan ɗin gisa ƙafar da yake gayo ne duk inda me kyau yake ya kai cikar haiba da kalama suka bi suka mai da shi wani irin nagartatcan mutum ilimi hutu jin dadi fatar sa yawa kafasa jini ya fito ba macan da zata gansa ta ɗauke idon'ta akansa shiyasa mata da yawa suke ɗilmiya cikin kogin'son sa kallo ɗaya zakai mai kasan a cikin maza ma sunan sa mazaje Da sauri John ya karɓe jakar hannunsa buɗe mai kofar mota yayi gurin me zaman banza ya shiga zaka yowa yayi ya shiga ya fara tuƙi a hankali yake tafiya har yabar katafaran asibitin nasa Kai tsaye hanyar GEZA suka nufa jaridar**CIKI DA GASKIYA DAILY NEWS** ya ɗauka gabansa ne ya waɗi da sauri ya ɓan ƙaɗa shafin Farko inda ake cewa Asifiya yau ne Jidda ita da Barde Tsula tsiyar ka ka gama lafiya suka cakcaki ɗan takarar shugaban kasa Inda suke bayyana al'umma cewa Asibitin koyarwa na jami'ar A.I.GEZA Teaching general hospital ya daɗe yana kashe rayuwa kan al'umma sakamakon ma'aikatan sa ba ƙararro bane Sauri rufewa yayi be karasa karantawa ba wacce wannan jidda woman leader dole ya nemo ko ita wacce ɗaukan waya yayi cikin sauri ya shiga nemo number ɗin hamisu bugu ɗaya ya dauka cikin girmamawa yake gaishe shi Amsawa yayi yace "Hamisu ka duba jaridar ***CIKI DA GASKIYA*** abu na biyu ka binciko min wacce wacce sukai hira da Barde a ina take zan dau komai amma banda sharri da taɓa martabar iyayena da addini na Cikin ladabi yace "To katsai wayar yayi dai dai isowarsa gaban wani tabkeken gida daga gani kasan me gidan baƙaramin attajiri bane a kofar gidan yayi parking fitowa yayi ya shiga cikin gidan cikin taƙunnan nasa na kasaita yake tafiya har ya isa kofar da zata sada shi da floor mahaifinsa cire takalmin sa yayi ya shiga baƙinsa dauke da sallama ya shiga Samin sa yayi yana kishin giɗe gaban sa kayan marmari ne ga ƙira'ar al'kur'ani ɗaukan remote yayi ya kashe cikin fara'a yace "Sannun ka da zuwa uban masu gida..., zama yayi cikin ladabi yace "Barka da war haka abba da fatan ka tashi lafiya...., Tashi yayi zaune yace "Lafiya qalau asharaf ya iyalin naka....?, Ƙasa yayi da idanuwan'sa dan ƙaramanin aikin mahaifinsa ne ya iya gano wanne hali yake ciki yace "Alhamdullahi na same ku lafiya.., Tufa mahaifinsa ya gutsura yace "Lafiya qalau ɗauko waccan jakar....., Tashi yayi ya dauko ta ya ajiye a gaban mahaifin nasa Abba buɗewa yayi wani daɗaddan photo ya dauko miƙawa asharaf yayi Amsa yayi ya duba gabansa ne ya waɗi na hannun dama ya tabbata mahaifin'sa ne na hannun hagu kuwa kamar su ɗaya sak yawa an zana shi lokacin yana yaro Dauko wani kaya yayi na sojoji lumshe idanuwansa yayi tuni kwallar da ta cika kurmin idon'nasa damar zubowa cikin kiɗima Ansh ya ɗauko tissue ya miƙawa mahaifin nasa ƙin amsa yayi yace "Muhammad gwara ka barni nayi kukan da najima ina so inyi Muhammad wannan na gefen nawa shine mahaifinka bani na haife ka ba.., Cikin kuɗi ma ya juyo ya kalli mahaifin nasa buɗa baki yayi zai magana abba ya daga mai hannu yace "Dalilin da kuwa yasa na fada maka nasan zuwa yanzu ka mallaki hankalin kan ka in zaka tuna lokaci kana yaro har zuwa girman ka bana barin karaɓe kowa ciki kuwa harda matana babban tashin hankali da na shiga lokacin da ka kawo min fadeela a matsayin matar da zaka aura har istahara nayi.... naga ba makawa sai anyi wannan auran shiyasa na haƙura ka aure'ta...., Ɗan nisawa yayi ya cije lips ɗinsa yace Shekara arba'in da biyar bayan Muhammad Yusuf Maɓaya shine asalin sunan mahaifinka ɗan asalin karamar hukumar maɓaya ne dake GEZA aiki ya kawo mahaifinsa GEZA BUZUNU ne inda ni kuma mahaifana barebari ne aminina ne na kut da kut haka muka taso cikin so da kaunar juna haka ma mahaifan mu aminai ne sai an faɗa maka sannan zaka gane cewa mu ba yan uwa bane Da muka gama secondary ni na zaɓi low inda na tafi jami'ar ibadan dake Nigeria naje na karanci low shi kuma ya zaɓi zama soja sai da aka kai ruwa rana tukunna aka kyale sa tare da binsa da addu'a Cikin hukuncin Allah muka fito da sakamakon me kyau bayan mun gama ni na sami aiki a koton musilci dake garin geza Inda shi koma suka tura shi barikin sojoji ta Afrika ta Kudu badan iyayan mu sun so ba haka suka haƙura ya tafi Ni kuma ba dadi nayi aure ba amma shi Muhammad ba zancan aure a rayuwarsa dan ko waya muke na ce mai yau she xai aure sai yace sai Allah ya nufa har matata saudat ta sami ciki Muhammad be dawo ba Ko sau daya be taba bani labarin takurawar da shugaban ninsa suke mai ba akan roƙon gaskiya da amana Cikin saudatu ya girma wata rana Litinin ta haihu amma dan barai ko da jin haka sai Muhammad ya dawo Duk wannan kyan nasa yayi baƙi ya rame na yi tambayar duniya ya faɗa min meke damun sai sai yace tension din aiki ne Kwansa biyu yaje maɓaya tare dani mun zaga ɗanginsa ana haka ya hado da khadiya ba adade na akai auran su ya dauke'ta suka tafi in da yake aiki Mahaifiyarta bata son auran saboda kankantar shekarun ta saidai Allah ya nufa matar sa ce Tafiya ta nisa tun muna samunsa a waya har abu ya faskara mahaifin nabeela shima sojane dan haka yau naji ance yazo na wanke kafafuwana Na tafi unguwar ɗan burmu sallama nayi a kofar gidan su shiru ƙara sallama nayi huru huru na shiga yi domin inne mo yaron da zai shiga yayi min sallama da shi gabana ne ya waɗi lokacin da kunne na suka jiye min bakin labari Mahaifin nabeela ne ya fito yana waya yace "Oga ya tura kanal Muhammad Yusuf maɓaya yaƙin tsibirin birni nanɗi amma da biyu ya tura shi in ya je can bazai dawo ba za'a kashe shi shi zai jagoranci yaƙin tsibirin birni nanɗi..., Bansan me aka ce mai ba naji ya bushe da wata mahaukaciyar dariya da baya da baya ba juya ban zame a ko ina ba sai a tashar mota Wacce zata kaini Nigeria kwanana hudu ina tafiya tukun na na isa Afrika ta Kudu Da yake lokacin da akai bikin naje nasan gidan sallama nayi Khadijah ta fito da tsohon ciki ta buɗe min har ƙasa ta gaishe ni na amsa nace "Lafiya kwana biyu bama samin wayar me gidan ki...., Hawayan da take riƙe wa suka sami damar kwaranyo wa tace "Yau wata guda kenan da tafiyar sa birnin nanɗi...nima tun ina bugawa ina samu ba'a dagawa har ta dena shiga..., Innalilahi wa'inna'laihir raji'un kalmar da nadin ga faɗa kenan Wata baƙar mota ce ta tsaya a gaban gidan nasa yayin da wasu suka fito dashi ruƙe da cikin sa yayi wani irin fari kal suka ce "Sun tsince shi a ƙabar tekun sindi sun duba jikin'sa suka ga information ɗin'sa godiya mukai musu suka tafi......inda suka ajiye mana wannan kwatin da take gaban ka Tashin hankali da dimuwa yasa mahaifiyar ka atake anan ta fara kaƙuda da maƙoncin su da matar sa tare muka kai Muhammad asibiti kallon ana haihuwar ka aka kawo ka gunsa..... Duk halin irin na ciwon da yake ciki hakan be hanashi daukan ka ba ya samaka albarka...naga baƙar rana guna dawo min da kai yayi ya damkamin amanar ka da ta Khadijah da kuma jakar da ya dawo da ita ya cika da kalmar shahada.. Iya firgici na shiga haka Khadijah itamana tana ji ya mutu ta bishi haka mu ka kawo gawarsa gida su nanne sun shiga tashin hankali domin iya shi suka mallaka binciken likitoci bayan harbinsa da akai har wata guba an bashi a hankali take mamaye jiki sai dai kawai aga mutum ya mutu haka na dauki ragamar komai ta rayuwar ka domin ban bawa su nanne kai ba ni na ke kula da kai ba ruwan saudatu da kai.....akwai lokacin da har sakin'ta nayi sakamakon ture ka da tayi ka waɗi shine sanadiyyar ɗingishin nan da kake Kabi a hankali Asharaf bance lallai sai ka faɗa min abin da ke faruwa da iyalanka ba amma jikina ya bani akwai wata munufa da yasa mahaifin nadeeya ya baka yar'sa bayan baya son mahaifin ka da haɗin bakin sa aka kashe da wasu manyan ƙasar nan na fara bincike abun ya faskara direct daga aka aikomin da takarda daga fadar shugaban kasa cewa in janya hannuna daga batun kisan kanal Muhammad maɓaya ba daddara ba na ci gaba sai da sukai min barazana da kai sannan na haƙura Mutanan gidan nan ma ba abin yarda bane saboda ko su nasan suka sami dama wallahi sai sun aikaka lahira ASHARAF wata irin sarkakiya ke tare da banso Ka shiga siyasar nan ba Asharaf saidai na fahimci burin kane Iɗagowa yayi idon'sa yayi ja jijiyoyin ƙansa sun fito rada rada da kyar ya iya buɗa baki yace "Abba jininsa bazai taɓa tsulwan'ta a banza ba insha Allah sai duniya tasan wayan da suka kashe shi ƙasar nan an gina tubalinta a rashin gaskiya duk wanda zai gaskiya ɓatar da shi ake....., Fito da wani littafi yayi duk yayi kora yace "Ungo wannan shine mahimman abu da sa mahaifinka yace abaka wannan akwati in Ka girma kaje kai bincike akai..., Amsa yayi hannu bibbiyu ya riƙe yace "Insha Allah komai zai zamo karshe nima akwai wasu ayoyin tambaya da nasawa mahaifin nata da ita kanta saidai duk abin da suke ina lura da su yanzu ainiyin wasan zai fara..., Kai ya jinjina yace "Allah yayi maka albarka ka cika ɗa na ƙwarai.., Amin yace sun ɗan tattauna wasu batutuwa akan takarar sa yayi mai sallama ya fita kai tsaye gurin hajiya sauda ya nufa dan mutuncin abbansa badan halinta ba Saminta yayi a zaune ta ɗora kafa daya kan ɗaya baƙinsa dauke da sallama ya shiga sauran yaranta suka amsa mai kadaran kada ham suka gaishe shi gaishe'ta yayi cikin mutun tawa Ɗan yatsuna fuska tayi ta amsa mai a guje wata sanye da riga da wando ta fito ƙanwar hajiya sauda ce yar autar su cikin so da kauna tace "Ya ansh barka da warhaka..., Tashi yayi cikin halin ko in kula yace "Yauwa ya juya yace na tafi ba wanda ya tamka maganar'sa ya fita shima ko kuwa ko a jikin sa dan adam yasan hali Komawa gun abba yayi ya dauki akwatin nan yafita kofar gida yayi tuni ya cika damƙam da mutane da yake duk sanda zai ziyarci mahaifinsa sai sun taro kuɗi ya bawa john yana rarrabawa Dakyar suka barsa ya huce tafiya me nisa sukai kafin suje inda gidansa yake Gaban wani tabkeken gida suka tsaya John yayi horn me gadin ya buɗe Parking space ya shiga inda ya ajiye motar ya fito ya buɗewa uban gidan nasa ya fito cikin izza yake tafiya John biye da shi har izuwa kofar da zata sada shi da shashinsa Amsar akwatin yayi John ya juya shi kuma ya shiga ciki ******* Sai yamma liƙis suka dawo gida a kofar gidan su me a napep ya kawo ta sauka tayi ta biyashi kuɗinsa ya ƙara gaba da baraka.....sanadin program ɗin nan da tayi gwamna ya cika mata jaka da kuɗi dan haka yau ji take tana shawagi a sararin samaniya da yar wakar'ta ta shiga gidan kahu hamisu ta yi kicibus da shi a tsakar gida cikin baƙin ciki ya kalle'ta yace "Yanzu jidda abin da kikai ya dace to wallahi bazan boye miki ba A.I.GEZA yasa inyi bincike akanki yace zai yarda ba wallahi in yayi miki wane daurin ko su wayan da suka saki basu isa su kunto ki ba...., Wani takaici ne ya kamata tace "Kahu wallahi siyasa yanzu na fara faɗuwar gaba a sarar na miji kasani sarai bana jin tsoro wallahi in ya fasa shi ba ɗan halak bane...., Tau ya dauke'ta da mari da sauri ta kama kuncin'ta tace "Ni ka mara to wallahi yau kowa na gidan nan bazai kwana cikin kwanciyar hankali ba MUZU BA MUGA NI ( shin KO kinsan me littafin MUZU BA MUGA NI nace kin sani ko kema ambarki a baya....?) tana kaiwa nan ta shiga ɗaki gwaggo ce ta fito cikin kumfar baki tace "Wallahi hamisu ka fita a idona in rufe kowa na gidan nan ya tsani marainiyar Allah nan.., Cikin takaici yace "Gwaggo yarinyar nan siyasa fa tashi ga ....., Turo daurin ta gaba tayi tace "To sai mai hamisu karkai ma ka fara yi mata hassada ne dan kaji muryar ta a gidan rediyo tab wallahi ka shiga hankalin ka tun kafin Ubangiji yayi mak kunar baƙin wake dan kaga shi wancan me fubfar kafurawan farko ba shi take ba ta tafi siyasar su tsula tsiya ka gama lafiya yo kululu akwai wayo ba ta tsaya fagen su yan kuci ku bamu ta tafi sama ɗoɗar..., Wani kululun takaicine ya tukare mai ma ƙogaro yace "Gwaggo ina jiye miki ranan na dama wallahi domin kar jidda ta ɗebo abin da yafi karfin ku..., Tub aniyar ka ta bika masaharranci ba ruwan ka da ita Fita yayi domin bazai iya zaman gidan ba shi yanzu besan me zai fadawa oga ba jidda ta cuce shi wallahi Cikin gida kuwa tana shiga ta cire kayanta zama tayi daga ita sai daurin kirji tana lissafa kuɗin da ta samu dubu hamsin cas gwaggo ce ta shigo ta washe baki tace "Kululu duk wannan su suka baki....?, Ajiye su tayi a gefe tace "Eh wallahi zan ware kuɗin motar tafiya kamfen sannan in baki ke da malam..., Buɗa tasaki tace "Ta gaban mota insha Allahu wata ran sai kinyi Kwamishina...., Cikin farin ciki tace "Amin gwaggo...gobe ma da huri xan fita zan raka gwamna kamfen..., Tashi tayi ta fita gun tattabarun'ta ta shiga buɗe su tayi fur suka fito suka tsagaye'ta gero take watsa musu suna ci suna hawa jikin'ta takan shiga farin ciki inhar tana tare da su ji take bata da wata damuwa.....baba lami ce ta fito tace "A'a woman leader kin dawo...?, ɗaga gira tayi tace "Ga shinan kuwa kin gani.., Ɗan dam baba lami tayi tace "Kululu yar gidan gwaggo nace ko zan sami rancan dubu wallahi jarina ne ya karye.., Wani kallon up and down tayi mata baba hansai ce tafi to hannun ta rike da buta da alama makewayi zata shiga Cikin dan habaici tace "Allah ka kara bamu da haifar ya'yan kuka..., Yaron'ta ne ya tsala ihu da yake sabuwar haihuwa tayi da sauri ta ajiye botar cikin sauri ta koma dakin'ta Kallon baba lami jidda tayi ta saki wani banzan murmushi tace "To jeki zuwa safiya zan baki rance amma Wallahi duk randa na bushi iska baki biyan ba tofa duk abin da nayi miki ke kika jawa kanki...., Da sauri tace "A'a zan ma biya ki nagode.., Banza tayi mata ta ci gaba da watsa musu hatsi Allah Allah take baba lami tabar gun aikuwa ta gaba yan abun da za ta yi ta bargun da sauri jidda ta watsar da hatsin hannun'ta ta shiga ɗaki Kullun wani abu ta dawo da shi cikin sanda ta buɗe wannan butar ta hansai ta juyai tsidugu tas a cikin ruwan nan kusan rabin leda fara a inda ta ajiye ta sa shi.....ai daman da tasu da mijinta dazu har shi zai mare'ta ya manta da Wacce jidda woman leader wanka ta shiga fitowar ta kenan hansai na tsaye tana jiran'ta yi tayi kamar bata ganta ba Ta bangaje ta ta shiga makewayin jidda bata kulaba ta koma ɗaki daman tayi al'wala jira take a kira sallar magariba tayi Wani irin wahalallan ihu hansai ta saki.........✍️ *Oum yasmeen* *HAUWA KULU WOMEN LEADER* *Banyar da wani ko wata ya mai da min wannan book audio ko document ba bazan fitar da document ba kuma ban bawa wani ko wata document na wannan littafin ba* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k 🔞book 1 *Typing..................* Wani irin wahalallan ihu hansai ta saki da sauri kowa na gidan ya fito ban da jidda da take kwance tana dariyar keta Fitowa tayi tana dafe bango tana tale kafa dafe kirji gwaggo tayi tace "Na shiga uku badai yaran da suke haurowa gida suna yiwa matan mutane ba sun kamaki hansai ji yadda kike tale kafa yawa wacce akai wa fyade..., Cikin yanayin azaba tace "Gwaggo barkono aka zabamin a ruwan da zan shiga bayi da shi...., Tunu gwaggo ta harbo jirgin me ya faru amma saboda bata ganin laifin jidda tace "Ke hansai bana son shashancin banza wa zai zuba miki barkono a ruwa...kidai nemi wani abun badai wannan ba, Kahu hamisu ne ya shigo yace "Lafiya nagan ku anan kunyi cirko cirko.., Tsaki gwaggo tayi tace "Wannan alimar matar ka ta tara mu inban da iskanci ta zuba barkono a buta tace zuba mata akai wata kila wata shegiyar ce zata ce maganin gyaran gaba ne..... saboda ita tazama me kan dosa ta dauka dan kaji zam-zam ai gashi ita taji a jikin'ta...., Ƙasa yayi da kansaa yace "Hansai shige mu shiga...., Cikin takaici tace "Wallahi jidda ce tayi min wannan aikin ba ɗazu ka mare ta ba...., Da sauri jidda ta ɗaga labulan ɗankin'su tace "Innalillahi wa'ina ilaihir raji'u ni kuma kiji tsoron Allah kuka tasa harda shashsheƙa tace Yanzu gwaggo kina gani ana cin zarafina dan anga bani da uwa wallahi yau bazan kwana a gidan nan ba gun inna ta gabas zani Kamo jidda tayi ta rungumi tasa kuka tace "Wallahi Allah zai saka mana yanzu dan rashin mutunci a gabana kuke cin zarafin yarinyar nan kai sokon banza kana tsaye kana jin baka ɓarar mata da haƙoraba ta rasa na zawarcii..., Ransa ne yayi matsifar ɓaci yace "Inna Dan Allah kiyi haƙuri....., Kahu musa ne ya shigo yace "Jidda gani na dawo zo ki bani kaso na duk inda nayi a garin nan cewa ake kinyi kuɗi nima figa min nawa kason...., Turus yayi ganin abin da yake faruwa yace "Lami me yake faruwa....?, Ina zan sani me gida hansai ce da wani abu wai jidda tasa mata barkono shine gwaggo take kuka Ai kafin ta ƙarasa wani zancan ta suka wasai sakamakon karurnuƙan mage da suka shigo da alama ya dawo ga yawan nasa Ihu ya saki yace "Dawa dai malam sai Ni uban mafarautan garin nan sai Ni wan kulu annuba cau cau cau an ja dani an barni.., Jidda ce ta fito ta saki buɗa tace "Duk wanda yace zai ja damu tofa karshan sa yazo....mukan hana mutum bacci..cau cau Ni RABEBE ARNAN DAJI..., Da sauri kahu musa ya fito har yana harɗewa da rigarsa yace "RABE anya kuwa kana da hankali..? kullum kana girma kana ƙara shiga dawa yau kwanan ka nawa rabon ka da ga gidan nan...wallahi Rabi'u dole in gyara maka zama a gidan nan.., Muciji ne ya fito ya tsaya ya saita kahu Musa mage yace "Kahu Allah yayi maka tambaya to kai bashi amsa danni bani da lokacin ka....., Zare idanu ya shiga yi yana waige waige yace "Dan girman Allah jidda mage ku yi min rai...., Dariya jidda ta sheƙe da ita tace "Kahu yanzu zan dauke maka shi amma gum ba ruwanka da shiga sha'anin da ba'a saka ba..., Da sauri ya ɗaga kai yace "Na yarda kululu yar gidan gwaggo..., Danna remote control ɗin mucijin yayi na ruwaba ne ai kuwa tuni ya dawo kusa da shi ya hau jikin'sa da sauri kahu musa ya bar gun dariya jidda ta shiga yi tace "Ya mage ina ka samu wannan mucijin roba me kama da na gaske...., Dariya ya sheƙe da ita yace "Kar inji abakin wani kiyi shiru yau mutan gidan nan sun shiga uku a tsakar gida zan ajiye shi duk wanda ya fito yayi farin gani...., Kai ta gyaɗa mai kasancewar an kira sallar magarib duk abin jidda tana da roƙon ibada da sauri ta shiga ɗaki tace "Ya mage tafi masallaci an kira sallah..., Idanuwan'sa ya zaro da yasha kwalli yace "To tasallah in nayi lokacin da na gadama kar ki amsa.., Girgiza kai tayi ta shaga ɗaki ******* Tafiya yake cikin natsuwa sai ka kula zaka san yana motsa baƙin'sa tasbihi yake ga ubangiji madaukakin sarki ɗan taƙi kallan yayi ya zo gida Da yake tsakaninsu da masallacin ba nisa tura get yayi sai ya tarar a buɗe da sauri ya shiga cikin gidan ko ina me gadin gidan ya shiga...... Tarar wa yayi baya nan da sauri ya koma ya rufe kamar ance kalli can megadin ya gani tare da nadeeya yana binne mata wani abu saurin komawa ciki yayi ya zauna a floor sa aiki ya shiga yi Sai guraran goma sha biyu ya tashi lokacin yasan nadeeya tayi bacci cire kayan'sa yayi ya sa marasa nauyi tare da face mask ya fita Cikin sanda yaƙe tafiyar har ya ƙarasa gun nan tuna gun ya shiga yi sunyi haƙa me zurfi tukun na ya gano fukafikin kaza da alama da ranta aka sata an rufe bakin'ta cikin rashin tsoro ya buɗe baƙin cin karo yayi da laya zurawa yayi a ajihun'sa ya rufe gurin ya wullar ga ƙazar a waje abin duniya ne ya ishe shi be gane yayi zaɓen tumun dare ba Sai a wayan nan kwanaƙin waje su neme shi haka gida ma to da me zai ji ..... Komawa yayi shashinsa toilet ya shiga tuɓe ƙayan'sa yayi cikin kyam kyami ya shiga wanke hannunsa duk kuwa da safar da yasa ya daɗe yana wanka tukunna ya fito daure da towel Gaskiya ansh ba ƙaramin ingarman namiji bane jikinsa duk a murɗe yawa ɗan dambe ji yayi an turo kofar be joyo ba ci gaba yayi da jafa mai ta maya ta rumgume shi tace "My man kai hakuri nasan na ɓata maka wallahi nakasa bacci..., Ture hannun'ta yayi daga jiki sa ya ci gaba da shiryawa akan mararsa ta ɗora hannunsa tasan wannan ɓangaran bashi da sauran zaɓi wanda ya huce ya bita ɗan murmushi yayi a zuciyarsa yace "Yau nadeeya zan shayar dake ruwan mamaki...., Kunce towel ɗin tayi saurin roƙo towel ɗin yayi cikin i don't care...yace "Nadeeya me kike yi haka yanzu bani da wani interest akan wannan abun Please ki barni na gaji...., Cikin sauri ta ɗago kai ta kalle sa bakin'ta har rawa yake tace "What.....my man me kake faɗi to aini ina da shi..., Idanuwan'sane suka kaɗa sukai ja cikin tsawa yace "Nace ni bani da shi ko ana dole ne...., Zancan da kullum take faɗa mai kenan in ya kawo kansa gare'ta Cire yaloluwar rigar baccin da tasa tayi kau da kansa yayi yace "Please fita zan yi sallah..., Kallon agogo tayi karfe ɗaya har da rabi cije lips ɗinta tayi tace "Okay...ta zura rigarta futa tayi ko rufo kofa batayi ba gama shiryawa yayi ya zura jallabiya ya kullo kofar'sa shin fiɗa prayer mat yayi ya tada kabbarar sallah A sujjadar'sa ta ƙarshe ya dade yana neman zaɓin Allah akan mulkin nan da Allah in ya bashi ya bashi inƙon sauke nauyin da ya daukarwa kansa sannan yayi wa ƙasar tashi addu'a tare da iyayensa ɗagowa yayi yayi sallama sannan ya ƙara ɗaga hannunsa ya miƙawa Ubangiji kukansa Tashi yayi ya kashe ko mai ya cire jallabiyar sa addu'a yayi kusan karfe uku da rabi ya kwanta ya ja blanket me uban taushi ****** Washe gari da sassafe kahu hamisu ya amsa kiran A.IGEZA a office ɗinsa ya tarar da mutane dan adan haka kuma sai da ya jira shi bayan ya gama sallamar mutane ya shiga gaisawa sukai cikin mutum'ta juna haka babban amininsa Shuram Abubakar suka gaisa ANSH yace "Ka binciko wace ita...., Gabansa ne ya waɗi besan da wannan baƙi zai faɗamai jidda a matsayin ya'take a gunsa kauda wannan tunanin yayi koma mene ai ita ta jawa kan'ta yace "Yar wanace..., Da sauri shuram yace "Yar wanka...?, daga kai yayi alamar tabbatar wa yace "Gwaggo ita ce silar taɓarɓarewar jidda bata son lefin'ta ko kaɗan daga dan girman Allah ina nemawa jidda afuwa yarinya ce yar yanzu ko sha shidda bata rufa ba..marainiya ce bata da uwa.., Shiru ANSH yayi yana juya biro tukunna yace "Bakomai Malam hamisu kafi karfin haka a guna.., ya dan dade tukunna ya bar office ɗin yana bari shuram yace "Man kaji wani abun takaici daga yaron da bashi da uwa ko uba yayi abu sai ace marayane shi besan bashi da gata ba yake aikata abin da ya gadama ni wallahi banga dalilin da zanbar ƙaramar yarinya tana shiga siyasa ba ko gujin daukar muguwar ɗabi'a basa yi..., Ajiyar zuciya ya sauke yace "Allah ya kyauta, shuram yace "Amin...ya nadeeya...?, Cije lips ɗin'sa na ƙasa yayi yace "Ba canji jiya i yau..., Dan jim shuram yayi tukunna yace "Ga shawara me zai hana ka ƙara aure hakan zai sa ta gyara halin'ta..., da sauri ansh ya daugo yace "Aure kuma...?Ni yanzu bani da burin ƙara aure.., wallahi in har kana buƙatar farin ciki dole ka ƙara aure ka auri ƙaramar yarinya wacce kai zaka koya mata yadda kake so ta zama me zai hana ba zaka auri wannan WOMAN LEADER ba ka jefi tsuntsu biyu da dotsai ɗaya ka gasa mata aya a hannu ko daga baya ka sake ta kaga kai maganin'ta ta cikin ruwan sanyi a kullum jifan ka take da mugayan maganganun in wani be dauka ba wani zai dauka kai tunani Da sauri yace "Shuram kana da hankali kuwa....me zanyi da wannan yarinyar bayan kuma ba mutuniyar kirki bace yarinyar da take yawa tsakanin maza ba kunya ba tarbiyya kana dai ji abin da dan uwanta yace akan'ta..., Dafa kafaɗar'sa shuram yayi yace "Calm down man ka yi tunani hajadi fa zakai.., Sakar baki Ansh yayi yana kallonsa yace "To kai kai jahadin mana...., Tashi yayi yace "Kaga tafiya ta kai tunani irin wayan nan yaran sune kadangaran baƙin tulu...., Dariya yayi yace "In Allah ya nufa zan zama shugaban ƙasa wallahi bata isa ta hana ba kai ko wayan nan mutanan ƙarya suke wallahi..., Hakane amma kai fa tunani me kyau na barka lafiya Mai da hankalinsa yayi kan system ɗinsa ya ci gaba da aikin gabansa Bayan kwana goma Wannan program ɗin da jidda tayi shi ya daga martabar ta ko ina in kaje sai zancan saboda yar gwagwarmayar siyasa da aka samu ake musamman yan jam'iyyar NBB me alamar gona Kahu hamisu kuwa ya zuba mata ido haka mahaifinta saboda gwaggo har cewa tayi zata tsine musu hakan kuwa ba ƙaramin dadi yayi wa jidda ba ta ƙara miƙe ƙafa tana abin da taga dama Yau ita da gwamna za su fita campaign dan haka tun safe ta shirya cikin material baƙin da adon flower ha sosai yayi mata kyau dauko mayafi tayi ja tasa ta rataya jakar'ta tace "gwaggo ni na tafi sai magariba zan dawo.., To yar albarka Allah ya temaka ya bada sa'a Murmushin jindadi tayi tace "Amin gwaggo ta..., Tasa ƙafa ta fita a tsakar gida ta tarar da hansai da lubabatu sai lantana suna gyaran zoɓo duk sunyi bututu ɗan ya tsuna fuska tayi ta dauke kanta sarai sun ganta amma ba wanda ya kula ta dan yanzu jidda ta ƙara koyo rashin mutunci yan zunan zata ɓadawa idon'ta toka ta ci uban mutum ba me magana Saboda yanzu da yan daba take yawa har taje kofar soro ta tsaya tace "Baba lubabatu malam yana ciki..., Wacce aka kira da baba lubabatu tace "Yana kasuwa yau kinsan kasuwar garin nan ke ci.., dafe kanta tayi tace "I for get ta saka kai ta fita ɗan isiya yana ganin'ta ya burga mashinɗin'sa yace "Tun dazu nake kijaranki...amma kin tsaya kina taku daddai..., Ƙara Sosa tayi tace "Wallahi bansan kana jirana ba ina baraka take...?, Cije baƙi yayi irin na yan daban nan yace "Owo mata ai gab nake da inci kut..., Ai kafin ya ƙarasa ta ɗaga mai hannu tace "Haba dan isiya wannan fa kawata ce kuma aminiyata duk abin da muka zama ita ce sanadi kawai yanxu na lura so take tayi baya baya dani...., Wata mahaukaciyar dariya ya sheƙe da ita yace "Ba dole ba baki san iliya ya kai kuɗin ta ba...., Ƙasa hawa mashinɗin tayi tace "Wanne iliyan....?, Wanda kika sani Ji tayi duniyar na juya mata ta dafe kanta daman shiyasa jiya taji su hansai suna magana ƙasa ƙasa har suna dariya lallai BARAKA ta cuce ta tace "Ɗan isiya yanzu kasan me...., Nida ba akuya ba ya za'ai in san mee.. cije lips ɗin'ta tayi tace "Please yanzu ba lokacin wannan maganar bane kai ni gidan su BARAKA dole in tauna tsakuwa dan aya taji tsoro.., A'a ba haka za'ai ba yanzu dai kinsan gwamna bazai tsaya jiranki ba akwai wayan da suke neman damar ki basu samu ba dan haka sai mun dawo ko karfe tara ne sai muje gidan su zan sa yarana su shirya mana makamai shegiya kinsan fa yanzu ta dena harkar siyasar nan ita zatayi aure maza sun gama kwakule'ta..., Kai ta jinjina tace "Haka ne kuma hawa tayi tace Muje tafiya sukai ba wanda ya ƙara cewa qala yayi da zuciyar jidda take cin kushe bata taɓa zaton ILIYA zai ci amanar ta ba haka BARAKA to wai ma ya akai ILIYA ya yarda da BARAKA bata san zancan zuci ya fito fili ba sai ji tayi dan isiya yace "Wai an ce ita da zulai kanwar'sa suka haɗa abun iyayen'sa suka ce bazai aure marajin magana ba...., Kwafa tayi tace "Aikuwa za suga rashin jin magan ganin idonsu..., Dariya yayi yace "Yauwa tawan...., Cikin ikon Allah suka isa gidan gwamnati har na fara taron shiga tayi ya tsaya agun ya jagaliya samin guri tayi ta zauna kiran sunan ta akai da sauri tashi ta isa gana table ta amshi speaker tace "Jama'ar gurin nan barka da warhaka da fatan kowa yana lafiya a gurguje duba da yanayi na lokaci zamu fara abin da ya kawo mu GEZA SAi.....? Tuni mutanan gurin suka ce sai SA'EED MAI GORO Gyara mayafin ta tayi da ya zafe tace ƊURMA sai....?, Haɗa mutanan gun sukai suka ce sai YUSUF JIRGA..... 🔊 To kununa mana soyayya ta haryar zaɓar mu a 2025 nan da sati biyu kenan mu kuma mu baku tallafi kala kala zamu inganta hanyar tsaron ƙasar nan tare da huta sai ruwa da tallafin lafiya inhar kuka zaɓe mu kowa zai makaranta kyauta Zaku yarda ku zaɓe gurgur mage....? Haɗa baki sukai suka ce "A'a...., Yauwa ai daman ku masu tunani ne sannan zamu raba muku dubu biyu kyauta RANAR ASABAR sha biyu ga watan Oktoba 2025 ku fito tsakin ku da kwarkwatar ku ku zaɓe jam'iyar NBB me alamar gona... Ran gwamna ne yayi fari tas da jawabin jidda komawa tayi ta zauna Wani ne ya ƙara fitowa yayi magana da ga shi aka rufe taro sallama me tsoka gwamna yayi mata daga nan ta tafi gidan Radio GEZA akwai program ɗin da zata yi ******** Shigowa tayi riƙe da kofi a hannunta miƙa mai tayi amsawa yayi a hankali yace "Thank.., Kai ta ɗaga mai ta koma ta zauna a kafaɗar'sa ta kwantar da kanta gyara mata kwance yayi ta hanyar kwantar da kanta a cinyar sa sosai yanayin na yau yayi mai dadi kasancewar ba wata sa'insa da ta haɗa shi da nadeeya kafa kofin yayi abakin'sa da sauri ya zare ya dube ta yace "Sweetheart wannan me kika kawo min....?, tashi tayi ta ɗan haɗe rai tace "Abin da kasa nayi maka yayi dad'i ko fiye da wanda kake order ko..?, Ajiyar zuciya ya saki baya so ya sace Mata gwuiwa amma wannan abin da tayi be yi kama da coconut juice ba yace "Yayi...., murmushi ta saki ta rungume shi tace "My man ina mutukar son Ka Allah ya barmu tare har abada...., Ajiye kofin yayi ya rungume'ta yace "Amin my dear...., wallahi my man duk macan da tayi gagganci kula ka Allah ranar lahira zata yi baƙuwa....., Zare ta yayi a jikin sa ya zuba mata lumshashshun idanuwan'sa yace "Me isa kishin ki yayi yawa in Allah ya ƙaddara cewa a rayuwa zanyi mata biyu ba yadda zanyi dole inyi saboda yana ɗaya ga cikin ƙaddara'ta...., Wasu hawaye ne suka kwaranyo mata tace "Wallahi ranar zan kashe ka in kashe ta in kashe kai na kowa ya rasa..., Sakar kafaɗar ta yayi ya jingina akan luxury sofa yace "Me isa kullum tunanin ki bashi da kyau kina tunanin Ubangiji zai barki kinsan hakkin rai kuwa.....? Wannan wanne irin kishine....? Shin baki karanta labarin littafin ( KIN CU CE NI ) ya fateesat tayi duk kishinta da Allah ya nufa Aryan sai yayi aure sai da ya auri ilham yarinyar da takewa kallon yar aiki...yar tallah.., My fan's kar ki sake a barki abaya in baki karanta littafin KIN CUCE NI BA ki gaggawar nemansa ta wannan hanyar 09061890481 yasha banban da labarin da na saba kawo muku kafa ɗaya kan ɗaya ta ɗora tana girgiza wa tace "Amma ai halina da na Fateesat daban..., Daga mata hannu yayi yace "Duk da haka shin kinsab mene dalilin da marubuta suke rubutu....?, a'a Kamamo hannun'ta yayi yana ɗan messaging ɗinsa yace "Saboda su faɗakar da al'umma ta hanyar nishaɗi cikin sauki su isar da saƙon su bawai suna rubutu ne kara zube baba a'a sai sunyi dogon na zari me ya faru a DESTINY LOVE baki dauki izinar da NUCY ta dauka ba duk kuɗin ki ko duk ta ƙamar ki Ubangiji yanayiwa mutum talala ne in ya tashi kama shi yayi mai kamun kukun kaza..., zare hannun'ta tayi domin har ta fara jin ƙasala tace "Sweetheart.......taja ƙarshan sunan..., Gira ya ɗaga mata yace "Na'am honey me ya faru...., Noƙe kai tayi tace "Bakai bane..., Kama kunnansa yayi yace "Na tuba me ya faru..., tashi tayi ta juya bayan'ta tace "Kai nake so....., Dariya ya saki ya tashi ya kama ƙugun'ta yace "Kin sameni....., Juyowa tayi ta sheƙe da dariya kama gemun'sa tayi ta na wasa tace "My man duk randa ka gujeni wallahi mutuwa zanyi bazan iya zama a doran duniyar nan niƙadai ba..., Kura mata ido yayi yace "insha'Allah bazan guje ki ba .....amma NADEEYA ki daina shan kwayoyin da kike sha zafa su iya a effecting ɗin ki ...., ɗan ya mutsa fuska tayi ta buɗe baki zata yi magana ya haɗe bakin su wani irin nishi ta saki sakamakon hannun'sa da ya zura a rigar'ta yana wana shafa breast ɗin ta zare bakin'sa yayi ya maida kan kirjin'ta mur kicewa tayi Ansh yasan lagwan mace nan danan zai hautsina miki lissafi bare da sanin ki ba shiyasa a koda yaushe take cewa tafi kowa sa'ar miji *NI KUWA NACE KO WACCE MACE JI TAKE MIJIN'TA YAFI KO WANNE MIJI A DUNIYA KO MY FAVOURITE SPECIAL HUSBAND MY LOVE YOU ARE THE BEST.......🗣️🗣 happy birthday to you my lovely ️* Ganin abin ya fi karfin floor ya dauke ta suka shiga bedroom sai da abu yayi nisa taga baza ta iya ba ta saki kuka dakyar ya sarara mata Komawa gefe tayi tana sakin kukan tabbas ta gurzu lallashinta ya shiga yi narke mai tayi tare sukai wanka suna dawo floor wayar sace tayi ƙara alamar shigowar messages ta gefen ido Nadeeya ta kalle'sa ganin bai da niyar dauka tace "Dear kamar wayar ka message ya shigo...., ɗago kansa yayi ya cire medical glasses ɗinsa saukar da laptop ɗin'sa akan Centre table yace "Najii....., Kauda kan'ta tayi ta taɓe baki halin mijinata sai addu'a miskiline na bugawa a jarida daukan remote tayi ta canza tasha cikin sa'a kowa ana haska program ɗin jidda da sauri ya ɗago Duk wannan dambarwar da ake be taɓa ganin jidda ba mai da hankali yayi sosai gurin hirar tata inda take tallata ɗan takarar shugaban kasa SA'EED MAI GORO da matemaƙin sa Joseph aken wale tsaki nadeeya ta saki tace "Wallahi sweetheart na tsani yarinyar nan a haife ka haife ta kalli wai kai ne gurgun mage ga wannan cin mutunci...?, ɗan murmushi yayi yace "Nadeeya ke aka ce wa gurgun mage...da har zakiji zafi....?, Amma dai daga mata hannu yayi yace "Sau dadama Nadeeya ina koya miki wani darasi da kika kasa dauka ita siyasa dole kasamu maƙiyi da masoyi dan haka ba abin da muwa bene dan kaji ana kushe zaɓin ka ba..., Kai ta juyar tace "Kai jama'a jibe ta Dan Allah wallahi sweetheart woman leader nan yan iskane karuwai..., Ki neda aibata ta baki san gaibuba kar Ubangiji ya tsaidake ranar tashin alƙiyama nadeeya kiyi shaida Daukan remote tayi ta canza tasha dauka yayi ya mai da ita Cikin fada tace "Wai kai wanne irin mutum ne....? Kamar bakai ake zagi ba na lurama kamar jindaɗin kallon wannan karuwar kake....., banza yayi mata fuuu ta bar flooe bedroom ɗinta ta nufa daukan wayar ta tayi da take kan dressing mirror cikin contact ɗin ta ta shiga ta kira wata number bugu daya aka dauka cikin hanzari tace "Hello tani kisa yarin ki suje gidan su waccan yar iskar su yi mata kaca kaca wallahi na gaji da abin da takewa mijina..., Dariya ta saka tace "Uwar ɗakina an gama yanzu zansa su jagwal su ya mutsa mata hazo..., Okay turomin da account number ɗinki Godiya tayi mata ta kashe wayar Komawa tayi ta zauna ta shiga charting da kawayan'ta ..........✍️ *Oum Yasmeen* *HAUWA KULI WOMEN LEADER* *oum Yasmeen* Sauran page two in gama book one Book 2 paid book 500 duk meso zai iya biya ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Yan niger zaku iya turo da katin Airtel na 300fcfa Ku dauke shiku turu min Ta wannan number 09061890481 *Kun zan zarta payment domin shiga group da huri* *Book two 🔞* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k ******* Karfe 7:30 garine yayi shiru abin ka da sanyi ba masu zaman majalisa kai tsaye yan daban nan gidan su jidda suka shiga hukakensu suka shiga kartawa a ƙasa suna bada wani sauti ran gwaggo ne ya ɓaci cikin faɗa tace "Wannan wanne irin ɗiban albarka ne badamar abar mutum ya ji kunne sai an ƙara shigo da wanni ibilisancin wallahi na fito nan na lahira sai yafi mutum jin dad...., Ai bata ƙarasa ba aka dalla reta da futula wani uban ashar ta lallayo zatayi sai ta tsaya mata a maƙogaro sakamakon qallin huka da ta gani yana yawa a fuskar ta zaro ido tayi tace "Na shiga uku....., Ina woman leader..., Cikin rikicewa tace "Mene man leda....?, Ɗaya daga cikin sune ya cije baki yace "Ke tsohowa Bama son rainin hankali ina take ko yanzu inyi gun duwa gun duwa dake....., Jikin gwaggo ne ya shiga rawa ita ba kifi ba ko nama ya za'ai ayi gunduwa da ita tace "Kuyi min rai wallahi ban san me kuke faɗe ba....., Ke tsohuwa bara muyi miki gwari gwari inna waccar yar akuyar yar ki take....?, Cikin tashin hankali tace "Kululu..., Ɗayan ne ya zaro wata siririyar huƙa yace "Au tambaya ma kike Bara in naɗo hanjin ki sai ki mana bayani...., Kuka gwaggo tasa tace "Yara bansan inda take ba wallahi ni kakar ta ce in cewa kukai in bar gidan nan wallahi a yau sai in barshi..... wannan tashin hankali dame yayi kama sai ta fyece majina..., Ganin abin da ta faɗa gaskiya ne babban su yace ."wallahi taci sa'a da sai mun mata walmu ƙali fatu.....amma zamu ƙara zuwa ku zo mu tafi Kai baba haka zamu tafi bare da mun reɗi naman fuskar'ta ba Ƙara sautin kukan'ta tayi tace "Haba yaron nan kuyi hakuri in wacce kuke nema tazo ai sai ku reɗi nata ko...amma ni na tsohuwa ba abin da zaku samu...sai fata.., Tafiya sukai bare da sun kulata ba Gyara fuskarta tayi ta fito tace "Kuna ina mutanan banza.....ai gashi nan na nuna musu jiya ba yau bace har ni yan daba za su zo guna..., Fitowa sukai lantana tace "Haba gwaggo kamar fa har kukanki naji..., Aa na uwarki kikaji haka ta ƙare musu tanadi tas ba wanda yace ƙala sai da tagaji dan kanta ta koma daƙin'ta ************ Wannan littafin ne kuɗine domin karanta book 2 ki gaggawar payment ₦500 Wanda bazai iya jira ba book 2 ₦700 ne complete na gama shi Sai bayan magariba dan isiya yazo dan haka ba ɓata lokaci ta hau a hanyar gangare suka haɗo da yaransa sai gidan su BARAKA a kofar gida suka tarar da mahaifin'ta jidda saukowa tayi tace "Baba ina annamimiyar yarka take...., daga tawa yayi da alwalal da yake ya dago yace "Jidda wace kuma annamimiya..., ɗan ya mutsa fuska tayi tace "Baba ba dogon jawabi ne ya kawo Ni gun Ka ba kalli da mutanan da nake tare da su...., kallon su ya shiga yi yana jinjina kai yace "Eh na gani me ya faru....., Naxo ne ka jawa yarka kunne ba ita bani dan wallahi ta sake ta ƙara shiga harka'ta sai na sa anyi filla filla da ita har Ni za ta ciwa amanag ta auri ILIYA kai ya jinjina yace "To zata ji...., ɗur kusawa dan isiya yayi ya kai huƙarsa kusa da kunnan mahaifin baraka yace "Kaji abin da oga tace ko sai na bar maka shedar da za a gani asan kunnan kashe ne da ku....., Bakinsa na rawa yace aa basai ka bari ba Tafiya sukai suka barshi da sakakken baki Sai tara da rabi ta shiga gida Sallama tayi da sauri gwaggo ta fito tace "Kululu yau ni yan daba suka rutsa ai kuwa yan bantan uba har karyawa ɗta hannu nayi haka suka fita suna kuka wai inja kunna ki...., Turus tayi tofa wannan shi ake kira da game over tayi anyi mata tace "Dan Allah gwggo...., Goro ta ɓantara tace "Zancan kike so...., Ƙarasowa tayi ta shiga ɗaki Washegari da sassafe jidda tasa aka tara mara mutane tana siyan kuri'unsu ran kahu hamisu in yayi dubu ya ɓaci lamarin na jidda yawa wacce ake mata baki daga wancan sai wannan da ta addabi al'ummar gari yan zu kuma ga abin da take girgiza kai yayi ya huce sai kuma ya dawo yace "Jama'a ina jan hankalin ku kar ku siyar da yan cin ku domin ita wannan kuri'a yan cin mutunce da shi za kuyi zaɓe ku zaɓo adalin shugaba wanda zai ji tausayin ku...., Taunar cingum take aikuwa ba shiri ta tofar ta kunce damarar da tayi a kugu tace "Kahu me zan gani ba gwaggo tayi min iyaka da akai ba...?, Jidda wallahi ki guji randa duniya zata koya miki darasi Turo dauri gaba tayi ta ci gaba da abin da take shiga cikin gida yayi ya barta To a kwana a tashi ba huya gurin Ubangiji yau ta kama asabar yau za ayi zaɓen GWAMNA dana yan majalisu wani satin ayi na shugaban ƙasa Al'ummar garine sukai turuwar ƙadawa sagir fegi kuri'a dan takarar jam'iyyar haske party jam'iyyar su ANSH tuni hankalin su me goro ya tashi duk yan daban da suka ajiye hukumar yan sanda ta nannaɗe su Ga uban tsari da suka fito da shi amma ji kake shiru ranar jidda huni tayi tana yawa a maza ɓa daban daban Har dare yayi dole ta koma gida sai jiran sakamakon shugaban jam'iyyar haske party ya tsaya tsayin daka ganin ba ai maguɗi ba inda baturan zaɓe ya sanar SAGIR FEGI yaci zaɓe gurin roɗewa yayi aka fara faɗa da kone basa yi hankalin SA'EED MAI GORO ne ya tashi ya din ga zirga-zirga dole a zaɓen gaba suyi shi ne musamman bazai laminci faɗowa ba shi kuwa dan takarar gwamna waɗowa yayi sai gadon asibiti aka kai shi Sosai suke tashin hankali sai da aka sa kafiyu Gidan ANSH kuwa sosai ya shiga murna ganin sun yi nasara zasu kawo karshen zalincin me goro Rana bata ƙaraya sai dai uwar ɗiya taji Kunya yau ta akama da ai zaɓen shugaban ƙasa Tun safe Ansh me ɗakin sa Hajiya nadeeya da tawagar sa suka isa mazaɓar sa ya ƙadawa ƙasan kuri a dagowa yayi inda kowa ya gani tuni yan jarida suka shiga dauka ake haskawa kai tsaye a gidajen rediyo da talabijin Wato (live) jidda ce ta iso ita da tawagar'ta ayayin da ANSH yake kokarin fita sai yau tayi gaba da gaba da wanda take zagi a gidajen rediyo da talabijin kallon kallo akai tsakanin ita da shi yayi da yan jaridu suka saita Camera ɗin su dan jin me zai faru wani irin kwarjininsa ne ya cika ta daman wai haka yake tsakanin su da tazara amma sai taga ta koma wata tsakuwa akan'sa gaban tane ya waɗi kamar ta taɓa ganin photo sa a gun inna ta gabas kardai ace shine wanda innar take bata labari wani ɗan jarida ne ya matso yace "Jidda woman leader me akice game da wannan zaɓen shin kina ganin zakuyi nasara.....?, Da sauri ta dawo daga dogon tunanin da ta shiga lokacin har an buɗe mai mota buɗa bakin'ta tayi da ya bushe yahun bakin ta yayi wani irin kauri tace.......✍️ Yanzu ainihin wasan zai fara Insha Allah mune da nasara tana faɗar haka tayi gaba ƙara binta yayi yace "Kamar kim karaya ba wani abu da zaki ƙara cewa...?, banza tayi mai in ban da ikon Allah da tuni kowa ya fahimci hankalin da take cikin tun ganin farko da tayi wa ANSH hankalin ta ya tashi bata da wata kwanciyar hankali saboda kallon da ya jefe ta dashi kamar fa .......kallo ne me cike da alamomi kala kala Kan Ansh dan jaridan ya koma lokacin har ya shiga mota yace "Me zaka iya cewa game da zaɓen nan da ake yi shin kana ganin nasara...duk da ga al'umma sai kada kuri'u suke..., Tsayawa yayi yace "Nasara tana gurin Ubangiji Allah ya zaɓawa al'ummar kasar GEZA adalin shugaba na gari.......wanda zai iya sauke nauyin da ya daukowa kansa ba wanda zai baba kere da duniyar al'umma..., kamar wannan maganar da kake gogar zana ce Dan murmushi yayi yace "Dan jarida wannan ai gaskiya ce ko ban faɗa al'umma da yawa sun san haka samu da rashi duk yana gurin Ubangiji....., To ranka ya dade shin gwamnatin ka me ta tanadar wa mata...?, daidai karasowar jidda dan murmushi yayi yace "Su mata abin a killace a gida ne macan kware bata fita yawo dan haka zamu basu jari su zauna a gida su yi sana'a.... duk macan da take da daraja bata fita yawo mace fa kamar kwatankwacin buredi ce da wanda ake siyarwa a bakery da wanda yake siyar da shi a kan taburin shayi ai kaga ba darajar su ɗaya ba .......kina mace be kamata ki shiga harkar siyasa ba da namiji ya dace....dan haka zamu tallafa musu su tafi gida su zauna... sannan duk wanda muka kama da siyan kuri'a sai mun kama shi shekara biyu a gidan yarin na zaɓin tara... sannan zan gyarawa kowa zama.., da sauri jidda ta shiga mota ran'ta inyayi duba ya ɓaci bata ankara ba taji hawaye na suntiri a kumatun ta driver motar ne ya ya zaro tissue ya bata amsa tayi tace "Nagode...., Kai ya jinjina yace "Ki hakuri mutumin nan magana ya faɗa miki a fakaice....amma ai matar sa ma'aikaciya ce kin ga kenan ita ma ta shiga sahun marasa daraja...., Hakane kai ni gidan inna ta gabas kar ka kaini gidan To yace da yake ya taɓa kai'ta tafiya sukai me nisa tukunna suka isa unguwar Tanko fitowa tayi ta rufe kofar tace "Nagode isuhu daga nan zaka gidan gwamnati ne..., Tab wanne gidan gwamnati su kansu takan su suke kina ji dazu fa your excellency sai da ya waɗi Saboda yaji kuri'un da waccan gurgur yake samu shifa na uku yake zowa na gari uku kacal aka faɗi yana da kuri'a miliyan daya da dubu dari bafa a zo nan ba ai ba wanda zai saurareka in kaje ke dai Allah ya fitar da muke.... Ajiyar zuciya ta sauke zuciyar'ta sai lugudan tara tara take gaban ta waɗowa take in ta tuno kallon da yayi mata tace "Amin dai in muka waɗi wallahi mun shiga uku yawo a gari sai ya gagare mu wallahi...., hakane sai dai kawai Allah ya fidda mu Amin ya Allah ta juya ta fara tafiya wani kawatatcan gida ya shiga iya kyau da tsarowa ya tsaru daidai zaman mace ɗaya sallama tayi cikin fara'a tsohuwar ta fito fara tas da ita tace "Jikalle yau ni kika tuna....?, murmushi ta saki tace "Inna kullum kina raina...., ja'ira kamar gaske shigo Shiga tayi kallon mamaki takewa dakin inna ta zauna a wasu hadaddun kujeru tace "Inna sake kayan daki kikai..., kitchen inna ta shiga ta tace "Dan albarka ne ya canza min..., Kai jidda ta jin jina tace "Masha Allah sunyi kyau....cak ta tsaya sakamakon arba da katon photon ANSH da tayi tare da inna da sauri ta tashi ta mustsika idonta tabbas zahiri photon sane a gidan innar'ta Inna CE ta fito hannun'ta rike da plate cike da fruit da kuma jug a hannun ta a Centre table ta ajiye tace "Jidda zo ki rabu da wannan photon in kika kwantar da hankalin ki zaku zauna ke da shi zama na har a badah..., da sauri ta juyi tace "Inna da wa .....zan zauna?, zama inna tayi tace "Zo ki ci wannan sai in miki bayani jiya ma naje gurin gwaggo da mahaifinki domin cika alkawarin da muka daukarwa marigayyah...., Kamar wacce kwai ya fashewa a ciki haka ta tako ta zo zama tayi tace "Gwggo wane shi a gun ki....?, tsohuwar me ran karfe kallo ɗaya zakai mata kasan hutu da jindadi ya zauna mata tace "Jika nane dan gidan Khadijah ne ya'ta da nake fada miki wacce ta mutu ita da mijinta...., Zaman dirshan jidda tayi tace "Uhmm.....ta tsakuri kankana tasa abakin'ta duk zakin ta dacin ta take ji ta rasa meke mata dad'i yau inna tace "Jidda...., .dago manyan idanuwan'ta tayi tace "Na'am inna..., .amma dai kwana zaki ko girgiza kai tayi tace "A'a inna ina da abin da zanyi kinga muta nan tsaka mai huyar dole gobe ko yau da safe a faɗi zaɓe in mu muka ci to komai dare zan tafi gidan Gwamnati...., cikin mamaki inna tace "Jidda ashe daman abin da ake faɗa gaskiya ne....kin shiga siyasa to wallahi ba inda zaki koma da raina haka daman kika koma jidda gaskiya ban yiwa karima adalci ba da na barki a hannun gwaggo duk da nasan halin'ta ba saiti ne da ita ba...dan uwanki shi kike cin zarafi abin da yayi shi......shi yayi ki.., ran jidda ne ya ɓaci domin ita kaf duniya bata da sama da gwaggo tayi mata komai matar da ko zata huni bata ci ba ita zata bata taci zare hannunta tayi daga cikin kankanar da take ciya ta tashi gyara mayafin'ta tayi tace "Inna ni Zan huce daman ziyara na kawo miki...naga kina wasu zance ban gane kansu ba ni zanyi gaba saduwar alkairi..., Ba inda zaki da sauri ta juya jin wanda yake magana kahu isa cikin mamaki ta buɗa baki maganar ce ta kakare mata ta kasa wannan abin bakinci da yawa yake da basu san cinta ba balle shanta ba sai yanzu sai nema su gwada fin karfi a kanta Shigowa ya karasa yi yace "Daman ko baki zo ba Ni ina da niyar inje in dauko Ni......wai ashe ko makaranta yanzu bakya zuwa jidda me kike so ki zama....so kike al'ummar gari su zage alhalin muna da karfin da za kiyi daga primary har izuwa University kin biyewa yan siyasa..., Juya idonta tayi suka kalli sama ta zube a ƙasa da sauri suka yo kanta cikin wata iriyar murya tace "Karka taɓata wallahi kana karasowa sai mun shanye maka allon ka faɗa....., Cikin sauri inna da kahu isa suka kalli juna kahu isa yace "Inna daman tana da aljanu....?, gumi ta share tace "Isa ina zan sani...., Kallo ya bita da shi yace "Inna kawai mu barta ta tafi kina da ji abin da suke cewa...., zuciyar jidda fari kalla tayi dan haka ta ƙara dagewa tace "Zaku barni na tafi ko sai na shanye wa wannan tsohuwar rabin ƙwaƙwalwa ......, a'a tashi Allah ya tsare hanya abin bekai haka ba... tashi tayi ta dinga jera ati shawa sai kuma ta dawo daidai tace "Kahu isa ina huni...., Kallon mamaki yake mata yace "Lafiya ya mutan gidan naku..., Tashi tayi tace "Suna lafiya inna kahu sai nadawo...., Allah ya dawo dake lafiya Futa tayi kofar gida ta dinga sheka dariya tayi maganin su Cikin gida kuwa inna zama tayi ta zuba ta gumi tace "Isa zauna..., Zama yayi tace "Isah bansan ya zanyi da alƙawarin marigayya ba ina son in cika shi kai ne wanda zaka temaka min gurin cika shi....komai ya dagule min kana ganin zai yarda da auran jidda mun Gama magana da mahaifinta yace Allah yasan ya alkairi daman ko ban zo da wannan magana ba aurar da ita zaiyi ya huta kar ta dauko mai abin kunya naso ace tafi haka girma amma Allah be nufa ba duk ɗan da fara fitina kawar da shi..... shi ne masalaha...., *HAUWA KULU WOMEN LEADER* daga alkalamin *oum yasmeen* Book 1 Domin malakar book 2 500 zaku iya biya ta wannan hanyar 8141785374 Amina alhasan Muhammad opay Yan niger zaku iya turo da katin Airtel na 300 fcfa Ku toro shaida ta wannan number 09061890481 Wasan yazu ya fara kar ki bari ayi bake *Yan amanar DESTINY LOVE sauran one page fa* 🔞 A jiyar zuciya ya sauke yace "Hakane bara komai ya daidai ta sai muyi mai magana tun da yanzu hankalin sa ba akwance yake ba..., To Allah ya kawo mana mafita amma jidda sai addu'a wallahi Amin yace ***** Bayan ta gama kwasar dariyar'ta ta fara tafiya ba kowa titi ma haka da kafa ta ƙarasa gida saboda ba motar hawa a kofar gida ta ci karo da malamin su na islamiyya ɗauke fuska tayi..... Tayi kamar bata gansa ba zata huce yace "Hauwa bukar Rabi'u.....huce ni zaki ba ko gaisuwa...?, juyowa tayi ta ɗan zamo da glasses ɗin'ta tace "Au sannun ka...saidai ban sheda ka ba..., Sakar baki yayi yana kallon'ta Bawan Allah nayi gaba tun da baka da abin cewa ka tsaya kana kallona Gauron numfashi ya saki yace "ba shakka hauwa'u ashe abin da ake faɗi gaskiya ne....nine yanzu baki gane ba malamin Kur'ani ....., Wani kallo tayi mai na up and down tace "Malam nifa dogun zance ne bana so me ya kawo ka kofar gidan mu kar dai muna....ko tsaka uwar munafukan duniya ce ta faɗa maka wani abu...., gyara tsayuwa yayi yace "Me ya haɗaki da Baraka....har kika ɗebo yan iska suka ra zana baba..., Mayafin'ta ta ciro taci ɗamara dashi ta ware idonta tar tace "Isuhu..., Hangame baki yayi yace "Isuhu gatsal ba malam....., Au karya nayi ba sunan ka haka ba ina cewa har mutane aka tara aka raɗa maka suna ISUHU ka fita a idona kana da sauran mutunci a dona in kuma kaki wallahi zan saka rigar rashin arziki in ci baka mutunci in banda iskanci har ni zaka zo kana tambaya Me ya faru lallai mutun garin nan sun manta wacce jidda...kai kasan wallahi inda dane da tuni wani zancan ake bawan ba sa'ar ku ɗaya yanzu bata ku nake ba siyasa ta ɗauke min hankali wane a garin nan besan ILIYA saurayina bane amma haka kuka rufe idonku ku dangantakar dake tsakanina da baraka baku duba kuka amshi kuɗinsa insha Allahu sai Allah ya bani wanda ya fishi...shima ILIYAN jira nake mu gama wannan dambarwar zaɓen wallahi ya shiga uku a garin nan Kee kina haka wazai aure ki yar iska irin ki wacce ta raba mutuncin ta ga mazan waje.... ba abin da jidda ta tsana sama da zina dan haka be ƙarasa ba ta zari katakon da aka jingine kofar gidan su ta loda mai a ka wani uban ihu ya saki kama kugu tayi tace "Wallahi kaɗan ka gani baka ga komai ka ka ƙara shiga sabgata wallahi sana sauke maka gana most go ɗin rashin mutunci har Ni zaka kira karuwa kaje gida ka binciki wace kanwarka....., Daga hannu yayi zai zabga mata mari karab aka riƙe hannu cikin jindadi tace "Ya mage barshi ka barshi Wallahi ya sake ya taɓa wannan kyakkyawar fuskar sai na datsai hannunsa.., Cika shi yayi yace "Kanwata mu shiga wannan ba asan yinki bane....., gyaɗa kai tayi ta shiga ciki ya bita Wani kululun baƙin ciki ne ya tukare huyan isuhu ba yarda ya iya haka ya tafi ******** Babban floor ne an kawata shi da kayan more rayuwa komai na floor up white ne da c green ga wasu hadaddun luxury sofa kallo ɗaya zakai mai kasan ya ɗan afa ya kara haske sumar da ta fito a fuskar ta kara bayyana ramarsa ka cewar bata sami kulawa ba kamar yarda take samu gefen sa jafar ne ɗaya kujerar Shuram ne zaune da biro da takarda suna ta aikin kirge Knocking kofar akai be ɗago ba nuna wa yayi kamar besan a nayi ba shuram ne ya ajiye biro ɗin hannunsa yace "Ansh ana fa knocking.....ina ga madam ce..., tashi yayi ba tare da tace komai ba ya buɗe kofar kamar yadda ya zata haka ne ya faru yar aikin su ce cikin sauri ta zube a ƙasa tace "Barka da wannan lokaci...., Cije lips ɗinsa na kasa yayi wai yaushe nadeeya zatayi hankali yafa da mata ba sau daya ba sau biyu ba baya son Yan aiki suna shigowa part ɗinsa aikin da ya kamata ace ita zata yi sai ta turo yar aiki baya son hulakanta Dan Adam dan haka ya amsa mata ciki ciki hajiya ce ta ce inzo in tambaye ku me zan dafa muku.... Ya Allah kalmar da ya faɗi kenan da kyar ya iya cewa "Bakomai...., Tashi tayi ta bar gun cikin sauri....sai da ya tabbatar tayi nisa tukun ya nufi part ɗin nadeeya kamar yarda yayi zato haka ce ta faru zaune take riga daban zani daban tana ta charting sai kawayenta suna ganinsa suka kowa ya saita kansa gaishe dashi sukai be amsa ba suka far gun ajiye wayar tayi tace "Haba honey ka saki ranka mana....wayan nan kawayena ne amma baka kaunata dashi why honey ha yarda suka gaishe ka ka share su....da baka yi wallahi yau cewa zanyi saboda wannan halin da muke ciki ne amma sabon kane gaskiya bazan dauki kana ci wa kawayena mutunci ba....nida nake fatan in muka sami gwamnati duk commissioner zan musu...., be ce mata komai ba ya juya zai koma da sauri ta rungume shi ta baya cikin deep voice ɗinsa yace "nadeeya sake ni kinsan yau ba mu kadai bane..ko, Lumshe idanuwan'ta tayi Allah ya ɗora mata jarabar son mijinta kan mararsa takai hannun'ta tace "Dear yau kuma nadeeya fushi kake dani ko....., Cije lips ɗin'sa yayi a birkice ya juyota sakamakon matsamai jijiyarsa da tayi zuba mata shashyayyun idanuwansa yayi masu kama da mejin bacci yace "Kar ki taso da abin da baza ki iya ba yana kai wa nan ya juya ya barta baki buɗe a yan kwanakin nan ta rasa gano kan mijinta tasan halinsa sarai ba wannan siyasar bace ta mai da shi haka akwai wani abu juyawa tayi ta shiga bedroom ɗinta nan su tani suka shiga tana shiga ta ja dogon tsaki ta zauna tace "Wai daman har yanzu kuna nan da wannan mugun halin naku.....ina cewa tun a boarding kuka dena....., tashi zeenatu tayi ta zauna tace "Me za'a fasa mutuwa ko hisabi.....?, kau da kai nadeeya tayi tace "To wallahi ba'a gidana ba haka kurum ku jamin wani tashin hankali.. Wallahi dear in ya gani kashi na ya bushe....., dariya suka sheƙe dashi TANI tace "Zeenatu bata son kan network ɗin da muke hawa bane... shi yasa kike faɗar haka..., Cikin kunfar baki tace "Wallahi bana fata na sani...., Matsowa kusa da ita Tani zeenatu tayi tace "Wallahi baza ki hana mu jin dadi ba....., blanket ɗin da Tani ta rufe jikin'ta zeenatu ta yaye tace "Haka kurum yau kana nawa muna yi miki alkunya kin ajiye mu sai bamu abinci kike..., Zigidir take haihuwar mahaifiyarta dan cabkar breast ɗinta zeenatu tayi tana ja inda ita tana matsa mata ɗayan wani irin numfashi suke fitarwa me kurnani Tashi nadeeya tayi da sauri Hadiza ta tashi tace bara mu basu guri tun da abin nasu ya zarce hankali magani ne ya waɗo a jikin hadiza lokacin da ta tashi durkuwa sa nadeeya tayi ta ɗauka tace "Wannan maganin mene...., planing zaro ido nadeeya tayi tace "Hadiza kema bin maz...kike!, me yafi raina auran in kayi in bakai dace ba hawala mutum yake sha wannan hanyar tafi kawo min kuɗi ke nifa bafa da kananan mutane nake ba kinsan dai me goro tsohun governor garin nan ni yarinyar sace Zaro ido tayi tace "Ke dan Allah shugaba da wannan harkar...., Tab kaɗan kenan Dan Allah yanayi.... Wani murmushi tayi wanda Allah ne kaɗai yasan manufarsa tace "In kika sha guda biyar zaki shekara goma ba haihuwa maganin yana da karfi sosai...., Da sauri tace "Bara insha kuwa..., buɗe baki TANI za tayi karab zeenatu ta haɗe bakin su kokarin tureta take kar tasha amma ina har ta ɓaro ta afa a bakinta ganin aikin gama ya riga ya gama zeenatu ta saki baƙin tani ta komar da kanta ƙasan ta Bayan ta gama sha ta fita itama hadiza fita tayi Karfe 2:49 na dare Shugaban jam'iyyar su anshe salim sani tsakuwa shi ne yaje ofishin hukumar zabe sosai gurin ya cika manyan ƙasar ne a guri duk wanda ka gani wane da wane ne yan kuci ku bamu suna waje ana jiran sakamakon zabe gumi ne ya zubowa baturan zaɓe sakamakon maganar da wani ya zo ya raɗa mai kawo mai wani sakamako akai inda ya ɗaga shi yace "Sakamakon yegzen ya ɓata...., wani irin ihu suka sa na ashe na waje sun ji fetur wani fusatatcan matashi ya siyo ya ɗaga murya yace "Wallahi karya ne ba mu yarda ba akwai mutanan da suka dauki sakamakon a takarda lokacin da ana kirga kuri'a wallahi kana baɗa mana ba dai-dai ba sai na kuna ka....., ganin rashin gaskiyar da yake so yayi bazai yuhuba in yace zai yi zai yine a ransa yace "Bisa duk sakamaƙon da muka fitar da irin kuri'un da ko wanne ɗan takara yaci halastatcan ɗan jam'iyyar haske party wato ASHARAF IMAM GEZA ya sami damar lashe zaben shugaban Kasar GEZA da halattacciyar kuri'a biliyan goma da dari biyar inda abokin karawar sa ya me girma governor jahar nan sa'eed mai goro ya sami miliyan goma sha biyu duk wanda yake ganin ba aimai a dalci ba kofa a buɗe take yakai kara gaba nan da kwana goma kafin rantsar wa amma mutukar yayi wa dan takara taya murna ba batun kai kara Yana faɗi sojoji suka rufe shi suka shigar da shi mota domin raka shi airport fitowar jidda kenan daga bayi yau shigarta bayi yafi sau goma tun dawowar'ta domin ba ƙaramin alkawari gwamna yayi mata ba hansai ce ta wara radio daidai gurin da aka faɗa ansh shi ya lashe zaɓe bata san lokacin da tayi ball da Radio ba Hansai tashi tayi tana hura hanci jidda kowa jinta ne ya dauke na wasu dakika sai maganar cin zaɓen ansh ce ke yawao a kunnanta da sauri baba lantana ta fito ta saki buɗe tace "Yau Allah ya bamu adalin shugaba wanda yasan kishin mu...., Malam kuwa daman baya su mai goro cikin farin ciki ya fito yace Hamisu...gaka zaɓin da Ubangiji yayi mana wannan mutumin ya dade yana kasa mana aya a hannu Allah mun gode maka ..., Hayaniyar mutane suka ji dan haka suka tsaya da hirar da suke Allah ya kawo karshan su jidda woman leader matasa ne suna buga ganga har wasu suna kokarin hawowa gidan ta bayan katangar gidan su tabi ta fita balla kofar sukai suka shigo da sharɓata sharɓatan huka kuka gwaggo ta rushe da shi ganin ana neman hallaka mata jika......✍️ *Me kuke jira ku harzar ta payment ɗin ko domin shiga group labari fa ya dau zafi wai kuwa Mai GORO zai hakura ne mu haɗo a littafi na biyu* *HAUWA KULU WOMEN LEADER* *OUM YASMEEN* End of book 1 *Zuwa dare zan buɗe paid group kame bukata yayi min magana domin fara posting da shi* Za ku iya biya ta wannan hanyar 8141785374 Opay Amina alhasan Muhammad 500 Yan nijar zaku iya turo da katin Airtel na300 fcfa Ku dauke shi ku toro ta wannan number 09061890481 "Yi mana shuro ko inyi sala sala da naman ki....., Editing shaf shaf Tsit gwaggo tayi ta koma bayan kahu musa ta ɓoya Kahu hamisu ne yace "Dan Allah ku hakuri kamata yayi yarda muka sami wannan nasarar murna za mu yi fa finaba...., Jikinsu ne yayi sanyi ɗayan yace "Mun tafi amma kuja mata kunne ba ita ba zagin kowa dan wallahi taci sa'ar ka da sai mun farke mata ciki...., Suna fadar haka suka juya suka fita Fitowa gwaggo tayi tace "Yau nake ganin wata masifa.., Gwaggo abin da tun huri kuka kasa fahimta kike ganin ke da ita Shiru gwaggo tayi domin yau ta gaskata komawa daki tayi Malam yace "Ai wallahi zan kira inna ayi abin da za ayi tun kafin ta dauko mana abin da yafi karfin mu dazu limamin masallacin gabas ya kawo min kararta sun ci mai mutunci ita da rabebe...har fasa mai kai sukai...., Dariya kahu musa yasa yace "Jidda baya ko rabebe shima wayasa shi shiga sabgar su ashe shi yasa ya kawo rawani har baki kai jidda shegiyar kaya ce ta iya bakin aiki ni da ta cinye mun uwar garke na ....., kahu hamisu yace "Allah ya shiryata ai ranar juma'a za a daura auran...., Tattaunawa sukai yarda abin zai kasance ***** Bayan saukar jidda daga kan ka tanga gudu tasa tafiya take har ta iso gidan inna taci sa'a kuwa kofa a buɗe take shiga tayi dai-dai fitowar aunty bilki daga toilet cikin mamaki tace "Jidda lafiya...., hannunta ta miƙo mata kamata tayi suka shiga daki da sauri inna ta tashi daga zaman da tayi tace "Me ya faru ko murnar ce tasa kika kasa hakuri kika tawo...?, Cikin tashin hankali tace "Inna inda bane suka zo har gida nemana...nan ta kwashe komai ta faɗa musu salati inna ta saki tace "Allah ya rufa asiri zaki bar musu garin...., Da yake jidda ba a hankalita take ba ba ta fahimce me take nufi ba Bayan ta huta ta yi wanka ta kwanta ****** Ansh yana jin shi yaci yayi sujjada ya godewa Allah yana dagowa abba ya kirashi bayan sun gaisa yayi mai maganar auransa ba yarda ya iya haka ya amince amma wallahi Allah ne kaɗai yasan tsanar da yayi mata Bayan ya kasai wayar shuram yace "Abokina kaga yarda kakoma wani abun abba ya fada maka...., "Kanwar mahaifiya ce ta bar wasiya lokacin da zata mutu in Allah ya raya abin da ta haifa a haɗa Ni aure da ita..., Wace yarinyar ya sunan ta "Wallahi na tsane ta ashe ma jinana ce amma bakomai na sami damar gasa mata aya a hannu.., Haba ANSH tun da muke dakai ban taɓa jin kace ka tsani wani ba me tayi maka da har ka tsane ta Jidda wacce take ci mutuncin a gidajen rediyo da talabijin wacce take min kazafi kala kala Cikin mamaki shuram yace "Lallai kuwa ka sami damar worata amma ya zakai da nadeeya in ta dani....., Ajiyar zuciya ya sauke yace "Nima abin da nake tunani..., Allah ya kawo maka mafita Amin Cikin gidan nadeeya kuwa Iya murna tayi yau yan makarantar su sai bugomata waya ake da abokanan arziki Alkawari kuwa sai yiwa mutane take ba adadi 🤔 🤔 Muje zuwa ****** Wallahi Allah bazan yarda ba ni za a ciwa mutunci dole in daukaka kara wallahi Mustapha Umar jiran lokaci yace "Ai his excellency kwantar da hankalin ka za mu tafi kotu dole muyi murda murda ka haye kujerar shugaban kasa..., Yusuf jirga yace "Ai wannan a zaune take muke da nasara...., ******** Bayan kwana shidda Rana bata karya ayau juma'a. Aka rantsar da ASHARAF IMAM GEZA bayan an gama ramtsuwar ne yan rakiya suka raka shi fadar shugaban kasa nadeeya ji take ba ya ita sai zagaye ko ina shashin da aka bata take yau ita ce *FIRST LADY* Mahaifiyar ta ummi sai daɗa hure mata kunne take tare da zugata ***** Bayan an sakko da ga masallaci aka daura auran*HAUWA'U BUKAR RABI'U DA MUHAMMAD MUHAMMAD GEZA* akan sadaki dubu dari da sittin abba ne ya bayar ko wanne a cikin su cikin farin ciki suke sun cikawa Amina burinta Kowa komawa gida yayi inda a daran yau a kai amarya gidan ta ****** Auty bilkisu ina wannan limon yake Miko mata shi tayi ai kuwa zama tayi ta fara sha tace "Allah aunty ina kaunar wannan limon kankanar da kike min yana da dad'i..., dariya aunty tayi yaro yaro in banda a haka ko a jikin ta ai taji canji gama sha tayi tace "Auty yau zan koma gida satina ɗaya fa a gidan nan....., A'a ki bari zuwa dare zan raka ki nima ina so mu gaisa da gwaggo To wallahi aunty saboda ke na yarda amma yau so nake in je gurin iliya in ci mai mutunci wai aunty ni iliya zai yaudara Duk irin son da yake faɗa mini na karya ne zama auty ta gyara tace "Allah zai baki wanda ya fi shi bana son kara jin wata magana akan'sa..., To aunty kahu isane ya shigo yace "Jidda ba mu guri za muyi magana..., Tashi tayi bata kawo komai a ranta ba ta shiga bedroom inna ce ta foto ƙasa ƙasa tace "Kunsan Allah sai dai a shakawa jidda powder amma yarinyar nan taji wata magana akwai tashin hankali gwara in taje can ya fada mata komai ba gurin gudu....., Hakane ai gata nan ma na samo karba aunty bilkisu tayi ta shiga bedroom din jidda har tayi bacci shaka mata hudar tayi da sauri ta buɗe idonta sai kuma ta rufe Daman ta gama shirinta karfe shidda mota ta zo daukan ta akai aka sa a cikin motar sai airport cikin sirri akai komai har zuwa birnin GEZA Suna sauka mota tazo ta dauke su sosai auty ta ware ido tana kallon ko ina gine ginan birnin geza ma daban yake kasan cewa ka zo unguwar kososhin gwamnatina ta kofar sirri aka shigar da su ainihin gidan shugaban kasar a geza zone 1 Waya tayi mai ga sunan fitowa yayi sanye da p-cap da farar t-shirt da jeans baki da baƙin glass daukanta yayi ya kai wani daki ya rufe....... Dawowa yayi umarni ya bawa driver da ya kawo aunty da ya akaita ma sauki inda shi kuma ya koma ciki....., Alhamdllh a yau na kawo karshen book 1 Mu haɗu a book 2 *Inda ainihin wasan zai fara* *🔞 Kar ku bari a baku labari* *JIKAR MAMMAN* Oum yasmeen Episode 2 *`🔞free book`* The writer of *Binta yar jagaliya paid book 300* *Mu zuba mu gani paid book 200* *Destiny love paid book400* *Kin cuce ni paid book 400* *Hauwa kulu women leader 500* *AFIF free book* *YAƊIN MAGE free book* *RASHIN SANI free book* https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k Ƙasa magana yayi haɗe baƙinsa yayi yahun baƙin yayi wani irin kauri wannan shi ake kira da baƙon yanayi tan ƙaɗa'ta yayi dafa bango tayi Allah ya temaka ta dafa bango cikin baƙin ciki tace "Allah ya isa dan iska....., haushin kansa ne ya kama shi be zai yi da wannan yarinyar yar kauye ƙazama tafin hannunsu ya duba yawa me shirin gano cutar da ya shafa ganin be biyo ta ba ta rage gudun da take ƙara ta ɗauka tana wasa da shi tun daga nesa ta hango an fara tsaron yan makaranta har an rufe gate ma kama kugu tayi ta kare musu kallo sannan ta ƙarasawa tayi jijjiga gate ɗin ta fara da sauri idi me gadi ya taso yace "To uwar yan makara ki koma gida shedimasta (headmaster) yace kar wanda aka bari ya shigo tun da kinga wa'yan can ma an raba musu aiki yanzu goma saura....., kallo ta ƙare mai sai da ya gama zancan sa tas ba ta tanka ba fakar idonsa tayi ta fito da wajin da ta ajiye domin cin taso tsai ta busa mai Allah ya rufa mai a siri be shiga idon sa ba sai hancinsa da ya shiga. kama hancin sa yayi ya zabga uwar a tishawa da ihu yasa yana cewa shikkenan hancina ya cire da sauri su malam Umaru suka yokan sa DIJE kowa tuni ta samu ta shiga cikin makaranta ganin hankalin kowa ya koma kan idi me gadi Saboda ba'a san me ya faru da shiba wa yanda aka tsare ma sukai nasu gu headmaster ne ya fito da rigarsa ta zarce ga ƙaton ciki yawa me ciki ɗan wata tara da wata zabgegiyar bulala yana tafiya tana jan ƙasa cikin mamaki yace "Malam umar me ya faru....., Cikin jimami malam Umaru yace "Wallahi ihunsa kaɗai mu kaji ba musan me ke faruwa ba...., Malam musa ne ya karo gun cikin tausayawa yace "Idi sannu.....ka waɗa komar jikar mamman..., Cikin rashin fahimta headmaster yace "Jikar Mamman kuma wace haka....?, ɓare gyaɗar sa yayi ya watsa a baki ya tauna yace "Khadijah sule Mamman....Dije yasin ita ce ɗan yanzu nan naga ta huce a guje...., Da sauri idi yace "Wallahi ita ce...., Headmaster yace "Wallahi kuwa yau zata ci ubanta sai an mata ruwan zafi a jikin'ta......kai idi yi hakuri daga yau bazata ƙara wannan sheganta kar ba ku biyo ni bin bayansa sukai kowa aji aji suka ɗin shiga saboda anje ajin su ba a ganta ba malam musa yace "Muje primary four akwai kawarta rabi shehu duk inda taje ma zata fito mana da ita...., Na'am sukai da shawarar sa suka shiga cikin ajin kowa shiry yayi ganin shugaban makaranta rabi shehu tana rubutu malam musa yace "Ke rabi faɗa mana gaskiya ina DIJE take...., ɗa sauri ta ɗago tace "Wallahi Allah yau ba mu haɗuba ɗan Allah shatu DIJE ta shigo ajin nan....?, Fiƙi fiƙi da ido shatu tayi domin Allah yayi mata tsoron duka cikin inda inda shatu tace "Wallahi bata shigo ba ..., haɗa rai malam musa yayi yace "Ku fito naga alamar baku da gaskiya....., Jikin su na rawa suka fito headmaster yace "Malam Musa Ni zan koma office har tafiyar nan dana yi har na gaji in Ka ganta ka faɗa min zata taci ubanta ne wallahi malam Umaru ka koma kan duty...., To suka ce mai zaga makarantar suka yi a tsakiyar wata bishiya suka tsaya malam musa yace "Wallahi duk wacce bata faɗa inda DIJE take ba na sami labarin kun san inda ta ɓoya sai naci kwal.....uban ku...., zarzare ido suka shiga yi kamar nace shatu ɗago sukai ido huɗu da DIJE tana shan mangwaro tayi dai-dai a bishiya taci ɗamara da hijabin'ta suna haɗa ido da shatu ta gallamata harara da sauri tayi ƙasa da kanta ta sani sarai in dai ta faɗa ta ga DIJE kashin'ta ya bushe alkur'an na lahira sai ya fita jin dadi tsawa malam Musa ya ɗaka musu yace "Ku shige mu tafi....., binsa sukai har office ɗin su guri ya basu suka zauna yasa su ɗaga hannu suka rufe idanunsu ci gaba yayi da yin marking Malam ɗan ladi ne ya shigo kallonsa yayi yace "har yanzu basu faɗi inda ta ɓoya ba....?, ɗagowa yayi yace "Eh wallahi ba su faɗi ba..., Ƙwafa malam ɗan ladi yayi yace "Ai kuwa yau in aka tashi su za su gyara makarantar nan...sai nayi muku gwala gwala gwala a makarantar nan...., hawaye ne ya zobo daga idon shatu domin ita tafi rabi tsoro ƙarfe ɗaya da rabi aka tashi kowa tanan DIJE tayi amfani ta shiga cikin ɗalibai ta gudu ba wanda ya ganta Cikin Makaranta kuwa ba kowa sai idi me gadi sai malam musa malam ɗan ladi sai su shatu malam musa yace "har yanzu kunyi shiru baku faɗa min inda DIJE take ba dan kunfi kowa sanin inda take...., Kuka Shatu tasa tace "Wallahi Allah ban sani ba ni yau ban ga DIJE ba...., Malam Ɗan kadi yace "Ke shatu zo....., tashi tayi duk gaɓoɓin'ta sai ciwo suke mata ɗurkusawa tayi kusa da shi ta zauna cikin tsawa yace "ɗaga hannunki sama ki rufe idonki cewa nayi ki zauna...., Cikin sauri ta ɗaga hannunta ta rufe idon'ta cikin tsawa ya dubi rabi yace "Ba zaki rufe idon ki ba......, rufe idonta tayi hijabin shatu malam ɗan ladi ya ɗaga da sauri ta buɗe idonta tsawa ya kara ɗaka mata a firgice ta mai da idon'ta ta rufe yace "Wallahi kuka sake kuka buɗe idon ku sai na kwaye muku fatar jikin ku da bulala...runtsai idanuwansu sukai ɗaga hijabin shatu yayi ya ɗaga rigar'ta sama tuni kirgaɗan gin da tafara suka bayyana lashe baƙin'sa yayi yawa wani maye hannu yasa yana shafawa zafine ya ziyarci shatu amma ba damar magana haka ma rabi gwara ita tafi ma shatu kuka shatu tasa Lokacin da ya fara yi mata wata irin tsotsa kai kace yaron goyene ****** Uwani kinga yarinyar nan har yanzu bata dawo ba cikin halin ko in kula uwani tace "Duk lokacin da ta ga dama ta dawo..., cikin takaici amarya tace "haba uwa kamata yayi ki tura sammani ya gano me ake a makarantar har yanzu bata dawo ba sufa ya'ya kiwo Allah ya bamu kuma zai tambaye mu wanne kiwo mukai musu be ƙamata ki ɗinga watsai da tarbiyar SHATU ba saboda ita mace ce ......, buɗa a ta saki tace "Allahu akubar wa'azin nan be shiga ba jiki masallaci saboda gidan malam habu ba wajan wa'azi bane...., fitowa yayi daga ɗaki daga shi sai wandon shadda duk ya koɗe cikin takaici yace "To kaji nazo ina hutawa ba baku kyale ni ba....., Uwani tace "Malam ba dole kaji murya'ta ba wannan gidan Malaman nan ce take min wa'azi wai in bincika shatu lafiya bata dawo ba ai duk inda shatu taje zata dawo ni babban takaicina yau nasan DAMA ke da ciniki shinkafa da wake na za suyi kwantai...., a fusace ya dubi amarya yace "Eh lallai kuwa aji muryar ki uwani anya amarya kikana so kiga annabi ina ruwanki da shiga sabgar da ba'a sakoni ba...., rai uwani ne yayi fari tace "Faɗa mata dai malam...., juyawa amarya tayi ta shiga ɗaki washe baki yayi yace "Uwani nace ba kin gama shinkafa da waken ki zuba min bashi in na fita na samo zan baki....., zani ta gyara ta soke shi tace "Gaskiya malam na gaji dubu biyu fa nake bin ka...., haba matar so in Allah yawar ware min zan baki bani fari tayi da idon'ta tace "to mijin uwani....., Allah ya barni da ke uwani'ni tawa...., Amin malam *********Gidan Mamman* ganin ba sarki sai Allah ya shiga cikin gidan baƙinsa dauke da sallama da sauri IYA ta fito tace "Muryar wa nake ji kamar imurana...., haɗa rai Imran yayi yace "tsohuwa kina fa batan suna...., ungo tayi mai da ƙuwa tace "Tun kafin a haife kana nasan wannan sunan ni ban iya ƙaƙale ba da uwar ka inyamura ta sa maka...., sumar kansa ya shafa fari ne tas irin farin ibo me haɗe da yellow ga idanuwansa dara dara haka sumar kansa kwance lublub ga sajansa ya sha gyara kallo ɗaya za kai mai kasan hutu da jin dadi sun zauna mai babban malami a *University of Illinoi of Medicine Osteopathic Medicine* nutsuwar da tarin shekaru sukai mahaifar mai ita wanda a shekarun baya da na yanzu ya sami ci gaba duk wanda yayi mai sanin baya bazai gane shi ba a yanzu har ta ast ɗinsa ya koma na american ast zama da turawa ya sa ya riƙede ya koma ba'amurƙe amma hakan be taɓa addinin sa ba sai ma abin da yayi gaba har haɗa hausarsa yayi wacce ya ɗaɗe be magana da ita ba dan ko mamy in ta kira shi da ibo suke magana yace..........✍️ *Na kusan dena posting a kowanne group sai channel ɗina kuyi following ɗin channel ɗina ɗan samin ci gaban wannan littafi*